Showing 159001 words to 162000 words out of 168813 words
Chapter 54 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt
sarki ya amshi lasifika yanuna godiarsa ga waziri sannan yad'auko wata alkyabba da rawani masu kyau yadamk'a ma Yarima.
Kar6a Yarima yayi cikin jindad'i sannan yanuna godiarsa, daga k'arshe yayi ma su memartaba sallama yaja shaheed suka fita, motarsa suka shiga suka nufi hospital d'insa.
Lokacin da ya isa sosai staffs d'insa suka nuna farin cikin dawowarsa, dr khalil ko rungumesa yayi cikin jin dad'i.
Yarima farin ciki yayi sosai alokacin da yaga komai yana tafiya daidai nan yanuna jin dad'insa tare da godia ga manyan staffs d'insa.
Bayan sallar isha'i bayan ya gama shirinsa na bacci saman gadonsa yahau yakwanta kad'an kad'an ya duba lokaci yayi tsaki ganin har wajen k'arfe tara ammah zarah batazo part d'insaba, daga k'arshe mik'ewa yayi yasaka alkyabbarsa sanan yafito yanufi part d'inta.
Koda yashiga babu kowa a parlour dan haka yawuce bedroom d'inta, kunna gloves yayi nan yahangota tsakiyan gado ta baje sai baccinta takeyi, murmushi yayi sannan yai light off yawuce yanufi saman gadon yahau yakwanta a gefenta.
Janyota yayi jikinsa yarungume ahankali tabud'e idanunta cikin muryar bacci tace bakayi bacci ba daman?
Uhm taya zanyi bacci bayan baki lek'aniba tunda muka dawo nifa ban yadda adinga nisa da niba dan ina buk'atar kulawa,
K'ara shigewa jikinsa tayi tace kayi hak'uri d'azun saida naje lokacin ka fita insha Allahu bazan dinga nisa da kaiba yanzu ma dan a gajiye nake saisa nakwanta.
Kina gudu kar inyi miki wani abu ko saisa bakijeba?
Marairaice murya tayi tace bahaka nake nufiba kawai dai baccine da gajiyar tafiya ammah nima naso inzo.
na k'i wayon naki yanzu dai kiyi baccinki babu abinda zanyi miki
K'ara tura kanta tayi cikin k'irjinsa tana murmushi.
Washe gari zarah part d'in yarima taje tagyara fes ko a gyare yake sannan tahad'a masu breakfast, bayan sun gama breakfast a part d'in yarima fitowa tayi tabarosa yana waya takoma part d'inta,
wardrobe d'inta tabud'e tad'auko wayanta takunna cikin jin dad'i tahau saman gadonta takwanta sannan tayi dialing d'in number d'in abbah ammah har ta k'arashi ringing baiyi picking ba dan haka talalubo ta mama, tana fara ringing mama tayi picking cikin Jin dad'i zarah tagaisheta nan mama ta amsa tace d'iyata ba dai kun dawoba.
Eh mama mundawo dafatan kuna lafiya? Ya su yaya rauda? Na kira wayan abbah ammah baiyi picking ba
Murmushi mama tayi tace duk muna lafiya nima sa'a kikayi wayartana hannuna kinsan yau ake d'aura auren Aisha.
zumbur zarah tayi tatashi zaune tace yau kuma mama? Shine baku fad'amana ba.
Haba zarah ke ai mun d'auke miki zuwa tunda kinyi nauyi yanzu, kuma shi suhail ai yana sane da maganar bikkin tunda kusan kullum muna gaisawa, kima tayamu godia a wajensa dan ya turo mana gudunmawa dasu mukayi ma Aisha siyayyar kayan d'aki kedai kinyi sa'ar miji mekirki saidai muce Allah yabiyasa.
Zarah kwallah ce tacika mata ido koda taji dad'in abinda yarima yaima iyayenta saidai abun yaimata ciwo da ba'asanar da ita yau ake bikkin Aisha ba, cikin fushi tace gaskiya mama ba'a kyauta minba ace ana bikkin 'yar uwata ammah ba wanda zai iya fad'amin.
