Showing 105001 words to 108000 words out of 121577 words

Chapter 36 - TURKEN GIDA BOOK COMPLETE by Janafty.txt

22 Sep 2025

3082

yo ma Baby tsaraba ya na mota na manta dashi."
Ban maida masa martanin mganar shi na tura shi zuwa kofa ina faɗin" Ka yo wanka."
Domin ni kaina na gaji barci na ke ji idanuwana har rufewa suke yi amma ban kwanta ba sai da na kwashe kayan da ya cire na zuba cikin kwandon kayan wanki na fito masa da wasu riga da wando masu taushi na barci. Lokacin da ya fito har na fara gangyaɗi sai da ya yarfamin ruwan hannunsa sannan na farka.

"Ki kwanta mana. Kina barci a zaune?

Ya faɗa ya na nufar gaban madubin ɗakin. Sai da na yi Hamma sannan na ce" Zan baka abinci ne shi ya sa ban kwanta ba."
Bai juyo ba amma ya ɗau mai ya na ɗan shafawa ya ce" Yi kwanciyarki kawai na yi buɗe baki a gidan Nene amma zan duba na gani ko zan iya cin wani abu kafin na kwanta."

  Ban damu ba na ce to sai kawai na kwanta ina jin sa ya na faɗin" Haka za ki kwaanta? Tsabar barci umh kawai na ce masa. Daga nan ban san yadda aka ƙare ba sai dai can ina jin sa ya na cire mini rigan jikina ina ta masa magagi sai da asuba da muka tashi sahur ne na fahimci rigar barci ya sakamin kuma wani ikon Allah duk gajiya da zan ji da mugun barcina ta bakin Yallaɓai huɗu na yi na asuba na ke tashi wani lokacin ma kafin huɗun na tashi Yallaɓai ne sai na yi ta fama dashi kafin ya ta shi har mamaki na ke yi ina faɗin haka maza suke? Ni dai Yallaɓai sai na yi da gaske ya ke iya tashi Sahur in na tashe sa tun lokacin da na tashi sai ya koma barci da cewa in na gama haɗa abin buɗe bakin sai ya tashi, to fa in na gama sai na haɗa da jan hannun shi ya ke iya tashi in kuma zan kyaleshi sai an fara kiran salla zai tashi lokacin an gama ma Sahur ɗin.

  Kamar haka ne yau ma uku da rabi na farka barcin da gajiya duk sun sake ni na ganni na nannaɗe jikin Yallaɓai duk na yaɓa masa kafa. Sai da na yi mirmishi bayan na sauko daga kan gado na gyara masa bargo sannan na fita zuwa tiolet na ɗauro alwala na zo na shimfiɗa darduma na yi salla raka'a biyu na ɗan zauna na yi addu'o'ina sannan na miƙe na cire hijabin na nannaɗe tare da darduma na mayar  ajiyar su ban ta da Yallaɓai ba sai na buɗe kofar bedroom ɗin na fita na bi ta cikin kitchen sai na ga Yallaɓai ya kwaso kololin da na bari a falo zuwa kitchen sai na bubbuɗe na gani bai ci alelen ba amma dai ya sha zoɓo kuma ya sha kayan marmari, ban damu ba tunda Baby ba ta azumi sannan nima zan ci alalen tunda jiya ban ci ba.

  Gas na kunna na ɗora ruwan tea kawai. Muna da sauran buredi tunda jiya ya shigo da shi. Bayan na juye a fulas sai na ɗumama alalen sannan na soya ƙwai saboda Jidda da Babanta  sai da na gama komai na kai falo sannan na shiga ɗakin su Jidda na tashe ta, ina tashin ta Baby na ji ta yi zaraf ta miƙe tana faɗin" Umma nima zan yi azumin."
Kai tssye na ce" To ku wanke baki ku fito mu yi sahur."

