Showing 93001 words to 96000 words out of 168813 words
Chapter 32 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt
nagode sosai Dr, Allah yasafketa lafiya, nan tacigaba da yin addu'a.
Fuskar yarima d'auke da murmushi yace Ameen mungode.
Dr feedoh jakkarta tad'auka sannan takalli zarah tace toh ranki yadad'e Allah yasafke mana ke lafiya, sai anjima.
Yarima ne kawai yace Ameen tare da mik'ewa yarakata har bakin k'ofa nan tak'ara yi masa godia sannan tatafi.
Yarima dawowa yayi bedroom d'in inda yatarar da zarah har a lokacin idanuwanta a lumshe suke, tunda taji an ambaci ciki gabanta yashiga dukan ukku-ukku dan ita ta ma rasa shin murna take ko bak'in ciki, a chan 6angare guda kuma murna take, bata ankaraba sai jin Yarima tayi ya d'age mata riga yana shafar cikinta, sharesa tayi tak'i bud'e idon nata, ya dad'e ahaka sannan yamik'e yace kitashi kiyi breakfast,
Zarah shuru tayi ta k'yalesa da mamakinsa sai ganin hawaye yayi sun gangaro daga idonta, da mamaki yake kallonta cikin ransa yace kar dai ace cikin ne bata so? Haushi ne yakamashi dan haka yashareta yawuce yafita daga d'akin.
Zarah tana jin fitarsa tabud'e idonta tare da bin k'ofar da kallo cike da tausayin kanta tace taya zan haihu da mutumin da baya sona, chan kuma gefe d'aya na zuciyanta tace ammah kuma yanason abinda yake cikin cikinki, hannu takai tashafi cikin cike da mamaki tace taya ciki yazauna min tsawon wannan watannin ban saniba? Toh wai ma duka yaushe akayi aurenmu?
Tunani tashiga yi sai kuma chan tace idan ban mantaba wata ukku da sati ukku kenan ya kama sati (15) kenan, gabantane yafad'i tace na shiga ukku yanzu cikin satina na biyu ciki yashigeni? K'wallah ce tacigaba da fita daga idonta, batasan lokacin da Yarima yashigoba sai ji tayi ya ce kitashi kiyi breakfast.
Zarah kallon yadda yahad'e rai tayi sannan tamik'e dak'yar, Yarima yataimaka mata yasa mata pillow a bayanta ta jingine sannan yahad'a mata tea mai kauri yamik'a mata, kar6a zarah tayi tafara kur6a jikinta yana rawa saboda wata irin yunwa da takeji.
saida tasha kusan rabin cup d'in sannan tamik'a ma Yarima ya amsa ya aje sannan yazubo mata chips, cikin sauri zarah tajanye kanta ahankali tace na k'oshi.
Yarima ido yazuba mata sannan yace ammah yanzu ba ke kad'ai bace kuma bakiga yadda duk kika rameba ya kamata kidinga daurewa kina d'an cin abinci.
Zarah rik'o hannunsa tayi tare da marairaicewa tace dan Allah kar kafad'a ma kowa ina da ciki.
kallonta yayi cike da mamaki yace saboda mi?
Rau-rau tayi da ido sannan tace kawai hakanan.
Yarima har ya bud'e baki zaiyi magana sai kuma yafasa nan yakwashi kayan breakfast d'in yafita da su parlour, zarah da kallo tarakasa har yaficce sannan takoma takwanta tare da maida idonta talumshe tana tunanin wai itace da ciki, hannunta tad'aura saman cikin, tana nan kwance haka sai ga Yarima ya shigo hannunsa d'auke da ledar drugs da injection da yabayar asiyo.
Ajewa yayi saman bedside tare da d'auko ruwa sannan yace kitashi kisha maganin,
Marairaicewa tayi kamar zatayi kuka tace idan nasha amai zanyi.
