Showing 15001 words to 18000 words out of 133269 words
Chapter 6 - Dan Makaho Complete Document by Biebee Isa--.txt
Ina guje maka dana sani Alhaji, Wallahi AbdulFatah ya nuna ya na sonta, gwara ka mata aure".
Labiba tace "Allah ya sauwak'e in auri mai shan taba, ki aura mishi Samira" Mami ta wurgeta da harara, Samira tace "Kinga Labiba Mama na ba tsaranki bane, wallahi ki daina maida mata magana in tayi" Alhaji Dakata yace "to nidai na amince Muhammad ka tafi da Labiba, amma idan Labiba ta kwaso abun kunya, ko tayi wani abun da zai kunyatani a idanun jama'a, to ba ruwana da kai da ita da Mahaifiyarku" Mami ta kalleshi cikin tashin hankali, Labiba kuwa ko a jikinta dom ta san ba zata taba basu kunya ba, dadi ya rufeta tace "Niko wallahi sai na baka Mamaki Abbah, zan zama abun alfaharinku, da Allah, ba zakayi dana sani ba, Mami karki damu, wallahi karatu kawai zani Katsina, sai na kula muku da jikokinku" wasu sukayi dariya wasu ko sukayi fuska.
Hakan kuwa akayi, Muhammad ya koma Katsina ya mata Appying HUK poly, don bin sharrudan uban, tunda Diploma Shekara 2ce, kuma akwai sharadin in ta samu Miji za tayi aure. Labiba na daga cikin wanda aka dauka da farko, saboda ko Jamb dinta Mark din yan jami'ah ne, ya gama mata preparation nan da wata biyu zata zo katsina fara lectures.
Abbansu ya kirata daki, ya mata nasiha sosai, ya bata kudi Naira dubu ashirin yace kuma InshaAllahu zai dinga turo mata ko da dubu uku ne duk wata, godia tayi sosai, ta rungume Abbanta.
Maminta ta ki rata daki tace "Na zauna a Katsina shekaru da yawa, na san yanda suke, yanda suke ma'amala da mutane ya sha bamban da yanda mukeyi a nan, baki taba barin Edo ba, Arewa zaki Labiba, dole ki koma halaiyar 'yan Arewa, kije kasuwa ki dinko atamfa da ankara, ki dinga shigan Hausawan usul, ba zasu miki uzurin ba a chan kika taso ba, zasu miki fassara in kikayi wani dabi'ar da ba tasu ba, ke ke son Karatu, dole ki zama irinsu ba zan so ki fito da wani penti duk kankantashi ba, kingane? Labiba ta gyada kai, Mahaifiyarta ta dade ta na mata nasiha kan kare Mutuncinta.
Tana son karatu, tana son fidda mahaifiyarta kunya, zatayi komai don ganin ta cimma burinta, ta shiga kasuwa ta siyo manyan gyaluluwa da atamfofi, ta dinka su. Lokacin zuwa Katsina Yaya Muhammad ya zo da kanshi don tafiya da ita, kowa na alhinin tafiyar Labiba, don tana da shiga rai, harta Samira da ba sa shiri tayi kukan rabuwa da ita, haka suka ma Edo Sallam suka taho Katsina ta dikko dakin Kara.
Gidan Yaya Muhammad dakuna biyu ne sai Parlo, da kitchen da toilet a waje, k'aramin Gida ne, Dakinta Aunty Asiya ta bar mata da Amira babban diyan Yaya Muhammad, ita kuma Aunty Asiya da Sabit suka koma dakin Yaya Muhammad.
Yaya Muhammad ya raka Labiba Registeration ba wai don ya san yanda ake ba, Sati guda ya kashe yana kaita Makaranta, ta hanyar bin School Bus, ya kuma koma ya daukota, ce mishi tayi ya bari hakan nan, ta gane hanya, zata iya zuwa ta dawo da kanta, a sati na biyu ne ta fara zuwa da kanta a lokacin har tayi k'awa Aisha Usman.
Wannan kenan.
Zaid ya gama jinta lokacin da ta gama bashi tak'aiceccen labarinta da murmushi dauke a fuskanta, kallon da yake binta da shi ne ya sa tace "ya akayi ne?" mur Zaid ya sha "are you stupid?" kallon mamaki ta mai tace "me ya faru?".
