Showing 60001 words to 63000 words out of 97338 words

Chapter 21 - YARO DA KUDI Book Complete by Binta Umar Abbale .pdf

10 Jul 2025

4290

bata bari gari ya waye ba"
[25/05/2019 9:48 AM] ®Binta Umar Abbale: Gabanshi ne ya fadi kadan yana addu'ar Allah yasa
kar yarinyar ta fada masa abinda ya faru ita dashi


Sai ya gyara fuska yace"Owk ai ni bangan taba ma kwata kwata a jiya"

Cikin mamaki Malam yace"tace kuma tazo gurinka tabaka hakuri"

Girgiza kai yayi kai tsaye yace"batazo ba"

Kawai ya fice ya bar Malam tsaye a gurin yana binshi da kallo

Zama yayi kan bainci dake gurin yana al'ajabin wannan abu ,amma zai zaunar da Maryam din
ya tuhume ta yasan yarinyarsa tsarkakkiya ce kuma ba zatayi masa karya ba.


Nasir kuwa Can wani guri ya nufa cikin estet din nasu da suke motsa jiki yafara motsa jikinshi
babu abinda ya dameshi.


Tsaf tagama hada komai tafito jikinta sanye da katon hijab dinta kamar yadda ta saba,ta aje

kayan dake hannunta kusa da Malam tace"Baba bari inje mu gaisa da Momy ko"


"To babu Laifi "
Malam yafada yana bin ta da kallo


Kai tsaye part din Momy ta nufa

Momy na zaune kan kujarar daining ita dasu Nafi'u sun shirya tsaf , Uwani mai aikinta tana hada
musu breakfast ,Maryam tayi sallama


Momy ta amsa mata fuska a sake tace"Dota shigo mana kika tsaya nan"


Kanta a sunkuye ta shiga ciki farlo sosai ta karasa gurin Momy din ta durkusa har kasa tana
gaida ta


Momy tace"Nima yanzu nake cewa Nafi'u ya gama karyawa yaje ya kirawo min ke"

Murmushi tayi batace komai ba


"Ina fatan kin karya ko"
Momy tafada tana kallonta

"Eh Momy na karya ga abinci can ma nayiwa su aunty"


Momy tace"ai da baki bawa kanki wahala ba ,tuntuni nasa Uwani tayi musu"

"Laa Momy ai babu komai sai su hada da nawa"

Dariya Momy tayi tace"to shikkenan sai ki jiramu mu gama karyawa a nutse sai mu tafi"

"To Momy"
Maryam tafada gami da mikewa taje ta zauna cikin daya daga cikin kujerun farlo

Ko minti uku batayi da zama ba Nasir ya shigo farlo

Idansu ya tsarke guri guda

Da sauri ta dauke kai ta mayar kan kayuwat TV plasma dake manne a farlo din, ta cigaba da
kallonta


Fuska ya hade sosai yana namakin mai yakawo yarinyar nan da sanyi safiyar nan , zuciyarsa
yace mybe ko Momy ce ta jajibo ta yasan halin Momynsa da kwashe kwashe

Kai tsaye Tv ya je ya kashe batare da ya saurari gaisuwar da su Nafi'u suke masa ya shige
dakinsa dake farlon


Baki a sake Momy take binshi da kallo tana namakin abinda yake nufi, girgiza kai tayi kawai
tacigaba da cin abincin ta

Bai fi minti biyu da shiga ba sai gashi ya fito yana ya mutse fuska hannunshi rike da wayarsa
yana daddanawa ya tsaya daga bakin kofar dakinshi yana kallon Momy yace"Momy wai Dan
bana amfani da room din nan sosai shine ba'a gyara min, yanzu inaso in shiga toilet na tadda
ko ina kaca-kaca"


Hararasa Momy tayi tace "sannu Ubana kashigo ba ka kula kowa ba shine yanzu zakazo ka
titsiye ni da tambaya"
[25/05/2019 10:06 AM] ®Binta Umar Abbale: Please Momyna kisa a gyara min dan Allah
,Wanka nakeso inyi zan fita"

Yafada yana karasowa inda take zaune

Momy tace"ko jiya sai da nasa, Kyauta, mai yimin goge goge ta gyara maka dakin kai dai kawai
kace zakayi min iyayi"


