Showing 1 words to 3000 words out of 53214 words

Chapter 1 - Hafsat Ilham Book Complete by Billy Galadanci .pdf

Advertisement
Advertisement

20 Mar 2025

3485

[1/8, 10:32 PM] Sha'awa: Hafsat Elham❤

Billy Galadanchi

Labarin kauna.

Haske writers Association.

*Karku yi mamaki Idan nace muku Wannan littafin ma na sadaukar dashine ga Babbar
Amiyata Hafsat Elham, wlhy ta cancanta ku yarda da kalamai na har cikin kasan zuciyana nake
jiyo kaunarta,Ku yarda dani komai zan mata bazan taba biyanta alkhairanta agareni ba,dan
Allah masoyana ku sota kuma ku kaunaceta tamkar yanda kuke sona*
*Ina rokon Allah ya bani ikon rubuta alkhairi acikin Wannan littafin dazan rubuta yakuma sanya
abin da zan rubuta ya amfane mu gaba daya*

*Ina rokon duk wanda ya ya bude Wannan shafin ya taimaka ya karanta kul huwallahu kafa
goma sha daya,ladan ya sauka ga yar uwata fad'matul zahra da yan uwa musulmi baki daya,na
rasata kusan shekaru hudu yanzu nagode*

01

Sosai ran Elham yake b'ace ba kad'an ba,ji take tamkar ta juya ta wanke yaron daya taka mata
farar socks d'inta tayi datti tunkan tashiga school ma da mari,aranta se mita take tana
kyankyamin kanta sabi da tsabar tsanda da kyankyamin da Allah ya halicce ta dashi, a class
sam kasa zama tayi da socks d'in,gashi sam ba'a bari Su zauna haka,tissue ta zaro a jakarta
fara kal ta nade ilahirin kafafunta dashi sannan ta zura sandal dinta,wunin ranar gabaki daya a
jaguje tayishi,driver din gidan sarkin fulanin Adamawa ne yazo daukarsu a school ita da feenah,
ko kallon juna basuyiba a haka suka Shiga mota,suna isowa gida feenah tayi gaba zuwa cikin
babban gidan,yayinda Elham tanufi b'angaren Masu gadin gidan tana tafiya tana dan saka
hanky tana karkad'e kasan wandon uniform dinta tana guntun tsaki dagowar dazatyi ta hango
yaa Abdul ya kura mata ido ya hard'e hannayenshi a k'irji se wani shan kamshi yakeyi,wani
yamutsa fuska taja d'an siririn tsaki aranta tana mamakin yanda za'ace mutum kullum yana cikin
dawaki ko k'yank'yamin Su bayaji ita sam bazata iyaba wlhy,se mayan kallo sekace wani d'an
kauye......A d'aya bagaren kuwa na Abdul mamakin iyayi da kuri da k'yank'ya mi irin na Elham
yakeyi yarinya ba kowa ba kuma ba yar kowa ba amma se kafirin iyayi da shegen gulman
tsiya,banda gulma kaje skul ka dawo ai sauri zakayi ka raba jikinka da uniform amma ita tsabar
kazanta wai hanky nata datake share fuskarta dashi kuma dashi take karkad'e dattin wando shi
aganinshi Wannan babbar k'azan tace....da sallama tashiga gidan nasu mahaifiyar ta dake
kokarin gyarawa akuya daurin da aka mata ta kalla yanda ta dage taketa damkar akuyar girgiza
kanta tayi tace tana yank'wane fuska "Sannu Innah,ina wuni?" Dagowa uwar tayi taga yanda
tayi kichi kitchen da fuska,ita abinma dariya ya bata tasani Wannan akuyar ne datake damk'a
kuma wunin ranar bazataci abinda ma ta girka ba tace

