Showing 66001 words to 69000 words out of 168813 words

Chapter 23 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt

08 Aug 2024

100557

barka da dare.




yarima batare da ya kalletaba yace barka.




bakin gadonsa zarah tazauna ta aje cup d'in coffeen a saman bedside, bayan yarima ya gama zarah tace masa ga coffee nahad'o maka, yarima kallonta yayi yaga itama kallonsa take fuskarta d'auke da murmushi zuwa yayi yazauna gefenta tamik'o masa cup d'in, yarima k'ar6a yayi yana d'an sha a hankali saida yasha kusan rabin cup d'in sannan ya aje tare da mik'ewa yanufi toilet.




bayan ya fito saman bed d'in yahau yakwanta ganin haka yasa zarah takashe gloves masu haske tabar marassa haske sosai, sannan itama takwanta gefensa, bayan kamar minti biyar ahankali tamaida kanta a saman k'irjinsa, ba yarima ba hatta ita kanta zarah saida taji wani iri,


muryar yarima taji yace ya dai?
zarah cikin wata irin muryar da ita kanta batasan tana da itaba tace bakomai ji nayi kwanciyar batayi min dad'iba saisa,
yarima kallonta yayi sannan yamaida idanuwansa yalumshe.


zarah murmushi tayi tace wannan mutumin jin kansa yayi masa yawa, tunowa tayi da lecture d'in da Hajiya kubra tayi mata, ahankali tad'ago kanta tana k'are ma kyakkyawar fuskarsa kallo tana tunanin ta yadda zata 6ullo masa, yarima bud'e idonsa yayi yana kallonta yace wannan kallon fa?


zarah har ta bud'e baki zatayi magana bata ankara ba saidai jin bakinsa tayi cikin nata, zarah biye masa tayi tashiga nuna masa nata salon, ammah nan da nan yarima yarikitata tafita hankalinta batasan lokacin da yarabata da rigar jikintaba, ko da tadawo hankalinta kyarma tashiga yi tana neman turesa ammah ta kasa. nan tafara k'wallah muryarta tana rawa tace dan Allah kadaina bana so.


yarima yanayin yadda tayi maganar ta so tabasa dariya, murmushi yayi yace ai naga abinda kikeso kenan,
zarah fashewa tayi da kuka tace wlh bashi nakeso ba dan Allah kakyaleni bana so, yarima shareta yayi yana jinta tana ta magiyarta ammah bai saurara mataba,


ko da ahankali yabi da ita ammah saida zarah tayi kuka, bayan ya samu nutsuwa janye jikinsa yayi yatashi yabar zarah tana kuka yaje yayi wanka.


bayan ya fito komawa yayi yakwanta, zarah harara tashiga wurga masa karaf suka had'a ido dasauri tajawo towel tad'aura tamik'e taje tashiga toilet, saida tagasa jikinta sannan tayi wankan tsarki.


bayan ta fito rigarta tamaida sannan takwanta chan k'arshen gado tare da juya masa baya, yarima murmushi yayi yajuyo da ita batare da yace komai ba yajuya chan gefen, zarah da mamaki take kallonsa cikin ranta tace shi kuma wannan me yake nufi da hakan? d'an guntun tsaki zarah taja sannan tagyara kwanciyarta.






da asuba bayan sunyi sallah bacci suka koma zarah ba ita ta farkaba sai wajen 11 da mamaki tabi d'akin da kallo, jin ba alamun yarima a d'akin yasa tamik'e har parlour tazo taduba ammah babu alamunsa zama tayi saman kujera tare da dafe kai tace badai fita yayi baiyi breakfast ba?


mik'ewa tayi tagyara ko'ina sannan tafita tabar d'akin, ko da takoma part d'inta ji take ba dad'i tausayinsa yakamata ganin baici komai ba yafita, wayarta tajawo takirasa har saida takusan tsinkewa sannan yayi picking.


zarah jin yayi shuru yasa tace dafatan ka tashi lafiya? yarima shuru yayi nad'an lokaci sannan yace lafiya.
zarah marairaicewa tayi tace shine kafita bakayi breakfast ba?
ai naga bacci kike, cewar yarima.
zarah kamar zatayi kuka tace ai da ka tasheni na had'a maka,
yarima shuru yayi baice komai ba,
zarah tace ko inhad'a yanzu inbada akawo maka?
yarima yace no kar kidamu kibarsa kawai, yanzu ina aiki ne bye,
bayan ya kashe wayar zarah murmushi tayi tare da bin wayar da kallo, dialing din number d'in number d'in abbah tayi suka gaisa sannan yaba mama itama suka gaisa a wajensune takejin labarin yarima jiya yaje suka gaisa mama ce take shaida mata har kayan abinci ya aiko musu, zarah murmushi tayi har cikin ranta taji dad'in yadda yake mutunta iyayenta har da 'yar k'wallarta, bayan sun gama wayar tashi tayi tashiga kitchen had'add'ar fried rice tagirka wadda taji kayan lambu sannan tayi pep chicken, bayan ta gama kunun aya mai dad'i tahad'a.


