Showing 39001 words to 42000 words out of 63190 words
bata tsaya rufe gida ba don abin ya girmi
tunaninta yadda ta ga Mai Gari yana zabgar gudu ta san tabbas akwai lauje cikin naɗi.
Baya ta take masa sai dai kafin ta je ya shige ɗakinsa ya banki sai ƙaran saka sakata ta ji,
nata ɗakin ta nufa, wanda tana shiga ta rufe ƙofar runawa da ta yi sakatar ta cire, sai kujerar
zaman tsakar gida ta mata ta saka a bayan ƙofar ta zauna tana haki tana tunanin to ina
Balaraben Malamin garin nasu da yake yaƙar aljannu.
Washe gari sai da gari ya waye tangararai aka fito sallah, saboda ƙarfin hali irin na Sheik ya
baro wata baƙar rigar jallabiya tana ta sheƙi ta ƙara haska shi, ya sheƙa uban turaren oud, ya
fito yana jan carbi, yana muzurai don kar a kawo masa raini, a haka ya ja sallar, bayan an idar
ya zauna a mazauninsa bayan ya juyo ya fuskanci mutanen masallacin ya ce
" Alal haƙiƙa jiya mun haɗu da wani ibtila'i, wanda aka samu wani aljani marar imani ya shiga
jikina don kawai yana son ya rikita wanann gari ku shiga halin ha,u'la'i, saboda sun san ni kaɗai
ne zan kawo mafita a wanann gari, sun san ni zan magance duk wata matsala da za ta tunkaro
gari, shi ya sa suka tura mini wani ƙasurgumin aljani ya shiga jikina, sai da daddare na ƙure
karatun qur'ani a wayata sanann na hau yi wa kaina da kaina ruƙiyya, a nan ne da ya buɗe baki
ya yi magana na gane ashe ba ni bane aljani ne" Kowa ya yarda da maganar Sheik sai suka ji
dk ya fara basu tausayi don sun yarda da abin da ya faɗa.
Mai Gari da yake da shi suka yi gudun famfalaƙin da Sheik sai ya kalle shi da mamaki ya ce
"Yanzu dama Sheik duk wannan abin da muka yi na gudun ceton rai ba kai bane?" Wani yawu
Sheik ya haɗiye jin kamar dai tambayar ta yi kama da tambayar tuhuma ko rashin yarda.
Cikin son ya kankarowa kansa mutunci ya ce
"Ashsha Mai Gari, haba kai kuwa ni ne zan yi gudu saboda gawa? Ko ana ha maza ha mata ai
ba zan yi gudu ba, sannan kuma ina horar mutane a kan rashin dacewar tuhumar malaman su
musamman malaman larabawa ko abu suka yi ba daidai ba, ba a tambayar mai ya sa" Shiru
Mai Gari ya yi sai ya ce
"Ni ma duk mamaki ne ya cika ni, ni ina ta gudun gawar yaro ashe ina tafe da aljani" Ya faɗa
yana ji babu daɗi.
Haka dai Sheik ya yi ta kawo maganganun da zai kama zuciyarsu, ya ringa faɗar maganganu
masu shiga rai, saboda cewa ya yi ma ko joya da suka ji shiru bai fito ba aljanin ne da bai sake
shi ba shi ya sa bai fito jan sallah ba, basu san abin da ya hana su fitowa ba shi ɗin ma shi ne
ya hana shi fitowa wato tsoro.
A ƙarshe dai ya ce musu wannan yaron ba mutum ba ne, aljannu ne suka ɗauke gawarsa
wanda ya taso ya shigo gari aljani ne ya yi shigar yaron, sai washe bari aka ga gawar yaron a
ƙofar maƙabarta, haka dai Sheik ya ari jarumta aka binne yaron.
