Showing 114001 words to 117000 words out of 168813 words
Chapter 39 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt
take maganaba,,,dada k'ulewa tayi ganin baida niyar yin magana tace watau ga sakarya tana magana bakaji ma zaka iya tankamin.
Saida yarima yayi Kusan minti biyu sannan yad'ago yakalli dada da tatsaresa da ita, murmushi yayi sannan yace toh ranki yadad'e na ji.
ta6a hannu dada tashigayi tace na shiga ukku yanzu saboda Allah suhail ni kake ma haka? Ko mahaifinka bai isa yayimin hakaba sai kai?
Shuru yarima yayi yakyaleta nan dada tayita masifarta daga k'arshe jingine kansa yayi da kujerar da yake zaune yamaida idanunsa yalumshe.
Dada tsura masa ido tayi takasa cigaba da fad'an dan gabad'aya yarima ya gama kashe mata baki, cike da takaici tanuna k'ofa tace tashi kafita kabani waje.
Yarima bud'e idonsa yayi tare da d'aukan wayansa yace na barki lafiya.
Dada binsa tayi da kallo har yaficce takaici yacikata saisa batason wani abu yahad'ata da yarima dan takaici kawai take kwasa, cikin ranta kuma tana jinijna ma halinsa, ahankali tace wannan mutumin halinsa sai shi, ina amfanin miskilanci irin haka, lallai matansa da suke zaune da shi suna k'ok'ari.
Yarima koda yafita daga nan 6angaren iyayensa yawuce, ko da yashiga parlour ummi batanan, bakowa ciki, dan haka yasamu waje yazauna tare da dafe kansa dan shi gabad'aya anhad'a masa zafi dayawa tsaki yaja yace ta ko'ina ba sauk'i.
Sultana bilkisu da tafito daga bedroom tsaye tayi tana kallon d'an nata da gabad'aya hankalinsa baya a jikinsa, cike da tausayinsa tataka ta isa inda yake daga gefensa tazauna, Sai a lokacin yarima yad'ago yakalleta nan yasakarmata murmushi.
Sultana bilkisu ma maida masa martani tayi sannan tace my son lafiya naganka nan zaune?
Yarima duk'ar da kansa yayi yace ummina barka da rana.
Ido tazuba mai tace dafatan kuna lafiya?
Lafiya lou ummi.
Toh ya wajensu sumayya da zarah.
saida yajingine kansa da kujera sannan yace duk suna lafiya.
Toh ya d'iyartawa da jiki?
Yarima d'an sosa kai yayi alamun jin kunya sannan yace ummi dasauki.
Toh masha Allah, Allah yaraba lafiya.
Shuru Yarima yayi baice komai ba.
Sultana bilkisu rik'o hannunsa tayi tace my son me yake damunka?
Yarima kallonta yayi yana murmushi yace bakomai ranki yadad'e.
Sultana bilkisu batayi mamakin jin hakan daga garesaba dan ta san halin d'an nata, murmushi tayi tace shikenan ammah dan Allah kadinga hak'uri ka san ganinka cikin irin wannan yanayi ba k'aramin d'agamin hankali yakeba.
Yarima kwantar da kansa yayi saman cinyar ummi yace kar kidamu ummina babu abinda yake damuna kawai dai ji nayi inaso inzo inganki.
Cikin jin dad'i sultana bilkisu tashiga shafa gashin kansa tace Allah yaimaka albarka my son.
Ameen ummina....nan Yarima yamaida idanunsa yalumshe, sultana bilkisu tazuba mai ido tana kallon d'an nata cike da so da k'auna.
Tun daga lokacin Yarima yadaina shiga harkar kowa dan yanzu tun safe idan yafita baya dawowa sai wajen 9pm saboda meeting da suke zama, kuma idan yadawo sai ya gargad'i guards d'insa akan kar subar kowa yashigo masa hutawa yakeson yi.
ba zarah ba hatta ita kanta sumayya saida tad'an shiga damuwa.