sawa tayi aka d'auka aka kai masa part d'insa.








da dare tun da takwanta part d'inta juyi kawai takeyi tana jin duk badad'i musamman ma idan ta tuno yanzu haka yana chan tare da gimbiya sumayya sai taja tsaki, a k'arshe tajanyo wayarta tahau chart ba ita ta safkaba sai wajen 1am sannan tasamu tayi bacci.






A chan 6angaren gimbiya sumayya tun daga ranar da suka had'u da zarah da yarima bata k'ara sa zarah a idoba dan a yanzu batada aiki da tazauna sai chart tana gudunar da online business d'inta da zinat ta jonata, harkokinta kawai take kud'i suna shiga a account d'inta.




da dare shiryawa tayi taje part d'in yarima saida sukayi 'yar rigima sannan suka kwanta.




zarah tun da tayi sallar asuba bacci takoma ba ita tafarka ba sai wajen 11am nan tayi wanka tashirya, sannan tafito tanufi part d'in yarima dan a lokacin tasan ya fita, tana zuwa daidai lokacin kuku d'insa yake shirin fitowa daga part d'in yarima d'auke da kayan abinci ganinta yasa yaduk'a Cikin girmamawa yagaisheta.




zarah cikin ranta tace toh wannan dama shi yake girka ma yarima abinci? zarah cikin sakin fuska ta amsa har yatashi zai fita nan zarah tace am me kake da suna?


washe baki yayi yace ranki yadad'e nine kuku halladu babu irin girkin da ban iyaba nine nake girka ma yarima abinci.


zarah tace ayyah Allah sarki halladu toh kayi hak'uri zan d'an dakatar da kai daga yi ma yarima girki dan nafiso yaci na matansa.




kuku cike da tashin hankali yaduk'a yace ranki yadad'e kiyi hak'uri kibarni incigaba wlh ta nan nake samu ana biyana.


murmushi zarah tayi tace kar kadamu hakan bazai shafi albashinka ba za'a cigaba da biyanka, kuma naji ance tunda shugaban masu kula da girkin gidannan yarasu ba'a nad'a waniba toh kaje kazama madadinsa.


cike da jin dad'i yaduk'a yak'ara yi mata godia, murmushi zarah tayi tace bakomai kaje ai ka cancanci fiye da haka tunda ka san aikinka.


bayan ya fita zarah gyara d'akin tayi fess sannan takoma part d'inta tashiga kitchen, burabiscon shinkafa da miya tayi masa sannan tahad'a had'ad'en zo6o tasaka a freezer.


bayan ta gama wanka tashiga tayi tashirya cikin gown d'inta ash colour har k'asa tana sharar k'asa sannan tayi rolling da veil d'in rigar tayi kyau sosai.


parlour takoma tazauna tana jiran dawowar yarima, saida ta daidaici lokacin da yadawo sannan tasa aka d'aukar mata abincin suka nufi part d'insa suna shiga daidai lokacin yarima da gimbiya sumayya suka fito daga bedroom d'insa, cike da mamaki gimbiya sumayya take kallonta cikin ranta tace wannan yarinyar bazata daina shiga hurumina ba?
zarah ganinsu saida gabanta yafad'i murmushi tayi tare da d'an rissinawa tace ranku yadad'e barkanku da fitowa, yarima ne kawai yad'aga mata kai.


gimbiya sumayya kamar daman jira take cikin 6acin rai tace ke! banason shishigi wa yabaki izini kigirka ma mijina abinci? abin naki yana nema yayi yawa watau har ranar girkina sai kin zak'e ma mijina?


zarah murmushi tayi tace ranki yadad'e ba haka bane kawai gani nayi mu yafi dacewa mugirka masa ba kuku ba.