Yarima zama yayi gefenta tare rik'o hannunta yace kar kidamu bazakiyi amai ba,
Toh kawai tace, nan yataimaka mata tatashi zaune sannan yabata maganin saida ta runtse idonta sannan takar6a takai baki cikin sauri takora da ruwa, sannan tabud'e ido,
Nan yafara k'ok'arin had'a injection, kallonsa take a tsorace ahankali tace kuma harda ita za'ayi min?
Shuru Yarima yayi saida yagama had'awa sannan yakalleta har da d'an guntun k'wallarta taso tabashi dariya ammah yadake yace kigyara sai inyi miki.
Zarah komawa tayi takwanta tana kuka ciki-ciki, kallonta yayi yace kar kimotsa fa.
Batace komai ba jin zai shigar da allurar yasa tarik'esa gam, tare da runtse idonta.
Murmushi Yarima yayi sannan yatsira mata ahankali, bata ma san lokacin da yazare inj d'inba dan kwata-kwata bataji zafintaba, sai ji tayi yana cewa toh shikenan angama, zarah k'in sakinsa tayi saidai ji yayi tana fitar da sautin kuka k'asa-k'asa.
Ahankali yajanye daga rik'on da tayi mai tare da zuba mata ido sai chan yace kukan fa?
Turo baki tayi cikin shagwa6a tace ba kaine ba kayimin injection ba.
Murmushi yayi tare da jan d'an k'aramin bakinta sannan yace toh ai banyi miki da zafiba ko ak'ara wata?
Cikin sauri tagirgiza kai tare da cewa a'a.
Ido yazuba mata itama shi take kallo, ahankali tace kaida ma kake fushi da ni,
Murmushi yayi yace ni ba fushi nake da keba, kidaina maganar ta wuce kinji ko?
Murmushi zarah tayi tare da d'aga mai kai, hannunsa tarik'o tad'aura saman cikinta tace kana son babynmu?
Yarima ido yazuba mata sai chan yace ke kina sonsa?
Cikin sauri tace eh,
Mik'ewa yayi yace bari inje inhad'a miki ruwa kid'an gasa jikinki.
Murmushi kawai zarah tayi tare da komawa takwanta.
Toilet d'insa yashiga yahad'a mata ruwan wanka, bayan ya had'a fitowa yayi d'auke da towel yamik'a mata, kar6a tayi tare da mik'ewa dak'yar tacire rigar jikinta sannan tad'aura, yarima kamata yayi yarakata har toilet sannan yajanyo mata k'ofar.
Kwance tayi cikin ruwan tana jin wani irin nishad'i a cikin ranta, tunowa tayi da sumayya saida gabanta yafad'i, tsintar kanta tayi cikin zuciyanta tana addu'an neman kariya daga sharrinta.
Nan tafara wanka duk jikinta ya yi sanyi ahaka tagama sannan tafito, lokacin yarima baya d'akin, gaban dressing mirror tazauna tashafa mai sannan tamik'e taje tagyara gadon, bayan ta gama parlour tafito tasami yarima da yake zaune yana jin wani irin dad'i a cikin ransa, kallonsa tayi da shima yakalleta, turo baki tayi sannan tace ni banda kayan da zansa.
Janye idonsa yarima yayi sannan yamik'e yafita yaje ya aiki d'aya daga cikin guards d'insa part d'in zarah dan yakar6o mata kaya.
Lokacin da yadawo zarah tana bedroom nan yarima yakar6a yaje yakaimata sannan yadawo parlour yayi Kwanciyarsa saman 3 seater.
Bayan ta gama kwanciyarta tayi saman gadonsa nan bacci yayi awon gaba da ita,
Saida aka kira azuhur sannan yarima yamik'e yashiga bedroom, kallon zarah yayi da take baccinta hankali kwance, takowa yayi yazo yazauna gefenta tare da yaye blanket d'in da tayi rufa da shi gani yayi tana zufa alamun zazza6in ya safka, hannu yakai yad'age mata riga tare da shafa cikin nata, ido yatsura ma fuskarta duk tayi fayau da ita, murmushi yayi sannan yamik'e yaje yacire kayansa yashiga bathroom,
Bayan ya fito wanka shiryawa yayi sannan yaficce yatafi masallaci, rufe k'ofan da yayine yasa zarah tafarka, ji tayi zazza6in ya safka, ahankali tasafka daga saman gadon saida tagyara mai sannan tafito takoma part d'inta.
