Showing 54001 words to 57000 words out of 121577 words
samu lokaci tare da unders ɗin Yallaɓai na na yara kuma ba su taru ba ko sati biyu ba a yi da kawo musu wanki ba.
Bayan na gama haɗa kayan na saka su cikin ghana must go ɗin da daman saboda kai wanki ne in kuma za a dawo dasu a ciki ne a goge. Gyara ɗakin na fara saboda ya ɗan yi ƙura, sai na fara tunanin unders ɗin Yallaɓai duk sun yi datti ya kamata na wanke masa. Amman sai na duba ya na da sauran wankakku zan bari in Alhajinmu ya koma gida ya samu natsuwa sai na yi mana wankin. Allah ya sa ma ya na da su da yawa tun da in na samu kuɗi ina siyan masa da turaruruka in yi masa kyauta a matsayinsa na mijina.
Ban ma gama gyaran ɗakin ba na koma kitchen na wanke shinkafar na saka kafin ma ya tafasa saboda in ya jiƙu ya fi danƙo. Ƙara komawa ɗakin na yi na gama gyaran na ɗauko abin shara na share sannan na ɗauko towel ɗin goge na gege madubi da jikin wardrope ɗina tunda ya na da glass. Sai kawai na ji yau gwara na yi aikin gidan tunda ba ma nan kar na ba ma Saude wahala tuna haka ya sa na ɗau waya na kira Sauden tun da ni na siya mata wayar saboda matsala irin haka bayan mun gaisa na ce yau ta yi zamanta ba sai ta zo ba sai ta ce mini toh.
Ina tuwona ina aikina. Ban share falon farko ba saboda Yallaɓai na aiki amman gabaɗaya na share gidan na yi mopping sannan na turare gidan da turaren wuta na kajiji a burner.
Kitchen kuma ma bari sai na gama girki gabaɗaya. Sai da na tuƙa tuwon sannan Jidda ta taso ta na murza ido ta ganni ina fito da sabbin kolilina in da zan saka abincin.
"Ina kwana Umma."
Na waiwayo ina faɗin" Lafiya lau jidda. Ina Baby ba ta tashi ba ne?
Ta na murza ido ta ce" Ta na wajen Abba"
Sai na gyaɗa kai ina faɗin" Akwai ruwan zafi a flasks a saman dining ni da Abbanku mun ƙarya. "
Ta na kallona ta ce" Umma ba ki tashe mu ba to?
Ina kai kololin wajen sink ina faɗin" Na ga yau weekend sai na barku ku huta. In kun gama karyawan ki yi ma Baby wanka tare za mu fita. Gwammaja za mu kai ku ku zauna har dare."
"Umma ya jikin Alhaji?
Na ce mata da sauƙi ina ƙokarin fara wanke kololin sai ta ce in kawo kallonta na yi ina faɗin" Ki je ku karya. In gama aikin sai ki wanke sauran ki gyara mini kitchen ɗin" sai ta amsa da toh sannan ta wuce. Ni kuma bayan na wanke su na saka Towel na goge su tas sannan na kwashe tuwon a leda na ƙulla. Wajen guda goma na saka a kula sauran kuma guda huɗu na bar mana a gida in mun dawo mu ci ban ɗora miyan ba tunda har lokacin musabahu bai zo ba.
Ban ko kai ga barin kitchen ɗin ba sai ga Jidda da leda ta kawo min ina karɓa na kalle ta ina faɗin" Uncle Musbahu ya zo ne?
Sai ta gyaɗa min kai. Ijiye ledan na yi na koma ɗaki na sako hijabin na fito falo in da suke da Yallaɓai muka gaisa.
"Anty Sadiya ya jikin Alhaji? Yallabai ke faɗa min bai ji daɗi ba?
Sai na amsa masa shi kuma sai ya yi masa fatan samun sauƙi na amsa da Amin Amin nan falon na bar su na koma ciki Ina ce ma Jidda in sun gama karyawan ta gyara ɗakin su kafin ta yi ma Baby wanka.
