Showing 132001 words to 135000 words out of 168813 words

Chapter 45 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt

08 Aug 2024

100553

hospital d'inmu.




Yarima dubawa yayi yaga upper ce ta aiki aka basa har da babban matsayi an nad'asa head of department d'in surgeon.




Girgiza kai yarima yayi yace gaskiya kayi hak'uri ba zan iyaba kaima sanin kankane ina da hospital d'ina.


Marairaicewa Dr mu'az yayi yace nasan da haka ammah dan Allah kataimaka ka amince ko yayane kasa albarka a cikin aikin nan kar kak'i amincewa dan muna buk'atar babban surgeon kamarka.


yarima shuru yayi kamar yana nazari sannan yace shikenan zanyi tunani akai.


Cikin jin dad'i Dr mu'az yace Allah yasa inji alkhairi.




Bayan yarima yadawo part d'insu kwance yake saman 3 seater ya yi matashin kai da hannuwansa kansa yana kallon ceiling,


Fitowar zarah kenan daga bedroom rik'e da apple tana ci, tsaye tayi tana kallon yarima da kwata-kwata batama san lokacin da yashigoba dan duk atunaninta bai dawoba.


Takowa tayi ta iso inda yake janye kansa tayi tazauna sannan tamaida kan nasa saman cinyarta, yarima lumshe idanunsa yayi.


shafa sumar kansa tayi tace ashe ka dawo ban saniba.


Murmushi yarima yayi yace uhm ban dad'e da dawowaba,
duk'o da kanta tayi takaimashi peck a saman idonsa da yake lumshe, ahankali yabud'e idanunsa nan suka sakar ma juna murmushi, d'age rigarta yayi yayi kissing d'in cikinta sannan yace ina fatana kuna lafiya keda babyna.


Cike da tsokana zarah tace lafiya lou muke prince saidai missing d'inka da mukeyi.


Shafa cikinta yashiga yi yace nima nayi missing d'inku sosai yanzu muje ciki inga in dagaske kunyi missing d'ina.


Dariya zarah tayi tace nak'i wayon naka babu inda zanje.


Mik'ewa yarima yayi yad'auketa yanufi bedroom da ita tana wuntsila k'afa bai direta a ko'inaba sai saman gado, zarah shirin safka take nan yarima yarik'ota yace toh sarkin tsoro ni ba abinda zanyi miki magana ce nakeso muyi.


gyara zamanta tayi tafuskacesa tana jira taji abinda zaice mata.




Yarima janye idanunsa yayi daga kallonta yayi shuru har na kusan minti ukku sannan yakwashe yadda sukayi da Dr mu'az yafad'a mata.




Zarah kasa 6oye farin cikinta tayi nan tashiga washe baki, kallonta yarima yayi yace toh ya kike gani?


Cikin jin dad'i tace wlh nima na goyi bayan hakan kaga kaima zaka ji dad'i kuma taimakone Allah zai baka lada dan irin wannan aikin naku duk abinda za'a ba mutum baza'a ta6a biyansaba ladarku tana wajen Allah.


Murmushi yarima yayi yace hakane shikenan tunda kin amince toh nima na amince.


cikin jin dad'i tarungumesa tace nagode sosai my soulmate Allah yabarmin kai ni kad'ai.


Dariya yarima yayi yace toh Allah yasa,


'Dago kai zarah tayi takallesa tace ashe ka iya dariya haka gaskiya tana yi maka kyau saidai kai bakacika yin dariyaba murmushinma kafin kayi sai ansha wuya.


Jan hancinta yarima yayi yace yau kuma tsokanata akeji?


Murmushi zarah tayi tace ba tsokana bace gaskiya ce nafad'a dan ranar da nafara ganinka lokacin da kukazo islamiyarmu ranar da muke walima saida nakusan rikicewa dan ka burgeni sosai saidai a lokacin fuskarka a d'aure take.


