Showing 165001 words to 168000 words out of 182238 words

Chapter 56 - RAYUWA DA GIBI Book Complete By Batul Mamman.txt

Ya wuce. Komai ya wuce in sha Allahu."

"Ba za ka bari na baka haƙuri ba?" Lura yayi Taj ya yiwa Hamdi alama suna shirin barin wajen ya koma gare su "kada ku tafi."

Abba Habibu ya tsaya tare da yaran nasu suna kallon Alhaji.

"Ƙaddarar auren ku ita ta kawo mu wannan ranar saboda haka ina so ku shaida kuma ku taya ni bawa Habibu haƙurin dukkan wani abu na rashi daɗi komai girma ko ƙanƙanta da na taɓa yi masa."

Da rashin jindaɗi Abba Habibu ya ce "Amma na ce ya wuce. Ban riƙe ka ba wallahi."

"Kayya dai Habibu. Zuciya tana son mai kyautata mata ne. Abubuwan da nayi ko bakin ka bai faɗa ba na san dole rai ya sosu."

Murmushi kawai Abba Habibu ya yi ya ƙara maimaita cewa komai ya wuce. Su ka koma ɗakin Yaya tare. Alhaji gabaɗaya ya kasa sakewa duk yadda Abba Habibu da Yaya su ka yi ta ƙoƙarin nuna babu komai. Hakan yasa su Hajiya tsangwamar kansu su ma.

Tun abin yana burge Taj har dai ya ƙosa su bari haka nan. Alhaji yana ta maimaita ban haƙuri. Abba Habibu yana ƙoƙarin nuna komai ya wuce. Iyayen su mata kuma suna taya mazan su.

"Alhaji da dai kun bar abin nan haka kun fara tunanin gaba. Misali kaga kai sai kayi fama da su Daddy (Yaya Babba) kafin su karɓi uzurinka na ƙin faɗa musu ciwon Happiness da wuri. " Ya juya ya kalli Abba Habibu "su Zee za su iya saurin fahimta idan ka kira su amma Inna Luba dai ban sani ba ko za ta yarda ba sayar da ƙodar Yaya kayi ba." Ya mayar da duban sa ga su Hajiya yana sosa tsakiyar kai "yau dai ya kamata ku kikkira naku ƴan uwan ku ma ko kuwa?"

Ɗakin ya yi tsit. Taj ya harba bomb ya barsu da jiran tashin sa. Wayar da basu yi tunanin kira ba a tsukin kwanakin baya sai yanzu su ke tsoron abin da zai biyo baya. Tabbas ƴan uwan kowannen su za su ji babu daɗin ɓoye musu zancen nan ba.

Da ya kula attention ɗin su ya samu don irin su Inna har an ɗauko waya sai cewa ya yi "amma dai kada ku kira yau domin tunda magriba ta wuce a gida dare ya riga ya yi. Zancen zai iya hana wasu bacci. Ga masu BP da ƴan rikicin tsufa."

Mama dai hannu ta ɗaga za ta kai masa duka ya zille da sauri yana dariya. Su ma ɗin su na son yin dariyar amma babu hali. Zungurin da ya yi musu akan wayoyi masu mahimmanci da ya kamata su yi duk ya ɗaga musu hankula.

"Zo mu tafi Hamdi. Its late and I am tired."

"Haƙƙun! Sannu mai mata. Wato ta zo ku tafi ko? Kai babu ruwan ka tunda mu tayar mana da namu BP ɗin kuma za ka hana mu bacci ba."

Umma ce tayi maganar tana harararsa sama da ƙasa. Dole kowa ya dara kuwa har Yaya akan gadon ta. Daga dai su ka yi sallama domin su ƙara raguwa. Abba Habibu kaɗai za a bari. Su Alhaji gabaɗayan su kuma su ka fito tare.

Agogo ya nuna ƙarfe uku da kwata na dare. A muhalli uku bayin Allah suna kan abin sallah cikin ganawa da Ubangiji SWT. Abba Habibu na zaune hannuwa a sama bayan ya idar da nafila yana mai ƙasƙantar da kai cikin neman yardar Allah. Fatansa Yaya da Kamal su koma gida da ƙafafun su. Sai kuma ya miƙa dukkan al'amuransa, na iyalinsa da na dukkan wanda mu'amala ta haɗa su komai ƙanƙanta ga Allah SWT.

