Showing 27001 words to 30000 words out of 63190 words

Chapter 10 - MALAMIN BOGI COMPLET BOOK by Ameera Adam.pdf

Advertisement

18 Jul 2025

5339

saboda kowa abin da zai nemi magani sirri ne a wajensa bai
kamata ake faɗa ba, hakan ya sa aka yi dogayen layi biyu na maza da ban na mata da ban, aka
ce idan mace ɗaya ta shiga sai namiji ɗaya ya shiga.
Wata mata ce ta fara shiga gidan da sallama, Sheik ya amsa, yana mai mata umarnin ta shiga,
shiga ta yi ta samu waje daga can nesa wajen ƙofar ɗaki ta zauna, shi kuma yana daga kan
sallay ya lanƙwashe ƙafa sai wani ƙaton baho a ajiye daga can bayansa.

Gyaran murya ya yi ya ce

"Mai yake tafe da ke?" Matar wani daɗi ne ya cika mata rai jin muryarsa, sai yanzu take tabbatar
da maganar mutanen gari da ake cewa maganarsa hausar ma bata fita, ba ma wannan ba farar
fatarsa kaɗai ji take kamar wanda ta je garin makka. Cike da ɗan diriricewa irin tana magana da
balarabe ta ce
"Malam dama mijina ne ko kaɗan ba ya kiran sunana, sai ya kira kishiyata sa sunanta amma ni
sai yake kirana madam, kamar wata inyamura mai bashi hayar gida" Ta faɗa cike da takaici don
dama ta daɗe tana son ta magance wannan matsalar amma du wajen malaman da ta je sai a
ce mata wai soyayya ce da girmamawa, waɗanda kuma take ganin sun cinye mata kuɗi ko an
bata maganin ma ba ya yi, amma dai yanzu tun da ta samu balaraben nan wanda aka ce
aljannu ma yana maganinsu, to tabbas ta san ta zo ƙare kukan ka.

Sheik a zuciyarsa ya ce

'Mata masu duniya, mata iyayen kishi wato ita ba wata babbar matsala ba ce da ita ma"' Amma
a fili sai ya ce

"Allah sarki haƙiƙa na jimanta miki, wannan ba ƙaramin abu bane a ce mijinki yana kiranki da
suna madam, kamar dai wata tunkiya, ko kuma bayerabiya mai gasa masara a bakin titi" Ya
faɗa yana ɗan mayar da fuskarsa abin tausayi. Kai ta kaɗa irin ka ji dai ji, a zuciyarta tana jin
daɗi don ta tabbatar da cewa wannan ba sunan soyayya bane ko na girmamawa.
Yana ɗakko wani ƙullin magani ya dube ta da kyau ya ce

"Wannan maganin ki samu ƙatuwar zabuwa ko kaza ki dafa da wannan maganin, ki juye masa
ita duka amma sai ranar bakin girkin ki, kar ki ci ko ƙafar kazar, ki ce masa takanas kika dafa
saboda kina son sa don ki faranta masa, sai ya kusa cinyewa ki ce masa kina da wata buƙata in
ya tambaya sai ki ce daga yau ya daina ce miki madam, zai buƙaci sunan da zai kira ki da shi
sai ki zaɓa ki faɗa masa, daga ranar zai daina kiran ki Madam!" Wani daɗi ne ya baibaye ta,
ashe ma aikin ƙarami ne take ta ƙunsar baƙin ciki, kullum in ta ji ya kira kishiyarta da sunanta ita
ranta ɓaci yake, ta lura idan ya ce mata madam kishiyarta har wata ɓoyayyar dariya ta cusa

haunshi take mata.