_*After one week later*_
Yau yarima kasancewar bai fitaba zaune yake d'akinsa a parlour yana kallo zarah ce tashigo da sallamarta.
Yarima batare da ya juyo ya kalletaba ya amsa, zarah wani irin sanyi taji a ranta da tagansa, takawa tayi ta isa inda yake zaune da mamakinsa sai gani yayi ta zauna saman cinyarsa,
Sai a lokacin yarima yakalleta shi kansa wani irin sanyi yaji a ransa, zarah k'irjinsa tashige tare da fashewa da kuka.
Runtse idonsa yarima yayi yana jin kukan nata har cikin ransa, rungumeta yayi muryarsa tana rawa yace zarah me yake samunki?
Zarah tsagaitawa tayi daga kukan da take sannan tace akwai abinda yake samuna bayan wanda kayi min?
Ido yarima yazuba mata batare da ya ce komai ba,
cikin sheshek'ar kuka tace shine kagujemin kadaina shiga sabgata gabad'ayama kadaina zaman gidan.
Yarima tallabo fuskarta yayi yace toh ya kukeso inyi muku naga kamar kinfison hakan, kefa kikace kin daina shiga sabgata saisa nabarki kihuta.
Zarah rungumesa tayi tace hakan da kayi ba k'aramin d'agamin hankali yayiba dan Allah kayi hak'uri na daina.
Yarima kallon cikin idonta yayi sannan yace meyasa bakison cin abinci?
Zarah turo baki tayi tace taya zanci abinci bayan babynka yana matsamin ina tunanin missing d'in daddynsa yayi......tak'arashe maganar tare da kashe mashi ido d'aya,
Yarima hannunsa yakai cikin rigarta yana shafar cikinta, zarah maida idanuwanta tayi talumshe tana jin dad'in hakan da yakeyi mata.
Gabad'ayansu shuru sukayi ba wanda yak'ara magana, ahankali taji hannunsa suna yawo cikin rigarta,
Chan kuma sai ya janye hannunsa daga cikin rigarta yace tashi muje kici abinci,
Zarah d'ago kai tayi takallesa tare da turo baki tace nifa na k'oshi.
Yarima zuba mata ido yayi sannan yace ammah ai ga shedanan yau bakici abinciba.
Zarah kamar zatayi kuka tace ni ice cream nakeson sha,
Jan hancin yarima yayi sannan yace toh kije kici abinci zan bayar asiyo miki,
Zarah mik'ewa tayi tana gyara rigarta sannan tace toh ammah fa kad'an zan ci.
'Daga kai kawai yarima yayi batare da ya yi maganaba.
Juyawa Zarah tayi tafita tabar d'akin, nan yarima yakoma saman 3 seater yakwanta yana ci gaba da kallonsa yana jin wani irin nishad'i a ransa.
Daga k'arshe yamik'e yazari key d'in motarsa yaficce yabar gidan.
Zarah koda takoma part d'inta kad'an taci abincin nan tazauna zaman jiran yarima yakawo mata ice cream d'in ammah shuru, zuwanta biyu part d'insa ammah baya nan.
Ahaka har akayi sallar isha'i taje tayi wanka tai shirin baccinta,,,,tana cikin saka night gown d'inta sai ga kiran yarima ya shigo wayanta cikin jin dad'i tayi picking kamar zatayi kuka tace shine kabarni ina ta jiranka.
Daga Chan 6angaren yarima cemata yayi tazo ta amsa gashinan.
Cikin jin dad'i Zarah tace toh.
Cikin sauri ta ida shirinta tafito tanufi part d'in yarima.
Tana shiga ganin baya parlour yasa tawuce bedroom d'insa ahankali tatura k'ofan tashiga, saman gadonsa tahangosa zaune yana ta waya hannunsa rik'e da paper da biro yana rubutu.
Takowa tayi ta iso bakin gadon, d'ago kai yarima yayi yakalleta sannan yai mata nuni da ledar da take aje k'asa.
