Showing 6001 words to 9000 words out of 63190 words
ya ziyarci harshensa, tuni ya tashi yana wata rawar larabawa yana juyi a
tsakiyar ɗakin, gijif ya faɗa kan katifa a reran tsabar murna, ya tashi ya dawo gaban kwanon,
ƙuri ya yi wa kazar yana ɗakkowa yana ɗorawa a kan marfin, tsaf ya irga sai ya ga babu cinyar
kaza guda ɗaya, tsaki ya ja a ransa yana ayyana don maita sai da suka taɓa masa, amma dai
zai sanar da su cewa su a ƙasar larabawa idan za a ba malami kaza kai da ƙafa kawai ake
fitarwa amma ba a cire wani sassa ya faɗa saboda ƙarfin hali.
Tas ya cinye ya shanye wannan ruwan shayin mai uban yawa, dam ya ji cikinsa yana sakin
gyatsa, ta window ya miƙo hannunsa ya wanke, da yake akwai ruwa a ɗakin.
Sai da ya gama danne-dannensa a waya, sannan ya cire hularsa da saje haɗe da gemu ya
ajiye, rigarsa ya cire daga shi sai gajeran wando, kan nan sai sheƙi yake, magungun ƙwaya na
bilicin ɗinsa ya sha, ya kwanta, ya yi ɗai-ɗai a kan katifa, a take ƙoshin da ya yi da kuma samun
ɗaki mai iska ya sanya bacci ya yi awon gaba da shi, ko addu'a bai yi ba, shi ya sha'afa ma da
maganar da Audu ya faɗa masa.
Yana cikin bacci ya fara mafarki da ƴan garin a mafarkin suna cewa
"Sheik, wannan gidan... uhm... ka dai dinga karanta ayatul kursiyyu da suratul Jinn a kai -a kai.
Saboda kowa ya san gidan…” Duk a mafarki ne amma sai da gabansa ya faɗi
Cike da ruɗewa ya ce
" Mai gidan yake? Sheik ya tambaya yana jan carbi da azama.
"Dama... Uhmm... Komai lafiya ne. kawai gidan yana da...” Ba a faɗa masa mene ne a gidan ba
ya farka daga nannauyan mafarkin, gabaɗaya ya haɗa gumi gabansa sai faɗuwa yake.
Lalume ya hau yi a jakar kayansa, ya ɗakko wata rigarsa wacce ta fi jallabiyar da ya cire
tsawo, zai saka amma sai ya kasa saawa kasancewar ta wuyan rigar yake ƙoƙarin sakawa,
ganin bashi da nutsuwar sakawa sai ya rataya ta a kafaɗa, ko sallaya bai shimfiɗa ba ya zauna
a ƙasa ya kalli gabas yana karanta “A'uzubillahi”Har sai da numfashinsa ya fara daidaita.
Yana cikin wannan halin sai ya ji ƙara daga ƙofar ɗaki "Gum, gum, gum!"
Sheik ya yi firgigit! Ya miƙe yana ƙoƙarin lalumo wayarsa sai kawai ya kara ta a kunne yana
faɗin
"Wayyo Mai Gari a kawowa Sheik ɗin yemen ɗauki" Ya faɗa cikin raɗa, sai lokacin ma ya tuna
bashi da number Mai Garin ashe.
Wata iska mai sanyi ta fara ɗaga labulan windown, sai ya hangi wani haske kamar walƙiya ya
wulga, sai ya ji ana buga katako.
Sheik ya miƙa hannu ya ɗakko wani littafi da yake yashe a tsakiyar ɗakin, duk tunaninsa ba
qur'ani ne saboda tsabar ruɗun da yake ciki, buɗewa ya yi yana karantawa, kawai yana girgiza
kai yana cewa
“Wallahi ni dai ban taɓa ganin irin wannan ba a ce ba damina ba ana walƙiya Allah mun tuba"
Ya faɗa yana ɓarkewa da kuka marar sauti, sai dai har yanzu bai ji yana da na sani a kan fitowa
harkar maluntar bogi ta cutar mutane ba.
