Showing 78001 words to 81000 words out of 168813 words

Chapter 27 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt

08 Aug 2024

100539

hannu zata tadasa sai kuma tafasa, rigarta tajanyo tasaka sannan tafara k'ok'arin janye blanket d'in da yake rufe ciki,
Jin ana jan blanket yasa yafarka, zarah saida tasafka daga saman gadon sannan tace katashi yau munyi late.
Tana fad'in haka tazura hijab inta tafita tabar d'akin.


Yarima janye blanket d'in yayi cikin sauri yamik'e yashiga toilet yana mamakin yadda yamakara yau baisamu jam'i ba, chan kuma yaja tsaki da yatuno basuyi bacci da wuriba.




Zarah ma ko da takoma part d'inta saida tatsarkake jikinta sannan tayi sallah, bayan tagama kitchen taje tashiga nan tafara tunanin me zata had'ama yarima na breakfast, chan kuma sai tayi tunanin tahad'a mai kunun gyad'a dan tasan yana sonsa sosai.


Nan tad'aura ruwan kunun sannan tafere doya tadafa, bayan ta dafu tadaka tayi yamball.
Bayan ta gama wanka tashiga tayi da tafito tashirya cikin swiss less d'inta, veil tayafa sannan taje tad'auki basket d'in taba wata kuyangarta tarik'e suka nufi part d'in yarima


A gaban dressing mirror tagansa tsaye yana fesa turare, d'an rissinawa tayi tagaishesa, tacikin mirror yarima yake kallonta saida yagama fesa turaren sannan ya amsa.
Fuskarta d'auke da murmushi tace breakfast d'inka na dining,
Shuru yarima yayi har ta juya zata fita ahankali yarima yace kije kishirya in ajeki gida.
Dasauri zarah tajuyo cike da jin dad'i tace yanzu?
Eh, ammah idan baki shirya zuwaba shikenan.
Zarah cikin sauri tace na shirya kagani?
Yarima kallonta yayi sannan yazo yawuce yafito yanufi dining,


Zarah bayansa tabi har yaje yazauna nan tayi serving d'insa sannan itama tazauna tayi serving d'inkanta,
nan sukacigaba da breakfast d'insu ba wanda yai magana, zarah saboda zumud'i bataci abun kirkiba tatashi, yarima kallonta yayi yace shi kuma sauran wa zai ida cinye miki?
Itama kallonsa tayi tace nak'oshi ne,
Wani kallo da yayi matane yasa takoma tazauna tacigaba da turawa ba dan tana jin dad'insaba yarima yarigata tashi yabar wajen, nan zarah tabisa da kallo har yashige bedroom d'insa, sannan takalli plate d'insa ahankali tace shi bai cinyeba ammah ni shine zai ce incinye,
Mik'ewa tayi tatattara kayan tasaka cikin basket tad'auka tafita tabar d'akin.




Ko da takoma part d'inta cike da farinciki tashiga bedroom d'inta tad'auko handbag d'inta sannan tacanza veil saida tak'ara gyara fuskarta sannan tafito.


Daidai zata shiga part d'in yarima sai gashi ya fito, kallonta yayi sannan yace muje, a tare suka jero suka fito, guards d'insa har sun taso nan yarima yad'aga musu hannu, d'aya daga cikin motocinsa suka shiga dakansa yayi driving d'insu tunda suka fara tafiya ba wanda yayi magana zarah ko k'agare take su isa gida taga iyayenta wani irin nushad'i takeji dan fuskarta takasa 6oye farin cikinta,
Yarima ta mirror yakalleta yaga tana ta murmushi ta6e baki yayi sannan yamaida kallonsa ga titi, gudu yake sosai cikin k'ank'anin lokaci suka isa gidansu zarah,
zarah cikin sauri tabud'e k'ofar tafita sannan takalli yarima da shima yake kallonta tace zaka shigo kugaisa?
Yarima duban agogon hannunsa yayi sannan yace saidai in nadawo,
Toh sai kadawo Allah yakiyaye,
Ameen yace sannan tarufe motar har saida taga ya tafi sannan tashiga gida da gudu ba ko sallama tana k'walama mama kira,


