Showing 138001 words to 141000 words out of 182238 words

Chapter 47 - RAYUWA DA GIBI Book Complete By Batul Mamman.txt

ne za a saka ta. Sai gata tayi ido huɗu da Baba da su ka sauko ƙasa.

"Ke Siyama hau sama ki ɗauko min wayar Ummi."

Firgigit duk wani baccin iya shege da hammar ƙarya su ka gudu.

"Wayata Baba? Ke tsaya Siyama."

Siyama ta dakata. Baba ya zaro mata idanu ta kama bin bene ba shiri.

"Baba me nayi? Don Allah kada ka duba min waya." Ummi ta juya za ta hau benen.

"Ki ka kuskura ki ka hau benen nan sai nasa Baballe ya karyaki."

Cak ta tsaya "Baba me nayi?"

Bai kulata ba don bata cancanci hakan ba har Siyama ta sauko ta bashi wayar.

"Ɗakinku ɗaya. Ki faɗa min gaskiya, akwai wata ko babu?"

Mugun kallo Ummi ta watsawa Siyama. Ita kuma jikinta ya ɗan yi sanyi.

Iyaa ta ce "Baki ji me aka ce miki bane?"

"Akwai"

"Ɗauko min."

"Baba don Allah..." Ummi ta zube a ƙasa tana magiya. Abubuwan dake cikin wayar dake ɗakin sun fi ƙarfin me wayar. Dukkan wata mu'amalarta ta waje da fitintinunta suna ciki.

Ba jimawa Siyama ta sauko saboda a ƙasan filo Ummi ta ajiyeta da ta raba dare tana dannata jiya.

"Zan saurari Habibu don nayi imanin indai wani abu ya faru gidan ƴaƴansa ba zai ɓoye min ba. Idan abin da Siyama taji kina ƙullawa ya tabbata to ki kuka da kanki. Sannan in ki ka saka ƙafa a ƙofar gida to kada ki dawo na yafeki." Ya kalli Iyaa da Siyama "duk wanda ya bata aron waya ba da yawuna ba."

Wayoyin ya kashe a gabanta ya tashi ya shige nasa ɗakin. Ummi ta rasa gane kuka ya kamace ta ko me. Abin da yake taso mata yafi ƙarfin hawaye ko kalaman da take jin tana son zazzagawa Siyama.

***

Ahmad ya so ƙwarai ya kira baban Salwa akan ya turo a ɗauketa. Da wannan niyar ya shiga ɗakinta inda ya mayar da Mami bayan tafiyarsu Anti Zabba'u ya shiga da ya gama wayar. Ɗakin wari yake yi mai ɗauke numfashi. Ya yi mata kallo ɗaya ya juya. Nan ya barta tana so tayi kuka amma bakin ma ya karkace sai dai hawaye kawai. Kallon da yayi mata na takaici ne da baƙincikin halin da ta saka kanta kuma su ma ta jefa su.

Mami bata da kowa sai ƴan uwa waɗanda ta jima da barranta kanta daga garesu saboda abin duniya. Bata zuwa sabgar kowa sai dangin dangiro da abokan arziƙi masu kuɗi. Jininta dai ta datse zumunci da rashin mutumci saboda ita tana gidan mai kuɗi. Yau ga ranar ƴan uwa amma babu wanda zai nema ya taimaka masa da kula da ita. In ya ɗorawa Zahra wankin kashi da fitsarinta ba ƙaramin rashin adalci hakan zai zama ba. Yau da gobe sai Allah. Gashi Mamin a baya bata nuna mata ƙauna saboda akwai wadda ta so ya aura. Wannan tunanin yasa shi fasa neman Salwa ta tafi. Ita ce mace kuma dolen Mami. Zai saka mata ido kafin ya sami wadda zai dinga biya.

Shawarar da ya yanke ya faɗawa Zahra. Ta bashi goyon baya da alƙawarin za ta dinga taimakawa ita ma.

"Ni ban san me yasa ka damu da komawarta ba tun farko. In don Taj ne ina ganin yanzu ai ta haƙura."

"Ke dai ayi shiru kawai. Allah Yasa ta haƙura ɗin. Ni dai duk ranar da ta fita daga gidan nan idan bana nan ki kirani."