Maganin ta karɓa ta ce

"Malam nawa ne abin sadaka" Sai da ya ƙare mata kallo yana son gane tana da halin kuɗaɗe
masu yawa ko kuma kuɗi kaɗan take da shi, sai ya daure ya ce

"Ai abin sadaka ba ya kaɗan ba ya yawa" Ita kuma jin haka sai ta buɗe jakarta ƙarama, ta fito
da wasu uban kuɗi ƴan ɗari biyar-biyar da ƴan dubu-dubu kuɗin gyaɗar yin ƙuli-ƙulinta ne
wanda za a sayo mata buhu guda, mai da ƙarago take na siyarwa, malam sai washe baki yake
a ɓoye yana ganin yana zaune a ɗaki zai ci bati.
Amma sai ya ga ta ajiye kuɗin a gefenta tana ta duba cikin jakar, a tunaninsa wani za ta ƙaro
sai ya ga ta fito da naira hamsin, sai kuma ta ɗauke kuɗin mai yawan da ta ajiye a gefe ta
mayar cikin jakar ta zige zip ɗin, ta ɗakko hansin ɗin da hannu biyu ta zo gabansa tana cewa

"Gashi Malam, Allah ya biya buƙatu, muna godiya babban balarabe na ƙasar larabawa" Tamkar
Sheik ya saki ihu haka ya ji, kamar shi Sheik amma ta bashi hamsin. Tsaye ta miƙe bayan ta
ajiye tana gyara mayafinta, ta juya tana masa sallama, ko amsawa bai yi ba, duk takaici ya ishe
shi, yana jin da na sani dama bai ce mata abin sadaka ba ya yawa ba ya kaɗan ba.
A fili ya ce

"Haka kawai shi fa za a dafawa zabuwa ma ai ya fini morewa, ni da na masa silar cin zabuwar
haka kawai na ƙare a kuɗin siyan goro, yo siyan goro mana hamsin in ba goro ba mai za a saya
da ita" Duk maganar nan da yake cikin hausa sak yake yinta, jin tahowar mutum ya ja bakinsa
ya yi shiru, yana mai yin sauri ya jefa hamsin ɗin cikin bahon gudun ma kar a ganta a gabansa
a zaci kuɗi kaɗan yake karɓa.

Wani saurayi ne gajere baƙi ya shigo da sallama, malam ya amsa saurayin bayan ya zauna ya
ce

"Malam ina da buƙata mai girma"

Sheik ya ce

"Ina jinka" Suarayi ya ce

"Matsalata guda ɗaya duk wajen budurwar da na je bata so na, sai ake cewa ba a son gajarta
ta, kuma wai na yi baƙi da yawa shi ne na ce ko za a bani maganin da zan kore baƙin jinin nan
daga jikina wato a bani maganin farin jini?" Shiru Sheik ya yi yana nazarin maganar, ya ƙara
kallonsa sai ya ga har wani sheƙi baƙin nasa yake, ga wani muni kamar me, hakan ya sa a
ransa ya ce

'Ni ɗin ma da kake gani duk bula ce, a toh ni ma ba farin bane mai ne ba don kar a yi saurin
gano ni ba da man bilicin ɗina zan ke tsiyayewa ina ɗaurawa a leda ina ba masu buƙata irin
taka, to kar a ce ni ɗin ma hakan take gwara in tsaya matsayina' A fili kuma ya ce

"Subhanalla, lahaula wala ƙuwwata illa billa, hasbunallahu wa ni,imal wakil, iyyaka na'abudu wa
iyyaka nasta'in" Saurayin gabaɗaya sai gabansa ya shiga faɗuwa jin abin da Sheik yake faɗa,
don har ya fara tunanin kar a ce aljana ce ta aure shi, ko kuma a ce ba zai taɓa auruwa ba a
haka zai rayu, gashi yana buƙatar aure.
Tun kafin Sheik ya ƙara magana ya ce

"Malam ba dai babu maganin jinyata ba?" Ya ƙarasa kamar zai yi kuka.

