Showing 75001 words to 78000 words out of 97338 words

Chapter 26 - YARO DA KUDI Book Complete by Binta Umar Abbale .pdf

Advertisement

10 Jul 2025

4353

tun lokacin da Abdul ya fada mata ga yadda sukayi da Nasir wai

lallai taje asibitinsa gurin wannan matar da ta tsana taji kwata-kwata aikin ya fice mata a rai
sabida in har Sofia ce zata mata intervio sai dai ta hakura da aikin



Momy tace"ban sanki da haka ba Dota kije kinji ko tunda dai yace ki je babu matsala"



"Shikkenan Momy zanje insha Allahu gobe"


"Yawwa Dota Allah yayi miki albarka, kema na kusa yin missing dinki ko"?



Maryam ta rufe fuskarta da gyale tana murmushi


Momy ta rinka dariya tace"ke kam kin fiye kunya wallahi"


Da sauri Maryam ta mike ta bar gurin fuskarta a rufe



Momy ta bita da kallo tana dariya kawai tana girgiza kai Yarinyar tana burgeta sosai
[06/06, 01:50] +234 808 996 5176: [01/06/2019 6:28 PM] ®Binta Umar Abbale: *YARO DA
KUDI*
*102*

Lokaci yana ta matsowa Malam Ya'u yayi shirye-shiryensa aunty ma ba'a barta a baya ba tana
ta gyara "yar ta Maryam kuwa ganin lokaci ya matso jikinta duk yayi sanyi komai take kokari
takeyi soyyayar Nasir tanata sasakar zuciyarta tarasa yadda zatayi da komai bata jin dadinshi,
saura kwana uku daurin aure Nasir ya dawo gada america, Momy ta rinka murna tare suka
shirya masa abinci mai rai da lafiya ita da Maryam, shiyasa suna kammalawa Maryam ta gudu
sabida Sam! Bata so yazo ya tadda ta ya ci mata mutumci

Momy ta rinka shi mata albarka

Wanka tayi ta kimtsa jikinta domin sunyi waya da Abdul yace gashi nan zuwa

Shi kuwa Nasir yana zaune Momy ta tisa shi a gaba tana lallabashi lallai sai yaci abinci shi
kuma yana botsarewa


Momy ta kalleshi tana shan kunu tace" yanzu zamuyi fada dakai wallahi dube ka fa duk ka yi
Dan wuya nasan baka cin abincin kirki ko a can sai ciye-ciyen da kasa ba"


Shagwaba yake mata sosai kamar wani yaro kankani

Ita ko kamar ta bashi abincin a baki haka takeji sabida yadda taga duk yayi rama sati biyu kacal
shiyasa kwata-kwata bata kaunar taga yayi wata dugowar tafiya


Sai da yagama sangartarshi sannan ya fara cin abincin


Momy tace"ni har fargabar kayi aure nake sabida ban San matar taka ko zata tsaya ta kula da
kai ba"


Murmushi kawai yake mata yana kara jin so da kaunarta cikin zuciyarsa


Bayan ya kammala ya goge bakinshi , ya maida hankalinshi kanta yace"Momy a wannan satin
zan fitar da zakka, zanje can birnin kudu zanyi musu a can"


"Masha Allah my Son Allah ya kara albarka"


"Ameen Momy"
Nasir yafada yana mikewa yace"zanje inyi Wanka in kwanta in huta Momy"


Momy tace "Allah ya huce gajiya sai ka fito"


Dakinshi ya nufa komai tsaf-tsaf dashi sai qamshin turaran wuta yakeyi sai ya zube tarkacan
dake hannunshi ya nufi toilet domin ya Dan watsa ruwa ko jikinshi ya warware dama wayoyinshi
duk ya kashesu sabida yasan yanzu, za'aita damunshi a hanashi hutawa da Abbas kawai
sukayi waya

Bayan ya fito ya sanye wando 3Q sai kawai ya kwanta kan bed dinshi yayi rigin gine gami da
dafe kanshi da duk hannunwanshi, shi kadai yasan abinda yake damun zuciyarsa
[01/06/2019 7:30 PM] ®Binta Umar Abbale: Kullum abin kara kaimi yakeyi mutukar zai kwanta
bacci babu dare babu rana sai yayi wannan masifaffaen mafarki wai gashi yana yin sex da
yarinyar da yai wa muguwar tsana a rayuwarshi.


