Showing 30001 words to 33000 words out of 68203 words

Chapter 11 - JARABTA 1 TO END Book Complete Document hausa novels by Maman Abdul Shakur--.txt

M Shakur   

29 Dec 2024

8269

kyau lallen amaryan yamata ba, sanan aka wanke mata gashi akai using handryer aka busar dakan sanan aka fara yaryada mata kitso yan mini mini. Sai Wuraren azahar suka gama sanan suka tafi yarage daga ita saisu Ihsan sosai tasaki jiki dasu sabida yanda suketa janta jiki kaman sun santa, sata tai wanka sukayi suka shiryata cikin wani ubansu lapaya, Fancy glamour suka dauko ta chanchara mata makeup din amare idan kun ganta bazakuce itabane, sanan suka kira Umma cewa sun gama, Umma tace "to, yanzu za'a zo ataho da ita". Anty Hindu ne dawasu mata duk sunci gayu sukazo gidan, rungume Anty Hindu Islam tayi zatai kuka ta girgiza mata kai, sanan ta lullubeta mata fuska aka dauketa suna wakoki aka tafi da ita gida fuskarta a rufe, ta lapayan ta take hango yanda gidan ya cika da mutane sai taga gidan su kaman ba biki akeyi ba, wani babban falo taga an shiga da ita an zaunar da ita akan kujera Anty Hindu ta zauna a gefenta tana gaggaisawa da mutane anata guda, wata matace dataga suna kama da Khaleel taci gayu sosai tazo gaban su, Anty Hindu tace "ga maman mijinki nan" yaye lullubin fuskarta Ammi tayi, ahankali tasa hannu ta daga habarta kasa dago ido tayi sabida kunya hawaye taji ya gangaro, murmushi Ammi tayi tace "masha Allah daughter" sababbin kudi taciro ajaka yan 500 tadinga mata manni ana guda har saida kudin yakare sanan takoma ta zauna, haka ma Umma tazo ta wanketa da liki, duk wanda yazo Anty Hindu tana fadamata waye, sosai aka dinga ihu ana guda sanan aka tafi da ita bangaren Goggo, Goggo Kam harda rawa sabida murna tai manni tai manni har saida duka kudinta ya kare, wata malama tagani ta tashi tai musu wa'azi da addu'a sanan Goggo tace "to kowa yatafi abarmata amaryan ta tahuta" haka duk aka watse ya rage Anty Hindu da Ammi da Umma, tashi sukayi suka shiga uwar daka Goggo sunata magana, muryan Goggo taji tana cewa gaskiya anan zata zauna. Fitowa sukayi Ammi tazo ta dafata tace "kinajin yunwa insa akawo miki abinci daughter?" akunyace ta girgiza kai, murmushi Ammi tai ta kalli Anty Hindu tace "daughter na badai kunya ba" dariya Anty Hindu tayi daga nan duk suka fita suka basu wuri, sosai Anty Hindu tamata wa'azi da fada akan tabi mijinta, sanan tacemata Khaleel yamata sabon akwati set daban daban har 6, Abban ta duk yahada an wuce mata dasu gidanta na Abuja. Sai bayan sallan Isha Anty Hindu ta tafi ba karamin kuka tasha ba hakanan ta hakura tai shiru gyangyadi tafara yi akan kujeran Goggo sabida yanda tagaji gakuma kukan datayi hakan yasa Goggo tace "tashi ki shiga ciki ki kwanta abinki ki huta kinji, sannu yarnan yan iskan yaran nan duk sun wahalar dake" murmushi tai dan hakanan taji Goggo ta shiga ranta gatadai tsohuwa amma akwaita da tsafta, "au bazaki tasoba" Goggo tai maganar tana kokarin tashi daga