Mama dasauri tafito d'aki tana cewa muryarwa nakeji kamar ta d'iyata, zarah rungume mama tayi tace oyoyoo mamanmu,
mama dariya tayi tace kai zarah har yanzu dai dasauran k'uriciya atare da ke, dariya zarah tayi tace mamanmu nayi missing d'inki fa, daidai lokacin yaya rauda da rahma suka fito daga d'akinsu sukace wa mukeji kamar zarah?
Zarah kallonsu tayi tana dariya tace nice dai, Aysha ce tazo tarungumeta tana murna mama tace sakarmin ita kar kikayar da ita.
Aysha sakinta tayi tana turo baki tace kai mamanmu ya za'ayi inkayar da ita.
mama jan hannun zarah tayi sukaje suka zauna saman tabarma.
Aysha da yaya rauda kallon juna sukayi sukai murmushi sannan suma sukaje suka zauna.


Cike da girmama zarah tagaishe da mama, nan mama ta amsa mata tare da tambayarta ya mutanen gida?.
Duk suna lafiya lou suna gaisheku.
Mama tace muna amsawa,
Sannan zarah takalli yaya rauda tagaisheta.
fuskar yaya rauda d'auke da murmushi ta amsa, zarah tace ya k'arfin jikinki?
Yaya rauda tace ai jiki ya warke,
Nan Aysha tagaisheta, zarah tace 'yar k'anwata ya gidan?
Dariya tayi tace Alhmdllh, ya yayana?
Zarah murmushi tayi tace yana gaisheku,
Aysha tace nad'auka ma tare zakuzo.
Eh shi yasafkeni yana saurine zaije hospital saisa bai shigoba ammah da anjima zai shigo.
Toh Allah yakawosa lafiya, sukace Ameen.


Daidai lokacin Abbah yashigo d'auke da leda yace a'ah yau mune da manyan bak'i?
Zarah cike da jin dad'i tace abbah sannu da dawowa, ina wuni?
Lafiya lou ya gidan da mijin naki?
Lafiya lou abbah kowa yana lafiya,
toh masha Allah.
kallon mama yayi da takar6i ledar hannunsa yace bari inje insamo abinda za'a dafa ma d'iyata mai d'an dad'i-dad'i.
Zarah murmushi tayi tace a'a abbah kabarsa agirka abinda ke akwai.
harararta rauda tayi tace toh baki isa kiyi mana buk'uluba sannan tace abbah ahad'o da kaji,
Dariya abbah yayi yace toh d'iyata yanzu kau dan yau dole aci dad'i.
gaba d'ayansu dariya sukayi sannan abbah yace sai nadawo, sukace adawo lafiya.
Nan suka zauna suna hira.


Mama shinkafa tabada aka 6arzo mata tad'aura burabusco, bayan abbah yadawo su rauda suka gyara kayan miya nan suka d'aura miyar dage-dage wadda tasha naman kaji, hadad'en kunun zak'i suka had'a.


Bayan sunyi sallar azuhur gabad'ayansu suka had'u saman babbar tabarma suka had'u suna ci cike da nishad'i.