Sheik ya ce

",A haba ɗan saurayi ai kowace jinya Allah ya saukar da maganinta, mutuwa ce kawai bata da
magani" Wani gauron numfashi ya sauke ya ce

"Alhamdulillah"

Sheik ya ce

"Matsalarka tana da magani amma da sharaɗi" Ya ce

"Zan bi kowane sharaɗi ne in dai mace za ta amince in na ce ina sonta har ta yarda ta aureni"
Sheik ya ce

"Zan baka wani ruwa da za kake shafawa a fuskarka tsawon kwana bakwai, amma fa ka
tabbatar a kwanaki bakwai ɗin nan ka samu wata ƙwaƙƙwarar sana'a da za take kawo maka
kuɗi, sannan a ranar da ka cika kwana bakwai, ka nufi wajen budurwa da kake so kana zuwa
kafin ka gabatar da kanka ka bata dubu goma" Idanu saurayin ya zaro saboda shi ko kyautar
naira ɗari bai taɓa ba wata mace ba.

Yana kallon Sheik ya ce

"Malam dubu goma? Ni ai bana ba mace kuɗi" Sheik a zuciyarsa ya ce

'Ashe shi ya sa ake gudunka, yo ga muni ga cin zanzana, ma'ana ga talauci ka muni wace
mace ce za ta yarda, da aka bayar da kuɗi ai babu wanda zai ga muninka" A fili kuma sai ya ce

"Wannan shi ne sharaɗin maganinmu" Shiru ya yi sai kuma ya ce in dai da biyan buƙata to zai
yi.

Sheik ya san muddin saurayin nan yake bada kuɗi budurwa ba za ta ƙi son sa ba duk da ba
duka aka taru aka zama ɗaya ba wasu ƴan matan basu da son kuɗi.

Ruwan da Sheik ya tsiyaya masa a ƴar kwalba ya karɓa, ya ce masa na farin jinin ne da kuma
wanke shi da munin mata su daina ganin muninsa, godiya yake kamar zai ari baki, bai san
cewa ruwan ma a randa Sheik ya ɗuro shi ya ajiye, don ya lura in ya ce maganin da ya saya
wajen malam zai ke bayarwa ba lallai ya haɗa kuɗin ya ƙara komawa ya karɓo wasu ba, wanda
ya san zai iya warware matsalarsu ba tare sa magani ba sai ya basu maganin BOGI.

Yana karɓa ya tashi zai fita ba tare da ya bada kuɗin sadaka ba, ran Sheik ne ya ɓaci ganin
zai fita ya ce

"Ɗan samari babu abin sadaka ne ?" Juyowa ya yi cike da girmamawa ya ce

"Ai a gari aka yi sanarwa cewa a zo nan a karɓi magani an samu baƙo daga ƙasar larabawa na
ɗauka ba a biyan abin sadaka" Cike da jin haushi Sheik ya ce

"Hankali za ka taka aljani burubutu a gabanka dama su ne masu karɓar kuɗin sadakar" Da sauri
sairayin ya ja baya yana mai ɗakko dubu biyu hannunsa yana karkarwa ya ajiye a gaban Malam
ya juya cike da tsoro ya buɗe ƙofar ya fita.

Yana fita Sheik ya ɗauke dubu biyu.

Wani tsoho ne ya shigo yana dogara sanda, saboda tsufa har ya ranƙwafa, dakyar ya zauna,
yana sauke numfashin gajiya hannunsa yana karkarwar tsufa jikinsa duk ya yi yaba sannan
kansa da gemunsa duk furfura. Sheik kawai kallonsa yake ya rasa ma mai zai kawo tsohon nan
shi da ya dace ya zauna a gida yakenta sallah yana neman gafara ya jira zuwan mutuwarsa.
"Bakinsa yana karkarwa ya ce

"Ɗana balarabe, na sha wahala a waje wajen bin layin shigowa, yanzu ma ganin an bige ni a
turarreniya shi ne wata mata ta bar min layinta na shigo, ka san ai namiji ɗaya sai a mace ɗaya
aka ake shigowa, shi ya sa ka ga na shigo" Har lokacin Sheik yana mamakin abin da zai kawo
tsohon.
Daurewa ya yi ya ce