"In sha Allah"

Taɓe baki Salwa tayi. Zancen ba a bayan idonta ake yi ba. Tana kitchen kuma suma sun san tana jinsu. Ba za ta nuna ɓacin rai don an barta zaman jinyar Mami ba. Za ta kwantar da kai ta bi Ahmad sau da ƙafa domin zamanta a gidan shi ne babban hujjarta da rufin asiri a Kano. Kafin nan dai da lokacin aurenta da Taj dole tana buƙatar gidan zama. Idan yaso in tayi aure sai taga wanda Ahmad zai ɗorawa aikin Mami idan ba Zahran ba.

Wayar Ummi ta sake kira bata samu ba. Ta doka tsaki ta ajiye wayar ta cigaba da wanke wanke.

***

Tsaye tayi a ƙofar banɗakinta dake cikin ɗaki tana kallon sauyin da gadon ya samu. Taj ya canja bedsheet ya gyare gadon. Halin da take ciki na ciwo da zazzaɓi bai hanata yaba kyawun setin american bedsheet da duvet ɗin da ya shimfiɗa ba. Navy blue da red flowers ne a jiki wanda kalar farkon ta dace da ta labulen ɗakin nata. Ita kam me za ta ce da Inna? Duk wani abu da uwa za ta yiwa ƴa ita ma anyi mata na gata. Akan sayen zannuwan gadon Inna da kanta ta kira Yaya ta faɗa mata sun saya a wadace. Indai ba akwai wanda ta tanada ba tuntuni to kada ta sayawa Hamdin wasu. Bayan wannan wayar sai ta turo aka kawo guda shida. Duvets biyu, normal bedsheets huɗu ta ce a rabawa Sajida da Zee. Sajida ta dinga murna kuwa da taga sunan dake jikin ledar.

"Ni fa a instagram nake following ɗinta (@nafs_beddings). Ashe zan ga kayanta zahiri."

"Kyau garesu ko me?" Cewar Zee da bata san murnar me take yi ba.

"Kyau ma ai faɗar ɓata baki ne. Ki je shafinta ki gani. Ina maganar quality ne. Ki taɓa ki san kin haɗu da kayan ƙwarai ba jabu ba. Yadin sam ba ya tashi ki ga yayi kurajen nan kamar pimples a fuskar budurwa."

Hamdi bata manta yadda su ka dinga dariya ba. Sai yanzu ta gane ashe dai da gaske ne maganar Sajida. Zama tayi tana shafa laushin duvet ɗin tana jindaɗin mallakarsa. (Kamar kullum ni ɗin ganau ce don har baby Ahmad na sayawa baby set a wajenta. Kayanta speak for themselves. Don Allah ku nemi Nafisa Tofa 08034581454 ku rabu da jabon zannuwan gado.)

Kwanciya tayi ta rufe jikinta. Bata ji motsin Taj ba. Ta dai yi tunanin ƙila yana nasa ɗakin. Gara ya yi zamansa a can. Bata son abin da zai sake janyowa su haɗa ido. Tashinta da yayi da asuba ma don babu yadda za ta yi ne. Zancen zuci ta cigaba da yi wanda gabaɗaya ya ƙare akan baƙuwar rayuwar da ta tsinci kanta a ciki jiya. Taj ya nuna mata so da ƙauna kamar ya haɗiyeta. Wata zuciyar ta ce mata ya kuma saka ki kuka kamar zai ƙarar miki da hawaye ba.

Tunaninta na kaiwa daidai nan ya buɗe ƙofar da sallama ya shigo. Da sauri kuwa ta sake yin ƙasa da kanta ta rufe ko ina.

Taj murmushi ya yi ya je bakin gadon ya soma buɗe lulluɓin da tayi. Bata bari ya gama ba ta kama duvet ɗin da nata ƙarfin. Sai ya saki, ya hau gadon daga gefenta ya turata ciki ta hanyar matsawa yana rufa shima.

"Matsa min, matsa min" ya dinga faɗi har su ka koma tsakiyar gadon sannan ya daina turata.

"Me ya hana ki bacci? Ko jirana kike yi?" Ya yi maganar yana rungumota gabaɗaya a ɓangaren damansa.

Hamdi ga tsoro ga tsiwa, ta haɗa biyun ta ce, "In jira ka kayi min me?" Da rawar murya.

Taj ya yi dariya "Hamdiyya matar Malam Tajo. Maida wuƙar ni ba wani abu nake nufi ba."

"Waye kuma Tajo? Ɗan uwanku ne?" Ta harare shi.

"Ni ne shi, shi ne ni." Ya nuna kansa.

Hamdi ta yamutsa fuska "A'a gaskiya."

"To ke ce shi, shi ne ke?"

"A'a fa." Ta ƙara da tura baki.

