Showing 126001 words to 129000 words out of 133269 words
Chapter 43 - Dan Makaho Complete Document by Biebee Isa--.txt
ko a da na san cewa ba yin kanka bane, shiyasa ban taba rikeka a raina ba".
Dalo tace "Baba nagaya ma tun ranar, wallahi muna sonka fiye da duk wani Namiji a duniyar nan, kar ka roke mu komai, mu zamu rokeka yafiya in bamu kasance 'ya'ya nagari ba".
Baba yace "Haram wallahi, kune ko 'ya'ya nagari, ina sonku fiye da komai wallahi, ku yi hakuri na kawo wacce ta rusa mana farinciki, ba zan taba yafe ma Shafaatu ba, gashi tun a dunia ta fara ganin sakamakonta, ina da Labarin ta haukace an kamata an tafi da ita Asibitin Mahaukata.
Tabe baki sukayi irin ko a jikinsu.
Yace "donAllah ku rokar min Mamarku gafara, ta yafe min".
Dalo tace "Allah Baba bakomai, kowa fa ya san duk abunda kayi ba yin kanka bane".
Yace "nidai please ku ce ta yafe min".
Zaid yace "InshaAllah Baba".
Baba yace "Zaid ka tuna Aunty Mariya?"
Zaid yace "Eh Baba, Mijinta ma ya rasu".
Baba yace "ka sani ohh nine dai bansani ba".
Zaid yace "me ya sameta".
Baba yace "wai Goggo wai na aureta".
Daria suka sa gabaki daya Zaid yace "to Baba ayi mana, ai dama ba zai yiwu ka zauna haka ba ba mata".
Baba yace "kun Amince?".
Sukace "dari bisa dari".
Yace "Allah ya muku Albarka ya sa ku gama da dunia Lafia".
Suka amsa da Amin.
Baba yace "Zaid Credentials dinka na nan, Alhamdulilah ban salwantar da su ba, Masters dinka kana da shaawar komawa London kayi ta?".
Zaid yace "Aa baba, barni in huta for now".
Baba yace "to shikenan, da degree dinka ai zan samo maka aiki mai".
Zaid ya yi alwashin tashi ya tsaya da k'afarshi yace "Baba, zan gabatar maka da abunda nike so nan ba da dadewa ba".
Ya kalli Dalo yace "ke kuma fa? Karatu ko Aure".
Dalo tace "Lahh Baba aure fa kace? Chab nawa nike ni? Ni gaskia Baba ka bari".
Baba yace "amma na fa ce ko karatu, bance aure zan miki ba, why are you focused on the last option?".
Zaid yace "because its what she wants, Aure take so Baba".
Baba yace "Exactly".
Dalo ta turbune fuska wai zatayi kuka.
Baba yace "wallahi Zaid ba zan kyaleka ba ka sa min yarinya kuka".
Sukayi daria, tare suka kasance aranar gabaki daya kafin suka koma gida Gab da Maghrib.
A na Gobe 'yan Edo da 'yan Abuja zasu koma garinsu suka hadu a wakeken Parlorn Alhaji Abu Shamsu dake nan garin Katsina.
Alhaji Abu Shamsu ya bude taro da addua.
Yace "To abubuwa da yawa sun faru, wanda duk abunda ya faru yana daga cikin pegin layin k'addararmu, dubararmu ba zata iya hanata faruwa ba.
"Alhamdulilah Allah mungode maka, Allah ka sa duk mu ci wannan jarabawar, Allah kanyafe mana duk mu yafi Juna, kuma wannan zumuncin Allah ya riga ya hada babu mai rabawa".
Alhaji Ahmad Dakata "ya dora nashi jawabin yana kuma mai bada hakuri, tare da cewa Jawad yayi hakuri da Labiba, don kamar ya kwareshi ne in ya bashi Labiba, Labiba zata cigaba da Makaranta har Allah ya kawo mata wani Mijin".