Haba zarah kuda bakunan kiyi zamanki kawai kihuta, yanzu dai bari inje inji da bak'i munyi waya anjima,,,,mama batajira jin abinda zarah zataceba takashe wayarta.
Nan zarah takira yaya rauda waya, yaya rauda tana yin picking zarah cikin fushi tace haba yaya rauda yanzu saboda Allah kun kyauta min ace yau ake bikkin Aisha ammah banda masaniya.
dariya yaya rauda tayi tace toh sarkin tsogumi kuda baku gari taya zamu fad'a miki bayan babu waya a wajenki kuma mijinki ai ya sani tunda har gudunmawa yaturo, abbah ne yace kar yafad'a miki dan ya san halinki matsamasa zakiyi sai kunzo.
Hawaye suka fara fita daga idanun zarah cikin muryar kuka tace toh ai yanzu mundawo kuma sai nazo ko bakuso.
Dariya rauda tayi tace wannan tsakaninki da mijinki ne mudai babu ruwanmu.
Cikin jin haushi zarah takashe wayarta nan takife kanta tafara rera kuka.
Wajen k'arfe d'aya yarima yagama shirinsa yafito yanufi part d'in zarah a bedroom yasameta ta kife kanta, kallonta yayi yace baby bacci kike?
'Dagowa tayi takallesa sanye yake cikin galilarsa maroon colour ya yi gwanin kyau, fuskarta a d'aure tace ina zakaje?
Da mamaki yake kallonta yace ikon Allah yau kuma tambayata ake inda zanje saikace mace?
Shuru zarah tayi tare da janye idanunta daga kallonsa cikin muryar kuka tace gaskiya baku kyauta minba wai ana bikkin Aisha ammah banda masaniya alhali kai kana sane, koda ace ba barina zakiyi injeba indai kafad'amin ko addu'a nayi musu ai yayi,,,tak'arashe maganar cikin kuka.
Takowa yarima yayi yazo kusa da ita yazauna cikin sauri zarah tajuya mashi baya.
murmushi yayi cikin rashin damuwa yace zarah kinsan dai babu yadda za'ayi mudawo jiya sannan aganki yau kinfita kuma ga ciki.
Toh ai fitar kamawa take kuma ko yayane nad'an lek'a ai yafi banjeba.
Kibari bayan bikki sai inkaiki kiyi mata wuni.
mak'e kafad'a tayi tare da k'ara sautin kukanta.
Dafe kansa yayi da hannu biyu dan babu abinda yatsana sama da jin kukanta ahankali yace toh shikenan yanzu tashi muje kilek'a da an d'aura aure zan d'aukoki mu dawo.
Juyowa tayi tana share hawayen fuskarta tace dagaske kake?
Murmushi yayi yace toh ya zanyi.
Rungumesa tayi cikin jin dad'i tace nagode sosai hearty ka gama min komai.
Janyeta yayi daga jikinsa yace yanzu dai yisauri kishirya kinsan k'arfe biyu za'a d'aura auren mik'ewa zarah tayi tahau cire kaya tace please bari ind'an watsa ruwa ba zan dad'eba.
Yanzu har sai kinyi wanka ina nan?
Turo baki tayi tace duka fa minti ukku zanyi.
Hmm toh shikenan ammah indai kika dad'e saidai kifito kitarar baninan.
Bama zan dad'eba insha Allah,,,,cikin sauri taje tashiga wanka, bata wani dad'eba tafito d'aure da towel dan tasan halin kayanta zai iya tafiya yabarta,,,d'ago kai yayi yakalleta sannan yamaida idanunsa akan wayarsa da take hannunsa yana dannawa.
