Showing 1 words to 3000 words out of 72993 words

Chapter 1 - Auntyn Yara Book1 Complete Hausa Novels By Sadnas.doc

Sadnas   

06 Sep 2025

198

??ࡱ?>?? +???????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????'????

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F, WordDocument????"0Table?????????Data
???????????????????? P? C
KSKS?"?????????pp5555?\?$5??????????$??*p55??5555?????????5 [7:07am, 4/2/2017] Sadiya Taheer: BISMILLAHIR RAHMANUR RAHEEM...


??@]???]AUNTY'N YARA??8]???]

Written by Sad-Nas
&
Hama gee muh'd



1-2 Had'ad'd'un motocine guda uku ne suke wucewa 406 ne a gaba,se prado a tsakiya, sannan benz a karshe suna tfy a titin GIREI local government.
Daga nesa kuwa wani tsohone kwance akan titi yanata birgima,sega wata budurwa tana rik'e da kwanon abinci da kuma ruwa mai sanyi tana tfy a gefen titi se idonta yakai gun wannan tsohon daya fad'in.
"Da sauri ta ajiye abinci tayi gun wannan tsohon da bisimillah sannan ta d'agoshi tana cewa sannu baba lfy? Meke damunka? Ita kanta tasan bazata samu amsar tambayanta daga gareshiba gashi babu yadda zatayi seta hango motocinnan suna zuwa. Kwantar da tsohon tayi ta mik'e tare da tsayawa akan titi tanata k'ok'arin tsaida motocin amma sam basu da niyan tsayawa. Ganin halin da tsohon yake cikine setak'i matsawa akan titin dole dai 406 d'innan ya tsaya ganin budurwan tak'i kaucewa. Da saurinta ta k'araso gun motan tanata buga glass, d'aya daga ciki ya sauke glass d'in gaba yace ke wace irin...bata bari ya k'arasaba tace dan Allah malam fito ka taimakamin wancan tsohon ya fad'i bansan meke damunshiba. Suka kalli junansu sukace bazamu iyaba, mamaki ya cikata seta rabu dasu taje gun pradon tanata buga glass d'in gaba dana baya. Glass d'in baya aka sauke nidai SAD-NAS idanu na bud'e da kyau dan ganin wani had'ad'd'en saurayi a ciki yana sanye da suit fari tas k'amshine kawai yake tashi. Budurwan ta had'iyi yawu sannan tace bawan Allah pls ka taimaka min wancan tsohon yana neman taimako sannan ni kad'ai bazan iya d'agashi daga kan titiba shiyasa na tsai daku. Cikin mamaki seya cire glas d'in idonshi ya ajiye a gefensa sannan ya bud'e mota ya fito batare daya ce mata komai seyayi mata nuni da hannunshi alaman muje. Da sauri ta wuce gaba yana biye da ita har suka k'arasa gun tsohon,budurwan tace toya ka tsaya kuma d'agashi ka maidashi gefe mana, saurayin yana kallonta har cikin ido yayi magana a hankali yace to ai ke nake jira mu d'agashi tare. Mamaki ya kamata tace yanzu kai a matsayinka NAMIJI bazaka iya d'agashiba harse na taimaka maka? Kai kawai ya d'aga mata alamar EH. Ba musu ta kama tsohon suka d'agashi zuwa gefen titi, saurayin ya lura da cewa farfad'iyace take damun wannan tsoho, dan haka ya koma gun 406 ya karb'i inhela sannan ya dawo ya taimakawa tsohon cikin ikon Allah tsohon ya dawo hayyacinsa sannan saurayin yace sannu baba Allah ya baka lfy sannan ya juya ya koma motarshi. Budurwan tace sannu baba ina zuwa kaji, sannan ta mik'e taje gun pradon ta sake buga glass d'in a hankali lokacin motar tana k'ok'arin tashi. Saurayin ya sake sauke glass tare da cewa me kuma? Budurwan tana murmushi tace nagode da taimakonka. Saurayin yace me alakarki dashi? Tace MUSULUNCI bayan wannan bakomai, saurayin yace dama "you don even know him? Budurwan tace yeah na taimaka mishine saboda yana buk'atan taimakon dan haka nagode Allah ya kiyaye hanya, harta juya ta fara tfy seyace 'yan mata. Na'am tace dashi tare da dawowa gun ta tsaya, yasa glass d'inshi yace nima nagode da kikasa na samu wannan ladan. Budurwan tace karkamin godiya bawan Allah amaimakon godiyan da zaka min, inaso idan ka sami dama toka taimaki mutum UKU kuma suma kace musu su taimaki mutane UKU inaga K'ASARMU zataci gaba tayin hakan se'anjima sannan ta tafi. Kalaman yarinyar sun burgeshi sosai yace da driver'n shi "lets go" nan driver yayi hon se 406 d'in tayi gaba sannan suma suka wuce saurayin yanata bin budurwan da kallo se karkad'ewa tsohon jiki takeyi sannan ta rik'e hannunshi ya mik'e yana cewa nagode sosai yarinya Allah ya miki albarka. Budurwan tace ameen baba, amma banason godiyan nafiso idan ka samu dama a rayuwarka toka taimaki mutum UKU kuma suma kace musu su taimakawa mutane UKU. Tsohon yace to shikena yarinya ya sunanki? Tace sunana MARYAM amma amfi sanina da AUNTY'N YARA,seta d'auki abincinta ta tafi yanata binta da kallo.