Koda tashiga saida tak'ara wanka sannan tad'auro alwallah.
Bayan ta yi sallah sawa tayi akayi mata faten tsaki taci saboda shi taji tana buk'ata.
tana cikin ci saiga yarima ya shigo, ido yazuba mata tare da yamitsa fuska,
Ganin haka yasa zarah tayi murmushi tace bismillah.
menene wannan? Cewar yarima.
Faten tsakine kazo kad'and'ana kaji akwai dad'i.
no, aci lafiya, ya jikin naki?
Dasauki, cewar zarah.
Ohk, Allah yak'ara sauk'i, idan kin gama kisha drugs d'inki.
Ahankali tace toh,
Juyawa yayi yafita yabar d'akin nan zarah tacigaba da cin faten.
A chan 6angaren gimbiya sumayya tun tana sa ido dan taga yarima ya kori zarah ammah shuru a k'arshema a gaban idonta yaje d'akin zarah sannan agaban idonta yafito.
Ahankali tafurta da alama aiki ya 6aci, takaici ne yacikata batasan lokacin da tace anya waccan munafukar bata asirce yarima ba? Tsaki taja cikin jin haushi tace akwai alamar tambaya a cikin lamarin nan, dan babu yadda za'ayi ace kullum itace da nasara, wlh duk sihirinta sai nayi silar barinta gidan nan
A haka zarah tacigaba da kula da cikinta, yanzu ta samu sauk'in zazza6in da takeyi saidai yawan amai idan taji k'amshin abinda bata so, abinci ko sai ta za6i irin wanda takejin zata iya ci, ta d'an rame ammah ta k'ara haske da kyau fatar jikinta ta k'ara laushi.
A 6angaren yarima yana zuwa yaduba lafiyarta, sannan yana kiranta a waya koda ace bai jeba, itama tana k'ok'arin ganin ta je part d'insa koda sau d'ayane a cikin kwana biyun, har lokacin ba wanda tabari yagane tana da ciki.
*BAYAN SATI BIYU*
A ranar da cikinta yacika wata hud'u, bayan sallar la'asar ji tayi kwanciyar ta isheta, mik'ewa tayi tanufi part d'in yarima lokacin da tashiga a parlour tasamesa yana sa agogo a hannunsa da alama fita zaiyi. kallonta yayi ganin ta zuba mai ido yace ya dai?
Murmushi zarah tayi tare da marairaicewa tace dan Allah inaso inje ingaishe da su dada.
Keda bakida lafiya kuma zaki fita? Cewar yarima.
Zarah shuru tayi sai chan tace na fa samu sauk'i kuma ni zaman ne ya isheni saisa nakeson ind'an mik'e k'afar.
'Daukan hularsa yayi yasaka sannan yace ohk, muje nima yanzu fada zanje.
Cikin jin dad'i zarah tafad'a jikinsa tare da cewa nagode,
yarima janyeta yayi daga jikinta tare da kallon cikinta yace kar kiji ma baby ciwo.
Murmushi zarah tayi tare da jawo hannunsa tad'aura saman cikinta tace kar kadamu babynka yana lafiya,
Janye idonsa yayi daga kallonta sannan yace muje memartaba yana jirana, zarah wucewa tayi gaba yarima yabi bayanta suna fitowa a jere suke tafiya, saida suka zo wajen turakar dada sannan zarah tashiga yarima yawuce fada.
koda tashiga a parlour ta tarar da dada da kuyanginta ana mata tausa a k'afarta, nan kuyangin dada suka dinga duk'awa suna gaisheta, zarah tadinga amsa musu cikin sakin fuska sannan tasamu waje a k'asa saman carpet tazauna gefen dada da take saman cushin, fuskar dada d'auke da murmushi tace a'ah yau amarya ce dakanta?