In ya farka kuka ne kawai baya yi sabida tsabar bakin ciki da bacin rai jikinshi kaca-kaca yake
tashi dole komai dare yaje yayi Wanka ko da yaje america ma bata canza zani ba, sabida abin
ma ya kara qaimi sabida yadda"yan matanshi na can suka matsa masa kullum sai sunzo sun
dameshi, sai tayi da gaske yake tsallake kai dinsu domin yayi alkawari bazai kara kusantar zina
ba ,shima romance din da yakeyi so yake Allah ya yaye masa



Da kyar bacci ya dauke shi mai dauke mafarkai kamar ko da yaushe yau ma haka ya tashi
jikinshi kaca-kaca yayi ta jan tsaki dole ya sake wani wankan ya fito yanajin nauyin jikinshi
sabida baccin magariba dama haka yake sawa jikin mutum duk ya mace


Momy ya samu zaune a farlo bayan yadawo daga sallah magariba sai kawai ya zube gabanta
yana rike cikinshi



Momy tace "Lafiya My son"


"Momy marana ta dameni da ciwa wallahi"
Yafada yana rimtse idonsa


Kallonsa Momy tayi tana nazarinshi kadan ta dauke fuskarta tace" mai ya jawo maka ciwon
Mara"?


"Momy ban sani ba nima"
Yafada yana kokarin bagarar da maganar

Momy tace"shiyasa banaso kake shaye-shayen kayan zaqin nan mybe sune suke haddasa
maka ciwon"
Momy tafada tana kauda kanta sabida ta Riga ta gama fahimtar abinda yake damunshi.
[06/06, 01:50] +234 808 996 5176: [02/06/2019 6:54 AM] ®Binta Umar Abbale: *YARO DA
KUDI*
*103*

Shima bai sake cewa komai ba, kawai sai ya lumshe idonshi gami gyara kwanciya kan kujera
Momy ta rika satar kallonshi tana nazarinshi, dole ne ta matsa masa yayi aure ,sabida duk ta
gama fahimtar abinda yake damunshi, ta sauke ajiyar zuciya kana tace"Myson " bude idonshi
yayi ya zuba mata su, tace"Yaushe kuka tsayar da maganar daurin auran"?
Zakudawa yayi yana ciccije bakinshi yace"zamuyi waya in anjima" Momy tace"mai zai hana a
hada dana Abdul, nan da sati biyu masu zuwa" gabanshi ne ya fadi jin abinda Momy tace,
amma sai ya gwada mata halin nashi


Yace"Momy waye Abdul kuma"

Girgiza kai kawai tayi sabida ta San halin kayanta


"Abdul latif na kawunka Muktar"

Yayi shiru kamar ruwa ya cinyeshi

"Kayi shiru baka ce komai ba"

"Wane date ne"?

"Ai lokaci yayi nan da sati biyu masu zuwa"

Gabanshi ya rika wani irin bugawa fat!fat!fat , ta tabbata kenan Abdul zai auri ta batare da ya
kawar da wannan muguwar sha'awar tata dake damunsa ba

Jikinshi yayi bala'in sanyi sosai da sosai

Yace"shikkenan Momy Allah ya nuna mana sai ayi yanda kikace"


"Allah yayi maka albarka,My son"
Momy tafada

"Ameen ameen Momy"

"Yanzu wane shirye-shirye kakeyi, yau tilas kaje gurin Mubina ku gaisa"


"To Momy za'ayi"
Yafada idansa a lumshe


Momy taga duk yayi sanyi tace" naga jikinka yayi sanyi My son ko Na takura maka ne"?


"A'a Momy ina da damuwa ne"


Ita ma jikinta tayi sanyi Yaron ta yana cikin damuwa lallai itama tana cikinta



"Kafadi min abinda duk yake damunka"?
Momy tafada babu alamun wasa a tartare da ita,gaba daya ta maida hankalinta kanshi


Shiru yayi yana da wurwurar abin cikin zuciyarsa yana jin ya fada mata ko kar ya fada mata.