Gaban dressing mirror tazauna tayi simple makeup sannan tamik'e tanufi wajen wardrobe d'inta kallon kayan da suke jikin yarima tayi tai murmushi sannan tad'auko shadda marron gown wadda tasha aiki da pink d'in zare tasaka, gaban dressing mirror tazo tamurza d'aurin kallabi sannan tad'auko veil da hand bag da takalmi duk pink colour tasaka, k'ara feshe jikinta tayi da turare sannan tayi masa gyaran murya.
juyowa yayi yakalleta nan tasakar masa murmushi, zuba mata ido yayi yana kallonta bai ko k'yaftawa, kashe masa ido d'aya tayi tare da d'aga gira tace nayi kyau ko?
Janye idanunsa yayi daga kallonta tare da mik'ewa tsaye yace muje, rik'o hannunsa zarah tayi tare da langwa6e kai tace bakace nayi kyauba.
Cize le6e yayi sannan yace ba laifi ammah da hijab kika ssnya da zakifi yin kyau.
Jin haka yasa zarah tawuce gaba gudun kar yace sai tasa hijab, murmushi yarima yayi sannan yabiyo bayanta.
Cikin motarsa suka fita, suna cikin tafiya zarah kallonsa tayi tace sunfa tashi daga wanchan gidan na mance ban tambayesu inda suka komaba.
Batare da ya kalletaba yace ba sai kin tambayesuba na san gidan abbah yaimin kwatance.
Gaban wani madaidaicin gida yai parking ganin mutanen da suke shige da fice yasa yagane nan ne gidan.
K'ik'irin bud'e k'ofa zarah take cikin zumud'i, rik'ota yarima yayi yace zan fa dawo ind'aukeki da and'aura aure.
Langwa6e kai tayi tai kalan tausayi cikin kwantar da murya tace please kabari sai dare.
Ta6e baki yarima yayi yace na dai fad'a miki.
Toh naji,,cewar zarah tare da bud'e k'ofar tafita nan kallo yadawo wajenta daman jira ake aga wanda zai fito daga motar, ratsa mutane tayi tashiga cikin gidan nan suka gaisa da mutane, yanayin tsarin gidan ya burgeta koda flat house ne med'auke da d'akuna ukku, dakyar tagano mama nan tarungumeta tana murna itama mama murna tayi sosai nan tatambayeta jikinta da mutanen gida.
Alhmdllh duk suna lafiya cewar zarah, nan tagaishe da abokan mama daganan tawuce d'ayan room d'in da taga abokan amarya suna shiga rumgumeta su yaya rauda da Aysha sukayi cike da jin dad'in ganin 'yar uwartasu itama zarah rungumesu tayi cikin jin dad'i, nan suka baje suna hira, Aisha kamar ba ita bace amaryar dan sakin jikinta tayi sukai hira sosai da zarah saida taji ana gud'a ana shelar and'aura aure sannan tadawo hayyacinta harda d'an kukanta.
Bayan sallar la'asar akasa amarya tashirya nan zarah tazage taimata kwalliya tashiryata sosai tayi kyau sannan aka tafi da ita wajen su mama dan suyi mata nasiha, zarah komawa tayi takwanta saman gado sukacigaba da hira da yaya rauda.
wajen k'arfe biyar akace amarya tafito atafi da ita dan dama abbah ya ce dakansa zai kai d'iyarsa saisa ba wanda yasa ran tafiya.
zarah fita tayi suka gaisa da abbah nan tatarar da yarima wajensa, bayan sun gama gaisawa yarima yace tafito sutafi, ba dan ta so ba haka tashiga tayi sallama da su mama taja yaya rauda gefe tad'auko cheque d'in 1 million tabata tace taba su abbah gudunmawarta ne.
Koda suka kama hanyar gida fushi kawai take a mota dan taso yarima yabarta takai dare.
Dariya yarima yake ciki-ciki har suka isa, yana yin parking batajirasaba tashige gida.
Bayan sallar isha'i yarima kiranta yayi a waya, zarah tana kallon wayar kamar bazata d'aukaba saida takusan tsinkewa sannan tayi picking batare da tayi maganaba.
Baby please kikawo min coffee insha yunwa nakeji.
umhum kawai tace takashe wayarta.