kan tabarmar data shimfida a tsakar dakin, kamo hanunta tayi tace "muje ki kwanta bakisan bacci nada amfani ga lafiyar dan Adam ba" kofar uwar dakanta ta bude da gadon ke agyare tsaf tace "jeki kwanta abinki zanga dan kan uban dazaizo yafita dake, jekiyi baccin ki saida safe kinji yar albarka" gyada kai tayi sanan tace "saida safe Goggo" kwanciya tayi akan gadon da aka gyara tsaf dakin sai kamshin turaren wuta yake within 2 min bacci yay gaba da ita, Goggo dake kishingide akan tabarma taji ana kokarin bude kofar ta tashi tayi ta zauna da kyau tana wawware ido, Khaleel ne ya shigo sanye da doguwar jallabiya sai kamshi yake yawani daure fuska yace "ina matata? Daga barinta tazo gidan naku shikenan kuma bakusan ku komar da ita inda kuka daukotaba?" ko kallonshi Goggo bataiba taja filo abinta takara kwanciya sanan tace "jeka tambayi uwarka, bata fadama daga yanzu anan gida zata zama ba, to saikun koma Abuja ne zata tare a gidanka" karaso wa ciki yay yace "nida matar tawa lallai nema" yazo zai wuce yay bedroom Goggo ta mike tsaye da sauri tasha gabanshi ta rike kugu hakan yasa yaci birki yana kallonta cike da bacin rai, dariya tayi tarike haba tace "mara kunyar banza, fitarmin daga daki tunda bakai ka ginamin ba wlh kona hadaka da ubanka" ganin Goggo ta daure babu alamun wasa tawani rike kugu yasa yajuya yafita daga dakin rai abace, Goggo tarakashi da dariya sanan ta maida kofa ta rufe harda saka Sakata tace "fitinannun yara" kwanciya tayi abinta rai fes tace "dan kanuba to yarinya sai tasha gyara sanan za'abaka, idanma nabari ka kara sata a ido ba sunana Lami ba" lumshe ido tayi tana sauke ajiyar zuciya. Direct part din Ammi yawuce duk ranshi a dagule Yusuf yagani zaune afalo yana jiran Ihsan tagama dafamai Indomie dayace tadafamai, yana ganinshi ya gimtse dariyar datazomai, ko kallonshi baiyi ba ya shiga bedroom din Ammi wata kawarta ya tarar tana magana da ita hakan yasa yaje kusa da ita ya zauna, sallamar matan tayi sanan ta juyo ta kalleshi tace "Ya akayi Son?" da kyar ya iya cewa "Ammi wai kekika cema Goggo karta bari Islam tabini anan zata dinga kwana" Ammi taso tai dariya da kyar ta saita kanta sanan ta kallai tace "eh nafiso kawai ran Sunday idan duk mun tafi Abujan basai ta tare wajenkaba, yanzu ga duka family anan mezataje tai ita kadai achan gidan kadaici zai isheta mana" zaiyi magana tace "ka bacemin daga nan I have alot of things to do" tashi yay yafita daga dakin duk ranshi acinkushe ta gefen ido yaga Yusuf ya ijiye Indomie hanunshi yanamai dariya ciki ciki haka yay kaman bai ganshi ba yana zuwa dai dai inda yake yadau plate din Indomie yace "wlh bazaka ci shiba" Yusuf ya kwalama Ammi kira yace "Ammi kinga wai akaina zai huce takaicin shi" da sauri Khaleel yafita yay part dinsu ya kulle kofa ya ijiye Indomie anan kan kujera yawuce bedroom yafada kan gado kasa bacci yayi sai juye juye yake daga baya yatashi ya shiga bayi kawai ya dauro alwala yazo ya kabbarta salla.