Yana a haka sai ya ji kamar ana tafiya, ma'ana ya fara jin taku a tsakar gidan, bai san lokacin
da ya yi cilli da littafin hannunsa ba, shi da yake kallon gabas sai gashi ya juya zuwa yamma,
bakinsa yana kaiwa da komowa, wannan karon, babu ƙalƙalar larabcin bogin nasa hausa ce
sak yake yi babu lanƙasa, shi kansa bai san mai yake faɗa ba. Yana cikin wannan hali ya ji wani
sauti ana cewa
"Sheeiiiik Ibra mun san kai ba malamin gaske bane na bogi ne, to ka sani muna sane da
zuwanka wannan ƙauye" Shi da yake zaune ya kalli yamma, bai san ya tashi ba sai ganinsa ya
yi a tsaye ya kalli kudu ƙafafunsa, suna barazanar kasa ɗaukansa, saboda karkarwar da suke,
tunaninsa ɗaya wai aljannun ne suka san da haka ko kuma shi tsohon da aka binne ne ya yi
fatalwa? Tun da gashi har sunansa na asali an kira shi da shi wato Ibra.
Wannan yasa Sheik ya buɗe ƙofar ɗaki da sassarfa, ya fito yana kwalalo ido kamar wanda ya yi
fashi aka kama shi. Ya yi gigin barin gidan da sassarfa.
Cikin sanɗa ya fito daga ɗakin daga shi sai gajeran wando, da rigarsa rataye a kafaɗa,
Yana fitowa ya ji gidan ya ruɗe da surutai kamar ana wani gagarumin taro, bai tsaya wata-wata
ba ya durfafi hanyar ƙofar gida, sai lokacin ya tuna lokacin da ya ɗauki wayarsa ta kawo haske
ya ga ƙarfe biyu da rabi na dare, amma da bala'in da ya fara fuskanta a gidan gwara ya fita.
Cike da tsoro ya buɗe ƙofar gidan, shiruuu garin tamkar babu kowa sai carar zakaru da yake
tashi da kukan dabobi lokaci zuwa lokaci.
Yana fitowa ya kalli, gabas da arewa ya ɗaga ƙafa zai fara sheƙa gudu ya tuna kansa babu
hularsa ta gashin larabawa mai haɗe da saje da gemu, sannan ƙafarsa babu takalmi, uwa uba a
tuɓe yake bashi da riga don bashi ma da nutsuwar saka rigar da take rataye a wuyan, amma
dai ya san ba ƙaramin abin kunya bane ya tafi cikin gari a haka a zo a ganshi da kai a
ƙwalƙwale, kai sunan zuwansa a haka mutuwa kusa don batu ne wannan na tonuwar asirinsa,
yana a wannan halin na cewa ko ya koma ya yi shigarsa ta balarabe, in ya so ko gidan ne sai
ya ce a sauya masa, duk da bashi da hujjar da zai faɗa a sauya masa tun da shi dai ba zai ce
yana tsoron aljannu ba, a wannan yanayin ne ya ji an ce
"Sheik, baby nah ina jiranka mu je mu kwanta" Idanu ya zaro yana mai juyawa inda ya ji sautin
wato ƙofar gidan da ya fito, wata budurwa ce tsaleliya riƙe da fitila mai haske, tana sanye da
sari na indiyawa"
Ga birni ga ƙauye, shi dai ba zai koma gida ba tun da ya san dai budurwar nan aljana ce,
sannan ba zai je cikin gari a haka ya bugawa mutane gida ba, tun da gidan kusan shi ne na
ƙarshe a inda yake, ganin ta doso inda yake sai fitsari ya suɓuce masa, ya fara sakin wata tusa
mai ƙara a kai- a kai...