Abin ya burge shi ya kwanta a jikinta "To ya abin yake?"

Murmushi tayi na kunya "Ni ce kai, kai ne ni...shi kuma Tajo bamu san shi ba."

"Taj ɗin ma in kin ce baki san shi ba sai a siyo rago a saka min sabo." Ya faɗi maganar da wani shauƙi dake kwasarsa saboda shagwaɓar Hamdi "duk yadda kike so haka za a yi Mrs Happy."

Wani sabon shafin ya so a buɗe ta ce sam bata san zance ba indai ba sumar da ita zai kuma yi ba. Ya dinga yi mata dariya. Su na ƴar hirarsu har bacci ya sake kwashe su. Ba su su ka farka ba sai da aka kira Taj.

Ƙanwarsa ce wadda a jerin haihuwarsu bayan Kamal sai shi sai kuma ita Rawda. Abincin amarya da ango na sati guda ta ɗauki nauyi saboda gidanta yafi na kowa yin kusa da na Taj. Kullum safe, rana da dare take turo yaron gidanta ya kawo a babur. Amarya da ango su ka sake samun lokacin shaƙuwa da sabo da juna.

Taj ya bar Happy Taj a hannun yaransa. Sai Abba Habibu dake zuwa amma ba kullum ba. Taj yayi yayi ya ɗauki hutu amma yaƙi.

Wata irin soyayya Taj da Hamdi suke yiwa juna wadda bata da shamaki ko basaja. Sak su ka fitowa juna tun farko, shiyasa alaƙar tasu tayi saurin ƙulluwa. Jin junansu suke yi tamkar tare da soyayyar juna su ka tashi. Ga Taj gwanin zolaya wadda a sati gudan nan Hamdi ta koya. Duk baƙon da ya shigo gidan sai ya fita da murmushi saboda nishaɗin da zai samu daga masoyan.

Abu biyu ne su ka so damun Taj amma dalilai sun sa basu yi tasiri ba. Na farko tafiyar su Kamal Umra bagatatan ko haɗuwa basu yi ba. Yayi mita kuwa kamar ya ari baki. A ranar da su ka tafi wadda ta kasance kwana biyu da tarewar Hamdi, da yamma ya tafi gida bayan wayar sallamar da Kamal ya yi masa daga cikin jirgi.

Cikin farinciki su ka gaisa da su Umma kafin ya hau sama da aka yi masa iso wajen Alhaji. Gaishe shi ya duƙa yayi Alhaji ya miƙa masa hannu yana girgiza kai.

"Kai ka san ba haka nake gaisawa da ƴaƴana ba."

Da sauri Taj ya tashi ya ƙarasa gaban Alhaji ya miƙa masa hannu. Alhaji yayi murmushi sannan su ka zauna.

"Ina matar taka?"

Kai a ƙasa yana susar ƙeya Taj ya ce "tana gida. Ta ce na gaishe ku."

"Ina amsawa idan da gaske kake."

Rantsuwa Taj ya fara sai yaga Alhaji yana murmushi. Da alama dai yayi furucinsa da zolaya ne. Sannan babu shakka yana sane da abin da ya yiwa Abba Habibu ya ɓata ran Hamdi. Ba dai zai ɗauko zancen ba saboda ba shi ya kawo shi ba. Yana da mahimmancin da shi ma zuwa da zama na musamman ya dace da shi.

"Alhaji maganar Kamal ce ta kawo ni."

"Kayi aure Taj. Bai kamata ka zauna kana ƙunƙuni don ya tafi ba tare da kai ba. Ya dace ka fara sanin ragamar rayuwarka da ta ƴar mutane ce a wuyanka yanzu. Ba dole bane Kamal ya daidaita tafiya da kai ba."

"Ba haka nake nufi ba" cewar Taj

Tausayi ya bawa Alhaji yadda ya yi maganar. Shi kuma ya katse shi ne kawai saboda baya son hankalin Taj ɗin ya kai ga abin da ake ɓoye masa.

"To ina jinka."

Shiru Taj yayi. Alhaji ya sami kansa da yin murmushi. Yayi matuƙar kewar Taj da halayansa. Idan kayi masa faɗa alhali bai yi laifi ba, haka zai yi ta marairaicewa sai ka koma rarrashinsa ko babu niyya.

"Ashe baka canja hali ba har yau? Mijin aure fa kake."

"To ai ba maganar tafiyar nazo yi ba. Duk da dai naji haushi. Ko ba a je dani ba da sai a faɗa min. Ɗan Adam ba ya rasa buƙatu a wajen Allah."