Bayan sati uku, komai ya kankama, a inda mata suke tururuwar zuwa wajen Sheik karɓar
magani, gabaɗaya a sati rana biyu ce ta maza amma kwanaki biyar duka mata ne aka warewa
suke ziyartar Sheik ɗin.
Hatta ƴan mata suna layi a wajensa, maganin farin jini, maganin karɓar kuɗi a hannun
saurayi, maganin samun bazawari marar mata, haka suka yi ta zuwa suna karɓar magani,
Sheik kuma kasuwa ta kankama yana ta damƙar kuɗaɗe.
A wata ranar laraba ne Sheik ya yi arba da wata budurwa da iyayenta suka kai masa ita ya
mata ruƙiyya tun da ya ɗora kansa a kan yarinyar nan ya ji ya kamu da son ta, yana so ya aure
ta amma kuma yana tsoron su mutanen gari su zargi wani abu ko ma wani ya harbo jirginsa, a
ga shi yana balarabe ya ce yana son baƙar fata, amma dai ya fara ƙagauta da zama babu mace
ya baro matansa biyu.
Shiru ya yi a fili ya furta
"Ba za ta saɓu ba bindiga a ruwa, in baro mace tana gugar mace har mata biyu amma in zo ina
zaman gwauranci, shi ma Mai Garin ban da sakarai ne ka bar baƙo babu mace haba ko da na
ce ni malami ne ina kwaana sallah da salatin annabi S.A.W ai ni ma ba dutse bane kuma ba
katako bane da zan ƙare kullum a cire aljannu da bayar da magani, ina nan ina zaune da abu
sanƙamƙam a jallabiya" Ya faɗa yana jan wani dogon tsaki.
Bayan kwana biyu da yamma ya ce zai yi lazimi ya dakatar da ba maza magani dama ranar
maza ce, shi kuma ya fi son ranar mata saboda wuni yake yana wadaƙarsa yana kallon su
shegen son mata.
Kuma maza basa bada kuɗin sadaka da yawa, amma ya fi morar kuɗin mata.
Yana kishingiɗe bayan ya gama kallon film a wayarsa, wanda ya sauke a youtube, wayar da
ya cewa su Mai Gari wayar babu komai sai karatun qur'ani.
Ɗan baccin da ya ɗauke shi ne yake mafarkin ya auri budurwar nan da ya ɗora rai. Bugun
ƙofar gidan ne ya falkar da shi, ji yayi ana ta rafka sallama, ya taso ya leƙo, jin ana hayya-
hayya, wata matashiyar mace ce aka shigo da ita maza ne ƙattai uku sun riƙo ta tana togewa,
dakyar ake janyota sai kamce saniya, da wata mata tana share hawaye da alama mahaifiyarta
ce, sai da Sheik ya kalle ta ya gane ido ɗaya ne da ita.
Aljannunta ne suka tashi, ɗaki aka sakawa Sheik ita duk da yana jin ɗarɗar haka ya shiga
mata ruƙiyya kafin a gama ruƙiyyar ta haɗa shi da ƙasa sau uku, yana cikin bayan ya fitar mata
da aljannun sai ta miƙe ƙafa ta ƙura masa idonta guda ɗaya har sai da ya tsargu, ko kuɗin
sadaka bai karɓa ga burinsa kawai su fitar masa ita.
Da daddare yana zaune ya gama cin abinci sai ga Mai Gari, Liman, da wasu dattijai guda uku,
suka zauna aka sake gaisawa, Mai Gari ya yi gyaran murya ya ce
"Ya Sheik a matsayina na Mai Gari na zo da wata buƙata" Buɗar bakin Sheik sai cewa ya yi
"Haba Mai Gari ai babu abin da za a nema a rasa a wajensa, har da cewa ya yi alƙawari tun bai
ji abin da ake buƙata ba.
Mai Gari ya ce
"Wannan yarinyar da ka yi wa ruƙiyya da yamma mai ido ɗaya... Gaban Sheik ne ya faɗi
tunaninsa ko za a ce aljannun ne suka sake tashi, saboda dama dai ya san lafawa suka yi ba
wai sun bar jikinta bane.