Murmushi zarah tayi tare da duk'ar da kai cikin girmamawa tagaishe da dada.
dada amsa mata tayi cikin sakin fuska tare da tambayarta ya suke.
Alhmdllh duk muna lafiya, cewar zarah cike day kunya.
Ina wannan miskilin mijin naki? Kwana biyu ban gansaba, ko kuma kun min k'wace yanzu ku kad'ai yasani, dada tafad'i maganar cikin tsokana.
Murmushi zarah tayi sannan tace taya zai mance da ke uwar gida? Ai mu bamu isa mushiga tsakaninku ba, aikine kawai ya6oyesa.
Gidanku ja'irar yarinya kawai, ammah shi aikin bai 6oye muku shi ba sai ni dan rashin adalci.
Dariya zarah tayi sannan tace ranki yadad'e taya zai mance da mu sabon jini?.
Knocking d'in k'ofan da akayine yasa dada tabada izini a shigo, d'aya daga cikin kuyangartace d'auke da wani tray, nan tazube takwashi gaisuwa wajensu sannan tacema dada ranki yadad'e gashi angama.
Murmushi dada tayi tace toh mik'omin shi nan itama kishiyata taci, cikin sauri kuyangar takai gaban dada ta aje.
dada kallon zarah tayi da take wasa da yatsun hannunta tace ga fa dambun kifi kici dada tafad'i haka tare da bud'e murfin da aka rufe shi da shi.
zarah k'amshin yadaki hancinta daurewa taso tayi nan zuciyanta yafara tashi, wani irin tuk'a taji yana taso mata cikin sauri tamik'e dagudu tanufi k'ofa, dada cike da mamaki tace lafiya me yake faruwa?
Batama san dada tanayi ba kafin tafita daga k'ofan sai aman yakubce mata nan tafara kwararashi..
_Comment_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'artโ๐ป_
๐๐๐
_*YARIMA SUHAIL*_
๐๐๐
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ยฎ*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE ๐ HEART TORCHING โค TEARS OF SORROWS ๐ญ CURDLES ๐ GIGGLES ๐ AND MARRIEGE THINK๐
*JUST GIVE US FOLLOW....*โ
_Jinjinar bangirma agareki mummyna chubad'o muhammad, nagode sosai da dedicated d'in book da nasamu saidai ince Allah yabarmu tare 4ever๐_
*PAGE* 4โฃ7โฃ
Dada da take zaune ido tazuba mata tana kallon ikon Allah ganin tana ta aman kamar zata amayen 'yancikinta yasa tafara yi mata sannu nan tasa kuyangarta d'aya tad'auke dambun kifin daga wajen.
Bayan zarah ta gama aman a galabaice alkyabbarta kawai tacire saboda ita kad'ai ta6aci.
dada kuyangi tasa sugyara wajen nan tacigaba da jera ma zarah sannu sannan tace tashiga ciki tagyara jikinta,
A kunyace tace toh sannan tawuce toilet da yake cikin bedroom d'in dada batare da ta kalli dada ba,
Dada ido tazuba mata tana kallonta har tashige sannan tayi murmushin jin dad'i tace Alhmdllh da alama mun samu rabo.
Zarah jiki ba k'wari tahad'a ruwan d'umi tayi wanka bayan ta fito kayan jikinta tamaida tunda su basu 6aciba, zaune tayi takasa fitowa saboda wata irin kunyar dada da takeji na amai da tayi mata a parlour.