Alhaji Abu yace "wani Miji? Ai Allah ya kawo mata tuni da dadewa".
Sun san inda ya dosa Alhaji dakata yace "anya amma Jawad Adalci in aka ba Zaid Labiba?".
Alhaji Abu yace "yo saboda me? Da Zaid da Jawad duk 'ya'yana ne, ko ni ba zan aura ma Labiba kowa ba sai Zaid, Sadakinta na hannunka ka manta wanchan mancewa nayi da naje Edo, so nayi nace nazo neman auren ma Zaid Aure na ce Jawad subutan baki ne".
Alhaji Ali Zaki yace "wai ya ake ta min passing passing da diya ne? In ba ku so ku bar min ita, na kaita madina tayi karatu ta kawo min balarabe, ha'an".
Sukayi daria Alhaji Abu yace "Allah baka hakuri su masu diya".
Alhaji Dakata yace "ni dai koms meye sai naji daga bakin Jawad, in har be amince ba, wallahi sai dai ciwon so ya kashe Labee, sai dai ta auri wani ba Zaid ba".
Jawad yace "Abba wallahi bakomai, na bar mishi ita, na yarda, Zaid ai danUwana ne, Allah ya kara musu Son So"..
Alhaji Abu yace "Fak'at, Hajiyoyi me zaku ce?".
Mancy tace "ai kun dai gama Magana, in aka raba Zaid da Labiba ai Nigeria ta mana kadan, don wallahi guduwa zasuyi".
Mami tace "in dai ba so kuke kunmata wani auren ba, Zaid ya zo yana bukatan dashin Zuciya Labee ta kaso aurenta ta je ta bashi ba to wallahi tun wuri ku aura mata shi, tunda dai ta ji tagani 'yar kutsun uwa.
A kayi daria yace "Na bawa Zaid Labiba".
Alhaji Abu yayi daria yace "na amsarwa Zaid Labiba".
Duk sukayi Hamdala.
Zaid ya saukar da kanshi yana ma Labiba Signal tare da kashe mata kannenen idonshi, ita ko bata ma kalleshi ba balle ta tankashi.
%%%
Da Yamma Aisha tazo wurinta ranta bace tace "wai ke yanzu Besty shikenan ba zaki auri danuwana ba?"
Labiba tace "danuwanki fa yace baya sona, ba zaiyi ba wai".
Harararta tayi tace "kafin yace baya so ai ke kikace ba kya so".
Labiba tayi murmushi tace "Allah zai ma Jawad zabi nagari, nidai ya min".
Aisha tace "dan Shaye shayen?".
Dif Labiba ta dauke wuta tace "kar ki sake bana so Aisha".
Bata taba ganin baci ran Labiba ba sai yau hakan ya sa Aisha wayancewa.
"Yi hakuri, yanzu Abu Sadik ai dole ya hakura da ke".
Labiba tace "bawan Allah".
Aisha tace "yanzu wai har da ke zaaa tafi Edo? Makarantar fa?".
A takaice tace "Abba ya cireni".
^^^^
Alhamis Aunty Mariya ta fita takaba, Jumaah aka daura mata Aure da Alhaji Ali Zaki.
Bayan anyi gyare gyare a Gidan ta tare tare da 'ya'yanta biyu wanda Alhaji Zaki ya bukaci ya rikesu.
Zaid da Dalo sun tafi Kano gidan Yayan Mancy Daga chan suka nufa Abuja.
B A Y A N 'yan kwanaki.
E D O
Labiba ta kira Aunty Bilkisu Matar da taimaketa a hanyar Katsina.
Bayan sun gaisa tace mata "Labiba ce".
Aunty tace "Allah Sarki Labiba, ya kike ya jikin Dan Makaho?".
Tace "Aunty baki manta ba?".
Tace "ina Zan manta beebs? Ai dan Makaho ya tsaya min a rai, tausayinshi nakeji".