Murmushi yarima yayi yace kedai kin cika tsokana nidai yanzu tashi muje muyi wanka mukwanta dan ni yau agajiye nake ga bacci da nakeji.


Mik'ewa zarah tayi tace angama ranka yadad'e, nan suka cire kayansu sukaje sukayi wanka bayan sun fito shiryawa sukayi cikin kayan baccinsu sannan sukabi lafiyar gado suka kwanta.






Wanshe kare koda yarima yaje ma mu'az da batun amincewarsa sosai mu'az yai murna,


bayan kwana biyu yarima motarsa yasiya maikyau da tsada sannan yafara zuwa wajen aikin.


Sosai ma'aikatan asibitin suke girmamasa musamman ma da sukasan matsayinsa da kuma matakin karatunsa, kamar dai yadda yake baya shiga harkar kowa toh nan ma haka hidimar gabansa kawai yakeyi.


Sosai sukejin dad'in aiki da shi musamman ma da sukaga k'wararrene sosai a 6angaren theatre.






Bayan kwana biyu
Zarah kwance take saman gadonsu tunanin 'yan gidansu kawai take dan tasan dole sai sun nemi wayarta, tana cikin tunanin batasan lokacin da yarima yashigoba saidai jin mutum tayi gefenta, murmushi tasakar masa tare da cewa sannu da zuwa ashe ka dawo.


Shima murmushin yayi sannan yace ai daman bazakiji dawowataba tunda kin tsunduma kogon tunani wai ma tunanin me kikeyi haka?


Ajiyar zuciya Zarah tasafke sannan tace tunanin su mama nake nasan zasuyita neman layina bazasu samuba,,,tak'arashe maganar kamar zatayi kuka,


Yarima kallonta yayi yace kar kidamu ai sunsan dai kina cikin k'oshin lafiya zan kira miki su wani lokacin kugaisa.




'Daga kai Zarah tayi cike da gamsuwa da maganar yarima, jikinta yarima yakwanta tare da tura hannuwansa cikin rigarta yana cakud'ata
Ganin yana shirin nemanta yasa tazame jikinta takoma parlour dan yanzu gabad'aya ji take batason yarima yana kusantarta saboda sai takwana jikinta yana ciwo ga yawan amai da tashin zuciya musamman yanzu da cikinta yafara yi mata nauyi, ammah indai wassani zaiyi da ita bata damuwa saidai tasan halin gogan nata dawuya ya iya tsayawa iya romancing.
Ganin ta gudu yasa yarima yashareta yai kwanciyarsa dan ya lura kwana biyu haka take masa Indai zai nemeta toh sai tasan hanyar da tabi takubce masa.










_Comment_
*nd*
_Share_












_Sis Nerja'artโœ๐Ÿป_[5/3, 9:51 PM] Sis Naj Atu: ๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘


_*YARIMA SUHAIL*_

๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘






_*Written By~Sis Nerja'art*_






_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_




https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/


*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ยฎ*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE ๐Ÿ˜˜ HEART TORCHING โค TEARS OF SORROWS ๐Ÿ˜ญ CURDLES ๐Ÿ™‚ GIGGLES ๐Ÿ˜ AND MARRIEGE THINK๐Ÿ’‘
*JUST GIVE US FOLLOW....*โœ”




_Aunty Aliyah Sharif bazan iya mancewa da ke ba akodayaushe kina raina dan haka kimatso kusa yau page nakine big Aunty, sai wanda kikaso zai karanta, jinjinar bangirma agareki ๐Ÿ˜_




6โƒฃ1โƒฃ


Sumayya tunda takwana biyu ganin dagaske aurenta ya mutu gashi bata ganin yarima yasa tahak'ura tasaki ranta, ahaka akaje aka kwashe kayanta a part d'inta sannan aka rufe gabad'aya 6angaren yarima aka kaima memartaba key d'in.