  Daga nan na fice tiolet  na shiga na yi brush ina fitowa hannuna da danshin ruwa na lallaɓa domin na shafa ma Yallaɓai ruwa a fuska saboda ya tashi sai dai ina zuwa dai dai saitin kan shi wayarsa ta kawo haske alamun ana kira ban saka hannu ba sai na leƙa sai na ga Daughter na kira. Mamaki ya kamani me ya sa ta ke kiran shi yanzu? Sai wata zuciyar ta ce min ko dai jikin Nene ne?

  Tunanin haka ya sa sai na yi niyyar amsa kiran sai na saka hannu na ɗauki wayar na buɗe bayan wayar ta yanke. Tunda na san password ɗin wayarsa ina shirin kiranta ne kawai sai ga saƙon ta ya shigo wayar har ga Allah ba halina ba ne duba wayar miji duk da wayar Yallaɓai ba ta da shamaki a wajena ban taɓa tunanin bin diddiginsa ba. Kuma har ga Allah lokacin da saƙon ya shigo hannuna ne ya faɗa kan saƙo sai ya buɗe kuma ban isa a lokacin na hana idanuwana karanta abin da ta rubuta ba.

  "Daddy na a tashi a yi sahur. Ko duk santin girkin nawa ne yasa ka kasa tashi? Na ga tuƙwaici na gode. Amma ka yi min laifi domin na ce ba zan karɓa ba yanzu haka ma za su dawo wajenka domin zan siya ma ƴaƴana kayan kwalliyar salla da su. Thank you so much for been their for me Daddy."

  Na yi ƙoƙarin bayan na gama karanta wannan na fita amma sai zuciya ta rinjaye ni na srolling sama ina ganin saƙonnin da ta ke tura masa. Tun da aka fara azumi  ta ke tura masa saƙo da asuba a tashi a yi sahur sannan sai ta tura masa sakon barka da shan ruwa wani lokacin ya ba ta amsa wani lokacin ya yi shuru. Na duba saƙonin har wanda ta na Abuja lokacin da mijinta ya rasu. Wani saƙo da ya ba ni mamaki ya sa na ji kirjina sai da ya buga dam! Shine ta tura masa" Na yi kewarka Daddy yaushe za ka zo?
Shi kuma sai ya ba ta amsa da Gobe in sha Allahu.

  Kirjina ne na ji ya fara suya, har ina ganin duhu duhu da ya sa ban ƙara gaba ba na ijiye masa wayar a nan saman side drower ɗin da ya ke kwance. Kallonsa na ke yi ina mamakin Yallaɓai ashe shima ya iya munafuncin maza? Ashe jiya ba Nene ba ce ta tsaida shi ba ashe Gimbiya ce ta tsaida shi, bayan ta yi masa girki ya ci har ya na santi daga karshe har ya na ba ta tuƙwaici ni kuma ko oho. Wani ƙululin abu ya tokaremin a kirji da wani haushin Yallaɓai don Allah menene na ƙarya tsakani ga Allah? Sai kawai na juya da na so na fita ne ba zan tashe shi ba sai dai yau ya yi ɗaure amma sai na danne zuciyata da na yi wani tunani sai kawai na dawo na fara buga gefen gadon yau ko sunan shi ban kira ba. Sannan ban taɓa shi kamar yadda na saba ba. Bai da wani nauyin barci sai gashi ya buɗe idanuwansa da suka yi nauyi yana kallona sai kawai na juya ina faɗin.

"Ka tashi lokacin Sahur ya yi."

  Da ga haka na yi ficewata na bar shi a raina kuma na kudiri niyyar ko bai tashi ba na gama tashin shi. Daga yau sai ita wacce ke tashin sa sai ta cigaba da tashin shi. Ban da munafunci ta san ya na da mata amma wai ta ce duk asuba sai ta kira shi ya ta shi ya yi sahur? Ban taɓa lura ba saboda da na tashi na ke zuwa kitchen domin samar da abin buɗe baki ban taɓa cin karo da kiran nata ba sai yau.