Nan tatashi tashiga kitchen saida tasoya mashi kwai sannan tahad'a mai coffee tad'aura saman tray, komawa tayi bedroom d'inta tak'ara gyara jikinta sannan tad'aura alkyabba saman sleeping dress d'inta.
Kuyangarta d'aya taba tray d'in tad'auka nan suka nufi part d'in yarima.
Guards d'insa tun kan ta iso suka bud'e mata k'ofa nan suka russuna cikin girmamawa suka gaisheta, amsa musu zarah tayi takar6i tray d'in da yake hannun kuyangarta tashiga.
Ganin baya a parlour yasa tanufi bedroom d'insa tare da yin sallama ciki-ciki, yarima da yake zaune yana waya ganin yadda tahad'e fuska yasa yad'anyi murmushi sannan yacigaba da wayarsa.
Wucewa zarah tayi chan gefensa tad'aura saman bedside sannan tajuya zatabar d'akin.
Janyota yarima yayi tafad'o jikinsa nan yai sallama yakashe wayar tare da kallonta yace baby haka ake ba miji abu?
Fuskarta a d'aure tace toh me kakeso inyi maka bagashinan na aje makaba ni kabarni intafi.
Hmm ammah ai kinsan agajiye nake kuma ga yunwa ina ji indai kinaso insha saidai kibani dakanki,,,yak'arashe maganar tare da kashe mata ido d'aya.
Kallonsa zarah take cikin k'ulewa tace chab ashe ba yunwar kakejiba.
Shima yarima idanunsa a kan fuskarta yace indai ba zaki baniba kid'auki kayanki kiyi tafiyarki na k'oshi.
Jin haka yasa zarah tad'auko cup d'in takai masa a baki, yarima kallonta yake yadda take cika tana turo baki, hannunsa yad'aura saman cikinta yana shafa.
sharesa tayi tacigaba da bashi nan tad'ebo wainar kwai takaimasa a baki, ahankali yake ci, ta k'ule sosai ganin yadda yake ci kamar ba ya so kuma ahaka wai yunwa yakeji.
Bai wani yi cin kirkiba yajanye kansa alamun ya k'oshi.
harararsa tayi tace daman ba wata yunwa da kakeji dukafa rabin cup d'in kasha.
Toh baby naga kamar ba'aso insha saisa nahak'ura yanzu dai tashi muje toilet kiwanke hannunki.
Tashi zarah tayi sukaje toilet saida yai brush ita kuma tawanke hannunta sannan suka fito.
Suna fitowa yarima janyo zarah yayi jikinsa yace baby kayannan sunyi miki yawa bari inrage miki ko alkyabbarce.
Harararsa tayi tace ni kakyaleni tafiya zanyi.
Tallabo fuskarta yayi yace baby please yakamata fushin yak'are hakanan Indai gidane kibari insha Allahu idan kin haihu zan kaiki kinga fushin nan da kikeyi yana ta6amin zuciya nasan shima babynmu bayajin dad'in yadda mummynsa take ma dadynsa yakamata kitausayamin,,,yak'arashe maganar tare da cire mata alkyabba sannan yarik'o hannunta yace muje kiji wata magana.
Turo baki tayi tace ni nasan ba wata magana da zaka fad'amin wayau kakeson yi min, kwanciya yayi tsakiyan gadon sannan yamik'a mata hannu alamun tazo.
Rik'o hannun nasa tayi nan tahau yajanyota a jikinsa yakwantar da ita nan yashiga shafa mata baya, a kunnenta cikin wata irin murya merikitar da ita yace baby please fushin yak'are hakanan kinji?
'Daga masa kai tayi alamun toh, nan yacigaba da shafa mata baya yana lasar kunnenta cikin wata irin siga da yasa zarah tafara sakin layi, ahankali yasalu6e mata riga.
Sanin halinta yasa yadinga binta ahankali ammah duk da haka saida tayi masa raki.
washe gari koda suka tashi yarima tarairayata yayi sosai har saida yaga gabad'aya ta safka daga fushin da take.
