Showing 117001 words to 120000 words out of 168813 words
Chapter 40 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt
sumayya kira.
Da gudu sumayya tafito daga bedroom d'inta tazo tarungumeta, tana murna dariya zinat tayi tace toh sakarni haka kar kikayar da ni dan agajiye nake.
Sumayya janye jikinta tayi daga na zinat fuskarta d'auke da murmushi tace sannu da zuwa babyna.
Dariya zinat tayi tace yauwa baby kinga yadda kika koma kuwa? Ni da naganki a video chart na d'auka camera ce tamaidake haka ashe kinma fi haka a fili, baby kodai kin k'unsa?
Ta6e baki sumayya tayi tare da shafa cikinta tace wlh baby bakomai nan.
Murmushi zinat tayi tace inma akwai ai zan gane...tak'arashe maganar tare da kashe mata ido d'aya.
Dariya sumayya tayi tace bare ma bakomai yanzu dai muje kici abinci kihuta.
Ohk dear, suna rik'e da hannun juna suka wuce suka nufi bedroom d'in sumayya, saman gado zinat tafad'a tare da furta wash.
Daga gefenta sumayya tazauna tace sannu baby kinsha hanya, bari in had'a miki ruwa kiyi wanka.
Kallonta zinat tayi tace saidai in ke zakiyi min.
Murmushi sumayya tayi tace bakida matsala koma me kikeso zaki samu dan ni yau ina cikin farin ciki,,,,,tak'arashe maganar tare da mik'ewa tanufi toilet.
Bayan ta had'a mata ruwan wankan fitowa tayi taga har a lokacin kwance take, dariya sumayya tayi tace kedai baby ragguwace wlh.
Harararta zinat tayi cikin wasa sannan tace eh d'in na ji, yanzu dai zo kitaimaka min incire kayan.
Kusan a tare suka shiga wankan, bayan sun fito shiryawa sukayi sannan suka fito parlour cikin plate d'aya suka zuba abinci suka ci,
Bayan sun gama a saman 3 seater kusa yada zango inda sumayya tayi matashin kai da cinyar zinat suna hirarsu suna dariya.
Zinat kallon sumayya tayi tace baby mushiga ciki kiban hak'ina kinsan d'azun da muna wanka daurewa kawai nakeyi.
Dariya sumayya tayi tace kai baby bama zaki bari mugama hirarba, yauwa yanzu taso mufara zuwa wajen wacchan 'yar matsiyatan dan inbanga mun aiwatar da k'udirinmu ba akanta toh hankali bazai ta6a kwanciyaba dan a yanzu nasan yarima baya gidan maybe ma sai dare zai dawo saisa nakeso muyi komai mugama.
Zinat dariya tayi tace hakan fa za'a baby tashi muje,,,kusan a tare suka mik'e suka fito suka nufi part d'in zarah.
Lokacin zarah tana zaune ita kad'ai tana kallo, dan gabad'aya kuyanginta basa nan, turo k'ofan da akayine aka shigo yasa tad'ago kai takalli su sumayya, tsaye sukayi su dukansu fuskarsu babu alamun fara'a.
Saida gabanta yafad'i ammah tadake tace sannunku da zuwa, bismillah mana kuzauna.
Harararta sumayya tayi tace ba zamane yakawomuba dan haka kar kidamemu.
Zinat ce tayi karaf tace sannu amarya ya ciki? Gaskiya cikin nan ba k'aramin kyau yak'ara mikiba saidai kiyi hak'uri dan sai mun cika k'udirinmu akansa.
Da mamaki zarah take kallonsu tace ban fahimci abinda kuke nufiba.
Zinat da sumayya kallon juna sukayi sukai dariya sannan sumayya tace kar kidamu yanzu zaki gane.
Zarah ganin suna nufo inda take Zaune yasa tayi sauri tamik'e tsaye tace wai me zakuyi min?
Suna isowa sumayya tad'aga hannu takwasheta da mari, cikin sauri zarah tadafe kuncinta tace sumayya me nayi miki da zaki mareni?
Bata rufe bakiba nan zinat itama tamareta,
Zarah hawaye suka fara fita daga idonta cikin zafin nama tad'aga hannu itama ta sharara ma sumayya mari,
Sumayya dafe kuncinta tayi tace kam bura'uba lallai yarinyarnan kin isa tunda har zaki iya marina,
Zarah cikin 6acin rai tace kamar yadda kika isa toh nima haka na isa, yadda bana shiga harkarki toh nima kidaina shiga tawa, juyowa tayi tanuna zinat tace kekuma inke babbar marar kunyace toh kik'ara ta6ani.
wlh duk wadda tak'ara ta6ani sai tagane batada wayau, ni kubani hanya inwuce.