MAMAN AFRAH
09025576222
[6/28, 6:21 PM] Mom mashkr & Afrah: https://chat.whatsapp.com/EBurrU2vz6OFGbE37xLhPS
♂️ *MALAMIN BOGI*♂️
NA
MAMAN AFRAH
First Class Writer's Asso.
Daga marubuciyar:
Ƙazamin miji
Bonono Rufin ƙofa...
Ruɓaɓɓiyar igiya
Ƴar zaman wanka
Ƙara'in inna delu
Beelal
Ƴan adaidaita sahu
Ungozoma
Jalli joga
Da sauran su.
*09025576222*
BOOK1️⃣
PAGE 3
*ƘAUYEN MAI MANGWARO*
Lami matar Sheik tun daga lokacin da ya tafi take cike da tsammanin jiran dawowarsa, tana
son idan ya kawo kuɗin nan ta ɗauki nata ta mayarwa mai saniya nata, shi ma Ibran ta
sammasa wani abu daga ciki saboda ta san shi da idon son naira. Tun bayan sallar la'asar
motocin kasuwa suka fara dawowa, tun daga lokacin take ta sintiri wajen da motocin suke
sauka amma duk motar da ta kawo mutane bata samub mijinta a ciki,duk sai ta shiga damuwa
tana fatan dai ba saniyar ce bata siyu ba, ko kuma ta ƙi yin daraja shi ya sa bai dawo da wuri
ba, duk da ta san ta faɗa masa ya siyar ko ma nawa ne ita ba asarar ta bane indai ta ɗauki
kuɗinta. Dab da magriba tana tsaye riƙe da tsantsa ta rasa mai yake mata daɗi, don zuwa
lokacin hankalinta ya fara tashi, tana tsaye kamar daga sama sai ta ji an fisgi kafaɗarta,
juyowarta ke da wuya idanunta ya sauka a kan Jummai tudun adashe, tana wani muzurai sai
huci take kamar kububuwa.
Rai Lami ta haɗe itama tana aika mata harara, cike da masifa Jummai ta ce
"Lami ashe baki da hankali ashe tunanin yara ne da ke, saniyar marayun kike je kika kunce? Ina
kika kaita, kin san dai tsohon mijina da ya mutu gadon ƴaƴana da aka bani na saya saniyar nan
tun tana ƙanƙanuwa na kiwata musu ita, a kan wani kuɗin adashe ki je ki since mini ita?" Ta
faɗa tana dawowa gaban Lami har zanin Jummai yana neman kuncewa ta gyara. Kallon ko in
kula Lami ta jefe ta da shi ta ce
"Wato kuɗin adashe ba kuɗi bane ko? Saniyar marayu ita ce abun kirki da tattalawa... Katse ta
Jummai ta yi da cewa
"Ni ba wannan ba mu je ki bani saniyar nan tun muna mu biyu kin dan dai ta marayu ce na faɗa
miki" Wata dariyar rainin wayo Lami ta yi ta ce
"To sai su ɗauki na annabawa, ki jira dawowar Ibra mijina daga kasuwa in ya kawo kuɗin
saniyar sai in ɗauki kuɗin adashena in baki ragowar in ya so sai ki sayi wata ƙaramar ki kiw...
Tun kafin Lami ta ƙarasa Jummai ta wani zaro idanu tana dafe ƙirji ta ce.
"Kanki ɗaya kuwa Lami?Saniyar kika bada aka kai kasuwa?" Ta faɗa cike da takaici dama
dawowar ta kenan, aka faɗa mata ko gida bata je ba ta kama hanyar gidan Lamin shi ne ta
hange ta tsaye.