Momy ta kara maimai tamasa tambayarta.


A jiyar zuciya ya sauke gami da bude idonshi sannan ya gyara zamanshi yana kallonta
yace"Momy wani mafarki nakeyi Wanda yake damun zuciyata kuma ba da kowa nakeyi ba sai
da wannan yarinyar ta cikin gidan nan, shiyasa nace miki mayu ne, kinki yadda Momy yarinyar
ta rike wuta a kaina kullum sai tazo cikin bacci Na ta takura min babu dare babu rana Momy ina
cikin musiba"
Ya karashe maganar gwanin tausayi, domin shi abin ma tsoro yake bashi
[02/06/2019 9:11 AM] ®Binta Umar Abbale: Momy tace"wane irin mafarki ne wannan My son"?


Shiru yayi

"Tambayarka nake fa"

"Momy mubar maganar"

"Naqi bari"
Momy tafada kai tsaye idanta tsaye a kanshi


Murmushi yake shima ya zuba ma ido

Momy tsaf ta fahimci abinda yake damunsa

Tace"My son fitinar ka yawa gareta,Allah ya rufa asiri"

Dariya ce ta subuce masa ya dinga yi


Momy itama dariya take tana girgiza kai

Yace"yau hutawa zanyi Momy babu inda zani"


"Gwara ka huta ai,amma dai dole da yamma kaje gurin Mubina ko"


"Eh Momy yanzu ma sabida ita na kashe wayana sabida tun ina jirgi take takuramin"


Dariya Momy tayi tace"soyayarku a ta mussaman ce"


"Wane irin ta mussaman Momy nifa Sam bata yi min ba wallahi Dan dai kawai Na faranta miki
rai ne"


"Nima nasani Myson yarinyar tarbiya bata isheta ba ,amma in dai tana sonka zaka iya juyata
kayi mata tarbiya"



Tabe baki yayi yace"wani babban abin haushi ma ,Hanifa kanwarta tana tan tana tada
hankalinta sai faman shirme take min a waya wai yaya zanyi mata haka"


"Wace Hanifa kake magana"

Momy tafada cikin mamaki


"Kanwarta, itama wai sona take Mtsss


Momy tayi dariya tace"to Allah ya sawaqe,Allah ya kawomu wani zamani ni "yasu"



"Momy shashanci ne da iskanci kawai babu maganar zamani anan"

"Allah ya kyauta"
Momy tafada

Nan dai suka zauna hira sama -sama har wajejan sha biyu Na dare ,sannan Momy tace yaje ya
kwanta


Yana shiga dakinshi ya kunna wayoyinshi nan da nan sakkoni suka rika shigowa, ko sauraron
wayar baiyi ba sai da yayi Wanka yayi shirin bacci sannan ya fara duba sakkonin


Message din Mubina sun fi goma tsaki ya ja yafara duba sakkonin mutanenshi, wayarshi tafara
kara sunan Mubina yana yawo kan fuskar wayar

Kin dagawa yayi har ta katse , ta kara kira a karo na biyu nan ma saura kiris ta katse ya daga
batare da yace komai ba.
[06/06, 01:50] +234 808 996 5176: [03/06/2019 1:18 PM] ®Binta Umar Abbale: [03/06/2019
9:22 AM] ®Binta Umar Abbale: *YARO DA KUDI*
*104*

Mubina kamar ta fashe da kuka tace"Yanzu Nasir ni kake wulakantawa, nafi sati daya ina
kiranka a waya Dan wulakanci kaki dagawa sai yanzu ka gadama"
Tsaki yaja yace"kinga Malam karki dameni, tunda dai na amince shikkenan kuma mai kikeso
nayi miki ku so kike in aje aiki in tsaya dan kin kira waya ina sauraron shirme da shiri ririta, karki
kara yimin makamanciyar magana irin wannan ya karashe maganar yana Jan tsaki a karo na
biyu