Turata sumayya tayi tafad'a saman kujera sannan tace wlh yau nice silar zubewar cikinki,,,tana fad'in haka nan suka rufe zarah da duka, ta ko'ina bugunta suke.
Zarah duk'ewa tayi gudun kar subugar mata ciki, kuka kawai take, daga k'arshe sumayya tajawota daga saman kujerar tafad'o k'asa, nan suka cigaba da bugunta suna takata zarah kuka take tana neman agaji,
Wata baiwartace tajiyo ihunta cikin sauri tanufo d'akin tana zuwa taga su sumayya akan zarah janta suke suna nema subugi cikinta ammah ta duk'e, k'ara baiwar tasaki cikin sauri tanufo wajen tare da rungume zarah jikinta tana kuka tace dan Allah kuk'yaleta,
Sumayya cikin 6acin rai takaima baiwar mari tace ke har kin isa ina waje kitako kizo har ma kinemi kishiga harkar da ba takiba tashi kiban waje ko yanzu in kasheki.
Baiwar ture sumayya tayi tace wlh saidai kukasheni ammah bazan bari kucigaba da dukantaba.
Kan baiwar suka koma suka fara dukanta dak'yar ta k'waci kanta tatashi taruga dagudu tabar d'akin.
Zarah amai tafarayi tana maida numfashi sama-sama, ganin haka yasa suka kwashe da dariya sannan sumayya tace a haka kawai idan muka barki mungama da ke matsiyaciyar banza.
Zinat kallonta tayi tace anya sumayya cikin nan ya zube?
Sumayya k'afa takai zata harbi cikin zarah cikin rashin sa'a sai k'afar tatsaya a k'irjinta
sannan sumayya tace ai dolema yazube muje kawai baby, nan tajawo Zinat suka fita daga d'akin suna dariya.
Zarah kwance tayi wajen tana maida numfashi sama-sama dan ko hannunta bata iya d'agawa.
Ko da baiwar tafita dagudu tayi part d'in yarima cikin rashin sa'a guards d'insa sukace bayanan dan haka tanufi hanyar waje.
Yarima koda yashiga part d'in ummi bayan sun gaisa zama yayi suka d'an ta6a hira da su Aunty husna saida aka kira sallar la'asar sannan yatashi yatafi masallaci.
Bayan ya gama sallah a hanyarsa ta dawowa tsayawa yayi suka gaisa da jama'a sai wajen biyar sannan yasamu yanufo gida, part d'in su ummi yai shirin komawa sai ga wannan baiwar da gudu tana zuwa gabansa tazube k'asa tana haki.
da mamaki yarima yake kallonta yace ke lafiya?
Cikin rawar murya tace kagafarceni ranka yadad'e ga su gimbiya sumayya chan d'akin gimbiya zarah suna dukanta wai zasu zubar mata da ciki.
A firgice yarima yace duka kuma!, kuna aikin mi kukuma?
Girgiza kai tashiga yi tace kagafarceni wlh na shiga intaimaka mata shine suka had'a da ni har suka fashemin baki dak'yar nasamu nagudo.
Yarima bai ida saurarentaba yayi gaba cikin sauri yanufi 6angarensu, bai damu da gaisuwar da akeyi masaba dan baima san anayiba cike da tashin hankali yawuce part d'in Zarah, yana shiga yaganta kwance k'asa tana maida numfashi, cikin sauri yanufi inda take tare da janyota jikinsa a rud'e yace Zarah sannu garin ya haka yafaru, hannu yakai saman cikinta yana shafa.
Zarah fashewa tayi da sabon kuka muryarta tana fita ahankali cikin wahala tace me natsare ma sumayya takeson ganin bayana? Me yasa tatsaneni haka? Wannan wane irin tsanace tayimin har take ik'irarin kasheni.
Yarima runtse idanunsa yayi dak'arfi yana jin wani irin tsanar sumayya a ransa,,,ahankali yabud'e idanunsa yasafke akan fuskar zarah sahun hannuwansu sumayya ne kwance a fuskarta, bakinta kuma jini ne yake fita, handchief d'insa yajanyo yagoge mata jinin, ahankali yakai bakinsa cikin nata yayi kissing d'inta, sannan yad'auketa chak yanufi toilet da ita,
Ruwan d'umi yahad'a yasakata ciki dakansa yaimata wanka sannan yad'aukota yafito da ita, zaunar da ita yayi bakin gado, cikin sauri zarah taruk'osa, kallonta yayi cike da tausayinta yace bari ind'auko miki kaya.