Labiba tayi daria tace "Aunty wallahi jikinshi ya warke sosai, next month aurenmu".
Aunty tace "ke haba bari donAllah".
Labiba tace "wallahi kam".
Sosai Aunty Bilki ta tayasu murna ta musu fatan Alheri.
Tace "baya da raayin Civil Defense dinne?".
Labiba tace "kinga ko gaya mishi ma banyi ba".
Tace "to InshaAllah, in yana so ki bashi Email address dina yanzu zan turo miki, kice ya turo CV dinshi da address din".
Labiba tace "yanzu kuwa zan Aunty, zan sake kira, gaida min da kannena".
Aunty Bilki tace "zasuji inshaAllah".
Numbershi ta latso.
Dauka yayi full of energy yace "Yes bee to the beebs bae to be".
Daria tayi da jin iyarshegenshi.
"Wai Masoyin kana son aikin Force?".
Yace "Soldier?"
Tace "Nope Civil Defense".
Yace "Sosaiii ma, zaki samo min ne?".
Ya tambayeta cikin wasa.
Tace "eh in kana so".
Cike da zolaya yace "ina so Comptroller Labiba Ahmad Dakata".
Tace "Send your CV to the email address din da zan turo maka yanzu".
Yaji she sounds serious yace "babe are you serious ?"
Tace "stop asking too much, just send the cv, zan kiraka anjima i love you".
Kita ta kashe wayar, ko 30seconds baayi ba ta tura mishi email adress din, da mamakin Labiba ya tura Cv dinshi ma address din.
Aunty Bilki ta kirata, Labiba na dauka tace "Zaid Aliyu Zaki? Age 27".
Labiba tace "wai har ya turo?".
Aunty tace "eh wallahi, ina son masu zafin nama, inshaAllah zanyi kokari naga ya samu, inshaAllah".
Labiba tayi ta zabga godia tare da sa mata Albarka.
K A T S I N A
'Y A N B E N C I N E S K A L E Y.
Su 4 Zaid ya ma jagoranci har Parlon Baban.
Cike da Ladabi da biyyaya suka gaida Alhaji Ali Zaki tare da zama kasan Carpet.
Alhaji Ali yace "duk ku gaya min A ina karatunku ya tsaya".
Eskaley yace "ni ban taba zaman Aji ba".
Terro yace "Ni tun Primary ban cigaba ba".
Haruna yace "ni ina da Diploma".
Master yace "ni ina da Secondary School Certificate.
Alhaji Ali yace "Alhamdulilah,
ina so kuje kuyi tunani ku dawo ku gaya min burinku, wani sanaa kuke so ku fara? Zan baku jari".
Dadi ya mamayesu.
Master yace "ai Baba a nan zamu gaya ma, ba wani tunani".
Yace "ina jinku".
Yace "nidai Baba shago nike so a bude min a sa ka min lemuka da yogurt a sawo min blender da generato, a saka min freezer , zan dinga dama fura da yogurt ina saidawa, a sama ko a buga min tambarin Master Fura da Nono and juices".
Daria suka sa, Baba yace "an yi an gama".
"Kai fa Eskaley?"
Yace "Baba ni dai so nake a fadada min Kiosk ina a cika min Shago a habaka min shi, duk unguwan nan nikadai ke da shago".
Baba yace "ba kiosk ba, wannan shagon gefenka Empty naji ance ana neman me siya, zan kama maka in cika maka shago da provisions kayi ta saidawa".
Terror yace "ni dama Baba chan da na iya irin Takalma da Jakka Handmade, ina so a bani jari da shago na dinga yi".
Yace "to naji"
Kai kuma Haruna me kake so?
Haruna yace "Baba ina da diploma na, ina so na koma Makaranta na hado Degree dinnan, sai na dinga bussiness".
Baba yace "bussiness din me?".
Haruna yace "ko Shadda haka".
Yace "to naji, dukkanku zan baku naira dubu dari biyar, miliyan biyu kenan."