A cikin ɗakin Alhaji ma shi kuka yake yi sosai yana roƙon gafarar Sarkin Sarakuna SWT.

Hakan kuma take tsakanin Taj da Hamdi. Gajiyar da su ka kwaso bata hana su raya daren da sallah ba domin kyakkyawan fata akan gobe.

A ɗakin Kamal, idanu ya buɗe tar cikin hayyacinsa. Tashin farko ya kai hannunsa ciki ya tabbatar akwai yanka alamun an yi masa aiki. Bai san lokacin da ya runtse idanunsa ba yana faɗin

"Allahu Akbar. Allahu Akbar. Allahu Akbar"


***
RAYUWA DA GIƁI 39






Batul Mamman💖



Allahumma Balighna Ramadan...AMEEN

Saƙon ta'aziyya ga ƴar uwa kuma shugabar mu ta WOMEN OF WORDS wato Hassana (Sanah) Sulaiman Ismail Matazu bisa rashin mahafinta da tayi. Allah Ya jiƙan shi. Ya gafarta masa. Allah Ya sa ya huta. Ya baku dangana. Amin






Idanun Salma tsilli-tsilli kamar an kasa gurjiya a faranti. Irin yanayin nan da akan samu a wajen munafukin da ƙaryarsa ta ƙare. Sam ta rasa gane me ma ya kamata tayi tun bayan mahaifinta ya sanar da ita baƙin labarin da a wajenta gara mutuwa sau dubu a kan shi. Wai an ɗaura aurenta da Alh. Usaini.

"Kaiiiii. Wallahi ba zan yarda ba. Ni ba zan zauna da shi ba ko sama da ƙasa za ta haɗe. Taj nake so kuma shi zan..."

Kaf taji saukar duka akan laɓɓanta. Dukan ya shige ta kuwa domin babu arziƙi tayi shiru sai zugi a bakin.

"Wallahi Salwa idan na ƙara jin sunan Taj a bakin ki zan iya tsine miki. Shashashar banza wadda bata san ciwon kanta ba."

Baki za ta buɗe ya juya bayan hannunsa a fusace zai kai mata mangara dole ta fasa yin maganar.

"Ko mata sun ƙare kina tunanin Taj zai aure ki? Ke ko yana son ki ina mai tabbatar miki Alh. Hayatu ba mahaukaci bane. Ba zai taɓa amsar ki a matsayin suruka ba."

"Na ji amma don Allah ka kashe auren nan. Ba zan iya zama da mushiriki ba"

"Har kura za ta ce da kare maye? Ba ki ji kin bawa kan ki dariya ba Salwa?" Ya faɗi yana yi mata kallo irin na wadda ta rainawa kanta hankali.

Tashi ya yi ya kalli ɗakin hotel ɗin yaji wani abu ya sake turnuƙe masa zuciya. Wato dai da gaske da bahaushe ya ce son zuciya, ɓacinta. Ko a tatsuniya shi bai taɓa jin an ɗaura aure a ɗakin hotel ba sai da shi da kansa ya karɓi sadakin ƴarsa. Yadda abin ya kasance ya fi kama da almara.

*

Ɗazu da azahar mahaifin Alh. Usaini ya je hotel ɗin da su ke shi da Salwa. He got the shock of his life lokacin da ƙanin Usaini ya ƙwanƙwasa ƙofar su ka ji muryarsa yana cewa.

"Ƙar ki taɓa ƙofar nan. Kada ki buɗe."

Ransa kuwa ya sosu fiye da tunani. Dama can barazana yayi a reception har aka rako su ɗakin. Saboda haka sai ya yi wa ma'aikacin hotel ɗin inkiya da hannu ya yi magana.

"Yallaɓai baƙo ne da kai a ƙasa."

Da sauri Alh. Usaini ya ce "kada ka bari ya hawo gani nan saukowa. Ƙanina ne. Dama mun yi waya na faɗa masa ya same ni a nan ɗin."

Ya ɗaga yatsa ya gargaɗi Salwa "zan fita kuma na rantse da Allah idan ki ka min halin jakancin nan naki ki ka fito sai na ɓaɓɓalla ki. Wawiya kawai. Dalla can gafara in wuce."

Ta murguɗa baki tana yatsine fuska "jaka tana can gidan jaki mai furfura."

'Yau kuma jakuna mu ka koma' Baban Alh. Usaini ya jinjina kai yana zancen zuci.