Zarah sakinsa tayi nan yawuce yanufi wardrobe d'inta yabud'e yad'auko kaya yataimaka mata tasaka sannan yad'auko magani yabata tasha saboda jikinta da yaji alamun zazza6i, zama yayi gefenta nan zarah tafad'a jikinsa tare da fashewa da sabon kuka.
Yarima shafa kanta yayi yace please kukan ya isa haka, zarah rage sautin kukan tayi sannan tace please kamaida ni gidanmu inba hakaba sumayya sai ta ida nufinta a kaina,
Yarima k'ara rungumeta yayi jikinsa sannan yace kar kidamu babu abinda zata iya yi miki wannan ma a bisa kuskure ta aikatasa ammah....sai kuma yayi shuru batare da ya ida fad'in maganar da take bakinsaba.
Janye zarah yayi daga jikinsa yamik'e, cikin sauri zarah taruk'o hannunsa, kallon fuskarsa tayi da gaba d'aya ta canza saboda 6acin rai,,,muryarta tana rawa tace ina zakaje? Please kar kayi mata komai.
wani irin kallo da yayi matane yasa cikin sauri tasakesa dan gaba d'aya ya gama tsoratata.
Batare da yayi maganaba yajuya yafita.
a 6angaren su sumayya koda suka koma part d'inta dariya suka cigaba da yi, sumayya cikin jin dad'i tace yanzu nasan burina ya cika, zinat tsagaitawa tayi da dariyarta tace baby toh yanzu idan mijinki ya dawofa ya zakiyi.
Ta6e baki sumayya tayi tace bazan damu da abinda zai min ba tunda nasan duk abinsa bai isa yasakeniba, dariya zinat tayi tace angaisheki gimbiyar yarima aikinki yana yin kyau, yanzu dai muje kiji da ni tunda hankali ya kwanta.
Kallonta sumayya tayi tace ina zuwa, nan sumayya tafito tasamu kuyanginta da suke tsaye waje tana yamutsa fuska tace kar kubari kowa yashigo min nan duk wanda kuka saki kukabari yashigo toh a bakin aikiku.
gabad'ayansu suka duk'a sukace angama ranki yadad'e.
juyawa sumayya tayi takoma ciki.
Suna rik'e da junansu suka wuce suka shiga bedroom tun a hanya suka fara cire ma junansu kaya, jikin sumayya har rawa yake tajanyo zinat suka fad'a saman gado.
Cike da 6acin rai yarima yake tafiya yanufi part d'in sumayya, duk bawan da yatunkaresa zai masa magana da yaga yanayinsa zaiyi sauri yaja baya.
Kuyangin sumayya da suke gadin k'ofa ganin yarima yasa sukayi saurin ja baya tare da duk'awa suna kwasar gaisuwa, yarima baibi ta kansuba yawuce,
koda yashiga a parlour yatarar babu kowa dan haka cikin sauri yawuce yanufi bedroom d'inta.
_Toh fa koya za'a k'are idan yarima yashiga yaga sumayya tare da zeenat?_
_ko wane irin mataki zai d'auka akanta?_
_*duk amsar tana cikin next page dan haka Muje zuwa*_
_Comment_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'artโ๐ป_
๐๐๐
_*YARIMA SUHAIL*_
๐๐๐
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ยฎ*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE ๐ HEART TORCHING โค TEARS OF SORROWS ๐ญ CURDLES ๐ GIGGLES ๐ AND MARRIEGE THINK๐
*JUST GIVE US FOLLOW....*โ
_Masha Allah, sak'on gaisuwa agareku masoya a duk inda kuka kasance, gaskiya ina jin dad'in yadda kuke comments a groups akan novel d'in *YARIMA SUHAIL* da yadda nake samun sak'on gaisuwa daga gareku nagode sosai saidai ince Allah yabar k'auna, Sis Nerja'art tana yinku over_
*PAGE* 5โฃ6โฃ
Cikin zafin nama yarima yatura k'ofan, abinda yaganine yafirgitasa a kid'ime yafara furta innalillahi wa'inna ilaihiraji'un.
Sumayya da zinat da suke manne da juna basu ma san shigowarsaba dan gabad'aya basu cikin hayyacinsu saida sukaji yana salati sannan sukayi saurin rabuwa da Juna, cikin sauri zinat tajanyo bedsheet tarufe jikinta.
Sumayya wata irin razanannar k'ara tasaki tare da furta na shiga ukku na bani na lalace dan Allah yarima kayi hak'uri ba laifina bane sharrin shaid'anne.