Hannu ya sa ya murza idonshi "wai ke lafiyar ki lau? Alk'awarin da kika daukar ma Maminki kenan? Don me zaki shigo dakina? Kare mutuncin kenan? Kinsanni ne? Yanzu in na danne ki, na miki abunda ba kya zato, me zakice mata? Kin san me kikayi risking? Farincikin ki, na Yayanki, na Mahaifiyarki wanda barazana ne ga aurenta, to kinyi risking kin shigo dakina, for what? Is it worth it?".
Labiba tayi shiru "nasan ban yi daidai ba, but kamar yanda nace ma, wallahi kamar ana controlling dina, bansan meyasa when it comes to you, nake yin abubuwa da yawa, i am just curious, Ya Rabb, amma kasan me? Wallahi banyi dana sanin shigowa dakinka ba, bansanka ba, bansan what you are capable of ba, amma na san ka san abunda kayi, shi za'ayi ma, na san kana da k'anwa Sadiya, na san in ka shiga gonan da ba taka ba, itama zaa shiga tata, nasan ba zaka min abunda ka san ba zaka ji dadi ba in an mata ba, na san fandarewarka a busa ma ciki hayak'i ne, kuma ina da tabbacin kai ba mazinaci bane".
Idon ya sake murzawa ya kwantar da murya, kamar zaiyi kuka, damuwa taji a muryarshi yace"Labibaah, you cant be so sure, ba a gane daniska a fuska, baki san abun da wani zai miki ba, ba kowa ke da irin zuciyar da kike tunani ba, wasu suna da abun ban mamaki, baki gane bak'in halinsu, nidai please kar ki kara shiga dakin kowanne namiji, ina tsoron abunda wani zai miki".
Ido ta lumshe ta bude ta sakar mai murmushi, tana me jin dadin muryar nan, tace "ka damu dani?" hannu ya sa a cikin gashi kafin ya daure yace "ke dallah, tashi ki tafi School" raurau tayi kamar me shirin kuka, nifa ba inda zani, already an fito 1st lecture, kawai na baka labarina sai kuma kace zaka koreni, ai ba haka mukayi ba?".
Tsaye yayi yana kallonta, itama kallonshi takeyi, sun dau mintuna fiye da uku suna kallon kallo, ko wannensu fa da abinda yake sak'awa, Wayarta ne ya katse su.
Aisha ce, dauka tayi "Hello Aisha? Ya kike, eh wallahi Ruwan Jiya ya mana gyara. Bangon Gidanmu ya fadi, shiyasa banzo ba, Ayyah Allah sarki, ya lectures? Ok to".
Ashe Aisha na tare da Abu Sadeeq, bashi wayar Aisha yayi suka gaisa ya mata jaje, ya shaida maya da yana missing Dimta, murmushi ta mishi kawai ta kashe wayar.
Har yanzu be fasa kallonta ba, wani kiran ya sake shigowa, kallon screen din wayar tayi taga Jay mamaki ta ba kanta da ta kasa daga wayar har wayar ta tsinke, don me zata k'i daukar wayar? ta tambayi kanta, kafin ta ba kanta amsa wayar ya sake ringing, sai ta daga ido a hankali ta kalli DanMakaho da sauri ta ajiye idonta k'asa tana wasa da hanayenta, wayar na kan Katifa tana ruri.
Wayar ta katse ta sake ruri, DanMakaho ya cire idonshi daga kanta, ya ga Jay a screen din, da kyar yace "Saurayinki na kira".
Da sauri ta daga kai ta kalleshi da kuma sauri ta sauke kanta kasa ta kawar da kai gefe, "Oh baki iya dauka a gabana?bari na fita" ta san in ya fita nan zai barta, ganinshi aiki ne tayi saurin cewa "aa, donAllah ka tsaya zan iya dauka".
Da sauri ta dauka "Hello Jay, zan kiraka, ina lectures ne" tayi saurin katse kiran, DanMakaho ya kalleta da mamaki.
Da murmushin mugunta yace "Lectures? Seriously? Wow, ashe kin iya k'arya" itama tayi mamakin k'aryan da ta sharara amma sai ta dake ta daure fuska tace "Ina Jinka, ka gaya min wanene kai?"