Ran Alh. Usaini ya ƙara ɓaci sosai ya ɗaga hannu ya zabga mata mari.

"Iyayena ki ke zagi Salwa? Iyayena?"

Kumatu ta fara riƙewa ta ce "Ni ka mara?" Sai kuma ta cakumu wuyansa "wallahi ba ka doki banza ba. Yadda kake jin kana da gata nima ina da shi."

"To gatan naki ya zo yanzu don uban mutum."

Daga nan sai sautin duka da kukan Salwa da kuma maganganun Alh. Usaini. Baban ya nuna wa ma'aikacin hotel ɗin lallai ya buɗe kafin ayi kisan kai. Da yake tsoron afkuwar ɓarnar tafi yawa akan privacy ɗin costumer, dolensa ya buɗe. Su ka yi mummunan gamo. Tsananin fushi da ɓacin rai ya sa Alh. Usaini yiwa Salwa dukan biredi. Ita ma kuma ta samu nasarar jifansa da abubuwa don har goshi ta kumbura masa.

Sandarewa ya yi a lokacin da idanun sa su ka sauka cikin na mahaifinsa da aka buɗe ƙofar ɗakin. Ya saki Salwa a gigice kamar wanda ya ɗauki garwashi ya kama rantse-rantse.

"Wallahi biyo ni tayi Baba. Duk abin da ka ke zato ba haka bane. Sam ni ba na harkar mata." Ya sassauta murya sosai "Salwa faɗa masa gaskiya. Ai babu komai tsakanin mu ko?"

Maimakon ta faɗi gaskiya sai ta zaɓi amfani da wannan damar. Zubewa tayi a ƙasa ta kama kuka.

"Mene ne tsakanin ku?" Baban ya fara tambayarta sai ya fasa ya dubi wanda ya rako su "kwanan su nawa a nan?"

"Kwana uku ne."

"Shike nan. Kana iya tafiya."

Bayan ya fita Baban Alh. Usaini ya buƙaci Salwa ta bashi numbar wani nata su yi magana. Tana jin haka idanunta su ka raina fata, ta kasa motsawa. Sai ya kalli ɗansa. Yana iya ganin tsananin tashin hankali a tare da shi.

"Ka karɓar min numbar wanda zai zo ya karɓeta ta koma gida."

Jikinsa na rawa ya tashi ya buɗe handbag ɗinta ya ciro wayarta. Wayar ma a kashe sai da ya kunna sannan ya bata don ta buɗe wayar.

Jikinta ya yi la'asar don ta kula tsoron babansa yake yi shi ne ta ce "Ka bani abin da nake buƙata in tafi da kaina."

"Ai baki isa ba. Wallahi gara a zo a ɗauke ki in san na rabu da ƙaya."

Tsawa taji daga sama kafin ma ta sake yin gardama daga babansa
"Ke! Bani number na ce yanzun nan. Ki tabbatar wadda za ki bani mai shiga ce."

Da ka ta karanto masa numbar Babanta saboda Ahmad dai baya nan sannan bata ga alamun za su wanye lafiya ba idan tayi ƙarya. Waje ya fita da ya yi dialing numbar. Salwa ta matsa kusa da Alh. Usaini kafin ya dawo.

"Kaga ka bani abin da nake nema na tafi tun kafin ya dawo. Ban san me yake shirin yi ba kuma ba na burin sani."

"Hummm...kin makaro. Ƙaryar da ki ka yi masa da alama ke za ki kwana a ciki don na san dole ya kira baban ki a zo a ɗauke ki."

Wajen rabin awa ya share yana wayar kafin ya dawo. Umarni ɗaya ya basu kafin ya fita.

"Zan dawo gobe in sha Allah. Ina fata idan na zo na same ku tare. Idan ka bari ta tafi Usaini to ka tabbatar babu ni, babu kai wallahi."

Yana gama magana su ka fice. Alh. Usaini ya ƙulle ƙofar ya dinga naushin bango kamar mahaukaci. Salwa jiki na ta tsuma ta ɗora hannuwanta akan kunnuwanta tana hawaye. Gabaɗaya a tsorace take kuma tayi imani motsin kirki idan tayi sai ya sake jibgarta.