Dariya yayi kadan abinda ya Dade bai yi mata ba ,yana kallonta yace"Momy kinsan halina
banason kazanta,wallahi tunda na shigo Farlon nan nakejin karni na tashi nake kamar zanyi
amai wallahi"
Ya karashe Maganar yana ya mutse fuska

Kowa yayi zagi a kasuwa yasan da Wanda yake ba Maryam kadai ba ita kanta Momy ta tsargu
da Nasir din domin tunda take dashi bai taba yi mata irin wannan maganar ba ,kasancewar a ko
da yaushe ko ina na gidan cikin kamshi yake sabida Allah da yayi Momy a kwai San kamshi.

Sai tayi shiru da bakinta domin bataso ta kara wata maganar Nasir din ya kwabo wata maganar

tasan zuciya batada kashi dole wata rana Maryam din tafara mai da martani kamar yadda tafara
ramawa jiya a asibiti


Minti biyu farlo yayi tsitt Maryam sai kokarin danne zuciyarta takeyi ,sabida yadda take jin kamar
ta tashi tabar gurin ,tana jin kunyar Momy ne kawai kuma tana ganin mutumcin ta, amma ranta
ya yi mugun baci da wulakancin da Nasir yake mata idanta ya Tara kwalla sai kokarin mayarwa
takeyi ,kawai tajiyo Muryar Momy tana cewa Maryam Dan Allah shiga ki gyara masa dakin kafin
mu gama kinji ko"

"Don Allah"
Tafada maganar cikin zuciyarta

Yanzu Momy ce take hadata da Allah

Allah sarki Momy ,albasa batayi halin ruwa ba

A nutse ta mike tsaye tana gyara hijab din ta juyo ,fuskarta a sake tace"to Momy karki damu
yanzu zanyi abinda kikace insha Allahu"
[25/05/2019 2:00 PM] ®Binta Umar Abbale: "Yawwa Dota Allah yayi miki albarka"
Momy tafada cikin farin ciki yarinyar tana burgeta sosai ,tanada hankali kwata-kwata bata
biyewa Nasir din da abinda yakeyi


Cikin nutsuwa ta nufi bed din ,Nasir ya dago kanshi dake sunkuye yana kallon wayarshi ya bita
da kallo yana ya mutse fuska ,yace"ke!"


Maryam ta juyo a nutse tana kallonsa

Yace "kar ki kuskura kiyi min binkice a daki domin a kwai muhiman abubuwana a ciki , duk
abinda na nema narasa to sai kin biya ni"


Shiru Maryam tayi a tsaye tana tunanin ta shiga ko tafasa tunda zargi ya shigo ciki

Momy tace"wai mai yasa kake hakane my Son mai Maryam tayi maka kuma kake mata wani
zargi na daban"


Shiru yayi baice komai ba ya cigaba da danne dannensa a waya babu abinda ya dameshi

Momy tayi kwafa kawai ranta a bace tace"Dota yi hakuri kinji ko ,kar ki dakata ta halinshi kiyi
domin ni"


Maryam tayi dariya mai ciwo race"Momy karki damu ai uncle yana da gaskiya , kar inje inga
wani abu nasa mai muhimanci in share ko in zubar, kwata-kwata raina bai baci ba"


Momy tasan Maryam din dannewa tayi kawai sabida kawaici irin nata,sai tace "to shikkenan
Maryam je kiyi sauri ki kammala muwuce ko"


Maryam ta wuce dakin ranta yana mata suya tarasa inda zata sa ranta sabida yadda takeji a
yanzu zata iya fito na fito da Nasir din ko dame yake taqama Kuwa



Babu wani datti a cikin dakin na kuzo mu gani ko ina tsaf in banda bedshit din da yayi datti
kadan kasancewarsa mai kalar haske ,cikin sauri ta dauke shi gami da zare rigunan filillikan
tabude sif ta Ciro wani sabo a ledarsa ,ta shimfida tsaf, sannan ta wuce toilet din shima babu
wani datti

Sai jirwayen sabulu na Wanka shima ba sosai ba asalima in banda kamshi babu abinda yake
tashi a ciki na irin kalolin sabulan da yake amfani dashi gurin Wanka da wanke sumarsa


