Showing 147001 words to 150000 words out of 168813 words
Chapter 50 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt
inyi dan yunwa nakeji inyaso daga baya naji da rigimar taki.
Kissing d'in bakinsa tayi tace angama ranka yadad'e yadda kakeso haka za'ayi sannan tamik'e tana tafiya dakyar tafita taje parlour tad'ebo musu breakfast sannan tadawo nan suka zauna sukayi breakfast.
Bayan sun gama bajewa sukayi saman carpet yarima yad'aura kansa saman cinyarta, turo baki zarah tayi tace ni kad'agani inba so kuke kai da babynka kukaryaniba.
'Dago kai yayi yakalleta yace shikenan tunda haka kikace bari ma kawai intashi intafiyata.
Cikin sauri zarah tagirgiza kai tace a'a kayi kwanciyarka ni da wasa nakeyi.
Dariya yarima yayi yace dad'ina da matarnan tawa matsoraciya ce toh me kikeji ma tsoro a ciki?
Zarah d'aure fuska tayi tace ai dole inji tsoro saboda 'yan matan garin nan kamar mayu nasan kullum idanunsu suna a kan mijina saisa duk fitar da zakayi hankalina a tashe yake har sai ka dawo,,,tak'arashe maganar kamar zatayi kuka.
Da mamaki yazuba mata ido yana kallonta, ganin hawaye sun fara zuba daga idanunta yasa yatashi zaune tare da janyota jikinsa yace zarah yakamata kisan abinda mijinki zai iya da wanda ba zai iyaba, ni a yanzu 'yan mata basu a gabana dan babu ma wacce ta isheni kallo.
Uhm ammah ai su kana gabansu idan su basa gabanka.
Janyeta yarima yayi daga jikinsa tare da jingine kansa a jikin kujera yamaida idanunsa yalumshe.
Ido zarah tazuba masa sannan tarik'o hannunsa ahankali tace kayi hak'uri.
Bud'e idanunsa yayi yakalleta yace zarah mekikayi min da kike ban hak'uri?
Cikin shagwa6a tace toh ai naga kamar fushi kake da ni.
Ta6e baki yayi yace no ko d'aya ni ba fushi nake da keba kawai rigimarkice naga tanaso tafi k'arfina.
Rik'o hannunsa tayi tare da marairaicewa tace toh nadaina kayi hak'uri.
Murmushi yarima yayi tare da duba agogon da take mak'ale a hannunsa sannan yace bakomai baby yanzu dai tashi muje kirakani wata 'yar unguwa, cike da jin dad'i zarah tace dagaske dear.
Murmushi yayi tare da d'aga kai.
Fad'awa tayi jikinsa tarungumesa tace nagode sosai dear wlh daman ina ta so infita inga gari dan tunda mukazo babu inda naje.
Dariya yarima yayi tare da janyeta daga jikinsa yace baby kibi ahankali kar kiji ma babyna ciwo.
Itama dariyar tayi tace ni na isa inji masa ciwo ai da sai na amsa query wajen dadynsa tak'arashe maganar tare da mik'ewa taje bedroom tacanza kaya, Cikin atamfa tafito d'inki riga da skirt sannan tayafa veil tayi gwanin kyau.
Koda tafito ido yarima yazuba mata, matsowa tayi tahura masa ido kad'an, ajiyar zuciya yasafke sannan yace koma kisanyo hijab.
Turo baki tayi tace kaduba fa babban gyalene a jikina,
Mik'ewa yayi tare da d'aukan key d'in motarsa yace tunda baki shirya fitaba ni na wuce.
Cikin sauri tarik'o hannunsa ahankali tace dan Allah kayi hak'uri toh bari insanyo.
Kumatunta yaja yace muje hakan kar inja saboda turo bakin nan yata6o k'asa, duka zarah takai masa cikin wasa nan yagoce yana dariya yace kisameni a waje, yana fad'in haka yawuce yafita.