Mai Gari ya cigaba da cewa
"Aljannu sun karɓi ƙarfin jikinta, sun hana ta sakat sun ce sai an ɗaura mata aure da kai, in ba
haka ba wani gagarumin bala,i zai sauka a garin nan sai sun kashe rabi da kwatar jama,ar
gari...
MAMAN AFRAH
09025576222
[7/11, 4:08 PM] Mom mashkur & Afrah: IMZEEDVENTURE
https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt
Duniyar kayan kitchen da na yara masu kyau da araha!
Kina neman kayan kitchen masu kyau, luxury da adashe, ko kayan yara masu kyau da tsada ko
gonjo mai kama da sabo?
To shiga group ɗin IMZEEDVENTURE!
Za ki sha mamaki! Muna da:
✅ Adashe na kayan kitchen
✅ Kayan yara sabbi da gonjo
✅ Kayan gyaran gida da na mata masu kyau
Tuntuɓi mu: +234 707 753 2253
DM: WhatsApp
IG/Tiktok: @imzeed_venture
♂️ *MALAMIN BOGI*♂️
NA
MAMAN AFRAH
First Class Writer's Asso.
Daga marubuciyar:
Ƙazamin miji
Bonono Rufin ƙofa...
Ruɓaɓɓiyar igiya
Ƴar zaman wanka
Ƙara'in inna delu
Beelal
Ƴan adaidaita sahu
Ungozoma
Jalli joga
Da sauran su.
*09025576222*
BOOK1️⃣
PAGE 11
*RAHMA*
Tsabar firgici da mamakin furucin Ma'aruf tsaye ta miƙe, shi kuma Ma'aruf ganin Sulaiman sai
hakan ya sanya ya shafawa idanunsa toka, don a yau ya ci alwashin babu gudu babu ja da
baya, dole ya bayyana sirrin zuciyarsa ko ta halin ƙaƙa ko da kuwa hakan zai zama sanadiyyar
afkuwar gagarumar matsala.
Hannu biyu ya saka a aljuhunsa ya yi wata irin tsayuwa ta yaran zamani, in ban da su da
suka san shi kuma suka raina masa hankalin cewa shi baƙauye ne babu wanda zai ce ya taɓa
zama a wani ƙauye, cike yake yau da kwarjini haɗe da haiba kyawunsa ya ƙara bayyana, yana
sakin wani shu'umin murmushi, yana mai kafe masoyiyar tasa Rahma da idanunsa da ta ji sun
zame mata tamkar miki, don yau sai ta ji ya mata wani kwarjini sai dai ba za ta bar kwarjininsa
ya rinjayi zuciyarta ba, dole za ta tauna tsakuwa don aya ta ji tsoro, saboda ma kar ya yi gigin
furta wata kalma a gare ta.
Mummy kuwa kallon ƙasƙanci da raini ta shiga jifan Ma'aruf da shi, ganin yana tsaye a inda
tilon ƴarta take sannan ga ɗan minista da take fatan ya zama sirikinta wato Sulaiman.
Sulaiman kuwa tun lokacin da ya ji furucin Ma'aruf sai zuciyarsa ta buga, tsanar da ya yi wa
Ma'aruf ɗin ta ƙara linkuwa a zuciyarsa, a gefe ɗaya su duka yana jifansu da kallon tuhuma,
musamman tauraruwar tasa wato Rahma.
Rahma ita ta rasa ma abin cewa don furucin Ma'aruf ya bata ɗimbin mamakin da ta kaaa furta
uffan duk da a ƙoƙarinta na ganin ta masa tatas.