"Lapia lau Hafsatu harkun taso?" A tak'aice tace da ita
"Ea Inna" tashige d'akin dayake mallakinta a gidan...duk da yake gidansu ba wani me muni
bane amma sam bazakayi tsammanin cewar d'akin Elham yakai had'uwar hakanba,komai naciki
pink & white har labulaye da gado closet nata center carpet tiles na dakin da komai ma,a kofar
toilet dinta akwai towel shid'inma pink&white ne,ajiye jakar skul nata ta farayi sannan ta zauna
kan kujerar k'walli d'aya dake cikin dakin ta zare takalmin skul nata ta cire Wannan tissue data
nad'e kafanta dashi ta wurga a dustbin dake gefen kofar shigowa dakin wanda yake pink&white
ne shima,mik'ewa tayi ta cire uniform nata ta daura towel d'inta na wanka zarar Su tashiga
bathroom d'in dan karamin washing machine nata ta budesu ta wurgasu har inner wear's d'inta
ma ta barsu anan sabida yana drying bayan ya wanke a tsanake tayi wanka wanda ankai 40
mnt ana yinshi sannan ta kai dubanta zuwaga dan mitsitsin agogon bangon dake toilet me kalar
pink& white taga biyu ta gota da sauri ta dauro alwala tafito daga ban d'akin,wurin dazayi Sallah
ma wani tashin kanshin turaruka yakeyi ga almiski ma kamshin shi se tashi yakeyi a haka ta
janyo hijab fari k'al me kamshi ta tada Sallah tajima awurin tana addu'o inta har aka kira sallar
la'asar sanda tayi Sallah sannan ta tashi,cikeda yanga ta zura wata doguwar rigar jallabiya baqa
me adon duwatsu jajaye ta dauko red mini veil ta yane kanta dashi gaban mirror taje ta watsa
turaruka na asalin masu kamshin gaske, sedai ba masu tashi bane masu sanyin kamshi ne se
kazo daf da ita zakaji numfashin ka na shirin dauke wa ya mata rakiya,wasu takalmi ta saka
masu d'an tudu suma black & red sannan ta janyo wayarta kiran iPhone 6+ ta kunna ta,tafito
tsakar gidan,kallon ta maman tayi tace

"Hafsat se ina haka?" Murmushi tayi tace "Zani gun momy Fulani ne,dasafe ban jeba"
"To zancen abin ci fa Hafsat?" Yamutsa fuska tayi wanda Wannan ya zame mata d'abi'a tace "
Innah na k'oshi" ,girgiza kai Innah tai tana jinjina k'yank'yami irin na Hafsat,sam abin baya mata
dad'i yarinya sekace me shafar aljanai.....Dannan wayarta take tana tafiya a yangace status
take dubawa kasancewar yau through out bata hauba, a hanyar dazata sadata da sashen
momy Fulani taci karo da yaa Abdul,dan yamutsa fuska tayi tace dak'yar

"Yaa Abdul ina wuni?" Ko kallon inda take beyiba yace "lapia" atakaice, haushi ne ya tarnak'e ta
taja d'an guntun tsaki batare da sanin taba,Ashe ya jiyota,cike da dakakkiyar yace

"Elham zo nan" rai a bace tazo kusa dashi ta sadda kanta a kasa tace "Gani yaa Abdul" yafi
minti biyu yana Kallonta beyi magana ba,harta fara tsarguwa gashi iya k'uluwa ta k'ulu a ganin
ta wani salon wulakncine yake shirin tsirowa dashi,se can har kwalla ya taru a idonta yace cikin
izzah da isa
"Wakike wa tsaki Elham?" Dago manya manyan fararen Idanuwan ta tayi dasuka Cika da
kwallah ta saukesu a kanshi amma ta kasa magana,a tsawace yace

"Dake nake magana wa kikewa tsaki?" Kwallar datake kokarin tarewa ne ya silalo a idonta da
sauri ta sadda kanta k'asa manya manyan eye lashes d'inta lokaci daya suka jike suka kara
bak'i da shek'i,ta kasa magana

"Idan yanayin amsa gaisuwa tane bakyaso Na sauke miki ki huta karki kara gaidani,amma
kinsani koba komai nafi karfin irinki tamun tsaki,balanta ina matsayin yayan ki" ta tsinkayi
muryarsa yana fada, murya na rawa tace

"Dan Allah Kayi hakuri yaa Abdul wlhy baran karaba" bece da ita komai ba ya wuce abinshi ya
barta gun a tsaye, harga Allah taji kunyar abinta tamasa batai tsammanin zeji ba,hankalinta ya
tashi ainun,gwiwa a sace ta juya zuwa cikin gidan

"Da sallama ta Shiga parlor din bakowa se feenah dake shan romon kan rago,fuskarta ba Yabo
ba fallasa suka gaisa tace
" feenah momy fa?" Kallon raini feenah ta mata tace "wace Momyn?" Idan da sabo Elham ta
saba bata biye taba tace "Momyn ki" dariya feenah tayi "Au momy na nazata bacin inna kinada
wata momy bansaniba,aida tun farko sabida rage kokwanto sekice momyna" Murmushi tayi
wanda ya kasance na yak'e ta nemi wuri ta zauna ta kurawa TV ido batare da ta ce kalaba,se
can momy tafito, da fara'a dauke a fuskarta tace