"To ka roƙa mana a inda kake. Allah Yana ko'ina."

"Amma dai ba kamar idan ana shafa Ka'aba ana ambaton suna na da buƙatuna ba ko Alhaji."

Sake faɗaɗa murmushi Alhaji ya yi. Ya dubi Taj ya ce "welcome home."

Tsabar daɗin da Taj yaji bai san lokacin da koma kusa da Alhaji ya rungume shi ba. Alhaji ya gama basarwa amma a ransa daɗi yake ji.


Da ya nutsu ne ya faɗa masa ainihin abin da yake tunani. Yana magana Alhaji shiru kawai yayi. Daga dawowa gida, bayan kwana biyu da tarewar matarsa ya zai yi idan yaji ciwon da yake damun ɗan uwa mafi soyuwa a gare shi?

"Baka yarda da ilimin Dr. Mubina ɗin bane har kake tunanin wani ciwon ne yake damunsa?"

"Ba haka bane Alhaji. Ban sani ba ko idanuna ne amma har wani kumburi naga yayi rannan. Yanayin bai yi kama da ƙiba ba."

Shi da baya son ɓoye abu bai san dalilinsa na son bawa Taj ɗan lokacin samun farincikin aurensa ba kafin ƙwai ya fashe.

"Yanzu mece ce shawararka?"

"Idan kun tafi don Allah ka tilasta masa zuwa asibiti. Idan da kai ne dole zai je ayi masa thorough check up."

Alhaji ya yi murmushi don ya ɓoye halin da yake ciki.
"In sha Allahu zamu je."

"Nagode." Ya dinga faɗi har ya fita. A zuciyarsa yana mai fatan Allah Yasa babu komai.

To tafiyarsu Alhajin ne kuma sau biyu ya sake samun kansa a yanayi na ɗaukewar jin ƙamshi da ɗanɗano. A na biyun da ƙyar ya iya ɓoyewa Hamdi ya shiga ɗaki yayi ta bulbula turare kafin daga baya abin ya daidaita. Ranar da ya tasar masa na ukun kuwa ana gobe za su yi sati ne. Saboda tsabar tashin hankali, yadda yaga rana haka yaga dare. Cikin tsananin kiɗima ya zame jiki daga wajen Hamdi ya koma falo ya kira Kamal a waya.
RAYUWA DA GIƁI 33





Batul Mamman💖






This page is sponsored by spicesbyMrsghaleetk....yep, MRS GHALEE TK. Nace ba, wai kina cikin masu cewa girki da spices baya daɗi? Ko kuwa kin saba saya kina bari ya siƙe a kitchen saboda baki gane ɗanɗanon da yake bayarwa ba?

Albishirinki, Mrs Ghalee TK dai za ta yi Ramadan promo. Dama ce ta samu gareki wajen sayen ingantattun kayan girki masu tallafawa cefane musamman a wannan marra ta tsadar kayan abinci. Ke dai ƴar uwa, harma da ɗan uwan da ya saba taimakawa iyayensa ko matarsa, ko kuma mai son burge iyali, ku yi tanadi don Mrs Ghalee TK ta zo da rangwame domin gyara tukwanenku. Ku sai ku garzaya ku nemeta akan wannan layin ta manhajar whatsapp ko kiran waya 08032834178.

Taku ce Batul Mamman, ganau akan kayayyakin da nake tallata muku.




***

A cikin yanayin ciwo da gajiyar jiki Kamal ya buɗe idanu ya miƙa hannu zai ɗauki wayarsa. A gadon asibiti yake inda yake samun kulawa ta musamman. Da yake dokar asibitin ba a zaman jinya, shi kaɗai ne a ɗakin. Alhaji da su Ahmad suna hotel kusa da asibitin. Tafiyar just ƙafa ke kawo su. Tare dashi su ke wuni sai takwas na dare idan an buƙaci duka baƙi da masu ziyara su fita sannan su ke tafiya. Kwanaki goma aka bashi ya gama shan magani da allurai kafin a fara dialysis.

"Happy lafiya dai ko?" Ya ce cikin bacci da firgici domin kuwa ukun dare harda kwata lokacin.

Kamar an tsunkuli Taj ya ɗaga kai ya kalli kyakkyawan agogon bangon falon. Baki ya buɗe gami da girgiza kai.

"Don Allah Happiness kayi haƙuri. Kasan Allah ban duba time ba. Ashe past one. A nan uku ta wuce ko?"