Da ya ke miyar ba ta da yawa sosai ba ta ɗau lokaci ba tunda agushin ma soya shi kawai na yi. Naman kuma na rago ne akwai ƙashi ƙashi a jiki sai da na tafasa sannan na yi amfani dashi kafin ka ce me gida ya ɗau kamshi miya. Na gama ɗiban ma Alhajinmu miya na saka a kula har na haɗa shi cikin kwandon da za mu tafi dashi sai ga Yallaɓai ya shigo kitchen ɗin.
"Ni fa an gama cika mini ciki da ƙamshi. Me muka samu ne?
Ya faɗa ya na tsaye a ƙofar kitchen ɗin. Kallonsa na yi kafin na juya ina goge jikin gas ɗin da miya ya ɗan ɓata. Mirmishi na yi kafin na ce"Sai anjuma za ka ci na ka fa Yallaɓai."
Koƙarin shigowa ya ke yi na wurgar da abin hannuna na nufe shi ina turashi waje lokaci ɗaya ina faɗin" Mu je ka yi wanka lokaci na tafiya."
Ba shi da mafita haka na riƙa tura shi har cikin bedroom ɗin mu. Takardun hannunsa na karɓe ina faɗin" Mai wankin bai zo ba?
Ya na saɓule dogon wandom jikinsa ya ce"Sakarai ne. Na fa kira shi ya riƙa ce mini yana hanya amman sama da awa ɗaya bai zo ba"
Ina dariya na ce"Kai da Sabitu ba" saboda suna shan dirama shi Sabitu karya da saɓa alƙwari shi kuma Yallaɓai ba ya son mutum mai ƙarya da saɓa alƙwari. Su yi ta samun matsala kuma ko ya ce ba zai ƙara bashi wanki ba sai Sabitu ya yi ta magiya domin ya na samun alheri a wajen Yallaɓai.
Cikin side drower na ijiye masa takardunsa ina juyowa muka ci karo da Yallaɓai fuska na kwabe kafin in yi mgana ya rumgumeni ni kuma ina ture sa na ce"Ban yi wanka ba Yallaɓai."
"Nima ai ban yi ba. Kawai yau mu bar ta ranar tsami na duniya ne."
Ina dariya na rumgume shi ta baya ina ɗan dukan bayan shi mun daɗe a haka kafin mu saki juna hammatar shi na ɗaga tunda bashi da riga ina rufe baki kafin na ce"Yallaɓai na na bukatar shaving gaskiya."
Hannuwansa ya ijiye saman kafaɗata yana faɗin" Sadiya ta sangarta Yallaɓanta. Ki zo kawai ki yi aikin ki Madame.'"
Dafa kafaɗansa na yi shima ya dafani muka fara tafiya ina faɗin" Muje Tiolet na gyara mijina."
Kallona ya yi ƙasa ƙasa kafin ya ce"To wai da na ce ko ni na fara gyara ki anan ne a ciki kuma ke sai ki gyara ni?
Ina jin haka na sake shi na yi gaba ina faɗin" bar shi kawai. Na gode Cafinter"
Sai ya biyo ni yana dariya har ya na cewa" Wai kada mu yi ta asaran ruwa. Gwara mu haɗa aikin."
Ko juyawa ban yi ba na buɗe kofar tiolet na shiga bayan na yi addu'a shima sai ya biyo bayana zai shigo na ce" Yallaɓai addu'ar fa"
Sai ya koma da sauri ya yi sannan ya shigo ya maida ƙofa ya rufe zai yi mgana na masa alama da bakina na ja zif alamun ya yi shuru sai shima ya yi haka alamun ya kama bakin shi mirmishi na yi masa kawai Towel na zaro daga hanger dake sama na mika masa sai ya karɓa ya juya yazare gajeren wandon da ke jikinsa ya ɗaura towel ni kuma sai na ciro veet din a saman wajen ɗan dirowan ajiye su kayan wanka a cikin sink na ce ya shiga ya zauna kamar dai yadda muka saba.