Bayan sun gama atare sukayi wanke-wanke sannan suka zauna hira,


Abbah ne yace zarah rauda tafad'a mana yadda kukayi da wannan saurayin nata saidai banji dad'iba da kika amsar masa kud'insa, murmushi zarah tayi tace abbah kadaina cewa haka hak'intane fa na amsar mata kaduba kaga irin wahalar da tasha ai dan taci kud'in bawani abu bane,
jinjina kai abbah yayi yace hakane to yanzu ya kuke gani ya dace ayi da kud'in?
Mama ce tace nidai atawa shawarar ina ganin yafi dacewa shine kasiyar da wannan gidan kasamu gida wanda yad'anfi wannan girma ko mai d'akuna ukkune kasiya mana tunda akwai sauran kud'i a wajenka,
Gabad'ansu sukace hakan ko za'ayi,
Abbah yace bank'i ta takuba toh yanzu idan maganar auren Aysha tatashi ya za'ayi?
Zarah ce tayi karaf tace aure kuma abbah?
Murmushi sukayi gabad'ayansu sannan abbah yace kiyi hak'uri bamu fad'a mikiba malam bello ne yazo yasameni yace yanaso abashi aurenta,
Zarah a firgice tace malam bello?
Mama ce tace Malam bello dai naki,
Zarah kallon Aysha tayi tace daman soyayya kukeyi?
Aysha dasauri tagirgiza kai tace wlh bahaka bane Aunty zarah shine yace yana sona da nak'i amince masa sai yasamu abbah yafad'a masa kuma nanashi labarin rayuwata yace ba matsala daman yasan komai tunda yanzu nadaina toh yana sona yanaso inmaye gurbinki, yanzu haka har danginsa sunzo sati guda da yawuce sun nemi aurena,
Zarah farincikine fal yabayyana a fuskarta cike da jin dad'i tace gaskiya nayi murna sosai kar kidamu 'yar uwata ni tuni nacire malam bello daga cikin zuciyata gaskiya nayi murna Allah yakaimu musha bikki.
Sukace Ameen,
bud'e jakkarta tayi tad'auko cheque d'in 500,000 tamik'a ma abbah tace abbana nima ga tawa gudunmawar ataimaka acanza mana gida insha Allahu ko da bikkin Aysha ya zo Allah zai rufa mana asiri.


Abbah yace a'a zarah baza'ayi hakaba ki aje kud'inki rannan ma fa kin aiko mana da kud'i kema kisamu abu mai amfani kisiya.


Zarah tace abbah bana tunani zan iya tara kud'i alhalin ku kuna nan kune yafi cancanta kutara baniba, ban ta6a tunanin samun naira d'ayaba batare da kun fad'omin arai ba, k'wallah ce tacika mata ido tace abbah dan Allah kataimaka kakar6a kusanya min albarka.
Dukansu tabasu tausayi yanayin yadda tayi maganar nan abbah yakar6a shi da mama sukaita sa mata albarka suna jinjina halin 'yar tasu tabbas sunsan sunyi sa'ar d'iya kamar zarah.
Abbah yace toh shikenan kuban lokaci zanyi tunani akan maganar canza gidan ammah fa kuyi hak'uri dan bawani babba za'a siyaba.
Sukace eh bakomai mun amince.
Abbah yace toh masha Allah, Allah yayimuku albarka gabad'ayanku.
Cikin jin dad'i sukace Ameen y rabb.
Nan abbah yamik'e yace bari inje wajen Yaya muda mugaisa.
Sukace Adawo lafiya.
Bayan ya fita nan suka cigaba da hirarsu.










_Comments_
*nd*
_Share_








_Sis Nerja'artโœ๐Ÿป_๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘


_*YARIMA SUHAIL*_

๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘






_*Written By~Sis Nerja'art*_






_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_




https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/


*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ยฎ*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE ๐Ÿ˜˜ HEART TORCHING โค TEARS OF SORROWS ๐Ÿ˜ญ CURDLES ๐Ÿ™‚ GIGGLES ๐Ÿ˜ AND MARRIEGE THINK๐Ÿ’‘
*JUST GIVE US FOLLOW....*โœ”






_Sak'on gaisuwa da jinjina agareki yayata takaina *SADNAF* kinfi k'arfin page a wajena kema kin sani ina ji dake irin sosai d'innan, nagode sosai da soyayyarki agareni saidai ince Allah yabarmu tare, I hrt u dear๐Ÿ˜˜_






*PAGE* 4โƒฃ0โƒฃ




Zarah sawa tayi Aysha taje gidansu khairy takira mata ita nan suka zauna suna ta hirarsu cike da jin dad'i da nishad'i.




Bayan sallar isha'i yarima ne ya iso k'ofar gidansu Zarah wayarsa yad'auka yakirata, zarah ganin maikiranta yasa tayi murmushi sannan tayi picking tare da yin sallama,


Daga chan 6angaren yarima amsa mata yayi sannan yace gani a waje,.zarah ahankali tace toh zaka shigo kugaisa da su abbah ko?