*
Ko awa guda ƙwaƙƙwara Abban Salwa bai iya sake yi ba ya biyo hanyar Kano tare da ƙannenta. Saboda munin labarin da ya samu sai ya kasance ko murnar ganinta da aka yi bai yi ba. Mutumin da ya kira shi ya faɗa masa cewa ya same su da ɗansa su na rigima harda doke-doke. Shin yaushe lalacewarta ta kai haka ba tare da ya sani ba? Yanzu ya ƙara yarda duk wanda ya sayi rariya dole ya ga zubar ruwa. Cikin dalilai huɗu da Manzon Allah SAW ya hori musulmi da aure, guda ɗaya tal ya duba lokacin auren Mami wato kyau. Ƙwarai ta haifa masa kyawawan yara abin nunawa ta wannan fannin. Amma a halin yanzu hatta mazan ba wai ya sami yadda yake so bane daga gare su. Kawai dai ana cikin yanayin da babu gara ba daɗi.

Takwas da arbain na dare a Kano tayi musu. Ko masauki bai nema ba ya kira Baban Alh. Usaini. Nan ya faɗa masa sunan hotel ɗin ya ce ya jira shi zai taho shi ma yanzu. Da su ka haɗu sun jima su na tattaunawa game da halin ɗan yau da abin da son zuciya ke kawowa. Baban Alh. Usaini shi ne ya kawo shawarar lallai a ɗaura musu aure. Wannan ne zai sa har ƴan baya ma su shiga taitayinsu.

Matsanancin tsoron da ya kama Salwa da Alh. Usaini a yayinda iyayensu da ƴan uwan su su ka shigo ɗakin da su ke ba zai faɗu ba. Banda ƙannen Salwa biyu akwai wasu biyun na Alh. Usaini da Babansa ya taho tare da su.

*

"Aure???"

Salwa da Alh. Usaini su ka yi tambayar da sun riga sun san amsarta ga iyayensu a lokaci guda. Kamar ba da mutane su ke ba. Babu wanda ya tanka musu. Sai ma Limamin Masallacin Khamsa Salawatin kusa da hotel ɗin da aka yi wa iso ya shigo ya zauna. Kafin wani lokaci ɗakin ya kasance babu masaka tsinke a dalilin mutanen da su ka shigo ganin ƙwaf. Labari ya bazu tun daga reception za a ɗaura aure. Sai ga mutane su na buɗe ɗakunan su suna tahowa kallo. Video kuwa harda masu yin live a social media handles ɗin su. Salwa sai wani ɗakin aka shigar da ita. Abu kamar almara. Aka ɗaura aure bisa sadaki naira dubu hamsin lakadan tsakanin Salwa hauka mai son ma so wani ƙoshin wahala da Alh. Usaini shugaban ƴan hassada da baƙinciki.

Aure ne wanda iyaye su ka yi alƙawarin yin baki ga ƴaƴan nasu idan su ka kuskura su ka rabu.

Bayan an watse ne Abban Salwa ya miƙa mata sadakinta a hannu. Shi ne take ta roƙo da magiyar ya yi haƙuri ya sa a sauwaƙe mata.

"Aure an yi kenan in sha Allah. Daga nan in kun fita ku yanki daji ku fara bokanci ko bori tunda silar haɗuwar ku kenan."

Kalaman sa sun yi mata zafi. Yanzu kuma bokanci yake kira mata kamar ba ƴar cikinsa ba?

"Daddy ni ce kuma zan yi bokanci?^"

"Meye a ciki? Boka mushiriki, mai zuwa wajen boka ma mushiriki abu na Ɗanjuma da Ɗanjummai."

Su na ji su na gani iyayen su ka tattara su ka watse abin su bayan dogon gargaɗi akan dole su zauna tare. Su ka tafi tare inda Baban Alh. Usaini ya ce yau a gidansa za su kwana. Sannan gobe zai kira duk wanda ya dace ya san da auren domin su gabatar da junansu a gaban shaidu.

Salwa kuka kamar ranta zai fita, Alh Usaini ko kallonta bai tsaya yi ba. Ya riga ya yi wa kansa alƙawarin zama da ita amma fa sai ta ɗanɗana kuɗarta. Son da yake yiwa kuɗin babansa bai kama ƙafar tsanar da ya yi mata ba. Ita ta ja masa komai. Ta saurari hukunci.

***

Gaba na faɗuwa Taj ya kama ƙofar ɗakin Kamal. Hannun nasa har wani sanyi ya yi kamar ba a jikinsa ba saboda tararrabi.