"Ras kuwa, ai da nake kai miki kuɗin zubin adashen kike karɓewa baki taɓa sanin kaina ɗaya
ne ko ba ɗaya ba sai yanzu da na ɗauki saniya" Masifa Jummai ta shiga yi tamkar za ta hau
Lami fa duka, ita ma da ba kanwar lasa ba suka haɗu suna yi har mutane suka fara taruwa ana
basu haƙuri, Jummai tana cewa ko Ibran ya dawo da kuɗin daga kasuwa sai ya koma ita
saniyar ta kawai ta sani.
Wani dattijo yaa basu haƙuri a kan a jira Ibra ya dawo amma har motar ƙarshe ta kasuwa ta
dawo amma babu Ibra a ciki, nan hankalin Lami ya tashi don ta fara wani tunani da ban, sai da
ta samu wani direban motar shanayen da Ibra ya shiga ta tambaye shi, nan yake ce mata suna
sauka a kasuwa ko cikin kasuwa Ibra bai shiga da saniya ba, aka fara tayawa, nan ya samu
wani ya saya ya bashi kuɗin don har la'ada ya bayar.Ya ce wata mota ma Ibra ya shiga, don a
yanayinsa ma bashi da niyyar komawa Mai Mangwaro. Jummai kamar ta yi hauka sai zage-zafe
da tsinuwa take, amma kuma tana riƙe da mayafin Lami a kan cewa ƙafar Lami ƙafarta sai ta
nemo Saniya, magana ya girmama har gaban mai gari.
Bayan an faɗawa mai gari komai, sai ya rasa ma yadda za a yi da Ibra tun da komai dai na
maganar yana hannunsa, don haka sai mai gari ya aika wani yaro ya zo da Tasallah kakar Ibra,
yaron da zuwansa ya samu Inna Tasallah tana kwance a kan tabarma daga yin sallar isha'i ta
ɓingire a kan sallayar. Sallamar da saurayin yake rafkawa ita ta falkar da ita daga ɗan baccin da
ya ɗauke ta.
Bayan ya gaishe ta ya ce
"Inna saƙon kira ne daga fadar mai gari" Inna warai ta ware daga ɗan baccin, tana zaro ido da
mamaki ta ce
"Idirisu Allah sa dai lafiya, ya za a yi a ce mau gari yana kirana da wannan daren?" Idrisu ya ce
"Inna Ibra ne dai yake son tada miki zaune tsaye, ya karɓi saniya a wajen Lami, kuma saniyar ta
Jummai ce, kasuwa Lami ta ce ya kai ya siyar amma har kowa na kasuwa ya dawo amma babu
Ibra, yanzu dai suna can gufane a gaban mai gari Jummau ta ce sai an biyata" Salati Inna
Tasallah ta shiga zabgawa tana tafa hannuwa ta ce
"Wannan yaro an yi taƙadari, yanzu Ibra ina zai je da saniyar mutane, a ce mutum ya girma bai
san ya girma ba, yanzu a ce mutum da iyalinsa shi ba wani yaro ba amma sai jan rigima, ni
yanzu ai ni ya tsunduma a masifa, ni da ko kaza bani da ita, wallahi Ibra albasa bata yi halin
ruwa ba, iyayensa mutanen kirki ne amma tun da suka mutu nake jigila da shi, tun yana yaro
bai barni na huta ba" Ta faɗa tana fashewa da kuka irin na tsofaffi.
Haƙuri Idrisu ya shiga bata, taba goge idanu tana face hanci ta shiga ɗaki jim kaɗan ta fito da
wata roba mai ɗan girma tana riƙe da ita, waje suka fito ta saka mukulli ta kulli gidan, suka farw
tafiya ta shiga faɗin
"Wannan kalwa da barkonon da kuka da suke cikin robar wannan su kaɗai ne mallakina a
duniyar nan, su nake kira suke amsawa, yau ban da cinikin naira ɗari ban yi ciniki ba, ita ma
ɗarin gata nan a cikin robar, idan mun je ko da an buƙaci wani abu daga gareni in biya kuɗin
saniyar sai in juyewa mai gari wanann kayan don su kaɗai ne da ni.