Ta dad'e a zaune sannan daga baya tamik'e lokacin da tafito parlour da mamakinta taga angyara wajen tes d'akin sai k'amshin turaren wuta yake, kallonta dada tayi har tazauna sannan tace sannu 'yar nan ai da kin fad'i bakison k'arnin kifin da ban bud'eba, kuma bakida lafiya baku fad'amin ba ai da nazo na dubaki, kokuma wannan miskilin mijin naki taya zai fad'a, abinda ma yashafesa bai fad'aba barema ayi tunanin fad'an na wani.
K'ara duk'ar da kanta tayi k'asa cike da jin kunya.
Ganin haka yasa dada tace yanzu me kikeson ci? Naga kin amaye duk abinda kikaci.
Cikin jin kunya tace na k'oshi.
A'a wane irin kin k'oshi keda ba komai cikin cikinki, k'walah ma kuyangarta kira dada tayi tace aje akawo ma zarah tuwo, cikin sauri kunyarta tace angama ranki yadad'e sannan tafita tabar d'akin.
Dada tace ai nasan shi tuwo zaki so shi, murmushi kawai zarah tayi.
Bayan 'yan mintuna sai ga kuyangar nan ta shigo d'auke da kular tuwo, wata kuma tana rik'e da na miya da plate nan suka aje gaban zarah.
Dada tace suzuba mata taci, nan suka zuba sannan suka bud'e miya kala biyu ce sukace ranki yadad'e wace za'a zuba miki?
Zarah kallon miyan tayi ganin miyan ku6ewa d'anya da ta ganye ce yasa tace azuba mata ta ku6ewa nan suka zuba mata sukace ranki yadad'e man shanu fa?
Cikin sauri tagirgiza kai tace kar kuzuba min.
Cikin sauri sukace angama ranki yadad'e sannan suka tashi suka fita daga d'akin.
Dada kallon zarah tayi fuskarta d'auke da murmushi tace kici man.
Murmushi zarah tayi sannan tafara d'iba taci, ta ji dad'in miyan sosai ga tuwon mai laushi irin mai wucewa silif wanda take so nan tacigaba da ci ahankali cike da jin nauyin Dada.
Ganin haka yasa Dada ta tattara hankalinta ga news d'in datake kallo dan zarah tasamu taci sosai.
Haka zarah tad'anci sannan tature plate d'in, kallonta dada tayi tace ba dai har kin k'oshiba?
Zarah ahankali tace eh dada na k'oshi.
Kidaure kid'an k'ara ko kad'anne, cewar dada.
Zarah cikin jin kunya tace na k'oshi.
Dada tace toh shikenan, nan tamaida hankalinta ga TV.
Zarah samu tayi tamik'e dan tawanko hannu.
Da kallo dada tabita cike da farin ciki dan ko ba'a fad'a mataba yanayin zarah da tagani yasa ta gane cikine gareta, ahankali tace Allah sarki sumayya naso inga jininki ammah da rabon na zarah zan fara gani....tana chan tana tunani batasan lokacin da zarah tadawo ba sai da tafara tattara kwanukan sannan hankalin dada yakai wajen, zaro ido dada tayi da cewa miye haka zakiyi?
Zarah batare da ta kalli dadaba tace ranki yadad'e zan d'an rage kayanne.
Dada tace a'a aje bari ma'aikatan suzo sukwashe keda bakya jin dad'in jikinki, kawai kizauna kihuta.
Dada ai zan iya, cewar zarah.
A'a kibari suzo sukwashe.
Zarah ajewa tayi sannan takoma tazauna,
Dada tace da kin shiga ciki kin d'an kwanta kihuta.
Murmushi Zarah tayi sannan tace dada ai yanzu ma nakeso inwuce gida.
Jinjina kai dada tayi tace kar kikwanta nan musaceki ko?
Yanayin yadda dada tayi maganar saida yaba Zarah dariya tace a'a dada kawai dai akwai abinda zanje inyine.
Cikin gamsuwa da maganar dada tace toh ai shikenan hakan ma mungode Allah yabada ladan zumunci, Allah yayi muku Albarka.