Mummy ce ta katse shirun da ya ratsa wajen, da kuma kallon tuhumar da wasu suke jifan
wasu, sannan da zulumi da taraddadin da zukatan wajen suke ciki ta ce
"Ma'aruf lafiyarka kuwa, wanann wane irin daƙiƙanci ne? Ko an faɗa maka bakin rijiya wajen
wasan makaho ne" Ta faɗa tana masa alama da hannu na tambaya. Amma abin mamaki
maimakon ya girmama ta kamar yadda yake yi a kullum sai ta ga ya ɗan murmusa ya ce
"Mummy ina baki haƙurin furucina sai dai, furucin da zan yi yanzu zai sha gaban wanda kika
saurara, amma sai dai ina so matsayinki na Mummynah ki tayani neman karagar mulki a zuciyar
Rahm... A ƙufule Mummy ta ɗaga masa hannu alamar dakatarwa tana huci kamar kumurcin
zaki ta ce
"Allah wadaran naka ya lalace wai jakin dawa ya ga na gida, an faɗa maka ni ina da wani ɗa a
duniya da ya wuce Rahma? Idan mafarki kake ka falka daga mummunan mafarkin da kake yi,
ka wartsake idanunka ka san da wa kake magana, Rahma ta fi ƙarfin talaka baƙauye irinka ka
taka a sannu in ba haka ba za ka ɗakko ruwan dafa kanka" Rahma ce da ƙwallar takaicin
furucin Ma'aruf ya cika mata ido saboda takaicin cewa yana neman karagar mulkin zuciyarta ta
shiga nuna shi da yatsa ta ce
"Wallahi ahir ɗinka, ko giwa ta faɗi ka sani ta fi ƙarfin gawurtattun karnuka, wallahi, wallahi,
wallahi, idan har baka taka a sannu ba za ka yi da na sani na har abada, rainin ma ya yi yawa,
ni Rahma kake wa wannan furucin? Ina so ka sani matsawar baka dawo cikin hankalinka ba to
za ka taka dakalin da yake ɗauke da ruwan ɗanyar kuɓewa, a ƙarshe ka zame ka karkarye a
banza a wofi" Ta faɗa tana hayayyaƙo masa.
Sulaiman fara takawa ya yi a sannu sai da ya zo har gaban Ma'aruf ya tsaya, kallon kallo aka
shiga yi, tsakanin Ma'aruf da Sulaiman, shi Sulaiman ransa a mugun ɓace shi kuma Ma'aruf
yana sakin wani shu'umin murmushi.
Hannu Sulaiman ya sanya a cire glases ɗin fuskarsa, ya kafe Ma'aruf da idanunsa da takaici
ya sa suka yi jawur, yana masa wani kallo irin na raini, ba komai yake baƙanta masa zuciya ba
sai yadda Ma'aruf ya fi shi kyau da cikar haiba, kai zai iya cewa Ma'aruf ya fi shi komai kuɗi ne
kawai zai Sulaiman zai faɗa masa.
Sai dai inda gizo yake saƙar shi ne, Sulaiman babu ɗigon ko da son Rahma a zuciyarsa, ba
komai bane a zuciyarsa sai yaudara yana so ne kawai ya raba ta da mutuncin ta, shi ya sa ya yi
amfani da zaƙin baki da nuna soyayya da kulawa na ƙarya har ta amince da shi, a halin yanzu
duk ta rabu da samarinta duk da dama su ɗin ma za ni ce ta tarar da muje mu, ma'ana babu
wani na kirki duk ƴan ƙarya ne ƴaƴan manya masu kuɗi.
Baƙincikinsa ɗaya shi ne ya fahimci matsawar Ma'aruf ya furta so ga Rahma to ko da a ce
bata son sa to zai yi iya yinsa ya ga ya hana shi cim ma burinsa, haka ya fahimta saboda ya
lura ko a cikin gidan za su hira, sai yake neman zame musu ƙadangaren bakin tulu, yana hana
su rawar gaban hantsi.