Sumayya kwance take saman gadonta sai a ranar tajanyo wayarta takunna dan rabonta da ita tun ranar da aurenta yamutu, number d'in yarima tayi dialing da mamakinta taji bata shiga, dan haka talalubo ta zinat nan tafara ringing har ta tsinke ammah batayi picking ba, nan ma sumayya tak'ara kira saida tayi mata 3 missed call ammah bata d'aukaba dan haka tatura mata message dan daman tasan mawuyacine zinat tayi picking d'in wayar.


Bayan kamar minti biyar sai sumayya tak'ara kira da mamakinta saiga zinat tayi picking, cike da jin dad'i sumayya tagyara kwanciyarta tare da cewa Hi baby.


Daga chan 6angaren zinat a tsorace tace sumayya ya dai?


Murmushi sumayya tayi tace ke fa tsiyata da ke kin cika tsoro toh kisaki jikinki komai ya wuce.


Uhm sumayya kenan taya zan saki jikina bayan d'an banzan dukan da wannan mugun yayimin ke yanzu dai ya maganar aurenki?


Murmushi sumayya tayi tace hmm kibarsa kawai ai yanzu aurena da yarima ya k'are wlh ban ta6a tunanin zaimin wannan cin mutuncinba haka koda nasan inason yarima ammah babu yadda zanyi dole inciresa a raina tunda ko giyar wake nasha aurenmu bazai ta6a komawaba.




Zinat cikin ranta murna fal ji take kamar tazuba ruwa k'asa tasha saboda murnar auren sumayya ya mutu, a fili 6oye murnarta tayi tace Allah sarki baby ba haka nasoba toh yanzu ya su memartaba sukayi da sukaji labarin rabuwarku Allah dai yasa basuji abinda mukayi ba.


Dariya sumayya tayi tace kefa tsiyata da ke kin iya tsoro, daman fa nasan miskilancin yarima bazai ta6a barinsa yafad'aba kuma koma ba hakaba nasan yarima bazai iya tonamin asiriba saboda bayason tashin hankali, nikuma gudun kar ma yatona min yasa nayi sauri narigashi kai k'ara......nan takwashe duk abinda yawakana talabarta ma zinat.


Ajiyar zuciya zinat tayi tace gaskiya kinyi namijin k'ok'ari toh yanzu yarima shikenan ya bar gida bazai dawoba?


Hmm ba zai ta6a dawowaba, ni wlh kin ban mamaki da kika iya tafiya kikabarni ban ta6a tunanin hakaba daga gareki zinat.




Kwantar da murya zinat tayi tace kiyi hak'uri baby wlh gabad'aya rikicewa nayi ammah insha Allahu wani lokacin zan shigo.


Cikin jin dad'i sumayya tace gaskiya da naji dad'i dan gabad'aya kad'aici ya isheni Allah yakawo min ke lafiya.


Ameen baby zankiraki anjima.
Ohk, sai kin kira,,nan sukayi sallama.








Tun daga ranar sumayya da zinat suka koma suka d'inke kullum suna manne da juna ta waya inba wayaba toh ta chart da video call, yanzu sumayya kusan kullum tana d'akinta suna waya da zinat.


Sultana sadiya ganin yanzu hankalin d'iyarta ya kwanta yasa itama tad'an kwantar da hankalinta ammah magana bata had'asu da ummin yarima dan da taga ummi zata fara d'aure fuska koda ummi tayi mata magana indai sukad'aine shareta takeyi inkuma gaban su dadane toh shine take amsa mata ciki-ciki.
Ummi tun abin yana bata mamaki ganin ba ita tayimataba ammah da ita take gaba, daga k'arshe abun yadaina damunta.






Dada da memartaba ma danne damuwarsu kawai suke akan tafiyar yarima ammah su ma suna jin abun yana damunsu cikin rai, daga inda suka tuna da abinda yayi ma 'yar jikarsu sai kuma suji ba dad'i, dan haka ne suke nuna ma sumayya kulawa sosai ga tausayinta da sukeji saboda akanta akafara sakin aure a masarautarsu.