Ni na shafa masa a ƙasan sa da hammatarsa sannan bayan minti biyar ya yi na kwashe na goge wajen sannan na wanke masa. Tare muka yi wanka ranar bayan na chuɗasa nima sai ya chuɗani muna yi muna ɗan wasannin mu da muka saba cike da so da ƙauna muka fito dukkanmu ɗaure towel shi a kugunsa ni kuma asaman ƙirjina.
Yallaɓai na fara tayawa ya shirya cikin shadda mai ruwan ƙasa domin ya ce min suna da ɗaure aure na wani abokinsu da suka yi secondary tare zai ƙara aure.
Ina saka masa link ina faɗin" Har da Uncle Abba zai zo daurin auran?
"E. Har da ma Tariq. Muhammad Bello ai ajin su ɗaya ma da Tariq lokacin muna makaranta."
Sai na jinjina kai kafin na ce"Abokan ku sun fara biyu kuma kuna hanya kenan"
Ya na yar dariya ya ce"Wasu ma ko ɗayan ba su ijiye ba. Irin su kawu ba. Da wani Salihu bala wallahi sun zame mana tazuran kawai. Yau ina ga yau sai sun sha caccaka tun da kaf mate ɗin mu za su zo wajen ɗaurin auran nan "
Ina dariya na ce"Kar a taɓa min kawunaa. Ina nan ina nema masa mata."
Yallaɓai na kallona ya ce"Allah ya sa kar kawun naki ya baki kunya. Tun da kika har Nene ta ƙyale Abba da mganar aure kin san lamarin ya fi karfin kowa"
"Bai fi ƙarfin Allah ba. Muna addu'a in sha Allahu in lokaci ya yi zai yi."
Sai ya amsa min da cewa" Allah ya sa muna da rabon gani." Agogo na ɗauko masa wani ɓaki na fatar damisa na saka masa.
Turare na fesa masa sannan ya ce na zaba masa takalmin da zai saka. Wani baƙin takalmi na zaɓar masa ni na siya masa kwanki lokacin ina da ɗan kuɗina na ga wata mate ɗina a BUK na tallarsu suka yi mini kyau na ce ina so 18k na siye shi Yallaɓai na son takalmin nan fiye da sauran takalmansa duk da ya na ma cikin masu saukin kuɗi amman saboda ni ce na yi masa kyautarsa ya sa ya ke ji da shi.
Sai da na gama shirya shi tsaɓ sannan nima na ce ya ta ya ni zaɓan kayan da zan saka. Mun daɗe gaban wardrop duk wanda na nuna sai ya ce a'a. Daga karshe dai ya tsaya kan wata super shi ya siya mini ita mai kalan green na ciro ta ina faɗin" Amman Yallaɓai mayafi zan saka ko?
Hararata ya yi kafin ya ce" Asibiti gidan biki ne?
Na marairaice ina faɗin" Don Allah fa. Atamfar nan ba ta kyau da Hijabi."
Jan gefen hannun rigansa na ke yi sai ya kalleni sai na marairaice ina faɗin" Haba My Yallaɓai na. "
Wani kallo ya yi mini kafin ya duƙa ya na faɗin" In kin yarda mu sabunta wanka."
Da sauri na ce" Bar shi na saka Hijabin."
Na faɗa ina tura baki shi kuma yana mini dariya.
Haɗe rai na yi ina faɗin" Ni ko? Ni ko ai shike nan."
Sai ya ce to na saka mayafin amman sai na yi alƙwarin amjuna akwai ɓarnan ruwa ya na iya sai na ce na yarda sannan ya bari na ɗauko mayafin kayan takalmi ma shi ya zaɓa min wani flat mai ruwan ƙasa irin kayan shi ya na da jaka sai na ɗauki jakar ina jin Yallaɓai na faɗin" Wai ko dai ba Alhaji za ki je gaisarwa ba. Biki za ki je?
Ina dariya na ce" Kai Yallaɓai na. Wani biki kuma! Jinya zan je."
"To ma su jinya."
Share shi kawai na yi domin na san yanzu in na yi magana sai ya iya ɓata mini shiri shi ya sa na yi shuru ina bin sa da mirmishi.