Bayan sungama breakfast zarah d'aid'aya tayi bisa yarima tana ta zuba masa shagwa6a akan kar yafita, kan dole yahak'ura yazauna nan sukaita soyewarsu, sai wajen azuhur sannan memartaba yakirasa yafito fada nan zarah tasamu talalla6asa ya amince akan zataje tagaishe da su ummi, nan kuyanginta suka take matabaya zuwa wajensu ummi.
Saida tafara zuwa turakarsu dada sosai dada tanuna mata kulawa, daganan tawuce wajen sultana sadiya nan ma sultana sadiya tarasa inda zata sanyata saboda farin ciki, duk nok'e-nok'en zarah saida sultana sadiya tasamu tad'an saki jiki suka yi hira, kwad'on zogale sultana sadiya tasa akayi mata nan Zarah tazauna taci sosai, tarairaya tasamu sosai ita kanta zarah tajidad'in yadda tayi mata ta dad'e a nan sannan tayi mata sallama taje wajen ummi a chan parlour tagamu da sumayya tayi matashin kai da cinyar ummi suna hira dan gabad'aya sumayya tadawo wajen ummi ammah duk da haka tana lek'awa wajen iyayenta da dada koda a yanzu ba kamar da ba sun sake mata.
Ganinta yasa sumayya tatashi zaune cikin jin kunyarta.
Zarah cike da girmamawa tagaishe da sultana bilkisu, cike da so sultana ta amsa mata tare da tambayarta jikinta da gida.
cikin jin kunya tace Alhmdllh sannan tajuyo tace Aunty sumayya ina wuni?
Amsa mata sumayya tayi batare da ta d'ago ta kalletaba saboda kunyarta da takeji.
ummi ce tace Zarah kizauna saman kujera man kin zauna k'asa.
Ummi nan ma ya yi nafi jin dad'in k'asan...tafad'i hakan cikin jin nauyinta.
Murmushi sultana bilkisu tayi tace toh lafiya lau, ya gida da hidima? Ashe bikkin k'anwarki akayi wlh bamusaniba ai da mun lek'a.
Eh ummi daman saida mama tayi min magana tace lokacin taji ance memartaba baida lafiya saisa bata aiko maku da invitation card ba.
ayyyah Allah sarki toh Allah yabada zaman lafiya.
ameen ummi.
nan ummi tak'walama wata kuyangarta kira tace akawo ma Zarah kayan motsa baki.
Duk'ar da kanta zarah tayi tace ummi subarsa kawai ak'oshe nake.
a'a zarah baridai sukawo miki.
kafin kace mi nan aka cika gaban zarah da kayan marmari da abinci, mik'ewa sultana bilkisu tayi tace ina zuwa nan tawuce tashige bedroom d'inta.
sumayya kallon zarah tayi a karo na biyu ahankali tace zarah zan k'ara rok'onki akan abubuwan da nayi miki dan Allah kiyi hak'uri.
kallonta zarah tayi cike da tausanta tace wlh Aunty sumayya ko kad'an ban rik'ekiba kuma ai komai ya wuce please kidaina tunawa.
k'wallah ce tacika ma sumayya ido tace hmm zarah taya kike tunani zan iya mance cin mutuncin da nayi muku, wane irin makircine banyiba akanki ammah daga k'arshe kinga yadda rayuwa takoma min nayi wasa da damana ni kaina ina jin haushin wannan halin da najefa kaina.
girgiza kai zarah tayi tace Aunty sumayya kidaina cewa haka kema fa wasu abubuwan kowa yasan ba laifinki bane, kuma ko ba hakaba ni wlh tuni na yafe miki.
Share k'wallar idanunta tayi tace nagode sosai zarah Allah yasaka da alkhairi, Allah yasafkeki lafiya.