  Tun da na zauna a wajen nan ban yi dariya ba. Tun kafin ya fito na ce ma Jidda ta zuba ma kanta da Baby sai ta kalleni kafin ta ce" Umma Abba fa? Wani kallo na yi mata kafin na ce" Kar ki ci ki tsaya jiran wani Abba."
Ita kanta na san ta yi mamaki domin sai da ta kalleni ni kuma na kauda kaina ina cin alalen da ma ɗumama sai ruwan tea wanda ban saka madara ba na ke sha dashi Baby dai sai cin ƙwanta ta ke yi ba ta damu ba Jidda kuma jikinta a sanyaye ta ke kurɓan tea ɗin ta ke sha tare da buredi ni kuma a raina ina ta roƙon Allah ya sa kar Yallaɓai ya tashi yau sai dai ya yi ɗaure sai dai addu'ata ba ta karɓu ba sai ga shi ya fito ya na sanye da jallabiya mai ruwan ƙasa Baby na ganin shi tana ƙoƙarin miƙewa ban san lokacin da na daka mata tsawa ba.

"Ke koma ki zauna ko na saɓa miki."

Haka na faɗa cikin zare mata ido. Daga Yallaɓai har Jidda da kallo suka bini, ita kuma sai ta kalleni ta ruɗe har ba ta san kafarta ya ture tea ɗin gabanta ba. Sai ga shi ya malale min a saman cafet kallon tea ɗin na yi yana gangarowa wani abu na tokaremin zuciya.
Ganin irin kallon da na ke yi ma Baby ne ya sa Jidda ta yi sauri miƙewa ta na faɗin" Ki yi hakuri Umma bari na gyara wajen."

  Yallaɓai na tsaye hannunsa harɗe a kirjinsa yana bin mu da kallo barin ma ni.  Kawai sai na yi kyafci ina kallon Baby da ta yi kamar za ta yi kuka na kaɗa kai kafin na ce" Lalle ko za ki ci ubanki Maimuna"
  Ta na jin abin da na ce ta barke min da kuka, tsawa na ƙara daka mata kafin na ce" Za ki yi min shuru ko sai na zo na tattaki a nan wajen?
  Na faɗa ina mata wani kallo, Sai kawai Yallaɓai ya kira ta sai ta kalleni ta kasa tashi shi kuma sai ya ce ta zo mana ya na kiranta ganin na kauda kai ne ya sa ta tashi ta nufe shi ta na kuka ta faɗa jikinsa ya rumgumeta yana faɗin" Shii Umma ce! Kyaleta kun kwance da ita ko?

  Kukan Baby ma ƙara harzuƙani ya ke yi amman ban yi mgana ba sannan ban ɗago kaina ba. Ina jin su yana ta lallashinta har sai da ta daina kuka sannan ya ce ta koma ɗaki ta kwanta ita kuma Jidda ta dawo da tsumma ta goge wajen tas ta gyara da na ce ta zauna ta ƙarishe shan tea ɗin ta sai ta ce mini ta ƙoshi. Uban gayyar kuma na tsaye ban kuma ce ya zauna ba sai da ya gaji sannan ya zauna a ƙasa kusa dani yana faɗin.

"Zuba min tea."

Da na so na ce ya kira Gimbiya sai kuma na fasa na haɗa masa tea ɗin na tura masa gabanshi da ƙwan da buredin ganin yadda na ƙi kallon shi ya sa cikin mamaki ya kira sunana.

"Sadiya."

Ban ɗago ba amma na amsa sai kawai na ji yana faɗin" Me ke faruwa ne?
Sai a lokacin na yi masa kallon ƙasa ƙasa kafin na ce" Me ka gani?
"Abubuwa da ya wa. Na ga kamar ranki yana ɓace ne me ya faru? Ke da yara ne?