Jim yarima yayi sai chan yace kizo kishigo da ni, yana fad'in haka yakashe wayarsa.
Zarah mik'ewa tayi tayafa gyalenta sannan tace ma su abbah ga yarima nan zai shigo sugaisa, abbah yace toh badamuwa.


Fitowa tayi waje tagansa zaune cikin motarsa ya jingine kansa a sit d'in da yake zaune sai yafiddo k'afa d'aya a waje inda d'ayar take cikin motar.
Takawa tayi ta isa inda yake tarik'e k'ofar motar tare da yin sallama.
Yarima bud'e idanuwansa yayi da suke lumshe yakalleta, ahankali ya amsa mata.
Murmushi zarah tayi tace sannu da hanya ya aiki?
Yarima saida yajanye idonsa daga kallonta sannan yace Alhmdllh.
Bismillah kashigo kugaisa, cewar zarah.
Ahankali yarima yafito daga motar yamaida yarufe chan kuma sai yabud'e yad'auko hularsa yasaka, kallon zarah yayi da tatsaresa da ido yace kallon fa?
Fuskar zarah d'auke da murmushi tace kayi kyau
'Dan guntun murmushi yarima yayi sannan yace kema haka.
Dariya zarah tayi tace ni kyaun mi zanyi ai kafini.
Yarima ma kallonta yake yace shikenan mushiga dare yakeyi,
Zarah tsayawa tayi tace wuce gaba sai inbiyoka.
Harararta yarima yayi yace gidankune ko namu?
Murmushi zarah tayi sannan tawuce nan yabi bayanta har cikin gida, da sallamarsa yashiga, nan suka amsa masa.


Saman tabarmar da aka shimfid'a masa yazauna, cike da girmamawa yagaishe da abbah da mama suka amsa tare da tambayarsa mutanen gida.
Kansa sunne k'asa yace duk suna lafiya suna gaisheku.
Abbah yace masha Allah muna amsawa.
Sannan rauda da Aysha suka gaishesa, cikin sakin fuska ya amsa masu tare da tambayar rauda ya k'arfin jiki tace Alhmdllh yanzu ta warke.


Mama kallon zarah tayi tace kikawo masa abinci man,.zarah mik'ewa tayi tace toh mama.
Murmushi yarima yayi yace Alhmdllh abarsa kawai a k'oshe nake.


Kusan a tare su abbah suka mik'e sannan yace a'a yarima nan ma ai gidane bari mubaka waje kaci, nan suka wuce suka shiga d'aki, daidai lokacin zarah tadawo d'auke da kulolin abinci ta aje gabansa sannan tazauna gefensa, tana bud'ewa wani irin k'amshi yadaki hancin yarima nan tafara serving d'insa, bayan tagama kallonsa tayi fuskarta d'auke da murmushi tace bismillah,
Yarima d'aukar spoon d'in yayi yafara cin burabuscon sannan yakalli zarah da take wasa da gefen gyalenta yace ke bazaki ciba?
Kallonsa tayi tana murmushi tace ni naci d'azun,
Daganan Yarima yacigaba da ci, bai wani ci dayawaba yature plate d'in saidai kunun zak'in da yasha sosai,
Zarah kallon plate d'in tayi tace ba dai ka k'oshiba? Bakafa ci dayawaba.
Yarima kur6ar kunun zak'in yayi sannan yace kinsan banason cin abu mai nauyi da dare.
Zarah shuru tayi sannan takwashe kwanukan, bayan ta dawo Yarima kallonta yayi yace kije kiyi ma su abbah magana muyi sallama dare yakeyi.


Zarah 6ata fuska tayi tace tun yanzu?
Banza Yarima yayi mata,
Ganin haka yasa tamik'e taje tasanar da su abbah, kusan a tare suka fito, sama-sama suka d'anyi hira sannan sukayi musu sallama, har wajen mota yaya rauda da Aysha suka rakasu, Yarima bandir d'in 'yan 1000 yad'auko yamik'a ma Aysha yace tasiya kayan kwalliya, godia Aysha tayi masa sannan suka tafi.