Shi kuwa wannan saurayin kalaman MARYAM kawai yaketa mishi yawo a kwakwalwanshi.
Suna cikin tfyane seya hango wasu mutane UKU suna bin wata yarinya a guje se kuka takeyi. Yace da driver tsaya, bayan driver ya tsayane seya cire farin suit nashi da glass d'insa ya fita da sauri ya fara bin bayan mutanennan da gudu harya cafko biyu. Jin hakan yasa yarinyar tsayawa tana cewa bawan Allah ka taimakamin wai fyad'e zasumin. Duka ya fara musu kamar ba gobe suna bashi hakuri, yace baku da tausayi sam,yanzu ku zakuso ayiwa k'anwarku fyad'e? Sukace a'a kayi hakuri bazamu sakeba, yace ina fata zaku gyara halinku inba hakaba wataran se anyiwa k'annenku koma 'ya'yan cikinku. Jikinsu yayi sanyi sukace kayi hakuri kema kiyi hakuri daga yau mun dena kuma mungode. Saurayin yace karkumin godiya,amaimakon godiyar da zakumin inaso arayuwa idan kun samu dama toku taimaki mutane UKU2 suma kuma kucemusu su taimakawa wasu mutane UKUN ya juya ya kalli yarinyar yace harda kema sannan ya tafi sunata binshi da kallo sukacewa yarinyar muje zamu rakaki har gida, dad'i taji sannan suka tafi.

Shi kuwa ya koma mota yasha ruwan FARO mai sanyi sannan ya goge takalminshi tare dasa suit da glass nashi sannan driver yaja mota se gida.
Suna isa saurayin ya fito ya shiga ciki. Wata kyakkyawar budurwace ta fito daga d'aki tana sanye da wandon jeans fari da kuma black top mai hannu d'aya kanta ba d'ankwali ta baza gashinta tana danna TAP ahannunta daga ganinta kasan k'anwar wannan saurayinne dan kamannin harya b'aci. Murmushi takeyi tare da cewa "The Prince! "The Captain!! "And d Bro MANOSH!!! Daga ina ka fito hakane dukka dawo a gajiye bro MANOSH? Suit d'inshi yake cirewa yanacewa "pls not now MIHER" Bari na watsa ruwa se inzo kinji? Alright tace dashi sannan ya wuce side d'inshi ita kuwa MIHER ta zauna tanata buga game d'inta. Sallama taji, ta masa batare data kalli kosu wayeba, tap d'in hannunta taji an karb'e seta d'ago kai da murna sosai tace "The 6 Emms" (M) yaushe kuka shigo k'asar without alartn me? dariya sukayi mata amma banda d'aya daga cikinsu, MIHER tace bro MARWAN miskilancin ya tashi kenan? Marwan yace ke ina MANOSH, tace yana ciki,duk suka wuce sukabar MAJID yana rik'e da TAP d'in yace bana hanaki irirn wannan shigarba? Tace am sorry luv aidan ina gidane kuma bansan kun dawoba wlh amma promise daga yau bazan sakeba tana murmushi. Shima murmushin yayi yace to shikenan kije kisa himar ina jiranki a side d'in PRICE, ok luv ina zuwa me za'a kawo muku? Karki damu a k'oshe muke ruwa kawai muke buk'ata kuma zamu samu agun bro naki dan haka ki huta my luv yana mata murmushi sannan ya bata TAP d'in ya wuce itama ta shige ciki dansa hima...
[7:07am, 4/2/2017] Sadiya Taheer: ??@]???]AUNTY'N YARA??8]???]