Zarah saida tabiya tashaida ma jamila zasu fita nan tayi mata adawo lafiya sannan tazo tatarar da yarima cikin motarsa zaune yana jiranta, tunda tafito yatsareta da ido har tabud'e motar tashigo sannan yajasu batare da yayi maganaba.
Gugu yakeyi sosai da motar zarah ko titi tazuba ma ido tana kallon tsarin garin cike da burgewa, gaban wani babban Boutique yayi parking daga sama zarah taga ansa symbol d'in baby's paradise, muryar yarima taji yace bismillah madam.
Murmushin jin dad'i zarah tayi sannan tabud'e tafito, tare suka jera suka shiga ciki yanayin tsarin wajen ya burgeta sosai bin ko'ina da kallo take duk kayane masu kyau da tsada ahaka har suka haura saman step nan kuma taga kayan jarirai da na k'ananun yara, kallon yarima tayi tana shirin tambayarsa nan yasakarmata murmushi yace kiza6ar ma babynmu kaya.
Zaro ido zarah tayi tace babyn da baizo duniyaba bamusan ko namiji bane ko mace.
Murmushi yayi a karo nabiyu sannan yace kar kidamu baby duk wanda Allah yabamu munaso kuma in munsiya zamu iya ajewa ko saboda gaba.
Murmushi tayi cike da gamsuwa da maganarsa tace hakane dear, nan tafara d'iban over roll saida tad'ibi kusan kala goma sannan tad'auki kayan baby gurl kala biyar na baby boy kala biyar.
kallon yarima tayi da yazuba mata ido tace nagama, janye idanunsa yayi batare da yayi maganaba nan yacigaba da d'iban kaya duk wanda yayi masa d'auka yake saida yahad'a kusan kala talatin, trolly guda yacika da kayan baby's, zarah ko baki tasaki tana kallonsa har yagama sannan suka dawo k'asa itama yasata tad'ibi nata kayan sannan sukaje wajen payment yabiya su kud'insu nan aka kaimasa har cikin motarsa sannan suka shiga yatada suka tafi.
Yawo yayi da ita sosai yanuna mata wajaje dadama sunje pack da malls iri-iri, sayayya yayi mata sosai tun daga kayan tand'e-tand'e zuwa na amfani dan ko turaruka masu tsada yasiya mata, sai gab da magrib sannan suka dawo gida agajiye.
Bayan sallar isha'i kwance suke saman gadonsu zarah tana rungume a jikinsa shikuma yana dannar wayarsa, ahankali zarah tad'ago takallesa, yanayin yadda take kallonsa yasa yagane magana takesonyi dan haka ya aje wayar gefe sannan yace ina saurarenki dan wannan bakin naki nasan akwai magana a cikinsa.
Murmushi tayi tare da gyara kwanciyarta sannan tace tabbas hakane my heartbeat taimako da alfarma nakeso kayimin.
zubamata ido yayi batare da yayi maganaba, zarah janye idanunta tayi daga kallonsa sannan tace dan Allah kataimaka kakira min su mama mugaisa kuma kaga k'ashen watannan za'ayi bikkin Aysha.
Murmushi yarima yayi yace ai muna waya da su suna ma cewa ingaisheki bana fad'amikine saboda gudun rigimarki sannan maganar bikki kuma saidai kiyi hak'uri bazan iya barinki kijeba kuma na fad'ama su mama mun d'anyi tafiya, suma sunsan yanzu kinyi nauyi, dan haka kibari idan Allah ya safkeki lafiya sai muje kigansu.
Mamakine da bak'in ciki suka cika zarah tamarasa abinda zatace masa daga k'arshe zame jikinta tayi takwanta saman gadon tare da juya masa baya.
Shareta yarima yayi dan yasan inyace zai lallasheta a wannan lokacin rigima zatayi masa sosai, daga k'arshe mik'ewa yayi yakoma parlour yai kwanciyarsa saman kujera a nan yagama abinda zaiyi yai baccinsa.