Tsaf ta wanke ta sanya turaran wuta Na ban daki ,sannan tahada masa kananun wan dunanshi
da vest dinshi a cikin abin wanki ,afili tace "wallahi bazan wanke ba masa Dan iska kawai,Dan
rainin hankali"


Ta fito tana Jan tsaki kai tsaye kofa ta nufa domin fita daga dakin,suka ci karo dashi,zai shi go


Maryam tayi baya da sauri tana dafe goshinta sakamakon yadda suka gabza karo,ya shigo
dakin yana bin ta da wani mutsiyacin kallo Na kaskanci ya mayar da kofar ya rufe yana bin
dakin da kallo ,fuskarshi a hade



Bata kalleshi ba ta sanya hannunta a Karo na biyu tana kokarin bude kofar

Taji ta a kulle gam!

Sai ta waigo tana kallonshi fuskarta a murtuke

Kallon kallo sukeyi minti biyar tukkuna yace"kika kuskura kika fadama mahaifinki abinda yafaru
jiya wallahi sai na kaiki inda baza ki iya dawowa ba kin tafi kenan"


"Kashe ni zakiyi Kenan"?
Maryam tafada kai tsaye tana kallonshi babu kifta wa


"Yes"
Yafada yana zare mata ido

Dariya ce ta subuce mata bata shirya ba ,tace "wallahi da naji dadin haka kaga dana huta da
ganinka a duniyar nan domin bana kaunar in bude ido in ganka a rayuwata"


Shiru yayi yana bin ta da kallo Sam maganganunta basu bata masa rai ba so yakeyi ya kirkiri
abinda zai bakan ta mata rai yanzu

Zama yayi gefan gadon yana ya mutse fuska yace "Ke boyi boyi na zo nan Dan Ubanki ki fito
min da kayan da zansa yanzu nan"


Wani mugun shocking Maryam taji a jikinta lokacin da ya kirata da wannan Kalmar Boyi-Boyi
,har da zagin Ubanta,lallai yau zata nuna masa tasan darajar iyayenta
[06/06, 01:45] +234 808 996 5176: *YARO DA KUDI*

*89*


Maryam ta juyo a nutse tana kallonsa fuskarta babu yabo babu fallasa,tace "Nasir inaso kasa ni,
ni Maryam wallahi nafi qarfin in zama boyi-boyin ka ,dukkanin abinda kaga ina yi maka ina yi
makane kawai sabida darajar Momynka,amma kasani cewar kudinka ko takamarka basu isa su
sa na yi maka bauta ba ,wallahi in har nice zan dauko maka kayan da zaka sa,to sai dai a
kwana a haka,amma kai baka isa kasani abinda banyi niyya ba"


Idanshi tsaye a kanta har ta kare maganar

Ranshi a bace yace"Na nawa kuma yarinya ,Wanda yayi silar zuwanki duniya ma gashi can
bakin get yana min gadi,ballantana ke!!"
Ya karashe maganar yana nunata da hannu cikin izgili

Kuka ne yakeso ya Kufcewa Maryam jin cin mutumcin ya shallake kanta ya dawo kan
Mahaifinta


Tace"tabbas kafadi gaskiya mahaifina ba komai bane ,kuma ba kowa bane a duniyar nan ,muna
nai man tsari da dukiyar da zata samu mu manta da Allah mu shagala da duniya murika sabon
Allah a cikinta"


"Ke kika sani dai yarinya na get out malama"
Yafada yana nuna mata kofa


Maryam ta bude kofa ta fice batare kawai tana girgiza kai cikin takaici wulakancinsa



Momy na tsaye da hijab a hannunta tana kokarin sawa tace"yawwa dama yanzu nake kokarin in
shiga in miki magana kifito mutafi naji shiru,nace Allah yasa bawani abin yayi miki ba"


Cikin kokarin danne abinda yake taso mata Na bacin rai tace "babu komai wallahi Momy nayi
duk abinda kika Sani"


"Yawwa Allah yayi miki albarka"
Momy tafada
Sannan suka fita a tare
Momy ta daukesu a motarta har Malam Ya'u suka nufi asibitin