Written by Sad-Nas
&
Hama gee muh'd


3-4 Palon manosh suka wuce kai tsaye suka baje akan kujerunsa masu kyau ga laushi. Muhammad ya kunna musu TV tare da d'ansa volume ta yadda manosh zaisan akwai mutane a palon,ball suke kallo suna hira. Manosh ya fito sanye da shets fara da kuma bak'in jeans,mamakine ya kamashi su kiwa dariya sukasa tare da cewa the prince captain manosh. Karasawa yayi ya zauna kusada muhsin da marwan yace gaskya bakuda kirki wlh,ashe kuna hanya shine har marwan kana cemin wayankane ba charg,marwan yai mirmushi yace muhsin ne yace karmu gaya maka,muhsin yace haba dude haka zakamin kuma,dariya sukasa dukkansu manosh yace to ina tsarabana naganku empty hand. Majid yace babu ya ibada ya hanya kawai se tambayan tsaraba,gaskya bakada kirki,manosh yace wannan tambayan ai mata kad'ai akeyiwa dan sune sakaltattu amma kana namiji dan kaje UMRAH harse anyi maka wani sannu,muhammad yace sosai kuwa ai haka ya dace,manosh yace toku rik'e tsarabanku indai hakane nasan marwan zai bani. Marwan yace ni ibada kawai naje ba sayan tsaraba ba my friend,muhsin ya mik'e ya d'auko ruwan sanyi yasha sannan yace to nidai zanje hira,kuda bakuda kowa sekuyita hiranku da kallon ball,harzai wuce manosh ya janyoshi yace wlh baka isaba nima na samu matar aure had'add'iya kuwa tamafi MIHER d'inka dan haka ka dena wani cika baki,ba majid kad'aiba dukkansu suka juya suna mishi kallon mamaki,domin duk cikinsu manosh ne kawai tun tashinsu bai tab'a ganin wata 'ya mace yace yana soba koda wasa. Muhsin yace "wow dude" gaskya zanso inga mai wannan SA'AN yau kaine da budurwa kodai wasa kakeyi? Manosh ya bisu da kallo dan dukkansu idonsu a kanshi yake suna jiran jin mezaice,yace wlh yauna had'u da wata yarinya bafulatana nitsatsiya gata tason taimakon wanda bata saniba sedai k'aramace,amma wlh ta burgeni sosai kuma kunsan wani abu dayasa na damu da ita "we luk alike dudes" zanso ku ganta she's so sweet. Majid yace harka tab'ata kenan,bugun wasa yakaiwa majid yace kai d'an iskanefa a hakanma wai k'anwata kake so shine kake min wannan maganan,majid yace to ai naji kace she's so sweet ne shine ban kane ba,manosh yace eh ina nufin voice nata yadda kasan mutum in yana mura kasan muryanshi yana canjawa,to amma nata yayi dad'i sosai kuma ba muran takeyiba natural voice nata kenan,bari dai in tak'aice muku kunsan dai muryan RANI dabanyake a cikin sauran matan indians da suke FILM,to haka dai itama yarinyan amma nata yafi na RANI dad'i idan tana magana bazakaso ta gamaba wlh nd.....marwan yace enoght me sunanta? Manosh yace nidai bansan sunantaba but zan dinga kiranta da MY APPLE. Ajiyar zuciya suka sauk'e muhammad yace gaskya zanso in ganta ko zan samu k'awarta nima,manosh yace ai wannan ne nakeso in samamishi k'awarta dan naga ya kusa ya tsufa baiti aureba,marwan yayi murmushi yace kai baka tsufaba seni,muhsin yace gara dai kam ka taimakawa marwan dan tunda FADILA ta rasu ta barshi gabad'aya bana gane mishi. Majid yace kuka sani kozai bitane ku kyaleshi kawai,duka marwan zaikawa majid se yayi sauri wucewa gun k'ofa yana cewa to ai gaskyane nidai na tafi gun luv d'ina prince ina tayaka murna dolene muje nemo soyayyar APPLE namu,manosh yace gaskya na baka k'anwata koba'ayi tambayana nariga dana baka ita. Dariya suka sa sannan majid ya tifa gun MIHER,su kuwa sukaita hira nada'an wani lokaci sannan suka fito kowanne ya shiga motarsa ya tafi.
Miher tace bro manosh k'awata tana sonyin magana da kai amma kuma idan kun had'u seta kasa saboda kunya. Manosh yace wata k'awarkin kenan,tace LUBNA nama bro kaima kasan banida da k'awar data kaita duk duniya,manosh yace to to ai bata cika maceba kenan tunda tana tsoron na miji,miher tace bafa tsoro takejiba kunyane da kuma tunanin disgin da zaka mata,manosh yayi murmushi tare dajan hancin miher yace wani irin disgi kuma luvlyn sis,tace bro SONKA fa takeyi wlh amma takasa gaya maka nace ta bari in sanar dakai amma tak'i tace wai ita zata sanar dakai kuma wlh bazata iyaba pls bro ka amin....shiii sis karki k'arasa pls kedai ki bari tunda bata sakiba harse lokacin dataga ya dace seta sanar dani kinji,miher tace hakan ya nuna kaima kana sonta kenan? Manosh yace nop ina dai sonta a matsayin k'anwan abokina kin gane yana mata murmushi,miher tace dat why nake so ku fahimci juna tunda k'anwar marwan ne. Manosh yace zomuje palo mu zauna,bayan sun shiga sun zaunane yace miher akwai abinda baki saniba inaso ki nutsu ki saurareni kuma bance ki gayawa kowa,miher tace haba bro kasan akwai sirri mai karfi a tsakaninmu kuma babu wanda yake sani se mutum d'aya,manosh yace wa kenan? Tace zuciyana mana tana dariya wanda yake kara mata kyau,shima dariyan yayi yace to kina jina