Ina Aljannah su sakashi, godia kawai suke kwasa, suna sanya mishi Albarka, "suna cewa sai Baba, mungode, Allah ya kare mana kai, ya sa ka fi haka, Allah ya maka Gwamnan Katsina, Allah ya kareka daga sharrin Mahassada".
Baba yace "To Amin nagode, amma fa da sharadi".
Suka natsu yace "ba cash zan baku ba, Idrisu zan sa duk ya siyo muku abubuwan da kuka lissafo da kudinku, don kar ku kashe su a banza".
Suka ce "mun yarda wallahi, mun fi so dama a siyo mana komai".
Yace "kuma duk wanda na sake naji ko na gani yana shaye shaye, to zan amshe abuna".
Haruna yace "nidai Baba na bar World na bar Sigari, dama wallahi rashin abun yi ne ya sa nake sha, amma yanzu haram".
Master yace "ni tun da naga Mankas kwance ya kusa warewa nace na bari don kar na baro ma kaina aiki uwayena basu da kudin biya a man aiki, Allah nidai na bari".
Terror yayi shiru, don ya san karya ne yace zai bar shan sigari lokaci guda, ya riga ya zame mishi jiki yace "nidai baba kar na ma karya, InshaAllah ba zaka ji ko ka gani ba, amma dai ka sani a addua, zan bari"
Baba yace "Allah ya sa, nidai na gaya muku, randa na ganku ko naji labari, zan amshe abuna ne, kaifa Eskaley ance kai ke sayar da world din yace "Wallahi Baba na bari".
Yace "kaifa Mallam Zaid?".
Zaid ya murmusa, Soyayyar Mahaifinshi na tsaga bargonshi da jinin jikinshi ya murmusa yace "Baba ni ai na bari, Labiba tace in ta kamani ina shan sigari wai zata sa a budeni a ciro mata hantarta
A maida mata cikinta wai ba zan kone mata hanta ba".
Sukayi daria ga baki daya yace "Diyata ta min daidai, to ku tashi ku tafi Allah ya muku Albarka".
Nan suka dinga shi mishi Albarka suna Gode mishi.
Cikin kwana biyu ya cika musu Alkawarin da ya daukar musu.
Kamar Shekarun Baya, haka aka dawo, ko wani Gida a Tudun Matawalle akwai kwanon Abincinsu a Gidan Alhaji Zaki, amaryarshi bata da kyashu bare hassada, duk wani mai neman taimako gidan yake zuwa, ya taimaki Danginshi, ya taimaki Na waje, kowa na yabawa da Alhaji Ali Zaki.
A B U J A
Jawad ya shigo Parlorn ya iske Mancy da Umma sai Abdulmajeed, Mimi na bacci.
"Jawad yadai?"
Yace "Mancy wai Sadyy har yanzu bata dawo ba?"
Ta kalleshi tace "Jawad Chan zata kwana".
Ya zaro Ido "don me zata kwanar musu a gida kamar basu da gida, nidai ta dawo".
Mancy tace "kamar dai wani gida taje? Gidan Abdulhafiz ne fa, matarshi take tayawa aiki ka sam tayi nauyi, ya gaji ne ba zai iya dawowa da ita ba yace sai gobe".
Jawad yace "yo ita 'yar aiki ce da zaa dinga daukarta tana tayin aiki? Nidai barinje in daukota gaskia".
Mancy tace "kayi hakuri Jawad gobe zai dawo da ita".
Jawad yayi dan guntun tsaki ya latso wayar baban yayanshi yace "Hello Yaya, ga Abba nan na ta fada wai ka dauke mishi diya, yace gobe da sassafe ka maido mishi diyarshi kar ya bata maka rai".
Jin muryan Abba sukayi a baya yace "karya ake mun, ni da bansan ma anyi ba?".
Umma tace "Wai Jawad, Wai Abbanku zai maida Dalo Katsina gun Babanta".