Mikewa yayi bayan fitarta ya nufi tolirt a gurgije yayi Wanka ya fito ya nufi inda kananun
kayanshi ,ya kwana biyu bai sasu yau sai yaji yana sha'awarsu ,tsaf ya shirya cikin wani mugun
wando jins mai mutukar tsada blue colour shart din ma haka ta matse masa jiki sosai power
dinshi ya fito ya gyara sumarshi tsaf sannan ya dauki agogonshi ya daura,ya nufi inda
takalmanshi suke ,sai da ya sanya safa sannan ya saka wani mugun takalmi fadar kudinshi ma
aiki ne ,sosai Yayi bala'in kyau ,sabida yadda dressing din ya karbe shi ,sabida yadda ya yi qiba
jikinshi ya murje sosai ya fito ,ya nufi inda motarshi take shima babu inda yayiwa tsinke sai

hospital din yanaso yaje ya duba marasa lafiyarsa ,sannan ya wuce can gurin Abbas domin
cigaba da tsare tsarensu na bude sabon gurin shakatawa da zasuyi
[06/06, 01:45] +234 808 996 5176: [26/05/2019 9:51 AM] ®Binta Umar Abbale: *YARO DA
KUDI*
*90*

Alhamdullihi jikin Baban gida yayi sauki sosai ,yana zaune gefan gado su aunty a kusa dashi ,
su Momy sukayi sallama cikin dakin, Yaya Rabi ta amsa tana yiwa Momy sannu da zuwa, fuska
a sake Momy ta karasa cikin dakin tace"A'a lallai jiki yayi sauki Baban gida Allah ya kara afuwa"
"Alhamdullhi kam jiki ya samu wallahi"aunty tafada tana bawa Momy gurin zama Momy ta
zauna suna gaisawa da Yaya Rabi cikin mutumci , aunty ma suka gaisa cikin sakin fuska Yaya
Rabbi ta kalli Maryam dake tsaye jikinta a sanyaye tace"ke kuma abinda kikayi kin kyauta cikin
dare ki fita ,kisa mi ta nai manki ko duk kin daga mana hankali"
Maryam ta sunkuyar da kanta kasa ,domin bata da abin cewa,tasan in tafadi abinda ya faru ba
yadda zasuyi ba



Momy tace"subahanallahi kamar yaya tafita cikin dare"?


Aunty ta girgiza kai cikin bacin rai tana kallon Momy tace"wai daga cewa in uncle dinta ya shigo
taje tabashi hakuri kan irin rashin kunyar da tayi masa jiya,shine da ta fakaici idon mu taga
munyi bacci shine ta gudu gida ,sabida tana ganin kyashin ta tsaya tabashi hakuri"


Momy tayi murmushi tace "Laifin mai tayi da har zaki titsiyeta kice lallai sai tabashi hakuri ,waya
gaya miki anawa yara haka,? Ni sam banga laifin ta ba ,Dan yaro ya tsare kare martabar
iyayenshi sai ace yayi laifi ,karki kara yin haka Suwaibah wannan ba hukunci ba ne"


Malam Ya'u yana tsaye jikin gadon da Baban gida yake kwance ,ya sauke ajiyar zuciya yace"
nima abinda nakeso ince mata kenan abinda tayi bai yi dai-dai ba ,jiya misalin uku shaura Na
dare naganta ta shi go gidan a furgice,hankali na ya tashi sosai ,duk Na tambaye ta dalili shine
take fada min

Yaya Rabi tace"kwarai hakan ba dai-dai bane wallahi kar kiso kiga yadda hankalinmu ya tashi
jiya

Sai da asubah da nace ta kira Babanta ta sanar dashi halin da ake ciki ,shine fa yake cewa gata
a gida mu kwantar da hankalimu"

Momy tayi ajiyar zuciya tana kallon Maryam din tace "kar ki kara aikata irin haka,yanzu inda
wani Abu ya sameki Na tsautsayi kice mai,Allah ya kiyaye ameen"


Maryam tace"insha Allah Momy bazan karaba"

Momy tace"ga kayan kari nan Rabi"

Yaya Rabi tace" to angode Hajiya Allah yakara girma ya jikan magabata"