Ya faɗa yana kallona nima sai a lokacin na kalle shi sai kawai na kauda kai kafin na yi mirmishi gefen baki na miƙe ina faɗin" Bakomai."
Abin ya bashi mamaki ganin na bar shi a falon na yi shigewata ciki kuma na san ya bi ni da kallo ban kuma ko waigo ba. Ban ƙara ganin Yallaɓai ba sai da ya zo daukan hula da carbi ina kan darduma ya ce mini ya tafi masallaci sai na gyaɗa masa kai kawai ba tare da na yi masa mgana ba.

Da safe ma haka na tashi gim da raina ko fara'a ban yi masa ba daga shi har ƴayan shi Jidda dai ta ga har da safen ban huce ba sai ta sameni a falo ina zaune domin ɗakin na bar ma Yallaɓai gabaɗaya.

"Umma ki yi hakuri don Allah."
Har da Baby ma kamar ta yi kuka ta ce" Ki yi hakuri Umma."
Sai suka ba ni tausayi laifin Ubansu ne ya shafe su sai na ɗan saki fuska na ce musu zo su wajena na haɗa su na rumgume na saki fuskata shi ya sa suka tafi makaranta suma sun warware. Amma shi kan Yallaɓai ya kasa gane kaina da ya matsamin sai na ce masa ban ji daɗi ne.

"To ko mu je asibiti ne? Me ke damun ki?

Kai tsaye na ce" Ba sai mun je ba. Ciwon kai ne kaɗan zai bari zuwa anjuma."

Kasa fita ya yi saboda yadda ya ga ina basar dashi ya san halina dole akwai wani abu da ya yi mini ne.

"Sadiya don Allah ki faɗa min me ya faru?

Na ce masa bakomai ba sau adadi amma bai yarda ba. Ganin ya damu sai na ɗan saki raina saboda na ga ya na damuna da tambaya tun da ba gaya masa abin da ke danuna zan yi ba gwara na saki raina ko zai kyaleni da tambayoyin sa.
Na ɗan sakin masa har muka zauna muna ta hira sai muka ganganro kan mganar kayan salla ya ce yana jiran cikon payment na aikin da suka yi a Rano ne a wannan sati sai a yi mganar kayan salla da ɗinki da sauran su ya so ba zai fita ba ne sai kuma Musbahu ya kira shi ya ce wasu mutane sun zo suna jiran shi. Da zai fita sai na ce bari na shirya ya sauke ni Gwammaja na duba Nene, da gayya na faɗi haka saboda na ji me zai ce sai kuma bai ba ni kunya ba.

"Nene ta samu sauƙi fa. Ke da ba ki da lafiya, ki bari ko zuwa jibi tunda ba ki ji daɗin kema."

Kai tsaye na ce" Na ji sauƙi mu je ka sauke ni zan iya zuwa."
Na ɗauka zai ƙara mgana sai kuma ya yi shuru sai da muka jira Saude ta zo na bar mata gidan daman mun yi wanka mun shirya ni shadda na saka da farim mayafi shi kuma sai ya saka kananun kaya.
Da ya kai ni Gwammaja bai shiga ba saukeni kawai ya yi ya wuce office ni kuma na shiga ciki sai da na lelleƙa daƙunan su Hajiya iya muka gaisa sannan na ƙarisa ɗakin Nene na ganta garas da ita ita kaɗai ce a shashen ita ta ke faɗa mini Gimbiya ta leƙa wajen aiki.

Da na yi mata ya jiki ta na mirmishi ta ce" Tafida sai da ya ta so ki? Ɗan zazzabi ne Gimbiya ta ɗaga masa hankali tun jiya ina shan mganguna na warware."
Sai na yi mata fatan samun sauƙi bayan tambayan yara na ce suna makaranta mun ɗan taba hira da ita anan na yi azahar ina shirin tafiya sai ga Gimbiya ta dawo mun gaisa sama sama kamar yadda muka saba. Ta dai tambayi su jidda na ce suna makaranta.