Bari muleka Faridan mu.
Idan kunga Farida saikun tausayamata ta rame sosai, da kyar Mum kesata taci abinci, bata da aiki sai daukar waya taita dailing number superman da baya shiga ko kadan, Abba kullum wa'azi yake mata da fada, Mum dai duniya yay mata zafi hakan yasa wani zubin idan Farida tafara kuka itama jonata takeyi suyi tayi tare, ba irin Allah ya isan da basuma Islam ba sabida bakin ciki.


Hakanan yau Wednesday taji tanajin fita kotadan ga rana, doguwar riga baka tasaka ta yana gyalen ko hoda bata shafaba tafito daga gidan danko Mum bata fadimawa ba, keke napep ta tare tace "yakaita Infinity gym" ta shiga ciki yaja har wajen yana ijiyeta ta ciro kudi ta bashi, sucurity ya bude mata ta shiga ciki, wani kukane yazo mata ganin treadmill din data taba ganin superman dinta akai, da kyar ta hadiye hawayen ta karasa wajen eatry din, order strawberry smoothie tayi ana kawomata ta karba tareda bada kudin tanata kallon smoothie din tana tuna ranan da superman dinta yasaimata yabata ahankali tace "menama Islam haka datamin irin wanan abu? Mesa nakasa cire sonshi araina why, please God inaso na manta dashi please" share da kwallan daya zubomata tayi tadau smoothie zatakai baki da sauri ta ijiye ta kife kanta akan table din tana wani irin kuka mai cinrai, "hey is everything okay" dago kai tayi suka hada ido da Yusuf dake sanye cikin sport wears hanunshi rike da cold bottle water, share ido tayi ta juya da sauri ta duba ko suna tareda superman dinta ne taga shikadai ne, juyoda kai tayi ta harari Yusuf tace "wat are you doing here?" kujera Yusuf yaja ya zauna yana kallon fuskarta yace "nothing banmasan kebace" tashi tsaye tayi tajuya zata bar wajen dan wani irin haushin Yusuf takeji da sauri yabita juyowa tai cike da masifa tace "kadena bina harda kai aka hadu aka yaudaran, Islam Islam" takira sunanta saikuma tajuya tafita daga wajen da sauri jin wani kukan ke zuwan mata suna fita Yusuf yasha gabanta yace "hear me out, kidena blaming sister ki wlh batada laifi, Allah kuwa trust me" bakin gyalen ta tasa akan fuskar ta tafashe dawani kukan, jitake kaman zuciyata zai fashe, ba karamin tausayin ta Yusuf yaji tabashi ba ya tsaya kawai yana kallonta da kyar tai shiru ta kalli Yusuf da rinannu idonta tace "koma menene at least for d sake of ni yar uwartace, tasan yanda nake sonshi saitaki auren shiko" ta dago kai ta kalli Yusuf tace "kataba son wata?" girgiza mata kai yayi alamun a'a hakan yasa tadanyi murmushi tace "bazaka taba iya gane wat am going through ba, Islam" tasake kiran sunan Islam tana wani irin dafa kirjinta da sauri tajuya tabar wajen akan bakin titi ta tare napep ta shiga tana goggoge ido da bakin gyale. Sosai Yusuf yaji jikinshi yay sanyi wanan wani irin sone, yanda take haukan son Khaleel dinan shikuma haka yake haukan son Islam, oh Allah kayaye ma wanan baiwar naka wanan son maso wanin, ahankali ya juya ya shiga ciki.
Islam dai sai gyaran jiki ake mata in and out, Goggo yanzu kulle kofa take idan baka kwankwasa ka fadi sunanka ba bazata taba budewa ba duk dan kar Khaleel ya ganta take wanan.