Bayan asuba su ka taho asibitin saboda kira da su ka samu akan tashinsa babu sauran magagin allura. Kowa ya kama shiri sai Alhaji ya ce su yi haƙuri a dinga tafiya in batches.

"Kun gan mu unguwa guda idan mu ka cika musu wuri irin na jiya ba za su ji daɗi ba. Idan wasu su ka dawo sai wasu su tafi."

Ba dai haka su ka so ba amma sun san tsarin nasa shi ne daidai. Nan ba a jinya ba kamar tamu ƙasar ba. Sannan babu damar zama idan ba layin ganin likita ba. Maimakon su yi ta zama a mota ana jiran juna gara kowa ya kintsa a cikin nutsuwa.

Taj da Hamdi da iyayensu mata ne su ka fara tafiya tare da Alhaji. Idan sun gama sai Ahmad ya taho da wasu. A hanya aka dinga mayar da zancen yadda ƴan uwa da abokan arziƙi su ka ƙarbi zancen abin da ya faru da aka kikkira su a waya. Don tausayi, sosai an tausaya kuma an jajanta. Amma fa hatta waɗanda su ke matsayin ƙanne a garesu babu wanda bai nuna ɓacin rai akan shirun da aka yi ba. Alhaji Babba ma cewa yayi zai zo amma ba don su ba sai don Kamal da kuma Yaya da tayi musu halacci.

"Duk wannan bai isa ba Taj sai da ka san yadda kayi ka juya magana a wajen Jamila (Amma) ka sa ta kira ni tana yi min rashin kunya. Ƴaƴan arziƙi da rufin asiri aka san su."

Taj ya kyaɓe fuska har sai da Hamdi tayi murmushi. Kunya ta kama ta da ta kula ashe Mama na kallonta lokacin da take kallonsa ita ma.

"Yanzu Alhaji ni ba ɗan arziƙi bane? Kuma dai maganar gaskiya ku ne fa ku ka hana mu yin ƙarya."

Alhaji ya bashi amsa da cewa
"Eh, amma kuma duk mai hankali ya san akwai lokutan da ake yi wa gaskiya kwaskwarima don a sami zaman lafiya."

"Mix ɗin ƙarya da gaskiya fa kenan Alhaji."

"Dama duk tsayin shekarun nan bakin ka bai mutu ba Tajuddeen?"

Me za su yi kuwa banda dariya. Tun farkon sanin ciwon Kamal sai yau ne aka samu sukunin yin farinciki daga zuci ba iya fatar baki ba kaɗai.

Sai da su Alhaji su ka fito daga wajen Kamal sannan Taj ya taho zai shiga. Hamdi dama tun shigowarsu ta tafi wajen Yaya. Idan ƴan uwan sun sami nutsuwa za ta je su gaisa.

"Rufe ƙofar" Kamal ya umarci Taj bayan ya amsa masa sallama.

Wani babbasarwa Taj ɗin ya kama yi kamar bai ji shi ba. Kamal ya yi murmushi.

"Da dai ka rufe kada kukan garada ya cika wa mutane kunne."

"Kuka za mu yi kenan? Abin babba ne"

Taj ya rufe yana juyowa don duk a zatonsa Kamal wasa yake yi sai kawai yaga ya fashe da kuka. Kuka ba na wasa ba. It was coming from the dept of his heart. Kukan tsoro, ciwo da farinciki. Taj ya ja kujera ya zauna a gabansa. Bai ce masa komai ba sai da ya kula cewa ya fara jin sauƙin damuwarsa.

"Was it that hard?" Ya tambaye shi a yayinda yake miƙa masa tissue.

Nannauyan numfashi Kamal ya sauke sannan ya ce "it was. Taj I was so scared. Na zata zuwa yanzu na zama tarihi. Kai kuma ka shigo kana wani ɓata rai. Ni da cuta kai da shan kunu."

Abin da yake ransa ya amayar duk da ya yi matuƙar ƙoƙarin danne ɓacin rai a fuskarsa
"Kamal kayi min adalci? Ni ne fa. Haba!"

"Don Allah kada ka tuhume ni akan shirun da nayi. It was extremely difficult for me. Bana son ganin kuna yi min kallon tausayi ko a dinga koke-koke."

"Ka ga sharrin kallon movies ko? Wannan wane irin banzan tunani ne? Da kuma ka tafi fa? Happiness da ace ba ka sami kidney ba fa? Sai dai na zo na tarar da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login