Yarima da yake tsaye jikin k'ofa ya runtse idonsa innalillahi kawai yake nanatawa dan samun sauk'in abinda yakeji a ransa inba hakaba ya san zai iya abinda za'azo ana da na sani.
Cikin sauri zinat tajanyo zanenta tad'aura tana zare ido saboda a tsorace take, Sumayya ko bedsheet d'in tayaye tarufe jikinta da shi har a lokacin kuka take tana jin abun kamar a mafarki.
Ahankali yarima yabud'e idanuwansa da suka koma launin ja saboda tsananin 6acin rai, murmushin takaici yayi wanda yafi kuka ciwo sannan yace Sumayya ban ta6a sanin ke dabba bace sai a yau, ke ko dabba ma ta fiki k'wak'walwa mai kyau, ace a matsayinki na mace kina aiwatar da wannan mummunan halayyar, wlh a yau na tsaneki Sumayya bana fatan k'ara sakaki a idona, na yi da nasanin amincewa da nayi na aureki.
kallon zinat yayi yace kekuma har da tako min gida kika daki matata sannan kuka aikata masha'a a cikin gidana!
Sumayya cikin kuka tace dan Allah yarima kayi hak'uri wlh nabi ka nai maka alk'awali bazan k'araba dan Allah kar katona min asiri.
Zinay had'e hannuwanta tayi waje guda tana kuka tace dan Allah ranka yadad'e kayi hak'uri wlh tsautsayine yakawoni.
Yarima maida d'akin yayi yarufe sannan yace da fari zan fara rama ma matata dukan da kukayi mata,,,wucewa yayi yajanyo adaptor irin mai kaurin nan yatsige kan yad'auki wire d'in, wajen da suke yanufa daga bakin gadon yatsaya yafara shaud'a musu, ihu suke suna kuka nan tacigaba da had'awa da mari daga k'arshe k'asa yajanyosu yacigaba da duka da harbi da k'afa, ihu suke suna kuka ammah yarima bai k'yalesuba saida yaga ya had'a musu jini da majina basu iya kotsin kirki sannan yabarsu,
Jikinsu duk sahun bulala ya kwanta duk saida sukayi da sun sani akan ta6a zarah da sukayi.
Yarima kallon Sumayya yayi da take kuka yace wannan ramama matata nayi, sannan kuma ada nazo da niyar inyi miki saki d'aya ammah ganin abinda kike aikatawa ya sa zan miki....cikin sauri Sumayya tace dan Allah yarima kar kasakeni please kacigaba da dukana kar kafurta kalmar.
Wani irin kallo yarima yai mata mai tattare da tsana sannan yace kije na sakeki saki ukku dan bana buk'atarki a cikin rayuwata.
Wata razanannar k'ara Sumayya tasaki tare da rarrafowa ta iso inda yarima yake cikin kuka tace dan Allah kabarmin saki d'ayan wlh shi kad'ai ma ya isheni please ka janye biyun tafad'i haka tare da ruk'o rigarsa.
Yarima fizge rigarsa yayi yace kar kik'ara ta6ani da wannan hannun naki mai najasa, wucewa yayi yabud'e bedside d'inta yad'auko paper da biro nan yarubuta mata saki ukku ya cilla mata sannan yace na baki nan da awa d'aya kitattara komatsenki kifita kibarmin gida inko ba hakaba zan sa6a miki.
Sumayya dafe kanta tayi tare da k'ara sautin kukanta tace na bani na lalace yau ni ya zanyi da rayuwata,,,,kallon zinat tayi da take raku6e waje guda fuskarta duk ta kumbura tace shikenan zinat kinja min yau nima aurena ya mutu yau ni nashiga ukku ina zansa rayuwata.
Yarima a fusace yace na dai fad'a miki kar kibari indawo in tarar da ke,,, yana fad'in haka yajuya yabud'e d'akin yafita.
Sumayya tana ta k'wala mai kira yai mata banza, nan tacigaba da kukanta.
Zinat na ganin ya fita ta rarrafa tajanyo rigarta da veil d'inta tasaka, dakyar tamik'e tsaye, sumayya ganin zata fita yasa cikin kuka tace zinat ina kuma zaki tafi kibarni kina ganin matsalar da kika jefani.
Zinat jakkarta tad'auka batare da ta kalli sumayya ba tace tafiya zanyi tun kan yarima yadawo ya6allani koma me kenan nidai sai munyi waya dan haka kinga ma tafiyata kisan yadda zakiyi kikare kanki,,,zinat na gama fad'in haka tabud'e k'ofan taficce cikin sauri, gudu-gudu haka tasamu tafita daga masarautar bata tsaya jiran abun hawaba tacigaba da sauri sai da tayi nisa sannan tasamu tahau abuabun hawa.