Ba ma wannan ba kawai zuciyarsa ta bashi raina masa hankali suka yi, ma'ana ya fara zargin
Rahma tana son Ma'aruf ne in ba haka ba ya zai zo ya tarar da su a lambu tare ya yi shiga mai
kyau, sannan shi da kansa ya ji Rahmar tana faɗin wasu kalmomi na soyayya ga Ma'aruf shi ma
kuma Ma'aruf ɗin ya mayar da martani, zuciyarsa ma ta bashi cewa zuwan Mummy wajen ne ta
musu alama da cewa ya iso wajen shi yasa suke masa wasa da hankali suke raina masa wayo.
Ya dara tunanin kawai ma amfani ake yi da shi ana cin kuɗinsa.
Hannu Sulaiman ya kai ya dafa gefen kafaɗar Ma'aruf amma sai Ma'aruf ya saka hannu ya
ɗauke hannun Sulaiman daga kafaɗarsa ya warɓar da shi, daga Rahma har Mummy baki suka
saki saboda yau ɗaya Ma'aruf ya sauya musu, ran Sulaiman ne ya ƙara ɓaci a ganinsa wannan
baƙauyen har ya kai ya masa haka? A ƙufule ya nuna shi da yatsa ya ce
"Kai ƙaramin ƙwaro, ƙaramin ɗan iska, ina so ka sani ko da mai ka zo an fika, ruwa ba sa'an
kwando bane kuma ni na fi ƙarfin in yi tarayya da kai a wajen mace ɗaya... Rahma jin wannan
furucin sai ta lumshe idanu, tare da sakin wani murmushi saboda ta lura Sulaiman zai ladabtar
sa Ma'aruf ko da kuwa da kalamai ne, Mummy kuwa jinjina ta hau yi wa Sulaiman a zuciyarta,
tana jin gwara ma a bar shi da Sulaiman ɗin ya nuna masa kudu ba arewa ba ce.
Sai dai me? Sai suka ji saɓanin abin da suke tunanin ji wato Sulaiman ya cigaba da cewa
"Don haka in dai Rahma ce ka je na bar maka" Daga Mummy har Rahma sai da gabansu ya yi
mummunar faɗuwa, suka shiga zare ido jin za su yi babbar asarar ɗan masu kuɗi, duk da suna
da kuɗi amma sun san Sulaima tsani ne a wajensu na cim ma wasu burika a rayuwarsu.
Da sauri Rahma ta matso tana kafe Sulaima da idanu ta ce
"Ka san mai kake faɗa kuwa Baby? Yanzu my love wannan ƙazamin kake yi wa furucin ka bar
masa ni, in ce dai wasa kake ko?" Ta faɗa tana kallonsa don so take ta ga ya wawwanke fuskar
Ma'aruf da kyawawan maruka, don ya zame masa izna kuma darasi a nan gaba, don su basa
so su masa wani abu cibi ya zama ƙari idan Daddy ya dawo.
A zuciye Sulaiman da yake jifan Rahma da kallon tsana ya ce
"Ke dalla malama dakata! An ce miki kowa sakarai ne, ko kin ɗauka ni ɗin ma sakarai ne irin
samarin da kika yaudara saboda kin same ni kika sallame su? To ni da hankalina, na san abin
da nake, ni za ki rainawa hankali, in zo in same ki kuna soyayya amma ki nuna mini bariki, to ni
nan na fiki sanin bariki idanuna a buɗe suke yadda bakya zato" Ya faɗa yana hayayyaƙo mata
tamkar zai kai mata duka.
Ma'aruf ya ji daɗin hakan ya san kuma ko da bai auri Rahma ba to tabbas ya cire mata mugun
iri a rayuwarta, saboda ya san Sulaiman mayaudari ne ba don Allah yake sonta ba, yana
amfani da ita ne saboda cim ma wata dama tashi daga ya samu biyan buƙata ya tabbatar zai
cikawa rigarsa iska, in ma bai barta da guzurin