_________________


Zarah ganin yarima kwana biyu bai nemetaba dan yanzu har romance ya dainayi mata saidai kawai yarungumeta suyi bacci, nan abun yad'an fara damunta.


Yau ma tana fitowa daga wanka ganinsa tayi a kwance yana duba wata newspaper dan haka taje tafad'a jikinsa, kallonta yarima yayi yace Zarah sai kin ji ma babyna ciwo?


Turo baki tayi cikin shagwa6a tace au ba ma ni zanji ciwon ba babynka zanji mawa ko? babyn da yanzu andaina kulamu.


Aje newspaper d'in da take hannunsa yayi yace wajen me nadaina kulaki?


Kwantar da kanta tayi a k'irjinsa tace toh ba kai bane kadaina min komai?


Yarima ya fahimci inda tadosa ammah yanuna bai fahimtaba yace magana nadaina yi miki ko kulawa?


Girgiza kai Zarah tayi cikin jin kunya tace ka daina making sex da ni.


Murmushi yarima yayi yace toh ai naga kamar bakiso saisa nabarki kihuta.


Zaro ido Zarah tayi tace karufa min asiri taya zan k'i son lada, kawai dai babynka ne yake wahalar da ni, dan dadyn nasa jarumi ne,,,tak'arashe maganar tare da kashe masa ido d'aya.




Murmushi yarima yayi yace kar kidamu nima banason babyna yana wahalar min da ke kihuta warki kawai nayi miki uzuri.




Da mamakinsa sai yaga Zarah ta fashe masa da kuka.
Cike da mamaki yace lafiya zarah? Me kikeyi ma kuka?
Cikin kuka tace toh bakai bane.


Murmushi yayi yace toh kinaso inyi?


Cikin sauri tad'aga kai.


Toh shikenan kidaina kuka, nan yakwantar da ita yashiga lashe mata hawayen fuskarta daga nan yalalubo bakinta yacigaba da tsotsa kamar wanda yasamu lolli pop, gabad'ayansu jikinsu rawa yake dan sunyi missing d'in juna sosai, daga nan yarima yazare towel d'in da yake jikinta yagangaro da kansa a k'irjinta, ahankali yacigaba da lalla6ata har saida yaga sun samu nutsuwa sannan yabarta.


Duk da lalla6ata da yayi ammah saida jikin zarah yai ciwo dan daurewa kawai take, ko shi kansa yana lura da yadda take cize le6e.


Cike da tausayinta yashiga yi mata sannu daga k'arshe yad'auketa sukaje yaimata wanka shima yayi nasa sannan suka fito hatta kaya shi yasaka mata, jin jikinta ya d'au zafi yasa yad'auko drugs yabata sannan yad'auketa suka dawo parlour nan yakwantar da ita saman cinyarsa yana wasa da gashin kanta ahaka bacci yai awon gaba da ita.




Ganin tayi bacci yasa yarima yajingine kansa a jikin kujerar da yake zaune cike da tausayin zarah, nan family d'insa suka fad'o masa a rai, tunani barkatai yashiga yi daga k'arshe janye zarah yayi yagyara mata kwanciyarta nan yasafko k'asa yadafe kansa da hannuwa biyu, tunowa yayi da yadda yarabu da danginsa kowa yana d'aura masa laifin da bashida laifi a cikinsa, kukan da ummi takeyi ne ahankali yashiga dawo masa a kunne da lokacin da tad'ago idanuwanta da sukayi ja tasafkesu akansa,
Girgiza kai yashiga yi yace taya zan samu kwanciyar hankali ummina kin zubar da hawayenki saboda ni, ya zanyi da rayuwata.