Jikinta ne yayi sanyi sosai dama tasan za'ayi haka dashi

Itama sai tau fada tace" kasan bazan jure wannan rashin mutumcin naka ba wallahi

[03/06/2019 1:17 PM] ®Binta Umar Abbale: Kashe wayar yayi kawai bai tsaya sauraronta ba
zuciyarsa sai zafi takeyi ,sakkonin yake dudduba wani kiran ya kara shigowa wannan baby ce
katse kiran yayi nan ma ya cigaba da abinda yakeyi , sai da yaga duba sakkonin sannan ya kira
Sofia a waya cikin turanci suke magana, nan ya ke tambayarta yaya aiki dafatan komai babu
matsala.
Basu jima suna magana ya kashe waya,


Ya dade kafin bacci ya dauke shi, biyar saura Na asubah ya tashi har an idar da sallahr asubah
duk jikinshi a mace yakeyin komai, tun jiya da Momy tafada mishi labarin auran Abdul da
Yarinyar jikinshi yayi sanyi nan falo ya zauna yana Jan carbi Momy na sama bata sakko ba Har
bacci ya dauke shi bacci mai tartare da damuwa da wahala gami da gajiya



Momy ta sakko kamar ko daushe cikin kwalliya, ta tsaya suna magana da Uwani mai aiki,
Uwani tace" naga uban gidana yana bacci a farlo ,Momy ta cikin sauri ta juya tana kallon farlon
Nasir ta hango kwance cikin kujera bacci yake sosai da sosai




Wani irin tausayinsa ne ya kama Momy sai ta zauna kusa da kafafunsa tana kallonsa cikin
tausayi da kauna irin ta uwa da danta , shi kam bai San ma abinda yake faruwa bacci mai nauyi
ne ya daukeshi.
[03/06/2019 2:21 PM] ®Binta Umar Abbale: Sai wajan karfe tara da rabi ya tashi , yana bude
idonshi ya saukesu kan Momy, cikin mamaki ya mike zaune yana mika ya kalleta gami da cewa
"Momy bacci nayi anan"?



"Bacci kayi sosai Myson" Momy tafada tana kallonshi


Agogon hannunshi ya kalla yana mamakin yaya Akayi bacci ya daukeshi a nan batare da ya
shirya ba



"Momy bari in yi wanka " yafada yana mikewa

"Sai ka fito My son"


"Ok Momyna"


Cikin sauri ya kammala komai ya fito ,Momy tace"kazo ka karya yau nasa Uwani tayi maka
kunun gyada gashinan yaji madara"



"Ok Momy"
Kai tsaye daining din ya nufa Momy ts hada mishi yaji madara sosai tace"ko in zuba maka
abinci ne"?


"A'a Momy kunun ma ya isa"

"Kadaure kaci ko yaya ne"

"Momy wannan ma ya'isa kinsan yanayin cikina yanzu sai ya rikice


"Amma dai yau karkayi ciye-ciyen kayan zaqin nan don Allah"
Momy tafada gwanin tausayi


Dariya yake yace"insha Allah Momyna"

Mikewa yayi yana gyara links din hannunsa, yace"zan wuce Momy amma kafin in tafi zan shiga
asibitin in ga abinda yake faruwa"



Momy tace"to Allah ya kiyaye hanya a gaida "yan uwa da abokan arziqi, har waje ta rakoshi
Giss yana tsaye yana jiran fitowarsa,


Yayi sauri ya karbi wata karamar dake hannun Nasir din , ya bi bayanshi inda motarshi take
Momy sai addu'a take ta zabga masa , Tony ya bude masa motar ya shiga da Sauri ya rufe ya
zagaya ya bude mazauninshi ya zauna gami da kunna mota suka fice daga gidan

Maryam ce take bin titi a nutse tana sanye cikin atamfa riga da zani mai kalar ja tayi amfani da
mayafi kalar atamfar, takalmin dake sanye a kafarta mai tsine ne sosai sabida haka a nutse take
tafiya, Maryam najin takaicin tafiyar nan sabida kafin ta fita babban titi akwai tafiya , sosai
yawanci dama duk da motoci suke fita in ba lalura ba babu Wanda zaka gani yana tafiya da
kafa cikin Estet din tunda guri ne Na wane da wane, so take ta fita babban titi domin ta samu
Napep , tayiwa Momy Alkwari zataje yau hospital din, amma in taga da wulakanci bazata jura
ba
[06/06, 01:51] +234 808 996 5176: [04/06/2019 9:18 PM] ®Binta Umar Abbale: [04/06/2019
7:26 PM] ®Binta Umar Abbale: *YARO DA KUDI*
*105*