Zarah ma saida tasha kukanta sannan bacci yai awon gaba da ita, cikin dare ko da tafarka talaluba taji babu yarima nan tatashi taduba bata gansaba dan haka tadawo parlour, ganinsa tayi kwance saman kujera yana ta baccinsa.
Zuwa tayi tazauna k'asa gefen kujerar nan tad'aura kanta saman kujerar ahaka tacigaba da baccinta.
Juyin da yarima zaiyi nan yaji abu ya takuresa, yana bud'e idanunsa da mamaki yake kallon zarah da take bacci a takure, dafe kansa yayi tare da furta oh zarah, sannan yamik'e yad'auketa yanufi bedroom da ita, yana kwantar da ita saman gado tana bud'e ido, daga gefenta yarima yakwanta yace kedai kinason wahalar da kanki menene nakwanciya a chan.
Kanta tad'aura saman k'irjinsa tace toh ai kaine kak'i kwanciya kusa da ni bayan ka sabamin ban iya bacci sai tare da kai, kuma fushi kake da ni,
Shafa kanta yayi yace ni ba fushi nake da keba zarah kawai na d'an baki wajene kihuta.
marairaicewa tayi kamar zatayi kuka tace toh kadaina guje min dan Allah kayi hak'uri na daina.
murmushi yarima yayi yace shikenan zarah nadaina yanzu dai kiyi bacci sai dasafe.
k'ara shigewa tayi jikinsa tare da cewa Allah yakaimu my heartbeat.
Tura kansa yayi cikin gashin kanta yana shak'ar k'amshinsa inda hannunsa yake shafar bayanta da shi ahaka bacci mai dad'i yai awon gaba da su.
_Comment_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'artโ๐ป_
[5/3, 9:53 PM] Sis Naj Atu: . ๐๐๐
_*YARIMA SUHAIL*_
๐๐๐
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ยฎ*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE ๐ HEART TORCHING โค TEARS OF SORROWS ๐ญ CURDLES ๐ GIGGLES ๐ AND MARRIEGE THINK๐
*JUST GIVE US FOLLOW....โ*
๐๐๐
_~Happy Born day momcy sady wsh u many more years ahead nd Allah's noor๐๐~_
๐๐๐
_*My friendy Beebah M Shehu nd my lil sis Aysha Eesho kumatso kusa yau page d'in nakune sai yadda kukeso zakuyi da shi๐๐*_
6โฃ6โฃ
A chan 6angaren memartaba koda yana a kwance ammah har a lokacin maganarsa d'ayace shidai yarima, ahaka yasa aka ware kud'i masu yawa yace agyara ma suhail d'insa part d'insa dan yana ji a jikinsa zai dawo garesa, kowa ya d'auka magagin ciwone har anshare maganar saida sukaga ran memartaba yana shirin 6aci sannan akasa akafara yi masa gyara.
Yanzu mulkin hannun waziri suka damk'asa dan bawani mai kwanciyar hankali a cikin 'ya'yansa, gabad'aya family d'in abubuwa goma da ishirin sun had'u sun cakud'e musu, kullum maganar d'ayace shine memartaba ya amince aje ayi scanning d'in ammah ya k'i saidai ruwan addu'o'i da malamai suke aiko masa da shi ake bashi yana sha, masallatai ko duk sallah sai sunyi ma sarkinsu addu'a dafatan Allah yatashi kafad'unsa.
Yau ma kamar kullum 'ya'yansa ne zagaye da shi daga gefensa dada ce, cike da damuwa sultan ahmad yaruk'o hannun mahaifin nasa yace ranka yadad'e kataimaka ka amince muje ayi scanning d'innan kaga gabad'aya hankalinmu atashe yake babu sauran mekwanciyar hankali dukkanmu nan a k'ark'ashinka muke burinmu d'aya shine muga kasamu sauk'i.