Gaban Jawad ya fadi ya zaro ido yace "Abba wai dagaske? Meyasa? DonAllah kayi hakuri, ba Babanta yace ya bar maka ita aure ya rabaku?".
Abba shima ya biye yace "ai Auren zan mata a Katsina".
Ya zaro ido sosai, sai chan yaga suna dariya, sai ya gane ashe zolayarshi suke
Jawad ya bubbuga k'afa cike da shagwaba
Su Mancy suka sa daria baki daya.
Abdulmajeed yace "ana so ana kaiwa kasuwa"
Ya murguda baki yace "ina ruwanka?".
Abdulmajeed yace "ko kayi making move, ko ma hadeta da Aisha nayi Mata biyu rana daya".
Jawad yayi hanyar kofa yace "in ka fasa".
Dariarshi sukeyi sosai Abdulmajeed yace "Mancy Your Boy is In love".
Mancy tace "ai na lura da kanwar taka itama ta na yinshi"
Alhaji Abu ya kalli Iyalanshi cikin dadi yace "Alhamdulilah"..
Washegari Yaya Abdulhafeez ya dawo da Dalo da safe don daga gidansu zai wuce aiki.
Suna kan table suna breakfast.
Sukayi Sallama tare da gaisar dasu.
Abba yace "Yadai? Wannan sammako haka? Kamar ana tsiranku".
Abdulhafiz yace "Abba ance kana ta fada, shiyasa nace in zan wuce aiki zan maidota".
Jawad ya dinga ma Abba Signal da yace eh don in ya gane karya ne zai bata mai rai.
Abba yace "yo eh, sai a dauke man 'Yar yainyata haka akeyi?".
Dalo dai tayi ta daria.
Umma tace "kuzo kuyi breakfast".
Dalo tace "wallahi a koshe muke".
Mancy tace "zo ki kwashe wanda aka ci".
Tace to Ta zo tana hada plates din da aka bata iya daukanta ta nufa kitchen.
Kamar an tsunkureshi ya mik'e yana hada cups yace "dama kitchen din zanje".
Ba wanda yace komai Illah murmushin da suke ta zabgawa.
A Kitchen ya isketa tazo wucewa ya rufe mata hanya.
"Sadyy kikaje gidan Yaya kikayi zamanki ko, kin sa zuciana wahala, yana ta missing dinki".
Bude idanuwanta tayi alamun hakuri tace "i am sorry, zuciyar ta daina Zafi, maganin tazo".
Yace "ni dai kar ki yarda ki sake nisa dani, jiya su Ya Majeed har da zolayana suke".
Shagwaba yake ta zuba mata shi ala dole dan auta.
"Ina ruwansu da kai da zasu zolayeka? Ka rabu da su, zanyi maganinsu".
Yace "Ina Sonki kinji?".
Murmushi tayi ta sadda kai k'asa tana daria.
Yace "wallahi sai kin fada yau, kullun in ta fada ba kya fada?"
Hannu ta sa duka biyu ta kulle fuskanta.
Ya sa cokalin hannunshi ya k'wankwashe mata hannu budewanta yayi daidai da futar "Ina Sonka nima".
Lumshe ido yayi yace "Princess"
Lumshe ido tayi tace "Prince".
"Umma, Mancyy wallahi ga su nan suna soyewa a Kitchen".
Umma tace "Me suke soyawa kuma?".
Mancy dai daria take kasa kasa
Dalo kamar ta shige k'asa saboda kunya.
Alhaji Abu yace "to abu yayi kyau, barin gaya ma Alhaji Ali, in zaa iya hade bikinsu Zaid wallah duk aurar da ku nake in huta"
Da gudu Dalo ta shige Daki.
Alhaji Abu ya kira Alhaji Ali, a handsfree aka saka wayar bayan sun gaisa Alhaji Abu yace "wai wasu sabbin tsuntsayen soyayya muka samo, nace ko dai mu aurar dasu mu bige aiki?".