Nan suka d'an ta6a hira kad'an-kad'an ganin marece ya yi yasa taje tayi ma ummi sallama tafito sukai sallama da sumayya tawuce part d'inta.
cike da sha'awa sumayya tabita da kallo tanaji ina ma ace itace da cikin hawayene suka shiga gangaro mata alokacin da tatuno zuwa hospital d'in da sukayi da ummi aka tabbatar mata bazata ta6a haihuwaba saboda pills d'in da tasha da injections d'in da take na tsawon lokaci sun6ata mata mahaifa, kukane yaso yakubce mata cikin sauri tatashi tashige room d'inta tafad'a saman gado saida tasha kukanta me isarta sannan taje tawanke fuskarta tare da d'auro alwallah, nan tashimfid'a darduma tad'auko alk'ur'aninta takaranta.
Zarah koda takoma part d'inta a parlour tayada zango nan kuyanginta suka zagayeta suna mata hira, haka tabiye musu har aka kira sallah sannan tamik'e taje tayi alwallah tai sallah.
Haka rayuwa tacigaba da tafiya yarima yana tafiyar da aikinsa, a gefe guda kuma ga mulki dan memartaba yanzu bai cika bari yai nisa da shi ba dan a kullum cewa yake nan ba da dad'ewaba ko rai yayi halinsa kokuma insafka daga kan karagar kahau dan gabad'aya yanzu shekaru sunja sosai,,,a duk lokacin da yake maganar yarima yanaji babu dad'i a ransa, shi kansa waziri idan yaji memartaba yai furucin cewa yake a duk lokacin da mulkinka yak'are toh nima nawa ya k'are dan haka dole waziri mejiran gado shima yadinga yawan zaman fada, haka ake matsama yarima da shaheed suna zaman fada sosai.
Zarah sosai take samun kulawa daga wajen dangin yarima, dan sultana sadiya da sultana bilkisu kullum sai sun kirata a waya sun tambayi lafiyarta dan wani lokacinma sultana sadiya da kanta take zuwa tadubata takawo mata abubuwan da tasan meciki tana buk'atar ci dan Zarah kulawa take samu sosai a wajenta kamar yadda zata kula da sumayya.
A 6angaren Dada ma tana aikowa aduba mata lafiyar Zarah kuma tanayi mata aike da kwad'on ganye iri-iri.
su kansu su rahama yanzu wani irin kulawa sukeba zarah dan nan da nan zarah tasaba da rahama.
Yanzu sumayya danginta sun sake suna nuna mata kulawa sosai shima saida sultan ahmad yak'ara tunatar da su akan batada laifi fa sosai tunda da sa hannun zinat take wasu abubuwan, nan suka fara janta a jiki ammah duk da haka sumayya tayi sanyi sosai dan yanzu batada yawan magana.
*BAYAN WATA 'DAYA*
Sumayya ce tafito daga room d'inta dasafe da mamakinta taga su ummi suna ta zirga-zirga da shirye-shirye cike da girmamawa tagaishe da ummi, fuskar ummi a sake ta amsa mata.
murmushi sumayya tayi tace ummi bak'i zamuyine naga kuna ta shirye-shirye?
Kedai bari sumayya wlh wani d'an yayanane zaizo daga agadaz zaikawo min ziyara dan rabonsa da garin nan tun yana k'arami lokacin da nahaifi husna akazo da shi.
Murmushi sumayya tayi tace Allah sarki Allah yakawosa lafiya.
ameen daughter yanzu dai je kiyi breakfast muma ai mungama komai dan ina sa ran nan da awa biyu zai safka.
Bayan ta gama breakfast d'inta zaune take ita kad'ai a parlour hannunta rik'e da hisnul muslim tana dubawa, sallamar da akayine yasa tad'ago kai takallesa tare da amsa masa sallamar.
Wani matashi ne wanda ak'allah bazai gaza shekaru talatin da shidda ba sanye yake cikin manyan kaya yanayin kamaninsa yasa tagane shine wanda ummi tace mata zaizo, ido yazuba mata yana kallonta, ganin kallon ba mai k'arewa bane yasa tagaisheshi.
tattare nutsuwarsa yayi sannan ya amsa tare da tambayarta ya gida?
Lafiya lou sumayya tace sannan tamik'e zata wuce room d'inta.
Gyaran murya yayi yace am ummi
08, February 2025
Shuraihu Usman
jjjjj