Murmushin k'arfin hali memartaba yayi sannan ahankali muryarsa tana fita dakyar yace Ahmad kucigaba da yi min addu'a in da rabon intashi toh zan tashi domin waraka ta ubangiji ce.
Dada fashewa tayi da kuka tace hakane ranka yadad'e ammah ai ubangiji bai safkar da cutaba saida yasafkar da maganinta dan Allah kataimaka aje asibitin kaga bamu kad'aiba hatta sauran mutane hankalinsu atashe yake.
Cikin dauriyar ciwo memartaba yace shikenan na amince muje ammah ubangiji ya gama tsara komai akan lamarinsa.
Cike da jin dad'i tare da neman gasgata kalmar da kunnuwansu suka jiye musu nan suka shiga kallon juna suna murmushi.
Sultan Abbas ne yace dagaske ya amince muje?
Shima sultan ahmad murmushi yayi yace nima kusan abinda kunnuwana suka juyo min kenan.
Dada share hawayen fuskarta tayi tace Alhmdllh yanzu kuje kusa ashirya motocin da zamu tafi da shi, asibitin suhail kawai zamuje.
Cikin jin dad'i sukaje sukasa aka shirya motoci nan aka fito da memartaba aka shigar da shi motar da aka tanada dominsa Dada kawai tashiga cikinta.
Su kuma cikin d'ayar motar suka shiga ahankali ake tuk'in duk inda aka wuce talakkawa d'aga masu hannu suke suna ma shugabansu fatan samun lafiya.
Koda suka isa Prince.S hospital, cikin gaugawa akazo aka tarbesu dan motocin kawai da suka gani yasa sukagane daga inda suke,
Dr khalil da sauran manyan likitocine tsaye akan memartaba a cikin wani k'ayataccen room suna ta bincike bayan anyi masa scanning d'in, inda shi kuma yake ta baccinsa.
Gabad'aya hankalinsu ya tashi saboda basusan yadda zasuyi sushawo kan matsalar ba nan sukayi 'yan maganganunsu.
Dr khalil ne yafito jiki ba k'wari yanufi inda su dada suke zaune, ganinsa yasa gabad'ayansu suka mik'e suna tambayarsa jikin memartaba.
Murmushin k'arfin hali yayi yace Alhmdllh dasauk'i sannan yasamu waje yazauna, ya umurcesu da suma suzauna bayan sun zauna, kallonsu Dr khalil yayi sannan yace Alhmdllh mun gano abinda yayi causing d'in ciwon cikin ba komai bane face 'yan hanjinsane da wasu suka nad'e,
Gabad'ayansu saida gabansu yafad'i sukace 'yan hanjinsa sun nad'e?
Ganin yadda hankalinsu yatashi yasa Dr khalil yad'anyi murmushi yace kar kudamu ba wata babbar matsala bace tunda daman ana samun masu shiga wannan condition d'in kuma suna rayuwa saidai ta hanya d'aya za'a bi.
Gabad'aya suka had'a baki wajen cewa ta wace hanya kenan?
Ajiyar zuciya yasafke sannan yace ta hanyar yin theatre.
Sultan abbas ne yace toh Dr indai ta hakan za'a samu sauk'i toh mu relatives d'insa mun amince ayi masa kawai.
Jinjina kai Dr khalil yayi yace abbah saidai wani hanzari ba guduba jinin memartaba ya hau sosai babu yadda zamuyi mu iya yin wannan aikin batare da jininsa ya d'an yi low ba.
Salati suka sanya cike da tashin hankali, dada kuka tasaka tace yanzu khalil babu yadda za'ayi a iya yin komai?
Cike da jin tausayinta yace ranki yadad'e kar kidamu zamu duba mugani.
Yauwa Dr dan Allah kubincika sosai.
Dr khalil yace kar kidamu ranki yadad'e zamuyi iya bakin k'ok'arinmu.