Wuri ya samu ya zauna daga gefe a sanyaye yace "Labarina bai da dadin ji" gyara zama tayi tace "zan iya saurarenka" yace "Labarina akwai tsawo" ta gyara zama tace "i have the whole day. (Ina da dukkan rana).
Murmushin takaici yayi
Yace "Sunana Zaid, Zaid Aliyu Zaki"
Da sauri tace "Meyasa ake ce maka DanMakaho? Meyasa ake kiranka da Mankas?"
A fusace yace "Zaki man shiru ko kuwa? in azarbabi zaki min tashi ki fita".
Hannu ta sa ta kama bakinta "Afuwan, nayi shiru".
A hankali ya soma Magana.
°°°°°°°
Wa zai iya mana hasashen Labarin Zaid?
Vote Vote Vote please.
#1love
#DM
#SonsoFWa
#anatare
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Bakwai (ASALIN SU)
Alhaji Aliyu Umar Zaki tsohon dan Siyasa ne da yayi tashe a Da.
Yana da Shekaru 28 ya auri Shafa'atu 'yar mutanen Jos. Ya hadu da Shafa'atu ne lokacin da yaje Gaisuwar Mamar wani Abokinshi.
A GURGUJE
A lokacin, Mamar Shafa'atu na da Gidan Abinci, kafin Ali yaje Gidan Rasuwan ya fara zuwa Shagonsu Shafa'atu dake bakin hanya don cin Abinci.
Shafa'atu ce ta zo ta same shi, a natse ta gaishe shi ta tambayeshi abunda za'a kawo mishi, kallonta yayi yace "ki kawo min Shinkafa da Miya da Wake, sai kan Kifi" Shafa'atu ta dago ta kalleshi da mamaki tace "babu kan Kifi, saidai gangar Jiki da Bindi".
Ya dan tuburne fuska yace "ni kuma Kan Kifin nakeso" ta dan sa yatsar ta a baki tana nazari, su ba sa ba Customers kan kifi, amma wannan ya buk'aci da a bashi, tace "ka dan bani mintuna na soya maka" murmushi yayi don sosai 'yar budurwar ta burgeshi.
Bayan wasu 'yan mintuna ta dawo da abunda ya buk'ata, sosai ya ci Abincin nan, don ya sha tafiya, rabonshi da abinci tun kafin ya baro Katsina, sai ruwan da ya sha a Tasha, tambayar kudin Abincin yayi, tace mishi "kudinka naira dari da hamsin ne" cirowa yayi ya bata.
Ali sai ya manta da abunda ya kawo shi garin Jos, ya ja Shafa'atu da fira, haka ta biye mishi, da yaga Maghrib na neman yi baije yayi abunda ya kawo shi ba, ya ciro takardan da aka rubuta Adireshin Gidan Rasuwan, ya gwada mata "ko kin san Anguwar nan?" tace "eh ba nisa" nan ta sake mai kwatance.
Sallama sukayi tare da shaida mata zai dawo Gobe, murmushi suka sakar ma junansu, Ali ya tafi kwatancen da ta mishi da taimakon wani mai a kori kura ya gane Gidan. Sosai Abokinshi yaji dadin ganinshi, ya mishi godia sosai.
Washegari Ali ya koma Shagon su Shafa'atu, tun wurin k'arfe 10 na safe, dama da tunaninshi Shafa'atu ta kwana, taji dadin ganinshi yau, nan suka zauna suna ta fira, ba abunda ke tadata sai in Customers sunzo da ta basu abincinsu take dawo gurin Ali, Mamarta bata damu ba in dai kudi na shigo musu bata da matsala.
Maimakon kwana 1 da Ali yayi niyyan yi, sai gashi har kwana Uku be koma Katsina ba, duk da yayi Sallama da Abokinshi.
A cikin 'yan kwanakin nan Shak'uwa mai k'arfi ya shiga tsakanin Ali da Shafa'atu don Soyayya har ta shiga tsakaninsu kamar Almara.
Ranar da yace zai koma kar hankalin 'yan Gida ya tashi, Shafa'atu ta sha kuka sosai, a cewarta in ya tafi ba zai dawo ba, shi kuwa ya mata Alkawarin dawowa nan bada jimawa ba don zuciyarshi na wajenta a k'arshe ma ya tabbatar mata da cewa da labarin Aure zai dawo Mata.