Ita dai LUBNA ba k'anwar marwan na jini bane, iyayen marwan suna son bby girl tun farkon aurensu tunma ba'a haifemuba,se Allah ya basu d'a namiji marwan kenan,sunyi farin ciki sosai kuma ke kanki kinsan yadda suke sonshi,amma ita mahaifiyarshi tanata so ta haifi mace gashi kuma bata sake haihuwaba shine sukaje gidanmarayu suka d'auko lubna tun tana jaririya suka riketa tamkar 'yar cikinsu. Mamaki sosai mihertayi dajin wannan lbrn da bro manosh ya bata,tace bro da gaske kake?murmushi yayi yace na tab'a miki karyane,tace wlh abun yaban mamaki amma to itama lubnan batasan da hakaba ko? Manosh yace bata saniba amma duk iyayenmu sun sani damuma,shiyasa banaso kiyinunakin sani kema. Miher tace to amma shine dalilin da yasa baka sonta kenan,manosh yace bahakabane sis yana jnkumatunta yace ai lubna yarinyar kirkice gata kyakkyawa duk namijin daya ganta zai sota amma kuma nid'in ban shirya neman mace bane yanzu shiyasa,ya kare maganar yana murmushi tare da barin palon ya d'auko key'n motansa ya fito yana cewa me,zan sayo miki sis,binshi kawai take da kallo tace bro ina zakaje kuma,yace gurin OGA na zanje yana nemana daga nan kuma zanje a rage min gashin kaina dan yana damuna sosai,miher tace pls kar'a rage dewa domin gashin yana maka kyau ai adai gyara maka shi,to luvlyn sis byee,itama hannun ta d'aga mishi guards d'insa sun mik'e da sauri yace no ni kad'ai zanfita karku damu,ok sukace dashi sannan mai gadi ya bud'e gate ya fita.

Auntyn yara har an gama abincinne,eh baba an gama ya rana ya kasuwan? Alhamdulillah yau na samu ciniki sosai se hamdala,murmushi tayi tace to madallah baba kaci abincin idan anzo saya se in sayar,to 'yar baba nagode ya maman naki,lfyanta k'alau tace in gaidaka,yace to ina amsawa yau kind'an dad'e yar baba,tace wlh baba wlh mutum ne farfad'iya ta kamasa akan titi ya fad'i shiyasa kaga na dad'e, yace Allah sarki 'yar baba Allah ya rayamin ke Allah ya miki albarka,Allah yasa kiyi kyakkyawan karshe a rayuwarki. Tace ameen baba harda kai da mama da dukkan 'yan'uwa musulmai. Tun daga nesa ta fara jin muryan yaran makaranta sunata cewa oyoyo auntyn yara2,da sauri ta fito daga cikin gidan FLOWER tana murmushi tare da tafa hannun tana cewa oyoyo kannen aunty suka rungumeta dukkansu yaran amma banda d'aya, seda suka gama oyoyon sannan d'aya yaron yace sannu auntyn yara,tace sannun Abdallah nah ya makarantan,yace alhamdulillah sannan ya gaida baban auntyn nasu,yaran sukace aunty mutafi gida to, tace to baba ka gamane? Babanta yace na gama kuje yana murmushi,suka mishi sallama tare da addu'an Allah ya kawo kasu mai albarka suka tafi.
Dad'i yakeji a ransada samun 'ya kamar maryam gashi tana da marrin jini kowa yana sonta manya da yara...
[7:07am, 4/2/2017] Sadiya Taheer: ??@]???]AUNTY'N YARA??8]???]