Tun daga nesa ya fahimci ita ce sai yace ma Tony yaja motar a hankali har suka iso daf da ita,
Nasir ya bawa Giss umarni ya fita yayi mata magana da yawonshi, batare da bata lokaci ba
Giss ya bude Mora domin cika umarnin da aka bashi.
Maryam gabanta yayi wata muguwar faduwa ganin Giss ya tari gabanta domin baza ta taba
mancewa da wannan fuskar ba ,gabanta yana faduwa tace"Lafiya malam kazo ka tare min
hanya"?
Cikin yanayi hausarshi yace" oga ne ya bada Umarnin haka"


Cikin mamaki ta tsaya tana kallon motar , ahankali glass din motar yake yin kasa fuskar Nasir ta
ban yanna, ya dago kanshi gami da kallonta, ita kuwa gabanta ya rika faduwa tamkar qirjinta ya
tsage



Kai tsaye yace"ina zaki je"?

"Ina zakije"?
Maryam ta maimaita maganar cikin mamaki!


Fuskarshi ta kalla taga ya hade fuska tamau!

"Ai kena a kayi"

Maryam tafada kai tsaye

Banzan kallo yayi mata gami da cewa" makaryaciyar banza da wofi, zaki tafi gantali kin dai"
Yafada yana mata wani kallon gani-gani

Maryam ranta yayi mugun baci amma sai ta dake kawai ta kama hanya zata wuce batare da
tace komai ba


Nasir yayiwa ma Giss alama ya shigo su tafi dama so yakeyi ya bata mata rai kuma yayi nasara


Haka Tony yazo ya wuce ta fuuuuuu da mota,


Zuciyarta ta dinga wani zafi, tanaji kamar ta juya ta koma gida kawai amma in ta tuno tayiwa
Momy alkwari sai zuciyarta ta karaya



Haka ta fita babban titi ta samu Napep ta hau kai tsaye (N Alhussen Specialyst Hospital)

A waje tace ya sauke ta tafito tana gyara zaman mayafinta sannan ta bude handbag din ta tafito
da kudinshi ta bashi, sannan ta wuce ciki


Tana shiga taga motashi a harabar gurin a aje Tony a jingeni da ita ,sai gabanta ya ruqa faduwa
da tasan nan zaizo wallahi da babu abinda zai kawo ta ,tasan yau za'ayi wulakanci a asibitin
[04/06/2019 8:32 PM] ®Binta Umar Abbale: Kafin tagama tunani sai ta hangi Nasir din ya fito
tare da Dr Sofia da wasu "yan mata uku a bayansu, kai tsaye gurin motarshi suka nufa sai tayi
saurin kauda kanta tana diri-diri kamar ta ruga a guje


Mamaki ya kamashi ganinta a asibitin zuciyarshi yace tazo kenan.


Ganin sun tsaya suna magana ne yasa ta karasawa gurin da suke din cikin turanci tace"sunana
Maryam Arma Ya'u
Ta mika Dr Sofia hannu suka gaisa

Dr Sofia ta rika tunanin kamar ta San wannan fuskar sabida kwata-kwata kammanin Maryam
din bace mata sukayi

Dr Sofia ta duba takkadun da suke hannunta tana duba sunan domin sai yaga kamar sunan
daya, tabbas hakane, tadago kai tana kallonshi gami da cewa "ita ne wannan kenan"?

Daga mata kai yayi kawai yana kokarin barin gurin batare da ya kalli inda Maryam din take
tsaye ba kai tsaye motar ya shiga Giss yabi bayanshi Tony yaja suka fice


Kallon kallo ake tsakanin Maryam da Sofia domin sai yanzu Sofia ta gane Maryam din


Cikin turanci tabasu umarnin da su biyo bayanta


Haka suka bita har Maryam din


Nan Dr Sofia tabawa "yan matanan biyu uniporm ko wacce tasan matsayinta, sannan ta kalli
Maryam a qasqance
Tace" Ke kuma zaki na mana goge goge da aike-ake a nan in kinga zaki yi to

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login