"Baba maganin basir kake so ko maganin ciwon baya?" Tsohon ya ce

"Haba ɗan nan balarabe, ni nan maganin maida tsoho yaro za ka bani, wato maganin ƙarfi ka
gane?Ƴan mata ne guda biyu zan ɗauka a rana ɗaya dukansu kowacce budurwa" Mamaki ne
ya mamaye Sheik dakyar ya danne harshen sa ganin bai yi magana da yaren hausa sak ba ya

ce

"Budurwa fa Baba?"
Tsoho ya ce

"Rass kuwa ba ma budurwa ɗaya ba ƴan mata biyu ake saka mini su a lalle gobe za su tare ka
ga kuwa aiki ya ganni dole in nuna musu basu auri tsoho ba"

Shiru Sheik ya yi ya rasa ma abin da zai faɗa masa, kawai ya ɗakko wani garin magani ya ce
ya saka a ruwan wanka ranar da amaren za su tare. Godiya kamar wanda aka bashi maganin
da tsofa zai barshi.

Dubu goma ya ba Sheik amma sai da Sheik ya kama shi ya iya dogara sandar ya tafi.

Wata mace ce mai ƙiba ta shigo, tana wani wurwurga idanu, ganin yadda take zazzare ido
tana wani soshe-soshen jiki sai Sheik ya ji duk ya tsargu, juyawa ta yi ta rufe ƙofar bai lura ta
saka mukulli ba, kuma sai ta cire mukullin, cike da ƙaguwa ya ce

"Mai yake tafe da ke?" Ta ce

"Ina so ka bani maganin da kullum mijina sai ni, sannan ka bani maganin da zan zubawa
kishiyata ta mutu, da wanda idan na shafa a hannuna duk inda kuɗi yake zai zo wajena" Ganin
kamar yadda take magana yanayin ya nuna kamar umarni take bashi ya ce

"Ayya ai ba a kisan kai a wajen nan, kuma kuɗin mutane ai kamar sata ce, zan baki dai wanda
mijink... Bai ƙarasa ba kawai sai ya ga ta tashi tsaye idanunta sun juye ta fara dalalar da yawu,
gabansa ne ya bada rasss ya shiga faɗuwa tamkar zuciyarsa za ta huda ƙirjin ta fito,
gadan-gadan ya ga ta biyo shi, ya ja baya ta matso ya yi wani tsalle sai ya ji ta riƙe masa
hiramin da yake rataye a wuyansa, jin za ta sheƙe masa wuya suka shiga kunce.

Idanunsa cikin nata ya gane aljannunta ne suka tashi ba ita ba ce, salati ya hau janyowa yana
ji a ransa anya ba zai haƙura da maluntar nan ta BOGI kuwa ba? Da gudu suka yi wajen ƙofa
sai lokacin ya lura ƙofar a kulle, idanu ya zaro gabansa yana faɗuwa ganin daga shi sai ita
kuma bashi da nutsuwar mata ruƙiyya, kafin ya yi wani yunƙuri sai ji ya yi ta fisge hular gashin
kansa, salati ya ɗauka a zuciyarsa kafin ya ƙarasa wani ya kamo wani , yana juyowa ya ga ta
tuƙunƙuna hular ta ɗaga rigarta ta totsa hular da gemo da sajen boginsa a bireziya. Kafin ya
gama tunanin asirinsa zai tono ta yi wani kukan kura ta shaƙo shi, rasa abin yi ya yi ya buɗe
baki ya ce

"Gabaɗaya na ƙofar gida ku shigo a guje ana ruwan kuɗi a ɗakin malam" Ya faɗi hakan ne don
a yi saurin kawo masa ɗauki, ya manta da cewa kansa babu hula, haɓarsa babu gemo, gefen
fuskarsa babu sajen larabawa...