Cikin jin dad'i zarah taje tad'auki ledar, a nan k'asa tazauna tabud'e tad'auko d'aya sannan tatashi tasaka sauran cikin freezer d'insa.
Dawowa tayi tad'auki wanda ta aje taje gefensa tazauna tabud'e tana sha.
Har a lokacin yarima yana ta 'yan rubuce-rubucensa, zarah ahaka tashanye sannan taje toilet d'insa tawanke bakinta.
k'arshen gadon taje takwanta tana kallonsa yana ta wayansa, daga k'arshe da taga wayar batada niyar k'arewa dan haka tamik'e takoma gefensa tazauna, marairaicewa tayi ahankali tace wai wayar ba a gamata hakanan dare fa ya yi.
Kallonta yarima yayi nan zarah tad'aga mai gira,
idanuwansa yamaida ga agogon da take manne ga bangon d'akin ganin har 11pm ta yi yasa yayi sallama yakashe wayar.
Kallon zarah yayi da tatsaresa da ido sannan yace bazaki kwantaba?
Zarah batare da tayi magana ba tamik'e taje takwanta, yarima kashe gloves d'in d'akin yayi sannan shima yahau gadon daga gefen zarah yakwanta.
Zarah tana ganin ya kwanta nan tamaida kanta saman k'irjinsa, yarima kamar daman jira yake nan yarungumota jikinsa tare da k'ok'arin rabata da rigar jikinta, yana cirewa Zarah tazame jikinta takoma gefe,
numfashi yarima yaja, cikin kasalalliyar muryarsa yace ya dai?
Zarah cikin tsokana tace ni bacci nakeji.
Yarima matsawa yayi gab da ita sannan yace tun d'azu me yahanaki baccin?.
Zarah turo baki tayi har ta bud'e baki zatayi magana sai ji tayi yarima ya had'e bakinsu waje guda yafara kissing d'inta cikin k'warewa,
Zarah gabad'aya tafita hayyacinta inda kowane 6angare na jikinta yake kar6an sak'onsa, k'ara rungumesa tayi jikinta ita kanta ta san ta yi missing d'insa.
nan yashiga sarrafata son ransa, har tagaji ammah yak'i barinta daga k'arshe kuka tasa mashi ammah Yarima baima san tana yiba dan gabad'aya hankalinsa baya tare da shi.
Saida yagaji dan kansa sannan yabarta zarah chan gefe takoma takwanta tana sheshek'an kuka.
Yarima duk sai yaji ba dad'i dan haka yajanyota jikinsa batare da ya yi maganaba yashiga d'an bubbugamata baya alamun lallashi.
nan zarah tarage sautin kukan nata daga k'arshe bacci yayi awon gaba da ita.
Yarima na jin ta yi bacci yajanyeta daga jikinsa yalullu6eta da blanket sannan yatashi yanufi toilet dan yayi wanka.
Bayan ya fito shiryawa yayi sannan yahau gadon yakwanta tare da jawo zarah jikinsa yarungume yana shafar cikinta d'an wata biyar, a haka bacci yad'aukesa
Da asuba saida yayo alwallah sannan yatayar da zarah yawuce masallaci.
jikinta duk ciwo yake haka tajanyo kayanta tasaka tafita takoma part d'inta, a chan tayi wanka tad'auro alwallah tai sallah bayan ta gama tahaye saman gadonta takoma bacci.
_Comment_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'artโ๐ป_
๐๐๐
_*YARIMA SUHAIL*_
๐๐๐
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ยฎ*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE ๐ HEART TORCHING โค TEARS OF SORROWS ๐ญ CURDLES ๐ GIGGLES ๐ AND MARRIEGE THINK๐
*JUST GIVE US FOLLOW....*โ
*PAGE* 5โฃ5โฃ
Bayan sallar la'asar yarima zaune yake saman cushin daga gabansa table ne ya d'aura laptop d'insa yana dannawa yanayin yadda yamaida hankalinsa gabad'aya akan laptop d'in zai tabbatar maka da abu mai muhimmancine yakeyi.