Dayake yau asabar yasa anata shirye shirye kowa na hada kayanshi dan gobe zasu tafi, Wuraren 11 Khaleel yafito daga part dinsu yana sanye da jeans black da blue t-shirt mai gajeren hannu, fuskar nan tashi adaure har wata yar raman dole yayi sabida rashin ganin Islam, dakin Ammi yayi yasameta zaune kusa da Dad datake hadama tea gaishe su yayi suka amsa, Dady ne yace "mekake so son" kallon fuskar Ammi yayi hakan yasa ta dauke kai ahankali yace "dama Dady inaso Ammi tasa Islam muje ta tayani hada kayan mune nachan gidan tunda gobe zamu tafi" Dady ya Kalli Ammi yace "kiramai matarshi tazo sutafi ta tayashi mana" Mum zatai magana Daddy yace "ki kirata nace banson jin komi" murmushi Khaleel yayi hakan yasa Ammi ta watsamai harara sanan ta wuce tafita tai dakin Goggo saida tai magana sanan Goggo tabude ta shigo Islam dake sanye da riga da sket nawani soft material mint green dake zaune rike da wayar Ihsan tana karanta wani novel tace "dauko Hijab dinki kizo Islam" ajiye wayar tayi tadau hijab Goggo tace "ina zata?" "Kiranta Alaji yake" black hijab tadaura akan kayan tabi bayan Ammi har falo, tunda ta shigo yake kallonta ganin yanda fatarta har wani kyalli take takara haske, dudda tasaka hijabi bai hanashi ganin yanda tawani kara cikowa ba tai fresh like honey wine, gaida Abba tayi cikeda girmamawa tana kallon Khaleel ta gefen ido dudda tadanyi kewanshi amma taki Koda kallonshi balle ta gaidashi, Abba ya nuna mata Khaleel yace "kuje kuhado kayanku na dayan gidan dan gobe da safe zamu tafi" ahankali tace "to daddy" fita Khaleel yayi batare daya kalleta ba hakan yasa tabi bayanshi kirjinta nadan bugawa, mota ya shiga hakan yasa ta bude gaban motar ta shiga ta zauna tarufe, kunna motar yayi suka fita daga gidan su aranta tace "nan da nanne bazai iya zuwa da kafaba, lazy fellow" horn yay mai gadinsu yabude yay parking yafito ya shiga ciki saida tai kusan 2min a motan sanan tafito jiki duk asake, ahankali ta bude kofar ta shiga falon, da kyar ta iya daga kafa takai tsakiyar falon ta tsaya ganin bata ganshi ba, tabaya taji anrungumeta hakan yasa saida tai yar kara sabida tsoro, tsamtsam ya rungumeta yakawo kanshi ta wurin kunnenta yace "I miss you" juyo da ita yay yakai hanunshi yay cupping fuskarta ya kalli cikin idonta yace "did you miss me" dan murmushi tai sabida yanda yay maganan ta dauke kai, zama yay ya daurata akan cinya yana kallon fuskarta yace "waye lazy fellow?" adan rude ta kallai ta dafe kirji, ganin yanda yake kallonta yasa ta tashi da guda tana dariya tai hanyar bedroom tace "bafa dakai nakeba" harta zauna akan gado taji yabude dakin da gudu ta tashi zata shiga bayi ya rikota tabaya tareda cire hijabin jikinta ya matseta yana kallon idonta yace "Wana kama?".
[6/22, 7:53 AM] Maman Jedda: *JARABTA*