Nan Momy tasa a ka hadawa Baban gida abinci a kabashi sannan tabashi magani da
kanta,suna hira kadan kadan,Nasir ya shi go cikin dakin Dr Sofia na bayanshi hannunta rike da
wasu takkadu
[26/05/2019 10:18 AM] ®Binta Umar Abbale: Sama-sama ya gaida su aunty hankalinshi na kan
Baban gida,Dr Sofia kuwa babu wanda ta gaida a cikinsu sai Momy ,to Momy Sam bata kawo
komai ba , sabida tasan yarinyar dama can ba wani hausa takeji ba sai turanci amma dai duk
da haka inda mutumci yadda ta gaida ita ta gaida sauran da suke tare
Aunty ma jikinta ne yafara sanyi sabida ta lura da irin kallon raini da Dr Sofia take musu ita da
Yaya Rabi,amma sai ta daurewa zucuyarta tace ko Dan yarinyar ba musulma bace shiyasa
batasan darajar Dan adam ba.



Maryam ko taci alwashi sai ta ci mata mutumci ko da me take takama wallahi bazata raina mata
iyaye ba,tana addu'ar Allah yasa kafin su gama zaman asibitin wani abu ya hadasu da'ita sai ta
wulakantata
Dama gashi tana jin haushin yadda take wani shishshigewa Nasir din Dan wani lokacin tana
lura jikinsu har haduwa yakeyi


Ya karasa bakin gado yana duba shi sosai Ya kalli aunty kadan yace"anbashi magani ko"?


Aunty tace"eh yanzu Momy tabashi"

Shiru yayi kawai ,ya dauke idonshi daga kan Baban gida ya dora kan Momy ,fuskarshi kamar ko
da yaushe yace"Momy ina ganin zan sallameshi tunda ya dawo normal So sai ya cigaba da
karbar magani a gida ,sabida ni banaso ana cika min asibiti kullum"
Duk cikin turanci yake maganar in banda ita Momy din da Dr Sofia da Maryam babu Wanda ya
fahimci abinda yake fada

Cikin turancin Momy tace"Why My Son mai yasa kake haka ne suwaye mutane ,ni ko kuwa
iyalan wannan bawan Allah ,uhumm! Wulakanci fa babu kyau"


Ya mutse fuska yayi kadan yana duba a gogo yace" Momy bafa haka nake nufi ba please
kinsan komai nawa a tsare yake ,wallahi kwata kwata tunda suka shigo hospital din nan daga
jiya zuwa yau komai ya sauya,gwara kawai su koma gida ,sai in cigaba da kula dashi"

Dr Sofia tasa baki ita ma cikin ya mutse fuska cikin turancin ta tace"yes Bama bukatar hayaniya
a wannan guri Momy sabida duk yawanci marasa lafiya suna bukatar huto da kwanciyar
hankali"


"Momy tayi kwafa tana kallonta rai a bace tace" wato koya min yadda aikin asibiti yake zakuyi
ko kuwa tun kafin a haifeku nake wannan aiki"


"Sorry Mom ba haka bane , kiyi hakuri in maganar tayi miki ciwo ,in babu damuwa abar mana
Mara lafiyar shi kadai kawai bama bukatar "yan jiya ,sabida a kwai masu kula da..

"Ya'isa"! Maryam tafada a hasale tana nuna Dr Sofia da hannu cikin turanci tace"ko kunce ko
baku ce ba dole Baban gida zai bar asibitin nan tunda ba Ku zaku bashi lafia ba , ni nan na isa
in kula dashi tunda nima abinda na karanta kenan baku kadai Allah ya bawa ilimin ba,akin
banza aikin wofi ,sai anyi magana ki dinga yiwa mutane turamci banza da wofi da wani rubban
bakin ki da yagaji da shan giya da kayan maye"
[26/05/2019 12:07 PM] ®Binta Umar Abbale: Shiru dakin yayi duk sun zubawa Maryam ido


Momy taji dadin abinda Maryam tayiwa Dr Sofia ,sabida ta lura yarinyar tana da girman kai


Dr Sofia ta kalli Nasir ranta a bace tace"kaji abinda wannan yarin take cewa ko, kamar ni zata
dinga zagi tana fadawa magana ,ina kan aiki na"


Shiru yayi kawai baice mata komai amma ranshi yayi bala'in baci da abinda Maryam din tayi
,wato duk kokarin da yakeyi a kansu bata gani,ya lura zaqewarta tayi yawa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login