Sumayya kamar anjefota tashigo d'akin ba ko sallama.
Yarima d'ago kai yayi yakalleta sannan yacigaba da abinda yakeyi,
Takowa tayi ta iso inda yake, tsaye tayi gefensa fuskarta a d'aure tace haba yarima gaskiya bakayimin min adalci.
Yarima d'ago kai yayi yakalleta fuskarsa ba alamun wasa yace ke baki iya sallama ba?
Ta6e baki Sumayya tayi sannan tace a inda yadace ake sallama, nidai na fad'a maka kaji tsoron Allah, kuma inma laifi nayi maka ai na baka hak'uri.
Ture laptop d'in yayi gefe tare da d'ago kai yakalleta cikin 6acin rai yace ke matsalata da ke bakida isassar tarbiya yanzu haka ake magana da miji?
Sumayya kallonsa tayi cikin 6acin rai tace nice banda tarbiya? lallai yarima nagode, ammah inaso kasani ba babbar marar tarbiya sai wacchan d'iyar matsiyatar da ka auro wadda talauci yai mata..... yarima a fusace yamik'e tsaye, marin da ya wanka matane yasa takasa k'arasa maganar.
Da mamaki Sumayya take kallonsa tace yarima ni kamara?
Nunata yayi da yatsa yace anmareki ko zaki ramane? Wlh Sumayya kikiyayeni na fara gajiya da wannan haukan naki, kuma wadda kike kira matsiyaciya Wlh ta fiki daraja a idona dan kwatakwata yanayin tarbiyanku ba d'aya bane,
Sumayya fashewa tayi da kuka tace wlh ba zan yardaba sai na rama abinda kayimin kuma sai na fad'ama dada saboda wacchan matsiyaciyar ka.... yarima k'ara wanketa yayi da mari yace indai kika k'ara kiranta da matsiyaciya wlh sai na takaki cikin d'akin nan kuma inda sabo toh kin saba had'ani da su dada saidai inaso kisani babu wanda ya isa yasani inyi abinda banyi niyaba, harara yawurga mata sannan yace fita kiban waje ko yanzu in6ata miki rai, shashashar banza.
Sumayya tana dafe da kuncinta tajuya saida takai bakin k'ofa sannan tajuyo tace kasaurareni zaka san ka ta6a Sumayya,,,,tana fad'in haka tajuya tafita tabar d'akin.
Yarima komawa yayi yazauna tare da dafe kansa zuciyansa tana masa wani irin zafi, takaicin Sumayya ne yacikasa cikin ransa yace ina amfanin auren irin wad'annan mata,,, daga k'arshe mik'ewa yayi yaje yashige bedroom d'insa.
Sumayya koda takoma part d'inta kuka take sosai takaicinta duk akan zarah yarima yayi mata mari biyu,,,nan tsanar zarah tak'ara kamata ji take kamar taje takashe zarah kowa yahuta,
Haka tawuni tana kuka, kiran zinat ne da yashigo wayanta yasa tatsagaita da kukan da take har saida takusan tsinkewa sannan tayi picking.
Daga chan 6angaren zinat cewa tayi baby tun d'azun nake kiranki ammah bakiyi picking ba why?
Sumayya shuru tayi, zinat tace hello baby kina jina?
Sai a lokacin Sumayya cikin muryarta da tadashe saboda kuka tace sorry bana kusa.
Daga chan 6angaren zinat dafe kanta tayi tace oh my god baby ke kullum bakida aiki sai kuka? Yanzu kuma wa yata6aki.
Sumayya cigaba tayi da kukan, cikin kuka tace dole kice haka zinat bakisan cikin halin da nakeba yau akan wacchan jakkar yarima yai min mari biyu.
Cikin d'aga murya zinat tace mari?
Sumayya cikin sheshek'ar kuka tace eh, wlh ba zan k'yaletaba sai na rama abinda yayimin akanta, inma saboda cikinta yaimin haka toh wlh sai na zubar da shi.