  Ƙarfe biyu na koma gida na.  Daga kuma ranar ko a fuska ban ƙara nuna ma Yallaɓai wani abu ba. Ban damu da ma ƙara saka masa ido ba saboda mu zauna lafiya amma ni na san ba ta fasa kiran shi da tura masa saƙo ba, amma dai bai ƙara buɗe baki a waje ba sai a gida mun shiga goman karshe an fara ibadar na tahujjud Yallaɓai masallaci ya ke zuwa ni kuma in ta da yara mu yi namu a gidaa.

  Ranar da za mu ɗau azumi na ashirin da 24 Yallaɓai ya dawo daga masallaci ya ɗan kwanta huɗu da rabi na tashe shi sai ya shiga tiolet yana wanke baki a lokacin na ga Gimbiya ta na kiran shi bayan ta katse sai ta tura mssa saƙo zuciya ta rinjaye ne na ɗau wayar na duba saƙon na ta.

"Daddy jiya ba ka zo ba? Kuma fa na yi maka kunin tsamiya mai daɗi"

Motsin fitowarsa na ji da na so na yi saurn ijiye masa wayar ne sai kuma na fasa sai da ya fito. Ya yi mamakin ganina tsaye da wayarsa sai da ya matso gabana sannan na miƙa masa wayarsa ya karɓa kafin ya samu sararin mgana na ce.

"An tura maka saƙo."

  Ina gama faɗin haka na fice na san kuma bayan ya duba saƙon ya ji nauyi domin ba na ce kunya ba tunda maza ba su san kunya ba. Har ya fito muka yi sahur jikinsa a sanyaye ni kuma sai na yi masa bariki ban nuna masa ko a fuska na ji haushi ba sai ya ɗan saki jikinshi amma a raina na kudiri niyyar koya masa hankali daga shi har Gimbiyar ta shi.
Washegari ya tura mini kuɗin kayan salla nawa da na yara sai na su Nene da na Gwaggo. Daman yana yi musu kaya duk shekara. Dija collaction na tura ma kuɗin daman mun yi mgana na zaɓi komai har Marwa na yi ma kaya da Saude saboda mun yi waya a gida za ta yi salla in ta dawo sai kuma ta gama pratical ɗin ta za ta koma makaranta. Kuma daman ta turo mini kayan na zaɓa tuni suna wajen ɗinki kuɗin ne sai da ya tura mini bayan mun gama lissafi na tura mata.

  Ni da yara kala huɗu ya yi mana. Leshi biyu atamfa biyu. Nene Atamfofi biyu su Hajiya Iya kowacce ɗaya sai Jawahir kala biyu Adanan kuɗi ya tura masa sai Gwaggo guda ɗaya Alhajinmu kuma shadda mai kyau. Sai ni mayafai guda biyu da Hijabi ni da yara sai takalman mu har Nene an siya mata takalmi da Hijabi gabaɗaya tun lokacin da a ka kawo kayan na nuna masa ya ce komai ya yi. Telanmu kuma daman na yi masa mgana kuma ga kuɗi har da na Nene na kai mana ɗinki tare da na Jawahir da Marwa Saude kuma na ta na bata mamanta na ɗinki ita za ta ɗinka mata. Gwaggo kuma da Alhajinmu na kai musu na su suna ta godiya duk da suma su Yaya Hamza duk sun yi musu. Nene ma na kai mata takalmi da hijabinta na ce kaya na wajen ɗinki ta na ta saka albarka.
Ranar da muka ɗau azumi na ashirin da shidda Mimisco ta aiko da kaya yan kanti kala biyu biyu na jidda da baby. Anty Bahijja ma ta aiko musu da material a ɗinke sai Anty Maimuna itama kala biyu amma Bby uku ta yi mata har da wani riga da wando masu kyau da takalma. Gimbiya kuma Yallaɓai ta ba ma kayan ya kawo ma su, kayan kwalliya ne sai hijabai da mayafai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login