Maman Abd Shakur


49 & 50


Dan dariya taji yazo mata, kawad dakai tayi sanan tace "sorry" ahankali, kamo hanunta yay ya zauna akan gado ya daurata akan jikinshi yana kallon fuskarta murya chan kasa yace "did you miss me?" daura kanta tayi akan hanunta akunyace tace "uhm" bakinta tarufe da sauri dan wlh batasan lokacin da maganan yafito ba, hade kansu yay wuri daya ya hade hannayenshi biyu ta bayanta yana dan jijjigata akan kafarshi, murya chan kasa yace "banjiki da kyau ba" dan dago kai tayi ta kalleshi suka hada ido batare data cire idonta daga kanshi ba ta sanya hanunta ta baya ta bige hanunshi ta tashi da gudu ta tsaya abakin kofa sanan ta juyo ta kallai ta gyadamai kai kaman yanda yara suke sanan tace "yea I miss yhu" bude kofa tai tafita da gudu tai kwanciyan ta afalo akan dogon kujera tareda daura filon kan kujeran akan fuskarta. Alamun tahowar mutum dataji yasa tadan zame filon kadan daga kan fuskarta ta kalleshi maida filon tayi da sauri ganin sun hada ido kirjinta na bugawa sosai, zama yay ya dauki kafafun ta ya daura akan cinyarshi yana mata waiwayi akafa, motsi ta dingayi tareda kara rike filon ta danne fuskarta aciki, jin bakinshi datayi akan babbar yatsar kafarta yasa taji wani yarr batasan lokacin data saki filon yafadi akasa ba, kasa daure yanda yake sarrafa yatsun nata yake ta mirgina ta kifa tareda daga kafafun nata sama hakan yasa sket dinta yay kasa kafafun suka bayyana ta lumshe ido tana cuccusa fuskar ta acikin kujera, ahankali ya kamo kafafun ya kwantar sanan ya kwanto ta bayanta yakai bakinshi saitin kunen yakira sunanta "Islaaam" yanda yaja sunan yasa takasa daurewa saida tabude idanunta dasuka kankance ta kallai, tashi yay ya zauna ya sanya hannu ya dagota itama ta zauna tana lumlumshe ido, hanunta yakama yarike gam ahankali yace "ina sonki dayawa Islam please don't ever leave me, I love you sama da yanda kike tunani, u know something" kai ta girgiza mai tareda kwantar da kanta kan kafadar shi, kanshi ya daura akan goshin ta yasanya hannayen shi yay cuddling nata very tight sanan yadan sauke ajiyar zuciya yace "are you fine?" gyada mai kai tayi, ahankali yasake sauke ajiyar zuciya yace "nai mafarkin kine jiya saisa nasa Abba yace kiboyini nan, I just wanted to know idan kina lpy" lumshe ido tayi akan kafadar nashi tana kara shakan kamshin dayakeyi datake mugun so cikin siririyar muryarta tace "mafarkin mekayi?" murmushi yay tareda kissing forehead dinta yace "it doesn't matter now, all I want you to know is I love you very much Islam" da sauri ta maida kanta kirjinshi tareda lumshe ido sabida yanda yakesa takejin kunya, ahankali yaciro kanta daga kirjinshi yana wani irin kallon fuskarta bude ido tayi kadan ta kallai da sauri ta kankame idon ganin ita yakema wani irin kallo, saukar bakinshi dataji akan lips dinta bazato ba tsammani yasa ta bude ido da sauri tana kokarin kwace bakin matseta yay ajikinshi yana mata wani irin zazzafan kiss, hanunshi taji abayanta yana shashafawa batare daya raba bakin nasuba zip din rigarta taji yaja kasa kokarin tashi tai daga jikinshi hakan yabashi damar cire rigar da kyau ya ijiye gefe, kankame idonta tayi sosai cike da kunya ganin yanda yake kallonta, ahankali yasaki bakinta da idanunshi dasuka soma ja yana kallon yanda take kakkare kirjin da hanunta, hanunta yakama yanadan murmushi yana wani irin kallonta ganin yanda taki bude ido, jin hanunshi akan bra dinta yasa tadanyi ihu ta shige jikinshi sosai jikinta na rawa ta fashe da kuka tace "please sto... " bai bari takarasa maganar ba yasake hade bakinsu wuri daya ya kwantar dasu akan kujeran ya shiga wasa da ita da zafi zafi gashi yaki bata daman yin magana hawaye kadai take iya zubarwa, bude kofa akayi aka shigo dakin kai tsaye hakan yasa ya dago kai tareda maida Islam bayanshi itama bude ido tai atsorace jin anshigo dakin tai lamo abayan shi duka hannayenta nakan kirjinshi dan rungumoshi tai tabayan, daure fuska yay tamau yace "mekika zoyi anan?" yana maganan ne tareda daukar rigar Islam dake kan kujeran yana bata da sauri ta karba ta saka, kasa cire ido tai akanshi ganin cikakken kirjinshi gawasu six packs dasukai layi gwanin ban sha'awa, jijiyoyi sun fiffito a muscle dinshi "mekekazo yi agidan mu nace?" Ya daka mata tsawa hakan yasa Islam tadan leko da kanta daga bayanshi bayan tagama saka rigar bakinta har rawa yake tace "Faa.. Faree" wani irin kuka ne da kishi yakawo ma Farida wuya da kyar ta iya kakalo murmushi tace "am sorry nazo gidan ku bada izinin kuba, dama damaa" takasa karashe maganan sabida wani irin kuka dataji yazo mata, da sauri Islam ta sakko daga kan kujeran zataje wajenta riketa yayi yasa hannun shi abayanta ya zuge mata zip din rigar, hakan yasa Farida taji wani sabon kuka yazo mata da kyar ta share idonta tace "dama nazo na roki gafarar kune akan duk abinda nayimuku, zan tafi Umara gobe, anjima zan tafi Abujama, so I just tot nazo sabida mu shirya, shine nace Bala yakawo ni tunda yace yasan gidan yataba kawo Anty Hindu" takarashe maganan tana kuka dan takasa daurewa yanda tagansu yasa taji kirjinta namata zafi, fizge jikinta Islam tayi daga nashi taje da gudu ta rungume Faridan hakan yasa ta fashe da kuka sosai tace "Islam am sorry, please kiyafe min abubuwan dana miki kinji kema naji Anty Hindu tana cewa gobe zaku tafi ko please forgive me" girgiza mata kai tayi tace "am sorry too Faree, please kiyafe min" girgiza kai Farida tayi tace "bakimin komiba, please kiyakuri da duk abinda nayi" tai maganan tana kallon Khaleel, rigarshi dake kan kujera yadauka ya saka sanan yazo wajen kamo Islam yay ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login