Ajiyar zuciya zinat tayi sannan tace baby kiyi hak'uri gobe zan shigo garin sai musan yadda zamu 6ullo ma lamarin dan wlh bazamu hak'uraba.
Koda Sumayya kuka take ammah kuma bai hanata murnaba, cikin jin dad'i tace dagaske kike baby gobe zakizo?
Dariya zinat tayi tace ai daman kiran da nake miki kenan kishirya gobe kina da babbar bak'uwa.
Hmm kinjiki da tsokana wai bak'uwa, ammah fa naji dad'i sosai baby ai dole inyi babban shiri, Allah yakaimu goben da rai da lafiya, wlh har kinja bak'in cikin da nake fama da shi ya ragu.
Dariya zinat tayi tace kai baby, yanzu dai bari inje inyi visa dan ta flight nakeson zuwa, me kikeso intafo miki da shi.
Shuru sumayya tayi kamar mai tunani sai kuma chan tace kiza6o min abu mai dad'i wanda zaisani farin ciki.
Ohk baby angama koma mekenan zan kiraki.
Sumayya kashe murya tayi tace baby kiyo shiri sosai dan gobe ba d'agi, kema kinsan nayi missing d'inki ga wanchan banzan kwana biyu rigima kawai muke bare ma ind'an samu sauk'i.
Dariya zinat tayi tace shikenan baby ai dole gobe mukasance da juna dan nima ba k'aramin missing d'inki nayiba, zan kiraki da anjima muyi magana.
Ohk baby sai najiki, nan sukayi sallama suka kashe wayan.
Sumayya hawayen fuskarta tagoge tace lallai gobe koma me za'ayi saidai ayi ammah sai nayi silar zubewar cikin chan nata, shi kansa sai ya gane kuskurensa na marina da yayi,,,murmushin mugunta Sumayya tayi sannan tamik'e tanufi toilet dan tawatsa ruwa saboda gabad'aya jikinta ciwo yakeyi mata.
A chan 6angaren zarah tana chan d'akinta kwance dan wata irin kasala takeji daga wanka sai sallah kawai suke tashinta, daga k'arshe da kwanciyar ta isheta tashi tayi tad'auko littafatanta na islamiyya takoma parlour tazauna tana nazari.
Bayan ta gama kiran ummi tayi a waya suka gaisa nan ummi take tambayarta idan akwai abinda take buk'ata.
Zarah tace bakomai ummi.
Toh indai kinji kina buk'atar wani abu kiyo waya kisanar da ni Zarah banason nok'e-nok'e ni uwace kinji?
Cikin Jin dad'i Zarah tace toh ummi insha Allahu, nagode sosai Allah yak'ara girma da d'aukaka.
Ummi ta ji dad'in addu'an sosai tace Ameen daughter adai cigaba da hak'uri,,,,nan sukayi sallama suka kashe wayan.
Murmushi Zarah tayi cikin jin dad'i dan har cikin ranta tanason matar.
Daganan takira su mama a waya suka gaisa.
Bayan sallar isha'i koda tagama shirinta kwanciyarta tayi part d'inta dan cewa tayi ba zata koma wajen yarima ba yak'ara wahalar da ita irin na jiya dan ita kad'ai tasan wuyar da tasha.
Yarima ma koda yagama shirinsa kwanciyarsa yayi dan shi kansa ya san inba sa'a ba dawuya yau Zarah tadawo, murmushi yayi wanda baisan ya su6uce masaba, shi kansa ya yi mamakin yadda yacanza haka cikin k'ank'anin lokaci, cikin ransa yace toh me hakan yake nufi?,, 6ari guda na zuciyansa yace kodai ka fara sonta?
Zumbur yayi yatashi zaune cikin d'aga murya yace hakan ba zai ta6a yuwuwaba, toh me hakan yake nufi?
Ahankali yace kawai dai na damu da itane saboda babyna da yake tare da ita ammah ban yarda cewa akwai macen da nakesoba dan har yanzu ban samu *ZA'BINA* ba, ajiyar zuciya yayi cikin gamsuwa da tunanin da yayi sannan yakoma yakwanta.