Daria Alhaji Ali yayi yace "Wa da wa?".
Alhaji Abu yace "Diyata da Jawad"
Cike da jin dadi Alhaji Ali yace "Sosaiii ma, ai kawai a buge aiki".
To sai ka gaya ma su Labaran cewa Su uncle Usman dinsu zasu zo neman aure da saka ranar ran jumaa"
Alhaji Ali yace an gama.
Haka ko akayi, a karshen satin aka kai kudin neman aure, da sa rana Family house dinsu Alhaji Ali zaki.
Shirin Biki ake tayi gadan gadan.
Kullum sai Umma da Mancy sun shiga kitchen.
Alhaji Ali ya turo 2mil wai a ma Dalo kayan daki.
Alhaji Abu ya kirashi yana fada "diyarka ce da zaka turo kudin kayan daki?".
Alhaji Ali yace "Allah Nagode, diyarka ce, wai da gudummuwa ce na turo, amma in ba a so a maido min abuna".
Alhaji Abu yace "baka isa ba, wanda yace ka turo".
Sukayi daria.
A Gidan Yaya Abdulhafeez, Flat ne Uku 3 bedrooms each, Abba ya gina ma 'yaranshi gida tun kafin Abdulhafiz din yayi aure, nan zasu zauna duka.
Sai ya kira Zaid a waya yace "to Ni dai bansan inda kake son zama ba, zaka zauna a Abuja in samo maka aiki ka hadu da yanuwanka?".
Zaid yace "Abba, nidai Katsina nake so, nan nake son Zama, aiki kuma akwai abunda nike jira".
Abba yace "to ba laifi, ka nemo gidan da ya maka, ni zan siya".
Zaid yace "Abba Baba ya bani Gida a Goruba road".
Abba yace "shifa Baban naku karambani, wa ya aikeshi baka Gida? To dama abunda na yi ma su Jawad nike son yi maka, to amma tunda an rigani, zan siya maka Mota kai da Matarka, sannan na samaka chanji a account".
Cike da jin dadi Zaid yayi ta zuba godia.
Alhaji Ahmad Dakata ya ma Labiba da Samira kayan daki, duk abunda aka siya ma Samira an siya ma Labiba, komai iri daya ne.
Zaid yace "ba sai sunyi komai ba, Baba ya gyara gidan".
Tace "ai da bakuyi wahala ba, nan ma anyi komai".
Yace "kuma sai anyi wahalar daukosu daga Edo?ai kawai a barsu"
Hayyakoewa tayi Labiba tace "a yi yaya dasu? wallahi, sai an sa min kayan da Abbana ya min".
Ganin rigima take neman tada mishi yace "to Baby, ba abun fada bane, sauki nake nema".
Tace "to angode amma sai an kawo".
Yace "Allah ya kawo lafia".
Ita fa zuciyarta a wuya yake, kowa ya tashi zai ce "wallahi ki rage son Zaid, wata rana zai miki wulakanci, namiji butulu ne, da ka nuna mishi So, wulakanci ke biyo baya"
Da sun fara maganar nan tashi takeyi ta barsu sai suce ba ta son gaskia..
Yan Bencin Eskaley suka hado mishi gudumuwar naira Dubu dari 25k suka hada each.
Da farko yace "ba zai ansa ba".
Master yace "kai yaro ka amsa wallah mun fika kudi don business mukeyi kai ko mai baka saidawa".
Daria Zaid yayi yace "Yan dunia, ku zo musha World don murna".
Master yace "uwar World zami sha, kana so Baba ya anshe tallafi ne ne"
Daria yayi ya musu godia.
Suka ce ka kaimu Gidan Nene.
Yace "wallahi Nene damuwa ce".
Suka mishi magiya ya rakasu.
Ashe leda sukayo mata.
Sai da sukayi drama a gidan