Tunda suka kama hanya ba wanda yayi magana har suka isa gida, yana yin parking d'in motar daidai lokacin sumayya tafito daga 6angaren iyayenta, tsaye tayi fuskarta d'auke da murmushi tana jiran Yarima yafito, zarah ce tafara fitowa sannan Yarima, ganin zarah yasa fara'ar da yake fuskar sumayya tagushe ahankali tace ina Yarima yaje da wannan matsiyaciyar? Watau dakansa ma yake kaita anguwa? tsanar zarah ce taji tak'aru a cikin zuciyarta, batasan lokacin da suka iso inda takeba saidai ji tayi yarima ya ce kekuma daga ina kike?


Sumayya ta6e baki tayi tace daga wajen ummah na amso wani sak'one, zarah d'an rissinawa tayi tace Aunty sumayya ina wuni?
Wata uwar harara sumayya tawurga mata tare da jan tsaki sannan tawuce tabi bayan yarima da yayi gaba,
Zarah ko kad'an batayi mamakin hakan ba nan tabi bayansu tawuce part d'inta.




Cire kayan jikinta tayi tashiga wanka, bayan tafito tayi shirin bacci nan tabi lafiyar gado takwanta.




Sumayya har part d'in yarima tabisa lokacin yana shirin cire kaya yashiga wanka tsaye tayi tana kallonsa, kallonta yayi yace ya dai?
Sumayya ta6e baki tayi tace gaskiya yarima baka kyauta min.
Da mamaki yarima yakalleta kamar bazaiyi magana ba sai kuma yace da akayi miki mi?
Matsowa tayi kusa da shi tace akan me zaka d'auketa kakaita anguwa alhali tana da motarta kuma zaka iya sawa akaita.


Murmushi yarima yayi yace ko da ace iyayenki ba a tare muke da suba zan iya d'aukarki in kaiki sumayya ammah banda gidan abokai dan baya cikin tsarina, yana fad'in haka yawuce yaje yashigewarsa bathroom,


Sumayya fitowa tayi cikin fushi tawuce part d'inta.


Yarima bayan ya fito shima shirin bacci yayi yakwanta.




Sumayya ma koda takwanta sak'e-sak'e kawai take a ranta ta yadda zata kawar da zarah, dan gani take itace kawai matsalarta a rayuwa.




*BAYAN KWANA BIYU*


Sumayya ce zaune a bedroom d'inta nan ta aika aka kira mata zabba'u bayan tazo tsugunnawa tayi tagaisheta cike da girmamawa, fuskar sumayya ba yabo ta amsa sannan tace kinsan dai ba akan komai zan kirakiba sai akan waccen matsiyaciyar yarinyar, kud'i sumayya tamik'a mata jikin zabba'u yana rawa takar6a tace ranki yadad'e me kikeso wlh zan iya komai kifad'i yadda kikeso ayi yanzu.


Murmushin mugunta sumayya tayi sannan tace matso kiji abinda nakeso kiyi min dan yau banso taje wajen yarima,
Dasauri zabba'u tamatso sumayya bata damu da tsamin da jikin zabba'u yakeba nan tayi mata rad'a a kunne, washe baki zabba'u tayi tace angama indai dan wannan d'an aikin ne ranki yadad'e kikwantar da hankalinki


Murmushin Jin dad'i sumayya tayi sannan tace haka nakeso zaki iya tafiya, bayan zabba'u ta fita sumayya zagaye d'akin tashiga yi cike da jin dad'i cikin d'aga murya tace yes yau burina zai cika.






Wajen k'arfe tara yarima kiran zarah yayi yace tahad'a mai coffee.
Bayan tagama saida tak'ara gyara jikinta sannan tazumbula hijab tafito, kuyanginta tasallama sannan tad'auki cup d'in coffeen tanufi part d'in yarima, tafiya take wani tsantsi taji ya ja ta wata irin k'ara tasaki kafin takai k'asa nan duka coffeen yazube a jikinta, duk yadda taso tamik'e kasawa tayi nan tafara hawaye saboda wani irin zafi da zugi dak'afar takeyi mata, waige tashiga yi ko Allah ya sa taga wani saida tayi kusan min biyar ahaka sai ga wata baiwarta tazo wuce, ganin zarah yasa tarud'e cikin sauri ta iso inda take tace ranki yadad'e meyake faruwa da ke?
Zarah tana cije baki cike da dauriya tace taimakamin intashi nan baiwar tataimaka mata tatayar da ita duk yadda zarah taso tataka k'afar kasawa tayi daga k'arshe saidai baiwar tarik'eta tana k'engasawa suka koma part d'in zarah, nan saman gado tazaunar da ita tare da taimaka mata tacire hijab d'inta,