______________
sumayya tunda tatashi shirye-shiryen tarban zinat take daga tasa a girka wanchan sai a sauke a girka wanchan, part d'inta wani irin gyara yasha a ranar duk ma'aikatanta saida sukasan tana cikin farin ciki,
Kad'an kad'an ta kira zinat taji idan sun tafo, zinat dariya kawai takeyi mata tace har yanzu muna airport.
Yarima ne zaune part d'insa rik'e da laptop yana duba wasu drugs da yakeso ayo masa order d'insu, nan wayarsa tafara ringing, baibi ta kan wayarba saida yagama abinda yake sannan yad'auko yaduba ganin Aunty husna ce yasa yayi murmushi tare da yin dialing, tana yin picking yace ranki yadad'e big sis.
Daga chan 6angaren Aunty husna dariya tayi tace da girman kujerarka Yarima mai jiran gado, daman cewa nayi bari inkiraka inji inkananan kazo mugaisa gani a part d'in ummi tunda mu ka fi k'arfinmu baka iya zuwa inda muke yanzu.
Yarima k'ayataccen murmushinsa yayi mai k'ara bayyanar da kyaun fuskarsa sannan yace sorry sweet sis wlh ina ta so inshigo hidima ce tahana ammah yanzu bari inshigo sai muyi magana.
Murmushi husna tayi cike da k'aunar d'an uwan nata sannan tace ohk ina jiranka sai ka shigo.
Murmushi yarima yayi sannan yakashe wayan tare da mik'ewa yashiga bedroom d'insa saida yawatsa ruwa sannan yashirya cikin wata maroon d'in gizna nan kyaunsa yak'ara bayyan feshe jikinsa yayi da perfumes batare da ya sa hulaba yafito yad'auki wayoyinsa a parlour yawuce yafita.
A chan harabar gidan yatarar da shaheed tsaye rik'e da waya da alama neman number d'insa yake, murmushi yayi sannan yawuce yanufi wajensa, sai a lokacin shaheed yad'aga kai yakallesa yana murmushi cikin sauri ya isa inda Yarima yake yace ranka yadad'e yanzu daman nake neman number d'inka sai ma gaka.
Hannu Yarima yamik'a mai sukayi musabaha sannan yace toh gani me aka kawomin?
Dariya shaheed yayi sannan yace nazo ingaishekane kawai, rahma ce taji zuwan Aunty husna shine nakawota sugaisa.
Murmushi Yarima yayi yace kace ka had'a zumunci, toh ya kake ya kwana biyu?
Ajiyar zuciya shaheed yayi sannan yace Alhmdllh ai mun kwana biyu bamu had'uba dan ko a fada ban ganinka.
Wlh kau busy nakene aikine yatisoni gaba banda lokacin zama.
Cikin tsokana shaheed yace aikin iyaliba,
Wata uwar harara yarima yawurga masa sannan yace kana tunanin mace zata hanani fita?
Dariya shaheed yayi sannan yace idan so yai so ai ba abinda bai iya faruwa, na lura da kai yarima kamar har yanzu bakasan menene so ba.
Yarima sharesa yayi tare da duba agogon hannunsa yace mushiga mugaisa da big sis.
Girgiza kai shaheed yayi yace a'a ni ai na shiga mun gaisa kawai kaje in ka fito kasameni a fada, murmushi yarima yayi yace mutum sai gulma kai a dole sirikine kunyar ummi kakeji.
Uhm dole inji kunyarta tunda ta ban auren d'iya.
Ta6e baki yarima yayi yace kaji da gulmanka, ni bari inshiga.
Toh shikenan sai mun had'e, nan sukayi sallama suka rabu.
around 3 o'clock, flight d'in su zinat yasafka, tun kan ta iso takira sumayya nan sumayya tatura driver yaje yad'aukota.
Lokacin da suka iso tun a parlour tafara k'wala ma
08, February 2025
Shuraihu Usman
jjjjj