Kamal ya gyara zama ya ce "Eh...mene ne ya faru? Haka kawai ba za ka manta lokaci ba."

"Gobe sai muyi magana in sha Allah. Am very sorry." Taj ya ce har zuciyarsa.

"Taj" Kamal ya kira shi da ɗan ƙarfi "me ya faru?"

Roƙonsa Taj ya fara yi akan ya jira safiya don har ya katse kiran amma ya sake kiransa. Su ka ɗan yi ja'inja ɗinsu sannan Taj ya faɗa masa abin da yake faruwa dashi game da ɗaukewar ɗanɗano da jin ƙamshi ko wari wasu lokutan.

"Zuciyata tana bani Covid ce. Nayi browsing naga ɗaukewar sense of smell da taste suna cikin symptoms ɗinta. Ni bana mura amma bayan magrib ina ƙirgawa sau bakwai Hamdi tayi atishawa."

Kamal yayi ƴar dariya "sannu Doctor."

Taj ya ɓata rai "Happiness its not funny."

"Na sani. Shi yasa nake mamaki da kana zaune a gida ka yankewa kanka cutar dake damunka."

Murmushi ne ya kama shi. Tabbas asibiti ya kamata yaje amma fargaba ta hana. Ba kuma kansa yake jiyewa tsoro ba. Idan ta tabbata yana da corona shikenan Hamdi ma ta samu. Daga tarewa ya haɗata da ciwo.

"Gobe zan je in sha Allah. Thank you and sorry."

Sai da safe suka yiwa juna. Kamal ya ce yana jiran jin sakamakon idan ya dawo daga asibitin. Da ya koma ɗakin a dunƙule waje guda ya sami Hamdi. Ta dawo tsakiyar gadon tana baccinta hankali kwance. Sama ya kalla ya sake yin addu'ar da ya wuni yana yi. Allah Yasa ba covid bace. Idan kuma ita ce yana fatan Hamdi bata samu ba. Sai dai abin da kamar wuya. Yadda su ke manne da juna ana amarci ai taimakon Allah ne kawai zai hanata kamuwa. Kwanciya yayi a can gefe. Ko minti biyu bai yi ba yaji Hamdi a jikinsa ta ɗora rabin kanta a ƙirjinsa. Wani ɗan murmushi yayi ya sake shige mata har yayi bacci.


***

Yawan kallon wayar da Kamal yake yi ne yasa Alhaji tambayarsa kira ko saƙon wa yake jira. Shi kuwa ya faɗa masa yadda suka yi da Taj a waya.

"Result ɗin nake dubawa ko ya turo."

Shiru Alhaji yayi na wani lokaci yana tunani kafin daga bisani yace idan ya faɗa masa yana son ji shi ma. Zuwa la'asar kuwa bayan Taj ya turo ya faɗawa Alhajin cewa ba corona bace.

"To Alhamdulillah. Ince dai bai hanaka faɗawa kowa ba? Zan kira shi nayi masa ya jiki."
Da jindaɗi Kamal ya ce Taj bai hana ba.

Alhaji bai tashi kiran Taj ba sai bayan sun koma masaukinsu ya shiga ɗakinsa. Bayanin yadda yake ji ya buƙaci ya yi masa.

"An baka magani?"

"Eh Alhaji. Sun ce stress ne kawai"

"To Allah Ya ƙara lafiya. Ciwon da ya shafi harshe da hanci a wajenka ba abin ɗauka da wasa bane duba da irin sana'arka. Ka mayar da hankali wajen shan magani."

Taj ya yi godiya yana cike da murnar wannan kulawa ta Alhaji.

*
Wando ne tight ruwan zuma a jikin Hamdi. Jikinsa yana da wani irin laushi ga rashin nauyi. Ta ɗora shirt ɗin Taj baƙa mai maɓallai a gaba da dogon hannu. Maɓallan gaban guda huɗu ne kaɗai a ɓalle ta bar na farkon. Hannuwan kuwa tsayawa tayi naɗe su har dantsen hannu. Ga gashinta da bata taje ba ta tattara tayi packing bai shige sosai ba. Fuskarta ko ɗigon kwalliya babu. Sai ƙamshi kamar a ɗauketa a gudu don daɗinsa.

Duka wannan saurin shirin saboda sun gama sati yau za ta fara shiga kitchen ne. Ta kwana tana tsara me za ta dafa saboda baƙin da zasu yi daga gidansu Taj. Shi kuma kawai yana tashi ya ce

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login