Zarah da tafarka tun lokacin da yajanye mata kai, ido tazuba mashi tana sauraren duk abinda yake cewa tausayinsa ne yakamata dan sau tari daman yarima yana k'ok'arin ganin ya 6oye damuwarsane saboda ita saidai inaaa tuni ta gama karantar hakan, safkowa tayi daga saman kujerar tadawo k'asa kusa dashi tazauna tare da dafasa,


'Dago kai yarima yayi yakalleta murmushi yasakar mata tare da 6oye damuwarsa sannan yace kin farka?


Zarah k'wallah ce tacika mata ido tace taya kake tunani ni zan samu kwanciyar hankali alhali kai bakada shi?


Ido yazuba mata cike da mamaki sannan yace wa yace miki bana cikin kwanciyar hankali?


Hawayen da take dannewane suka zubo tace suhail me kamayar da ni, ko duk farkawar da kake cikin dare katashi kayita tunani ka d'auka ban san komai ba?




Mamaki k'arara yabayyana a fuskar yarima yace Zarah wa yafad'a miki haka?


Fad'awa tayi jikinsa tana kuka tace yarima babu abinda ban saniba sau tari kana k'ok'arin 6oye damuwarka idan kana a gabana saidai in bamu tare shine kake zama kayita tunane tunanenka, meyasa kake haka, kai doctor ne kasan illar yin haka tunda kuna fad'a ma wasu sudaina yawan damuwa ammah sai gashi kai kanayi.




Yarima rintse idanunsa yayi da k'arfi yana jin wani iri a ransa dan tunda yabaro iyayensa bai ta6a samun kwanciyar hankali ko na second d'ayaba saidai yana k'ok"arin 6oyewane saboda Zarah ga kuma ciki da take d'auke da shi bayaso ta silarsa wani abu yasamesu,
janyeta yayi daga jikinsa tare da bud'e idanunsa da suka kad'a sukayi ja, cikin sanyin jiki yace Zarah kukan ya isa haka, kidaina sa damuwa a ranki idan kin ganni haka, kinga bake kad'ai bace kar wani abu yasameku ke da babynmu.




Girgiza kai Zarah tayi tace taya hankalinmu zai kwanta bayan wanda muke a k'ark'ashinsa yana cikin damuwa? Taya zan yafe ma kaina bayan ta dalilina karabu da kowa naka?
K'ara fashewa tayi da sabon kuka sannan tace banso karabu da sumayya ba dan 'yar uwarka ce ko bakomai itace matarka ka tafarko, indai har saboda ni kasaki sumayya toh wlh na yafe mata abinda tayi min duniya da lahira, please ka amince mukoma gida kamaida matarka kazauna cikin danginka, ko da ace hakan zaiyi silar mutuwar nawa auren.




Wani irin abu yarima yaji ya soki mak'ogwaronsa jin ta ambaci rabuwa da shi, tureta yayi daga jikinsa cikin 6acin rai yace Zarah na sha fad'a miki ko babu ke zan iya rayuwata, ammah kar kik'ara min zancen sumayya dan na riga nayi mata saki ukku kuma kidaina tunanin ta dalilinki nasaketa wlh ko d'aya, na saketane saboda wani dalili nawa kuma idan kin gaji da zama da ni zaki iya fad'amin,,,yana fad'in haka yamik'e yad'auki key d'in motarsa yaficce yabarta nan zaune dan gabad'aya ya kashe mata baki ta ma rasa abinda zatace masa.
Cigaba tayi da kukanta kamar wadda aka aiko ma da sak'on mutuwa, ita takaicinta rabuwar yarima da danginsa gashi kwata-kwata ya kasa fahimtar inda tadosa, dan ita tasan tanason yarima sosai, k'ara sautin kukanta tayi cike da tausayin kanta da mijinta saida tayi mai isarta sannan takwanta nan k'asa.






Har akayi sallar isha'i yarima bai dawoba dan haka Zarah tana nan zaune inda take, sallah kawai take tayar da ita, koda yadawo taddata yayi inda yabarta tahad'e kanta da gwiwa cikin ransa duk sai yaji ba dad'i haka yawuce yashige bedroom nan yai wanka yashirya har ya hau gado ya kwanta sai kuma yaji bai iya barinta a wannan halin dan haka yamik'e yafito parlour.