"Au Mamana dama kin shigo,yanzu nake cewa yau d'innan baki leqo minba sam ko lapia"

"Lapia lau momy na tashi makarene kuma yanzu na dawo bansamu nayi Sallah a school ba"
Murmushi tayi

"Lallai kam nasan da babban dalili,kinmaci abinci kuwa?" Girgiza mata kai kurun tayi alamun a'a
Momyn ta tashiga ciki batare da tayi magana ita kuwa feenah tace

"Yana dai da kyau mutum ya godewa Allah da kalar cimar gidan ubansa,ace mutum se tsabar
kwadayi baka cin abinda aka girka gidanku tsabar had'ama" ran Elham ya baci matuka sedai
batace da ita kalaba,kasancewar ta dama bame yawan san magana ba,kawai mikewa tayi tabar
sashen gaba daya zuwa swimming pool na gidan,cire ta kalmin kafarta tayi ta kwashe rigarta ta
zura kafafuwanta aciki tana wasa da ruwan a hankali....kuka me karfi ya kwace mata ta zauna
tayi abinta ma'ishi koda taji an dafa ta ta dago se ganin yaa faruk tayi yana kallonta,nad'e kafar
wandonshi shima yayi ya zura kafafunshi acikin ruwan yace

"Elham mesa ne bakya gajiya da kuka,ke sam abin kuka baya miki k'ank'anta,yanzu sanar dani
menene nasani yanzu zakice ba komai" kallon shi tayi amma batayi magana ba kawai dai ta
tsagaita kukan nata,rike mata hannu yayi yace

"Ba kasafai nake san tsoma kana a personal life nakiba,amma kisani ina damuwa aduk lokacin
da naganki a damuwa kema,dan Allah kirage yawan kukannan har zaki bata kya wawan
idanuwanki my swt sis" Murmushi tayi sannan ta sanya hannu ta share hawayenta tace "karka
damu yaa faruk zan dena Inshaa Allah" Murmushi ya sakar mata aka wuce wurin.....
Washe gari tun 7 ta shirya ta wuce gidan momy Fulani,akan hanya ta hadu da yaa Abdul,dan
durkuso tayi "Yaa Abdul ina Kwana?" Ko Kallonta beba balanta na ya amsa gaisuwarta,bata

wani damuba ita tama matsu yabar kasar kowa ya huta,mutum se mugun girman kan tsiya,tana
saqe saqen ta se ga yaa faruk a gabanta

"Good morning beautiful" ya fada yana me sakar mata lallausan murmushin sa" murmushin
itama tayi

"Good morn sweetest bro ever and how was ur night?" Tsayawa Abdul yayi ya juyo ya kallesu
se fara'a suke

"It was sweet dear and u?"

"Splendid" tabashi amsa tana kokarin barin wurin,hannun ta yariko,Shikuwa Abdul ya dauke
kanshi daga dubansu yayi gaba abinshi......"Bazaki tsaya mu gaisa da kyau ba pretty?" Agogon
dayan hannunta ta kalla tace "I'm going be late sweetest bro, w'll do that when I come back from
skul" sake mata hannun yayi "OK cutee all the best" Murmushi tamasa tajuya kurun,Raihan
dake tsaye daga garden tana kallonsu tace a ranta "Zakaci k'aniyarka wlhy yaa faruk,sena
gayawa ummah abinda kake shirin yi" ta juya zuwa b'angarensu kallonsu Haj Fati tayi tace
"Raihan Yaya kin gama shiri nki? " Sosa kanta tayi tace

"Harma nafita na dawo?"" Mantuwa kika yine hala?" Zama tayi ta fuskanci ta

"Ummah kinga yaa faruk bayajin maganar ki ko? Kinganshi can ko yanzu yana wa yar me gadi
magana,baze taba iya rabuwa da itaba inhar ba tsaye kika tashi masa ba" nisawa tayi tace
"Raihan ki barni dashi ze ganene wlhy dani yake zancen,tashi kiyi tafi yarki" mikewa tayi domin
batasan tayi fashi jiyama ciwon ciki be barta tafi skul,dukkanin Su a wurin mota suka hadu susu
hudu,ba wanda yayiwa dan uwansa magana haka suka d'unguma zuwa school,Raihan ce
bayan sun sauka ta kalli feenah tace