sumayya a fusace tace toh sarkin iyayi toh bari kiji ba za'a girkaba ke in girkawar kikeson yi toh kibari sai ranar girkinki ba nawaba, murmushi zarah tayi batace komai ba tamaida kallonta ga yarima tace ranka yadad'e lunch fa yana jiranka,




yarima wucewa yayi yanufi dining nan zarah tabisa suka bar sumayya tsaye takaici duk ya cikata, a gaban idonta zarah tayi serving d'in yarima sannan tawuce tafita tabar d'akin, sumayya ji take kamar tashak'eta dan bak"in ciki, tsanar zarah nan tak'aru a ranta, ta dad'e a tsaye sannan daga baya a fusace tawuce tafita takoma part d'inta, saman gadonta tafad'a tare da k'walah ma shugabar kuyanginta kira mairo, cikin sauri mairo tazo, sumayya cike da 6acin rai tace bani wayata, dasauri mairo taje tad"auko mata wayar tamik'a mata rikicewa tayi ganin uwargijiyar tasu tana k'wallah, cike da tashin hankali tace ranki yadad'e me yake faruwa? sumayya batace komai ba takar6i wayar takira ummanta, ummah tana d'auka cikin 6acin rai tace badai akan wannan gajar yarinyar bace kike kuka,


sumayya cikin shashek'ar kuka tace ummah kece kike hanani d'aukar mataki akan yarinyar chan toh wlh nagaji da abinda takemin,


a chan 6angaren sultana sadiya da take zaune mik'ewa tayi tafara zagaye dakin cikin 6acin rai tace wlh nabaki dama kid'auki duk matakin da kikaga ya dace, kikwaci mijinki tun kan wannan maรฝyar tak'wace miki shi, kema ai har da naki laifin, sumayya tsinke wayar tayi batare da sun gama magana ba, dan a rayuwarta ta tsani taji ummah tace tana da laifi.




kallonta tamaida ga jakadiyarta da take tsugunne tace zaki iya tafiya, jakadiyar d'ago kai tayi takalli gimbiya sumayya tace ranki yadad'e yanzu akan wannan yarinyar kike 6ata ranki? aini daman tunda naganta banga alamun mutunci a tare da itaba ranki yadad'e a duk lokacin da kike 6ukatar taimakona ashirye nake zan taimaka miki wajen ganin kin kwaci mijinki daga hannunta, tana kaiwa nan tak'ara dukar da kanta tace Allah yahuci ran gimbiya nabarki lafiya, mik'ewa tayi har zata fita daga d'akin sumayya ahankali tace dawo muyi magana.........










_Comments_
*nd*
_Share_












_Sis Nerja'artโœ๐Ÿป_
๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘


_*YARIMA SUHAIL*_

๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘






_*Written By~Sis Nerja'art*_






_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_




https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/


*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ยฎ*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE ๐Ÿ˜˜ HEART TORCHING โค TEARS OF SORROWS ๐Ÿ˜ญ CURDLES ๐Ÿ™‚ GIGGLES ๐Ÿ˜ AND MARRIEGE THINK๐Ÿ’‘
*JUST GIVE US FOLLOW....*โœ”




_~Masha Allah *Dr Zain* ina tayaka murnar kammala novel d'inka mai suna *YAN GUDUN HIJIRA* hakika ka fad'akar, ka ilmantar sannan ka nishad'antar gaskiya na jinjina ma namijin k'ok'arin da kayi a cikinsa Allah yabada ladar abinda kafad'a daidai, kura-kuren da suke ciki Allah yayafe maka sai munjiki a new novel ๐Ÿ˜~_






_*My classic Feedoh marubiciyar SUHANA yau page d'in nakine kiyi yadda kikeso da shi my friendy ina ji da ke har cikin zuciyana Allah yabarmu tare*_




*PAGE* 2โƒฃ8โƒฃ




ko da jakadiya tadawo tatsugunna, gimbiya tattare nutsuwarta tayi tamaida gareta tace bakomai yasa nakirakiba sai dan naga alamun zaki iya taimaka min, inaso kirik'e min sirrina Indai kikayi haka toh zaki ji dad'ina ammah duk ranar da kika nemi kitona min asiri. murmushin mugunta gimbiya sumayya tayi sannan tace kinsan wacece ni


jakadiya duk'ar da kanta tayi tace ranki yadad'e kar kidamu a kodayaushe ina tare da ke zanyi duk abinda kikeso.