Muna nan sai ga Sabitu ya kira ya ce ya na waje sai ya ɗau kayan ya fita dashi ni kuma fita zuwa ɗakin su Jidda na ga sun shirya dogayen riguna suka saka na Abaya saboda halin Yallaɓai na ce su cire mayafan su saka Hijabi yanzu nan zai ce yara ma ƙanana ina koya musu saka mayafi. Yallaɓai ba wai yana da tsanani ba ne amman fa ya na da saka ido kan iyalansa. Wani lokaci zai yi mini tsanani wani lokacin kuma sauƙin kanshi har ya na yi mini yawa.
Jidda na ce ta ɗau kwandon abinci zuwa mota ni kuma na koma ciki ina fesa turare. Har na ɗan fesa kaɗan sai na tuna da Yallaɓai yanzu raina zai ɓaci. Da sauri na ijiye na koma ina shinshina kaina in ƙamshin ya fito na shiga uku da faɗan Yallaɓai.
Hon kawai ya yi ta mini daga haraba ni kuma sai da na kashe duka wutar gidan sannan na fito na kulle ƙofar falo.
Su Jidda na gidan baya ya na hira da su ina buɗe gaban mota na shiga ya juya ya na kallona kafin ya ce" Alhaji ki ka fesa ma turare ko likitocin ?
Ya faɗa cikin haɗe rai. Da sauri na ce" A'a. Turaren kayan ne ina ga."
Ƙura mini ido ya yi da sauri na ce" Da gaske ban fesa turare ba."
Bai ce mini komai ba ya yi ma motar key sai na koma na jingina da kujeren mota ina maida numfashi. Mun ɗau hanya na ji ya na faɗin" Mu fara zuwa asibiti in na duba Alhaji sai na kai su gwammaja ɗin"
Ni dai na amsa masa domin na ga ya wani haɗe rai ne.
Mun isa asibitin wajen sha ɗaya saura ne. Amman na iske har Ma'u ta zo ni da Rahila ne kawai ba mu iso ba amman har su Yaya Auwal da matansu da Amina ma ta iso daga kaduna. Mun gaggaisa da su har da Yaya Murja Baaba ta na nan ita da Gwaggo suma na gaishe su Baaba a dakune ta amsa ban damu ba. Yallaɓai kuma ya fara musabaha da mazan matan ma suka gaisa ga duka har ƙasa ya gaida Gwaggo da Baaba.
Ma'u har da cewa" Yallaɓai barka da safiya.'
Ya juya suna gaisawa su Jidda ma suka bi kowa ɗaya ɗaya suka gaishe su. Suna waje Alhaji na ciki ya na barci Yallaɓai ne ya shiga tare da su Jidda. Ba daɗewa ya fito ya ce za su tafi ni na raka shi har bakin mota muka rabu akan cewa sai anjuma za su zo tare da su kawu ina ɗaga musu hannu suka bar haraban asibitin Baby sarkin rigima jin wajen Nene za a kaita sai ta fara murna.
Abincin da na zo da shi Gwaggo na ba ta karɓa ta na ta saka albarka.
"Ba wacce ta zo hannu rabbana. Yadda kuke jin ƙan mu kuma Allah ya jiƙan ku wata rana."
Aka amsa da Amin Amin Baaba ta na ta wani taɓe ba ki ni ko ba ta isheni kallo ba
Mun gaisa da Ma'u da tambaya ya jiki daga nan na karisa saman darduman da Amina ke zaune ita da Laila da Khaleesat suna hira. Sai bayan na natsa ne na tambayi Baba Aminu aka ce ya koma tun safe Baba Sani kuma ya koma gida ya huta sai anjuma zai dawo.
Na kira wayar Rahila ta ce min ga su nan a kan hanya ba daɗewa ta iso itama da kwandon abincin ta.
Kowa da wanda ya saba dashi ya zauna su Yaya Murja yan wajen Ma'u suna zaune waje ɗaya har da Zaitunan Yaya Abubakar. Yaya Aina ce ma ta ɗan zauna a wajen Rahila kuma daman kowa ya san kaf gidanmu na fi shaƙuwa da ita shi ya sa ko an gamu tare muna hira ba wanda zai bi ta kai.