MAMAN AFRAH
09025576222

TALLAH TALLAH

*INA MANYAN MATAN SUKE?*
*Masoyana ina ƙara talalta muku kayan sana,ata kamr su*

*Less, atamfa, laffaya, kamfala, mayafai zannuwan gado, kayan yara, takalma na yara da
manya, abayas, huluna na maza, mata, yara frames, sarƙa ɗan kunne zubuna banguls.*

*Akwai kayan maganin mu na kamfanin meera b herbs, maganin sanyi, maganin ƙiba,
maganin rage ƙiba maganin rage tumbi, maganin cire tabo ga wanda suk shafa mai ya ɓata
musu jiki ko fuska, sannan uwa uba maganin mata.*

*A ƙarshe ina tallata muku FURA dakan mai, wacce muke yi mai garɗi da ƙamshin man
shanu, muna yi don biki, ko suna, ko taron naɗin sarauta da dai sauransu muna aikawa ko ina,
akwai nono galan galan da bokitai ga masu buƙata, ku nuna min ƙauna ta hanyar siyar abin da
nake siyarwa* .
*Mai so ya min magana a number ta 09025576222 idan ba saya za ki yi ba kar ki min mgn.*


https://chat.whatsapp.com/BcJ4LIJJQlfHRgfiJUnBJo?mode=r_c


‍♂️ *MALAMIN BOGI*‍♂️


NA

MAMAN AFRAH


First Class Writer's Asso.�

Daga marubuciyar:

Ƙazamin miji
Bonono Rufin ƙofa...
Ruɓaɓɓiyar igiya
Ƴar zaman wanka
Ƙara'in inna delu

Beelal Da sauransu
Ƴan adaidaita sahu
Ungozoma
Jalli joga
Da sauran su.
*09025576222*


BOOK1️⃣
PAGE 8

Sanye take da doguwar rigar less wacce ta kama jikinta, ta yi ɗaurin ɗankwali wanda ya zauna
daram a kanta sai mayafinta wanda yake kala ɗaya da leshin da ta saka, ƙarami ne mayafin
yana rataye a gefen kafaɗarta ɗaya. Ƙaran takalmin ta mai tsine wanda take sakkowa da
saman benen shi ne ya janyo hankalin Hajiya da take zaune a kan kujera tana waya.
Tana riƙe da wayarta ta ƙaraso tsakiyar rangameman falon, lokacin ya yi daidai da gama
wayar Hajiya. Ɗagowa ta yi ta kalle ta, ta ce

"Inyeee ka ga ƴan matan Daddyn ta, kyakkyawar mace kuma matar manya ƴan boko masu
faɗa ji, sanann matar masu kumbar susa" Wani daɗi ne ya mamaye zuciyar Rahma tana jin daɗi
jin furucin da Hajiya ta mata, tabbas a duniya ta tsani talaka, ta tsani talauci kuma, tana son
saurayi ɗan manya wato ɗan gidan masu kuɗi sannan ɗan gayu ko ma dai yaya yake in har za
a iya nunawa sa,a shi to tana son shi sosai. Kai ta langaɓae gefe cikin shagwaɓaɓɓiyar fuskarta
ta ce

"Ai ni sai na zaɓa sai wanda ya isa ne zai aure ni Mummy bana son duk wani namiji in har bashi
da masu gidan rana" Murmushi Hajiya ta yi ta ce

"Da gaskiyar ki ko ni talauci ya yi gabas na yi yamma, kuma ke da kika tashi a gidan naira ai
dole sai ɗan naira" Murmushi ta yi ta ce

"Bari na je baby nah yana jirana" Hajiya ta ce

"Ya zo kenan" Rahma ta ce

"Eh ya zo" Tana faɗa ta kiya cikin takunta na maau aji irin na mata masu ji da kansu.

Yana zaune a wajen da aka tanada don zama a sha iska zaune a kan ɗaya daga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login