Ameen ranki yadad'e, nan Zarah tayi ma dada sallama tafita.
Dada binta tayi da kallo cike da sha'awa tace Allah sarki sumayya kema Allah yasa ina da rabon ganin naki d'an,
Ita kanta dada tana mamakin yadda cikin jikokinta ta fi son sumayya, hakan ya samo asaline ta dalilin duk cikinsu ita sumayya tun tana k'arama daman itace ta wajen dada inbata wajen ummanta to tana wajen dada, dan a k'arshema dada ce tayi yayenta.
Zarah tana cikin tafiya har zata shiga 6angarensu sai ga sumayya ta fito, saida gaban Zarah yafad'i dan rabon da taga sumayya Ita kanta ta mance dan zata iya cewa tayi kusan 2 weeks.
Tsaya sumayya tayi tana kallon zarah cike da mamaki ganin yadda tacanza tak'ara fresh da kyau, chan sai taja tsaki sannan cikin fad'a tace ke dabbar ina ce kina ganin mutane zasu wuce ammah kikasa basu hanya suwuce.
Zarah murmushi tayi cikin rashin damuwa tare da dakewa tace kar kidamu ke ai naga ko cikin dangin namu na dabbobi kamar makauniyace tunda duk fad'in hanyarnan kirasa ta inda zakibi sai ta wajena.
Cike da mamaki sumayya takalli Zarah dan bata d'auka zata iya yada mata magana irin hakaba, ran sumayya in yayi dubu toh ya 6aci cikin d'aga murya tace eh dole kice haka dan a yanzu kinsha jan miya kin waye kina gani kamar daidai kike da ni, toh wlh bari kiji ni nan da kike gani bani ta6uwa kuma duk ubanda yace zai ta6ani toh aikam zai ta6o ma kansa masifa da bala'i ke sai kinyi kuskuren abinda kika aikata agareni.
Zarah dafe kanta tayi cikin kwantar da murya tace please malama kiban waje inwuce idan ke kinsaba hargagi toh ni ban sababa dan har kin fara haddasa min ciwon kai.
Sumayya a harzuk'e tace ke ko ubanki bai isa yafad'amin maganaba bare ke jakkah,
Zarah murmushin takaici tayi sannan tace Allah sarki kar kidamu nasan jahilcine yayi miki yawa ammah dan Allah ya kamata kikoma islamiyya gimbiya, tana fad'in haka tacanza hanya tawuce tabar sumayya tsaye tana ta balbalin bala'i.
Sumayya cikin 6acin rai tawuce tanufi turakar iyayenta, a parlour ta tarar da sultan Abbas da mahaifiyarta, ganin Abbanta yasa tad'an saki fuska gefensa tazauna cikin sakin fuska tagaishesa.
Murmushi sultan Abbas yayi sannan ya amsa mata tare da tambayarta mijinta.
Sumayya cikin shagwa6a tace Abbah yana lafiya.
Toh ya 'yar uwartaki dafatan kuna zaman lafiya?
Sumayya ji tayi kamar ya da6a mata wuk'a a mak'ogwaro jin ya kira wadda tafi tsana a rayuwarta a matsayin 'yar uwarta, murmushin yak'e tayi sannan tace abbah tana nan lafiya.
Toh masha Allah adaicigaba da hak'uri sumayya kizauna da ita lafiya banason fad'a ko tashin hankali.
Toh Abbah daman muna zaman lafiya.
Cikin jin dad'i sultan abbas yace yauwa 'yar abbah Allah yaimiki abarka.
Ameen abbana, cewar sumayya sannan takalli sultana sadiya da tazuba musu ido tana murmushi, itama sumayya murmushin tayi sannan tace ummana ina wuni?
Lafiya lou daughter ya gidan?
Alhmdllh ummah,
Toh masha Allah ina fatan mijinki da 'yar uwartaki suna lafiya.
Sumayya cike da mamaki take kallon ummah
08, February 2025
Shuraihu Usman
jjjjj