Da wannan batu suka rabu Ali ya dawo Gida Katsina.
Ali ne Babba a Gidansu, yana da k'anne Maza da Mata.
Yayi karatun Arabi da Boko a Kano, be da wani aiki takamaime, amma yana da shige-shige da kutse-kutse, in yaje wuri sai ya tabbatar da an san shi a wajen kafin ya bar gurin, shiyasa abokan shi ke mai Inkiya da Ali Zaki ko suce Zaki kawai.
Tunda ya dawo Katsina yake ta tunanin Shafa'atu, hankalinshi dungurugum na gurinta, zuciyarshi na gaya mai ya koma Jos, nan ya bi zuciyarshi, ya sanar da Mahaifiyarshi zai koma Jos don ya samu Mata a chan, Mamarshi tayi mamaki sosai, amma sai tace "yanzu Ali duk Matan da ke garin nan da k'auyen garin nan basuyi maka ba sai ka dangana da Jos? Da dai ka bar maganar ta Jos ka zo ka bincika cikin Dangi, kasan Babanku dai" nan ya hau mata Magiyan donAllah ta goya mishi baya, zai samu amincewar Baban in har ta goya mishi baya, bayan ya dan sha wahala ya ci nasarar convicing dinta daga k'arshe.
Bayan 'yan kwanaki ya Koma Jos da Babanshi da k'anenshi sukaje ma Maman Shafa'atu da maganar Aure. Ta amince da hannu bibbiyu, Baban Shafaatu be da ta cewa don sai abun da Mamar tace, abu dai kamar wasa aka daura Auren Shafa'atu da Aliyu Zaki.
Bisa Alada aka rakota nan Gidansu Ali da ke Katsina inda a ka kaita dakin Ali.
Sosai Ali ke Son Shafa'atu, itama haka take sonshi, tana kyautata ma Mahaifiyanshi da k'anenshi, zaman lafiya sukeyi sosai.
Ali na dan fita yayi 'yan buga buganshi ya samu na cefane, ya kawo Gida a dafa kowa ya ci, zama suke na tsakani da Allah.
Bayan wasu yan Shekaru
Har Shafa'atu tayi shekara 3 a gidan bata taba ko da bari ba, wannan ya ja hankalin Dangin Mijinta gareta, abun ya soma damunta. Alin ne ke kwantar mata da hankali yana sake tunatar da ita kan Haihuwa ta Allah ce, yana ba wanda ya so a duk lokacin da ya so.
A lokacin ne Ali ya fara Shiga Siyasa, da yake yana da baki, ya iya magana sai hakan ke jawo mai Alheri daga Manyan 'yan siyasa, nan ya siya fili dan madaidaici ya fara gini, don su koma tare Matarsa duk don ya kwantar mata da hankali don ya lura rashin haihuwar nan, na damunta sosai.
Har wasu Shekarun suka k'ara shudewa, Shafa'atu bata yi ko da batan wata ba, abubuwa da yawa sun faru, Baban Ali ya rasu, duk nauyin Gidansu ya dawo kan Ali.
A Lokacin Ali ya shiga Siyasa tsundum don a yanzu ya wuce dan kwarako, a nan ta buk'aci da ya kaita Jos don a ganinta bata da Lafiya, ya kan ce mata "ta bar irin maganganun nan, don Haihuwa ta Allah ce, k'ila lokacin Haihuwar beyi ba" bata saurarenshi sai tayi ta kuka don danginshi sun sanga mata udo, habaibaici sukeyi mata, don Matan k'anenshi daga mai yara daya sai biyu, ita dai ya taimaka ya kaita ta samu magani".
Ba don ya so ba, ya kaita Jos da Motarshi, ya barota chan, nan Mamarta ta shiga dirka mata magungunan samun ciki.
Watanta daya a Jos Ali ya dawo daukarta don yayi kewar Matarshi sosai.
K'ulle mata magungunan akayi, har da na hayak'i, a ka kuma hadota da k'aninta Hudu dan shekara 4, Ali bai damu ba, don zai iya yin komai don Matarsa..
Shiru-Shiru bayan Watanni babu wata alama, hankalinta yayi mugun tashi da taga ba sarki sai Allah, sai ta bar yin maganin ta zubawa sarautar Allah ido.