Zarah jingine kanta tayi da jikin gadon tare da runtse ido, baiwar cike da rikicewa tace ranki yadad'e bari inje infad'a ma yarima, har ta mik'e cikin sauri zarah tarik'ota dak'yar tabud'e baki tace kar kifad'a masa please je kikira min sahura (kuyanga) dasauri baiwar tafita daga d'akin,


bayan minti biyu sai gasu sundawo, a firgice Sahura tanufi wajen gadon tace ranki yadad'e me yake faruwa da ke?


Murmushin k'arfin hali tayi tace kar kidamu bawani abu 'yar fad'uwace nayi, yanzu so nake kitaimaka kihad'omin coffee kikai ma yarima.


Sahuru matsar k'wallah tafarayi tace ranki yadad'e ya akayi hakan takasance?
Murmushi zarah tayi tace kidaina kuka inaji miyar ku6ewa ce aka d'an zubar da ita ammah nidai yanzu kitaimaka kije kihad'a min coffeen, mik'ewa sahura tayi tace toh ranki yadad'e Allah yabaki lafiya,
Gyad'a kai kawai zarah tayi, bayan sun fita ta6a k'afar tad'anyi kad'an dasauri taruntse ido tare da furta wash saboda wani irin zafi da taji, ahankali takwanta tare da runtse idonta tanajin wani irin zogi.






A chan 6angaren yarima zaune yake a parlour yana kallo ammah gabad'aya hankalinsa baya ga kallon kad'an-kad'an ya duba time ammah shuru zarah batashigo ba, nan yak'ule tsaki kawai yake ja.




'Daya daga cikin guards d'insane yashigo yace ranka yadad'e wata kuyangace tazo ta ce gimbiya ta aikota
Yarima izini yabada yace abarta tashigo.


Sahura ce tashigo d'auke da cup tsugunnawa tayi cike da girmamawa tace ranka yadad'e gimbiya ce ta umurceni inkawo maka coffee,
Yarima da tunda tafara maganar bai kalletaba sai alokacin yajuyo yawatsa mata wani mugun kallo yace ke nasa kihad'o min ko ita? Kikoma kimaida mata abunta kice ita tafi k'arfin tazo takawo min?


Duk'ar da kanta kuyangar tayi tace ranka yadad'e kagafarceni wlh gimbiya bata jin dad'ine,
Yarima a firgice yace bata jin dad'i? Me yasameta?
Kuyangar k'ara duk'ar da kanta tayi tace ranka yadad'e lokacin da tafito zata kawo maka sai tazame yanzu tana chan k'afarta ke ciwo.




Yarima a firgice yace what! Garin ya hakan yafaru.
K'ara duk'ar dakanta tayi tace kagafarceni miyar ku6ewace aka zubar a waje itace ta zameta.


Yarima lumshe idonsa yayi tare da jin gine kansa jikin kujerar da yake zaune, d'aga ma kuyangar hannu yayi alamun tatafi, saida tak'ara duk'ar da kanta tagaishesa sannan tatashi tafita tabar d'akin.




Yarima wani iri yakeji a ransa ya dad'e zaune sannan yamik'e yafito yanufi part d'in zarah, bai samu kowaba a parlournta yana shiga bedroom yatarar da ita zaune saman gado kuyanginta biyu tsugunne k'asa suna yi mata sannu,
Yarima bai kula da gaisuwar da kuyangin sukeyi masaba yanufi wajen zarah, cikin sauri kuyangin sukabar d'akin.


Yana zuwa rikicewa yayi ganin yadda take cize le6e, k'afar yarik'o a rud'e yace sannu ko muje asibiti? Nan

08, February 2025
Shuraihu Usman

jjjjj

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login