Muna nan har bayan azahar Laila Yaya Auwal ya ɗauke ta zuwa gidan su. Alhaji ya farka wajajen biyu duk mun shiga mun gaishe shi da jiki ya ce ya ji sauƙi yau ma ya ce likita ya sallame shi.
Yaya Hamza ya ce ya bari ko zuwa gobe in ya ƙara jin sauƙi.
Baaba na gefe ta ce"Gaskiyar Hamza ka ƙara kwana ka samu hutu sosai Yaya Sule."
Shi dai Alhaji an fi ƙarfinsa kawai ne kawai shi ya sa ya yi shuru. Sai ya koma ya kishigiɗa bayan Gwaggo ta kara mai filo
"Yara nan fa duk sun taho maka da abinci me za ka ci?
Gwaggo ta faɗa ta na kallon shi.
"Allah ya saka muku da alheri. Allah ya yi musu albarka na gode."
Dukkanmu muka amsa da Amin Amin
Abincin ya ce sai anjuma amma ya sha ruwa. Ni ya kallah kafin ya ce"Dubu yau ke kaɗai kika zo? Ina kika baro min uwargidana Hauwa'u?
Ina dariya na ce"Ta zo ka na barci Alhajinmu. Yallaɓai ma ya zo amma anjuma zai dawo in sha Allahu."
Sai ya jinjina kai kafin ya kalli Ma'u ya na faɗin" Asma'u ki yi ma megidanki godiya maimuna ta faɗa mini bai bar yaran nan sun kashe komai ba. Allah ya ƙara ma arziƙin sa albarka Amin."
Ma'u ta amsa da Amin Baaba har ta amsawa da Amin Amin da karfi na kalle ta lokaci ɗaya ina taɓe baki. Ba mu daɗe a dakin ba muka fita waje saboda dokar likita. Muna asibitin nan har la'asar sai ga kiran Hauwa ta na ce min ga su a asibitin ita da Mutaƙƙa ina ne barayin ɗakin da aka kwantar da Alhajin? Ina jin haka ni na fita haraban asibitin na taho da su.
Shi ya sa na ke son Hauwa in dai abu ya same ni ita ke fara zuwa ta yi mini jaje ko murna ita da mijinta. Mutaƙƙa ya shiga ya gaida Alhaji duk da ba lokacin dubiya ba ne na faɗa ma Alhaji ƙanin mijina ne ya na ta saka albarka. Mutaƙƙa ya zo da kayan marmari Hauwa kuma har abinci ta zo dashi kuma nan ya bar min ita karfe shidda ya ce ta koma gida. Na ji daɗi matuka ko da ganin sauran yan'uwana dangin mazajensu na ta zuwa gaida Alhaji. Ma'u har uwargidanta Hajiya Zainab ta zo da sauran ƙanensa.
Hauwa ta zo ba daɗewa sai ga Anty Bahijja ni na yi mamakin ganinta har a cikin zuciyata na san ba domin ni ta zo ba illai Ma'u ce ta je ta taro ta. Hauwa ta saki baki ta na kallon su har da rumgume juna muna ji ta na faɗa ma Baaba matar Yayan mahaifiyar Alhaji Mustspha ne. Sai ta ɗago ta ga ina kallonta sannan ta ce"Kuma Yayar mijin Sadiya ne.".
Gwaggo na ta saka albarka da godiya ina ji Ma'u ta nuna Baaba ta na faɗin ga mahaifiyarta. Anty Bahijja har ƙasa ta duka suna gaisawa Rahila na in da muke Khaleesat ta shiga cikin gari gidan ƙanwarta Anty Aina ma ta koma gida Amina ma ta je gida ta huta. Yaya Murja ma dazu ta koma mu da Yaya Balki ne kawai mu ke asibitin.
Daga zaunen da na ke na gaisar da Anty Bahijja sai lokacin ta kallemu ni da Hauwa.
"To su Hauwa ashe a nan nan?
Cikin rawan jiki ta ce" E. Ban daɗe da zuwa ba. Tare da Baban Sahla mu ke ya kawo ni