Written by Sad-Nas
&
Hama gee muh'd


5-6 Maryam ko kuma ince auntyn yara suna tfy suna hira da yara se bata lbrn makaranta sukeyi ita kuwa tanata dariya dayake ita d'in akwai fara'a ga kowa. Abdallah yace auntyn yara wai yaushe uncle ibrahim zai dawone,tace yadai kusa akwai wani abune,yace kawai dai naga nauyin ya miki yawane,tayi murmushi ta e aiba komai koda ya dawoma ai aiki zai kama tunda bautar k'asa ya tafi,abdallah yace har inaso in girma da wuri kodon indinga taimakawa kamar ke,dariya tayi tace insha Allah burinka zai cika abdallah. Haka dai suketa hira da yaran unguwansu suna tafiya jama'an dake wucewa sunata d'agawa auntyn yara hannu tare da gaisuwa maza da mata kowa ya santa a garin girei.

Maryam ita kad'aice agun iyayenta suna sonta sosai fiye da ransu gashi sunyi sa'an yarinya tunda ta taso da son mutane take musamman yara k'anana kowa nata duk gireim ana alfahari da ita tun tana primary ita take zuwa na d'aya har secondary kuma ko'a islamiyama haka gata da murya mai dad'i musamman idan tana karatun Qur'an kyaututtuka sosai garin girei ta samu dukta dalilin maryam har gasan Alqur'ani mai girma tana zuwa state state kuma ita take zuwa na d'aya kona biyu ta hakanne takai iyayenta makka da kyautar kujeran da take samu agun MUSABAK'A,dayake ta samu kujeran sau dewa dan haka aminan mahaifintama dukta basu kyautar su uku kuma itama taje amma sam bata hakorin makka ba. Maryam tana da son yara sosai, dan haka take koyar dasu acikin gidansu bayan yaran sun dawo daga makara,duk fanni arabic da boko tana koyar dasu daidai iyawarta,dan tana da ilimi sosai. Ayanzu dai sun gama secondary suna jiran result kenan, yaranma suna sonta sosai dan tana kula dasu sosai komai k'azartar yaro bata kyamarsa gashi ta iya sayomusu abin wasannin musamman balobalo da ice cream na dela kananan nan,indai ta shiga gari toseta sayo musu shiyasama bata rabuwa da katon din biski da su sweet a d'akinta.
Wannan daliline yasa ake kiranta da auntyn yara babba da yaro dan yanzu ba'ama ganeta da maryam sedai kace AUNTY'N YARA,itama tana jin dad'in sunan da ake kiranta dashi. K'awayenta su hud'u ne kuma kansu a had'e yake dukkansu, rashida muh'd,amina babale,zahida abba,da kuma samira jauro. Sune k'awayen maryam tare suka gama makaranta kuma duk y'an girein ne,abdalla shine k'anin rashi muh'd yarone mai hankali da nutsuwa ga son addini kuma yana da ilimi sosai yaron yana da shiga rai sosai shiyasa duk cikin yaran maryam tafi sonshi,saboda mahaifinsu baya raye suda mamansu kawai suke zama uncle ibrahim shine babban yayansu.

Bayan sallan la'asar baban maryam ya dawo gida,daga maryam har mamanta sunyi amakin ganinsa,yace kuna mamaki ko wlh flower dai kad'an ya rage duk an saye yanzuma cikin JIMETA zan shiga in sayo wasu. Maryam tace baba yanzu duk sun k'are,yace wlh addu'arkuce ta d'azu ta karb'u kinsan bakin yara wani mutumine yayi sabon gida kuma yana so ya shuka flower shine ya sayi fiye da rabi,sukace Alhamdulillah baba ka kawo inje tunda nima nasan gurin kaika huta a gida,yace to 'yar baba gashi.
Nan da nan maryam ta shirya cikin after dress bak'i ta d'auki pos d'inta tace sena dawo,sukace to Allah ya kare tace ameen sannan ta wuce titi tana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login