Yafuto sultan Ahmad yayi da ido sannan yamik'e yace ina zuwa.
Saida yafita sannan sultan Ahmad yamik'e yabi bayansa.
A office d'insa suka je, bayan sun zauna Dr khalil kallonsa yayi cike da damuwa yace daddy adai cigaba da yi masa addu'a dan jininsa ya hau over, kuma a wannan condition d'in da yake ciki baikamata ad'au lokaciba batare da anyi masa aikinba, ammah a yanzu zamu d'aurasa akan wasu drugs tsawon kwana ukku idan har jinin baiyi low ba toh saidai afitar da shi abroad.
Innalillahi wa'innah ilaihiraji'un daddy yashiga nanatawa cike da damuwa.
Dafe kai Dr khalil yayi kamar mai tunani sannan yace yauwa akwai wani mai irin wannan condition d'in da aka kawo mana bamuyi aikinba sai dagabaya akace mana ankaisa a wani gari wani likitane yayi masa aikin saidai ban tambayi wane gari bane ammah gaskiya ance yanzu haka mutumin yana nan lafiya lau ya warke.
Cike da damuwa sultan ahmad yace dan Allah khalil kataimaika kagano wane garine inyaso sai muje.
Murmushi Dr khalil yayi yace insha Allahu daddy zan bincika yanzu dai bari inje infara kawo drugs d'in da zai fara amfani da su mugani, Indai har akayi kwana ukkun bai safkaba sai kutafi chan.
Jinjina kai daddy yayi cike da gamsuwa da maganar Dr khalil yace Allah yashige mana gaba.
Ameen,,cewar Dr.
Sannan suka tashi suka fito tare inda sultan ahmad yakoma wajensu dada yai musu bayanin rik'esu da za'ayi tsawon kwana ukku ad'aurashi akan magani, ammah bai fad'a musu sauran bayaninba gudun kar hankalin tsohuwar tasu yatashi sosai.
Haka Dr khalil yaje yakawo drugs d'in, tun daga wajen d'akin dogarawane aka zuba suna gadinsa, sultan ahmad ne yace zai dinga kwana da mahaifin nasa ahaka su dada suka amince suka koma gida.
Kulawa sosai memartaba yake samu daga ma'aikatan asibitin ba a awa d'aya batare da anzo anduba lafiyarsaba, abinci dakyar ake samu yana d'an ci kad'an kafin yasha magani, su dada kullum suna hanyar asibitin sai dare suke komawa.
Mutanensa dadama sunzo dubasa dan ma ana hanasu shiga wajensa saboda ba aso ana damunsa dayawa.
*BAYAN KWANA UKKU*
Nan likitoci suka k'ara taruwa akan memartaba aka k'ara bincikawa ammah har a lokacin jinin nasa bai yi wani low ba saidai d'an ragewa da yayi kad'an.
Gabad'ayansu hankalinsu ya tashi, nan Dr khalil yakira sultan ahmad da sultan abbas cikin damuwa yasanar da su,
Su dukansu hankalinsu ya tashi, ganin haka yasa yace ammah Alhmdllh na binciko garin da kwararren doctor d'in yake ance min garin Abuja saidai sunce bazasu iya tuna sunansaba ammah yana aiki a babbar asibitin garin, insha Allahu inaji a jikina za'a dace idan akaje chan.
Cike da gamsuwa suka ce insha Allahu zuwa gobe zasusa ayi masu komai sukama hanya dan yanzu ma dare ne kuma sunaso suyi shirye-shirye saisa bazasujeba a lokacin.
Dr khalil yace Allah yasa adace.
Nan sukaje suka sanar ma dada akan batun zuwansu jihar abuja, saida ta jinjina ma lamarin sannan tace toh shikenan Allah yakaimu goben yanzu muzo mutafi gida muyi 'yan shirye-shiryenmu.