"Feenah muyi nan plss,ke kullum bakya taba raba hanya da talaka,talakan ma d'an masu gadi
bakida labarin cewa annabi da kanshi yace munemi tsari da talauci,had'a hanya da talaka ma ni
gani nake zunubi ne" feenah bata ce kanzil ba kasancewar itadin ma ba barinta Raihan tayi
ba,Elham kuwa Idan da sabo ta saba da tsangwamar dukkansu,kazalika ire iren wayannan
zantutuukan basa damunta, SS3 A take itada feenah yayinda Raihan take 3C, suna iska class
yan class suka fara mss neat ta iso, yanzu zakuga iyayi cike da zolaya suke maganar Murmushi
kurun ta musu ta zaro duster ta goge sit nata na zama da table sannan ta dauko wani fari se
sheqi yakeyi ta shinfida sannan ta zauna,ihu suka saka suna dariya wasu na mamakin tsafta irin
tata,Sune wayanda ba'a taba musu gwaninta.

Yau bayan sun iso gida hanky d'in ta zaro tafara aikin karkad'e kafar wandonta,hanky dinne
ya sub'uce mata adaidai lokacin data d'a goshi domin karkad'e wa,a daidai Wannan lokacin yaa
Abdul yashigo ya zo wucewa hanky d'in ya saukar masa akan fuskarsa,cireshi yayi ya juyo a
fusace wurgar dashi yayi akasa yad'ago yana Kallonta ita d'inma shi take kallo,rikicewa tayi
ganin yanayin fuskarsa tace murya na rawa

"Yaa Abdoul, dan Allah Kayi hakuri wlhy sub'uce mun yayi ban kuma san yanda akai yaje kan
fuskar kaba" matsowa yayi daf da ita

"Karyane Elham,tunda kika iya mun tsaki to my face komai ma zaki iya yimun,nasani sarai
kinsani kika wurgomun Wannan kazanta ajikin,an gaya miki kowa k'azamine irinki,wlhy na
tsaneki bakida kirki ko kad'an ko ganinki ma bana sanyi dalilinki zanbar kasar nan inkoma inda
nafi wayo,and this should be the last concrete warning dazan baki akan Shiga sabgogina daki
keyi, next time ko kallon inda nake kikayi wlhy se kinsha mamaki,now get out from my sight"
tana kuka tabar wurin Sa'a taci bakowa agidansu hakan ya sanya kai tsaye tawuce dakinta ta
rufoshi acan tasha kuka sannan tayi wanka ta gabatar da sallah ta kwanta lamo baccin ya
dauketa.......

Yaa Abdul yana tsaye yana Shafa jikin dokinshi Raihan tazo ta same shi, Murmushi me sanyi
ya sakar mata yace "hii dear how r u?" Murmushin itama tayi

"I'm fine yaa Abdul u?" Be amsa mata ba yace "ya akayi Raihan?" Dan Shafa fuskarta tayi tace

"Yaa Abdul bakaga message nawa bane?" Murmushi ya sakar mata ya riko hannunta suka
fitowar gidan dawakan yace "Raihan kiyi hakuri tafiyar nan tawa tazama dole ba yanda
zanyi,kinsani company nakewa aiki kuma sun buqaceni yanzu,amma kin sani kullum zanna rika
miki Waya so biyar arana kuma chat ma haka" sadda kanta tayi kasa tace "Allah yasa shine
mafi alkhairi"
"That's my beautiful wife,Allah ya miki albarka,momy ta aikeni anjima bayan magrib so ki shirya
muje tare keda feenah zan muku siyayya....

Bayan isha ya shigo part din momy anan ya taradda Elham,gaida momy yayi cikeda
girmamawai,Elham ma ta gaidashi ya amsa a dak'ile,yace " Momy list d'inkifa?" Murmushi tayi
tace "Yana wurin Mamana tare da ita zakuje" murtuke fuska yayi yace "momy Idan zaki aika
driver ya kaita mana" bata fuska tayi itama tace
"Kaga Babana nafa kula kana takura mamana dayawa ka dauki karan tsana ka dora mata ji
yanda ka ansa gaisuwar ta sekace ba kanwar kaba,yanda fa kuka dauki duniyar nan bafa haka
take bafa tam,aiko dan darajata ka sota,itada feenah nace suje tare dakai Idan kuma bazakaje
da Mamana ba Kayi tafiyar ka da kudinka banaso" durkusa wa yayi yashiga ban baki,arayuwar
ya tsani yaga ya bata ran mahaifiyarshi,sassauta fushinta tayi tace "ke Elham jeki d'aki bamu
wuri" bayan tafita ta kalleshi tace cikin taushin murya