*GIDAN ALHAJI ADNAN JIBO*
Hajiya Nuritya ce zaune a tangameman falon ta da ya gaji da kayan alatu, tana zaune ta harɗe
ƙafafunta hannunta riƙe da waya ƙirar iphone 16 pro mx sai wani ɗan yatsina fuska take lokaci
zuwa lokaci. Shigowar mai aiki falon ɗauke da tire wanda aka ɗora plate da ta yanka kayan
marmari, ko sallamar da ta yi bata amsa ba, haka ta ƙarasa gaban Hajiya Nuriyya ta durƙusa ta
ajiye tiren tana mai cewa
"Barka da hutawa Hajiya, na kammala yankawa" Shiru Hajiya ta yi bata amsa ba, kamar ba za
ta yi magana ba zuwa can ba tare da ta kalli mai aikin ba ta ce
"Ki je ɗakin Rahma ki sanar da ita kin gama yanka mata" Da to ta amsa cike da girmamawa,
sama ta haura ta je ƙofar ɗakin ta tsaya, tana tsoron ta ƙwanƙwasa ta yi laifi, amma haka ta
daure son babu yadda za ta iya tun da in bata sanar da ita ba ɗin ma, laifin ne gwara dai ta
sanar ɗin.
Kamar tana jin tsoro haka ta shiga ƙwanƙwasawa a hankali, duk don gudun laifi" Sau biyu
kawai ta buga sai ta dakata tana jiran jin amsa, tun da ta san dai in har idanun Rahma biyu to
tabbas za ta ji bugun sai dai amsar ce sai an kai ruwa rana.
Sai da ta ɗauki kimanin minti biyu zuwa uku tana jira sannan ne cikin muryar Rahma mai
sanyi ta ce
"Waye?" Cike da girmamawa ta ce
"Ni ce Hajiya ta ce an gama yanka kayan marmarin"
Cike da izza Rahma ta ce
"Na ji" Baki mai aiki ta taɓe tamkar Rahma tana ganinta, juyowa ta yi ta bar ƙofar ɗakin, tana
zuwa ta sanar da Hajia ta fita don zuwa ta cigaba da aikinta.
Sai bayan kamar minti goma sha biyar, sai ga wata kyakkyawar budurwa wacce ba za ta fi
shekaru ashirin ba kuma ba za ta gaza shekara sha tara ba, tana tafiya kamar bata so, sanye
take da fararen kaya tas riga da wando a jikin gaban rigar an yi zanen heart da pink colour, sai
aka rubuta BEAUTY.
Kyakkawa ce ajin farko, sai dai bata da ƙiba, ƙarasowa ta yi ta zauna a kusa da Hajiya
Nuriyya, Hajiya cike da soyayya da son nuna kulawa ga tilon ƴar tata, ta ajiye wayar hannun, ta
mayar da hankalin ta kanta ta ce
"Mai kike so ne eh baby nah?" Ta tamabaya tana kallonta cike da soyayya.
Ɗan yatsina fuska ta yi tana ɗan tura baki ta ce
"Fruit ɗin ne ba zan iya ci ba" Ta faɗa cikin muryar sangartattun yara.
Murmushi Hajia ta yj ta ɗakko ta shiga bata, suna cikin haka sai Alhaji da Yaya Ma'aruf suka yi
sallama suka shigo, Yaya Ma'aruf ɗan gidan yayan Alhajin ne a ƙauye yake shi ne ya zo karatu
birni ya sauka a gida ƙanin mahaifin nasa.
Yaya Ma'aruf mutum mai ibada da kula da addini, yana son ganin mutum yana riƙo da sallah,
sai dai kuma ya sauka a gidan kawunsa inda yake ganin ana wata rayuwa ta da ban.
Da gudu Rahma ta tashi ta je ta rungune mahaifinta