Koda suka koma gida kayansu suka shirya nan sultan abbas yaje yayankar musu ticket, su sultana bilkisu da sultana sadiya sunso subi aje dasu dada tace a'a subari sai daga baya sai suzo ammah yanzu in suma sunbi wa za'a barma gidan.
Haka suka hak'ura suka zauna tare da yin fatan Allah yasa adace.
Da dare koda waziri yashigo duba jikin memartaba, rik'o hannunsa memartaba yayi cikin muryarsa da bata fita sosai saboda zafin ciwo yace ga amanar gari da talakkawana nan na damk'a maka.
Rik'e hannunsa waziri yayi kwallah duk tacika masa ido yace na amsa ranka yadad'e Allah yabani ikon cikawa kaikuma Allah yabaka lafiya.
Cikin jin dad'i memartaba yayi murmushi tare da maida idanunsa yalumshe.
Wanshe kare tun dasafe motoci kusan guda goma sukayi layi suna jiran fitowar su memartaba, wajen k'arfe goma suka fito, inda su sultana bilkisu sukayi musu rakiya har airport, inda dandozon mutane suke tsaye ahaka suka shige jirgin mutane na d'ago musu hannu tare da addu'an Allah yaba shugaban nasu lafiya, saida sukaga tashinsu sannan kowa yakoma gida.
*GARIN ABUJA*
Suna isa garin nan sukatarar da motoci da shi kansa sarkin garin tsaye suna jiran isowarsu, kasancewar daman tun jiya sun sanar da shi akan zuwan da zasuyi.
Cikin karamci da jin dad'i suka tarbesu daga nan suka d'unguma wani k'ayataccen gida da aka tanadar masu dan suzauna a ciki, sunso sufara wucewa asibitin ammah sarkin garin yace sufara zuwa su huta sannan.
Haka suka hak'ura saida sukaje suka kimtsa suka ci abinci sannan sukafito suka shiga motocin da sarkin ya aje musu aka jasu zuwa asibitin.
Koda suka isa yanayinsu kawai aka gani da motocin da suke ciki yasa aka gane daga inda suka fito, koda daman sarki kabir ya kirasu ya sanar da su akan zuwan sarkin gazban.
Tarbarsu akayi sosai inda aka wuce da memartaba a amenity, nan suka duba history taken d'in da ke cikin folder d'insa na chan garin, saida suka k'ara yi masa scanning d'in dan tabbatarwa nan kowa yai shuru.
Sultan Ahmad ne yasanar da su abinda Dr Khalil yafad'a musu akan wani mai irin condition d'in da aka ta6a yi ma theatre kuma BP d'insa yayi high.
Jinjina kai MD Dr Muhammad bashir yayi sannan yace shikenan zanje intuntu6i Dr S domin nasan shine kawai zai iya hakan.
Cikin jin dad'i sukayi masa godia nan yatashi yanufi office d'in Dr suhail da baisan wainar da ake toyawaba.
Lokacin da M-D yashiga zaune yatarar da shi yana research a cikin system d'insa.
Nan yamik'a masa hannu suka gaisa, bayan sun gaisa nan yake sanar da shi akan zuwan wasu da irin condition d'in da patient d'in yake ciki.
Shuru Dr suhail yayi na d'an Lokaci sannan yace zan iya ganin file d'in patient d'in?
Nan Dr muhammad bashir yayi waya, ba a wani dad'eba saiga wani Dr hannunsa rik'e da file nan yabud'o yamik'a ma Dr suhail, saida gaban Dr suhail yafad'i ammah yadake yana karanta history taken batare da ya duba sunan me file d'inba.
Saida yagama karantawa nan gabansa yai wani irin fad'uwa lokacin da yaga sign d'in Dr khalil, cikin sauri yajuya bayan folder d'in, baisan lokacin da saki folder d'inba lokacin da yaga sunan da yake jikinsa, nan gabansa yacigaba
08, February 2025
Shuraihu Usman
jjjjj