jinjina kai gimbiya sumayya tayi tace shikenan zaki iya tafiya




zarah ko da takoma part d'inta zama tayi saman cushin cikin ranta duk sai taji bataji dad'in abinda tayi ma sumayya ba dan tasan hakan da tayi bai daceba, ko da daman tayine dan tanuna mata talakka ma daidai yake da kowa, kuma duk saboda haka take daurewa tana nuna ma yarima kulawa dan har a lokacin batajin sonsa a cikin ranta, jikinta taji duk yayi sanyi cikin ranta tace insha Allahu bazan k'ara shiga hurumin da banawa ba dole inje inbata hak'uri dan bansan yanayin da zata shiga ba.




sawa tayi aka fara kira mata kuku nan tayi masa bayani tace yakoma bakin aikinsa ammah banda ranar girkinta, dan bata buk'atar mijinta yaci girkin wani ranar girkinta, nan yayi mata godia sannan yatashi yafita cike da jin dad'i.


zarah tashi tayi tanufi part d'in gimbiya sumayya daidai lokacin sumayya tafito daga bedroom d'inta, cikin 6acin rai sumayya tace me kikazo yi min nan munafuka? ko munafuncin da maitan akazo yimin nan?


toh bari kiji Indai kin shanye yarima toh ni kurwata fes take duk wani maita da asiri bazasuyi tasiri akainaba.




zarah k'wallah ce tacika mata ido ahankali tace dan Allah kiyi hak'uri da abinda yafaru wlh...... A fusace sumayya tace wlh me munafuka? toh bari kiji wlh dole kirabu da mijina duk wani zak'ewarki daman ku 'ya'yan talakkawa haka kuke baku iya samun wajeba ina gargad'inki da kifita harkar mijina inko ba hakaba zan fiddo miki halina a fili zakisan wacece gimbiya sumayya,


zarah k'wallar da take cikin idonta tanemi tazubo dasauri tagogeta tace dan Allah kiyi..... ke! ni fice kiban waje tun kan in karyaki a nan wajen, matsiyaciya kawai.


zarah da mamaki take kallonta ahankali tajuya tafita tabar d'akin kwata-kwata bataji dad'in yadda gimbiya sumayya takasa fahimtarta ba.






tun daga lokacin zarah tadaina shiga sabgar yarima indai ba ranar girkinta bace.






_*Bayan Sati 'Daya*_




zarah tana zaune saman cushin hannunta rik'e da wayarta tana operated d'inta, kiran da yashigo wayartane yasa tabi wayar da kallo cike da mamaki ganin mai kiranta, ahankali tayi picking tare da yin sallama, daga chan 6angaren ciki-ciki yarima ya amsa mata sannan yace kizo inason ganinki, yana fad'in haka yakashe wayarsa.




zarah cike da mamaki tabi wayar da kallo cikin ranta tace ko me zanyi masa, mik'ewa tayi taje tad'auko veil d'inta tayafa sannan tafito tanufi part d'insa.


sumayya da bata dad'e da shiga ba zaune take gefensa tace sweetheart kiran me kakemin a wannan lokacin ko akwai abinda kake buk'ata? banza yarima yayi yakyaleta, har ta bud'e baki zatayi magana shigowar zarah yasa tafasa a wulak'ance tad'aga kai takalleta cikin tsawa tace me kikazo yi mana nan kuma uwar shishigi? zarah d'an rissinawa tayi tace barkanku da hutawa, sumayya tace kifita kibamu waje tun kan ranki ya6aci.




zarah kallon yarima tayi da yake kallon TV ammah hankalinsa yana wajensu, ganin baida niyar yin magana yasa tajuya zata fita,
muryar yarima tajiyo yace umurninta zakibi ko nawa?




ahankali zarah tajuyo takallesa har a lokacin kallonsa yana ga tv, ahankali yajuyo yakalleta tare da nuna mata kujera tazauna,


key d'in mota yad'auko yamik'a ma sumayya yace ga wannan key d'in motarki ne da nasiya miki,


sumayya kar6a tayi tana juya key d'in tace dagaske tawa ce yarima? cike da Jin dad'i tarungumesa tace nagode sosai gaskiya naji dad'i, Allah yabarmu tare d'an bak'in ciki kuma saidai yamutu.


murmushi zarah tayi tace Allah yasa alkhairi Aunty gaskiya natayaki murna, sumayya harararta tayi tace inma bak'in ciki kike toh saidai kimutu.




yanayin yadda tayi maganar taso taba yarima dariya, d'ayan key d'in da yake hannunsa yamik'a ma zarah yace kekuma ga naki, zarah da mamaki take kallonsa ji take kamar a mafarki ahankali tace ni kuma?