BAYAN WASU 'YAN WATANNI
Alhaji Ali yayi suna, ya lula cikin siyasa tsundum, a lokacin shine Dan Majalissar dake wakiltar Katsina a Birnin tarayyah Abuja. Tunda Allah ya buda mishi yake kai danginshi aikin Hajj.Ya hada da Mahaifan Shafa'atu.
Wata rana, Alhaji Ali na hanyar zuwa Katsina daga Abuja shi da Drivernshi, suka tsaya a Masallacin Matafiya da ke Zaria. a gidan mai Masallacin yake. Bayan sun idar da Sallah ya hadu da wani Abokinshi Alhaji Usman Shehu da suka yi Karatu a Kano tare.
Da Murna suka rungume juna, bayan sunyi gaisuwa, Alhaji Ali yace "Haba Abokina ka boye" Alhaji Usman yayi dariya yace "Ina talaka zai ganka kana dan majalissa, ai ka zarce ni" Dariya sosai Alh Ali yayi yace "kai har yau baka bar iskanci ba" sukayi dariya baki daya. "Daga ina zuwa ina?" Alh Usman yace "daga zariya zamu koma Kano , chan nake zaune da wallahi iyalaina" Alhaji Ali yace "yaranka nawa?" "su 3 ne muje ku gaisa na san sun idar da sallah suna Mota" Tare suka je inda yayi parking Motar shi, ya bude yace ma matarshi ta fito su gaisa da abokinshi, fitowa tayi daga mota yaran suka fito su ma suka gaisheshi, daya bayan daya ya daukesu yana tambayan sunayensu yana mai sha'awarsu, sosai yake son yara, barin ma na k'annenshi, so yake ya dauki wasu daga cikin yaran k'annen nashi, amma da yake suna da yawa be son daukan dan wani ya bar na wani, kar ace ya nuna bambanci ko fifiko ga wani da kuma be so Shafa'atu taji an mata ba daidai ba don ita bata haihu ba, shiyasa be taba bijirowa da son rike 'ya'yan kanenshi ba.
"Kaifa yaranka nawa?" dan murmushi yayi yace "tukunna dai Allah bai kawo ba" Alhaji Usman sai yayi nadamar tambayarshi don kar yaga kamar yana son ci mai fuska ne, Alhaji Ali ya lura da yanayin da abokinshi ya shiga yace "kai daniska, kar ka damu, haihuwa ai ta Allah ce, idan da rabona zan samu D'an cikina ko ba dade ko ba jima zan samu, kawai ka tayani da Addu'a" InshaAllah Abokina inji Alh Usman.
Alhaji Usman ya kalli matarshi yace "wai ina Maryama ne?" dan murmushi tayi tace "ta na cikin masallacin mata muka barota bata idar ba" da mamaki Alhaji Usman yace "k'assarun?" tayi dariya tace "shi fa, ka santa da dadewa gun sallah" yace "danAllah je kirata muna kan hanya kar muyi marece" kafin waninsu ya sake magana hankalin Alhaji ya kai bakin Masallaci da wata halitta fara ta fito daga ciki tana gyara zaninta wanda shine matsayin mayafi.
Yauwa gata nan ta fito cewar matar, bude baki yayi yace "sallatu yi sauri ko?" da murmushi ta k'araso, ta kalli Alh Usman da ya shagala wurin kallonta tace "ina wuni" kasa amsa mata yayi sai da abokinshi ya lura dashi ya sa hannu ya zunguro shi kafin ya amsa mata. Oya a shiga mota, ya umurce su.
Alhaji Ali yace "Abokina wacece wannan?" yace "Maryama ce kanwata ko" dan shiru yayi kafin yace "indai har baku yi mata miji ba ina so, zan aureta".
#############
Dariya Alhaji Usman yayi "kai wallahi Ali ba ka rabuwa da shiririta" tamk'e fuska Alhaji Ali yayi yace " kai ni wallahi dagaske nake, in dai wallahi ba kuyi mata Miji ba, ina so".
Kallonshi Alhaji Usman yayi sosai yaga iyakar gaskiarshi kenan, yace "in har dagaske kake, to wallahi ka samu Maryam, kai dai kawai ka