"Babana ya kamata ka fahimci Elham yarinya ce me hankali kuma sanin kankace agidan nan
aka haifeta ta cancanci duk wani matsayi daga wurinka kodan kasancewar iyayenta masu
nagarta,ina sone danni kawai kadauketa matsayin kanwarka kamar yanda ka dauki feenah
kuma duk wani abu dazaka was feenah itaama kamata,kai mata wasa da dariya kuma ka
saurari matsalolinta daidai gwargwadon yanda kakeyi wa feenah,Babana Wannan ita kadaice

alfarmar danake nema a wurinka ina sone konbayan raina ka tallafi yarin yarnan Banso tashiga
wata damuwa kabata dama ta kusance ka ta hakane kadai zaka san wacece Elham,Allah shine
shaidata ina yowa ilham soyayya me tsanani Wannan rarrabewar kan naku da rashin jituwa,se
inaga kamar uwarku daya ubanku daya kuke Wannan,wlhy Babana idanbhar kamun Wannan
zan dinga zabga maka albarka daga nan har ranar mutuwa,kuma aljannah dakake nema
awurina Idan har ka dena wannann kiyayyar wlhy namaka alkawarin daga ma kafar ka shige tun
yanzu" nisawa yayi yace "kiyi hakuri momy ni dama ba kinta nakeyi ba kawai dai Yarinyar komai
seta riqa nuna wa mutum k'yama sam bata ajiye kanta kusaba wlhy,amma duk da zan jata ajiki
zan kuma nuna mata rashin dacewar hakan" godiya momy tamasa daganan taki rasu suka bar
gidan,a hanya Raihan se yada magana takeyi ba wanda ya kulata,bayan sun isa mall din ya
baiwa kowa 30k yace Su siya abinda suke so,ya kalli Elham yayi da sauri ta sauke kwayar idon
ta kasa yace "Kizo muje kina kwasar kayan momy kina had'awa da naki " bin bayanshi kurun
tayi batayi maganaba,Su kuwa Su Raihan sun zare suna can suna kwasar kayan maku lashe
abinsu,ita kuwa seda ta gama siyawa momy duk abinda ta rubuta,tabaki wurin biya kud'i sannan
tajuya wa nata,mamaki ne ya kama Abdul ganin takalmi kurun ta dauka me tudu se turaruka na
10 10k guda biyu,se kuma ta dauko clips na 4800 kwalli d'aya,kasa hakuri yayi yace " Elly
Wannan abin kurun zaki siya?" Yamutsa fuska tayi wanda hakan ya zame mata d'abi'a tace "
Yaa Abdul turaruka ne fa masu kamshi ina matukar sonsu dama nawa sun kusa karewa duk na
damu" takarashe maganar tana yarfe hannaye nta ,Murmushi yayi yace "To clip's d'imfa me
zakiyi dashi?" Ya tambaya yana me hard'e hannayenshi a kirji ya sanya Murmushi a fuskar sa
wani langwabe kai tayi ta yamutsa fuska tace "to ai yaa Abdul Kaine baka siyawa kanka komai
ba shine na siya maka" mamakin Yarinyar yakeyi duk da yake can kasan zuciyar sa yanajin
tsananin tsanarta amma ta burgeshi godiya ya mata suka gama abinda suke suka bar mall d'in,
kallon Raihan yayi yace "Bara muje wurin amadu me kajin hausa karna bar kasar ban Ciba" a
haka sukaje yab siyawa kowa tasa,kallon kazar Elham tayi tace "Ayyah yaa Abdul ai da baka
siyamun ba bana cin kazar hausa" wani dogon tsaki Raihan tayi tace "kaji jaka,ko ranar naji
tana gayawa yaa faruk batacin kazar Hausa wai kwata takesha,ina agidan ubanki har kiwonsu
ake seki kaiwa tsofaffi Su suci tunda ana kiwo tsabar maqo ba'a iyaci,yanzu gata Banza nan
saci" tsawa yaa Abdul ya daka mata

"Bakida hankaline Raihan? Ina komai ra'ayine? Tunda bata ra'ayi meye naki aciki,tsabar hauka
seki sako iyayenta kina zagi,wlhy karna kuma ji ko ganikin zagi iyayen wata ma ba
itaba,wannan ba tarbiyar damuka daura ku akai bane,and to be Frank I'm so very disappointed
in you,Elham u should take hrt plss don't be angry,and do not take what she says to hrt,do
forgive her,zan siya miki na turawa yanzunnan" Murmushi ta kakalo tace "Don't worry yaa Abdul
its fine with

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login