yarima yace kikar6a mana, zarah tasowa tayi tad'an rissina takar6a tace nagode Allah yasaka da alkhairi Allah yak'ara girma da d'aukaka,


sumayya da tunda taji yace ga ta zarah yasa tacanza fuska, cikin 6acin rai tace ban fahimcekaba? ya naga kaba wannan d'iyar talakkawan kana nufin matsayinmu d'aya da ita ko me?


yarima shuru yayi yakyaleta, sumayya a fusace tace gaskiya yarima baka kyautamin akan me zaka dinga had'ani da wannan 'yar ma..... kallon da yayi matane yasa takasa k'arashe maganarta, maida kallonsa yayi ga zarah da kanta yake sadde k'asa sannan yace motocinku suna parking space zaku iya zuwa kugansu, ke za'a fara koya miki taki ko da ace ba fita zaku dinga yi ku kad'ai ba na mallaka mukune abisa ra'ayin kaina.




zarah ce kawai tace toh mungode Allah yasaka da alkhairi Allah yak'ara bud'i, mik'ewa tayi tace nabarku lafiya sannan tafita tabar d'akin takoma part d'inta.




sumayya kallon yarima tayi tace haba yarima gaskiya banajin dad'in abinda kakeyi min.


yarima da mamaki yake kallonta yace sumayya me nayi miki?


shuru sumayya tayi batace komai ba,
kifad'a min abinda nakeyi miki Wanda ba daidai ba, cewar yarima.


Jin batada niyar yin magana yasa yamik'e yashige bedroom d'insa yabarta nan parlour, cike da 6acin rai sumayya tatashi takoma part d'inta.




tun daga ranar yarima yasa aka fara koya ma zarah mota kasancewar sumayya da dama chan ta iya.




*Bayan kwana biyu*


gimbiya sumayya ce tafito daga part d'inta zataje turakar mahaifiyarta, tsaye tayi tana kallon zarah da tanufi part d'in yarima bayanta kuyangarta ce d'auke da tray.


gimbiya sumayya kallon kuyangarta mairo tayi tace ya kike ganin ya dace inyi inaso kar yarima yaci abincin,


murmushi mairo tayi tare da d'an rissinowa ahankali tayi ma sumayya rad'a nima kaina bansan abinda take cewa ba saidai gani nayi gimbiya sumayya tayi murmushi tare da jinjina kai tace hakan kuwa za'ayi yanzu nasan yarima bai dawoba, mukoma ciki nafasa fita.




Bayan sun koma gimbiya sumayya sawa tayi aka duba mata fitowar zarah daga part d'in yarima, Bayan anzo anfad'a mata mik'ewa tayi tanufi part d'in yarima fuskarta d'auke da murmushi.






yarima ba shi yadawoba sai around 3 o'clock, zarah saida ta daidaici daidai lokacin da tasan yadawo sannan tatashi tanufi part d'insa kasancewar itace take da girki ranar.




tana shiga part d'insa daidai lokacin yafito daga bedroom d'insa hannunsa rik'e da waya yanayi, kallon zarah yayi da take murmushi sannan yawuce yanufi dining ko da yazauna zarah serving d'insa tayi sannan tazauna kusa da kujerar da yake zaune tana jira yagama waya.




gimbiya sumayya tana ganin wucewarta murmushi tayi tace munafuka yau zanso inga yadda zaki kwashe da yarima bari ma inbi inga yadda za'ayi wannan dramar.




lokacin da gimbiya sumayya tashiga part d'insa daidai lokacin yarima yagama wayar da yake, ganinta yasa zarah tamik'e tsaye fuskarta d'auke da murmushi tace ranki yadad'e sannu da zuwa,


murmushi gimbiya sumayya tayi tace yauwa gimbiyar yarima,


da mamaki zarah takalleta dan wannan ne karo nafarko da taga murmushi a fuskarta gimbiya sumayya,




yarima d'aukar spoon d'in yayi yad'ebo abincin zai kai bakinsa, kallon sumayya yayi da tazuba masa ido yace inzakici kizo kizauna kici.




gimbiya sumayya jayo d'aya daga cikin kujerun tayi tazauna nan zarah tayi serving d'inta, yarima ahankali yakai lomar farko a bakinsa, yana fara taunawa dasauri yazubar da abincin yana yamitsa fuska, zarah da mamaki take kallonsa tace yarima lafiya?




mik'ewa yayi dasauri yashige bedroom yanufi toilet, zarah kallon sumayya tayi itama sumayya kallonta

08, February 2025
Shuraihu Usman

jjjjj

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login