Zarah da tana jin shigowarsa ammah tashare jin bai kulataba ya wuce bedroom yasa siraran hawayen bak'in ciki suka zubo daga idonta, tunani tashiga yi anya yarima da yace yanasonta da gaske yake? Anya ba kawai ya fad'a bane dan yakwantar mata da hankali?, tana cikin haka sai jinsa tayi ya dafata, ahankali tad'ago kanta takallesa,
Cike da damuwa yarima yace Zarah meyasa kikeson d'aga min hankali? Menene abin kuka, ke kuka baimiki wahala na lura, yanzu dai taso muje kiyi wanka ga ice cream chan nasiyo miki kisha kinji?


Zarah shuru tayi nan yarima yataimaka mata tamik'e suka shiga bedroom saida yad'auko mata towel sannan yaje yahad'a mata ruwan wanka, lokacin da yafito har tacire kayanta ta ma d'auka zai taimaka mata tayi wankan ammah sai taga ya je yai zamansa dan haka tawuce taje tayi tana mamakin yarima yadda kwata-kwata shi bai iya lallashin maceba saidai shi a lallashesa.




Bayan ta fito wankan lotion kawai tashafa sai humra sannan tawuce taje tabud'e wardrobe tad'auko sleeping dress d'inta tasaka, zuwa tayi tahau gadon takwanta, yarima kallonta yayi yace bazakisha ice cream d'inba yau?


Kamar tace masa eh ammah ganin tanason sha yasa tamik'e batare da tayi magana ba taje tad'auko tazauna tasha, saida tashanye roba d'aya sannan tamik'e taje tasaka sauran cikin freezer taje tawanko bakinta tadawo takwanta, lokacin yarima har ya kwanta, daga gefensa itama takwanta dan yau haka sukayi kwanciyarsu batare da sunji d'umin junaba, tana jin yarima yana ta juyi batasan ya yak'areba har bacci yai awon gaba da ita.






Da asuba bayan sunyi sallah baccinta takoma inda tabar yarima zaune yana dannar system d'insa.


Wajen k'arfe goma da tafarka da mamakinta baya nan, kallon agogo tayi taga har k'arfe goma ta yi, mik'ewa tayi tafito parlour nan ma bainan dan haka tasan ya je wajen aiki, gyara d'akin tayi sannan tashiga tayi wanka tashirya.


Bayan ta gama fitowa tayi main parlour nan tatarar da jamila zaune tana kallo,
Cikin sakin fuska zarah tagaisheta.
Murmushi jamila tayi tace maman baby kin farka, ya gidan.
Lpy lou Aunty jamila, halan har sun ficce.
Dariya jamila tayi tace lokacin kina bacci suka fita dan prince cewa yayi akwai theater d'in da zai shiga k'arfe tara saisa tun 8:30am suka fita.


Numfashi zarah taja tace gaskiya Aunty jamila kina k'ok'ari tun da safe kike tashi kina had'a breakfast.


Toh zarah ya muka iya, indai kace bazaka girka da wuriba ai sai miji yafita batare da yayi breakfast ba daganan kuma sai afara cin abincin masu siyarwa nikuma natsani inga mijina yana cin abincin waje ke ni ko na 'yar aiki banaso inga yana ci.


Jinjina kai zarah tayi tace wlh nima Aunty jamila banaso inga mijina yana cin girkin 'yar aiki ammah ba yarda na iya.
Murmushi jamila tayi tace toh ya kuka iya ai gidan sarauta ya gaji haka, kedai shawarar da zan baki kikula da mijinki sosai dan kinsan 'yan matan yanzu bare ma irinsu yarima na tabbata bakowace mace

08, February 2025
Shuraihu Usman

jjjjj

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login