Sumayya na ganin zinat ta fita nan ma k'ara fashewa da sabon kuka tayi tace na bani ni yanzu ya zanyi da kaina wai nice yarima yasaka wlh ba zan yardaba sai anmaida aurenmu,,,,rarrafawa tayi tajanyo wayarta tana kuka tai dialing d'in number d'in ummanta.
Ummah tana yin picking taji kukan sumayya yana tashi, ahankali tace ya salam sumayya me kuma kike ma kuka kedai inba kukaba ba abinda kika iya.
Cikin kuka sumayya tace ummah ya sakeni.
Ummah da take kishingid'e zumbur tamik'e tsaye tace me kikace sumayya saki?
Eh ummah.
Innalillahi wa'innah ilaihiraji'un garin ya haka yakasance sumayya? Nashiga ukku ni halima, dan ubanki kifad'amin me kikayi yasakeki.
Sumayya cikin sheshek'ar kuka tace ummah daga na daki matarsa shine yasakeni.
Dan Allah asashi yamaida ni
Sultana sadiya ajiyar zuciya tayi tace sumayya kin tabbata abinda kika fad'amin gaskiya ne?
Eh ummah.
Toh shikenan yanzu yi maza kije wajen su dada kisanar da su, nima ganinan zuwa ai dole kikoma d'akinki.
Sumayya cikin kuka tace Toh ummah,,,nan takashe wayar tare da mik'ewa tajanyo kayanta tasaka.
A firgice tafito cikin sauri tanufi turakar su memartaba, tana shiga parlour dada ce kawai nan sumayya taduk'e k'asa tare da fashewa da sabon kuka.
Dada rud'ewa tayi tace lafiya sumayya me yake faruwane? Bakida lafiya ne?
Sumayya girgiza mata kai tayi tace kod'aya dada, yarima ne yasakeki.
Dada dafe k'irji tayi tace Innalillahi wa'innah ilaihiraji'un, saki fa kikace?
Memartaba da yake ciki yana shirin fita jin hayaniya yasa yafito yana cewa hayaniyar me nakeji haka?
Sumayya duk'awa tayi tagaishesa cikin girmamawa,
Saida memartaba yazauna sannan ya amsa mata tare da cewa lafiya sumayya kike kuka?
Dada girgiza kai tashiga yi tace ranka yadad'e wlh yarima baya da mutunci yanzu saboda Allah ace ya saki 'yar uwarsa?
Memartaba cikin d'aga murya yace saki kuma? Anya kuwa sakinta yayi dan bana tunanin yarima zai zartas da wannan hukuncin batare da na saniba.
Dada tallabe ha6a tayi tace wlh indai yarima ne zai aika.
Memartaba kallon sumayya yayi yace ke kallanni nan fad'amin me kikayi masa yasakeki?
Sumayya rage sautin kukanta tayi sannan tace banyi masa komai ba daga matarsa ta ja ni fad'a har da cemin juya marar haihuwa, shine nikuma nabiye mata nan mukayi fad'a shine yakamani yai min duka,tafad'i hakan tare da d'age hijab d'inta su memartaba salati suka shiga yi da suka ga kwanciyar bulala a jikinta.
Cikin sheshek'ar kuka tace bayan ya gama dukana shine yasakeni.
haushine yacika memartaba yace banyi tunanin hakan daga wajen yarima ba banta6a tunanin zai iya min cin mutunci irin hakaba ammah bari inkira iyayenku suzo asan yadda za'a 6ullo ma lamarin.
Memartaba wayarsa yad'auka yakira mahaifin yarima da na sumayya yace duk suzo da iyalansu susamesa.
Bayan kamar minti goma sai gasu su duka sunzo harda Aunty husna da rahma da suke gidan basu koma gidajensuba,
Lokacin su memartaba suna zaune suna tattauna al'amarin gabad'ayansu suka duk'a suka gaishesu, kowa da mamaki yake kallon sumayya.
Bayan su memartaba sun amsa gaisuwa, gyaran murya yayi yace wani ya aika akira min yarima dan na kira wayansa a kashe.
Abban sumayya ne yace toh ranka yadad'e nan yamik'e yaje ya aiki wani dogari yace yaje yakirasa.
Yarima bayan ya baro part d'in sumayya nan yakoma 6angaren zarah yanayinsa kawai zaka kallah kasan ba k'aramin tashin hankali yake cikinsaba, kallon zarah yayi da take kwance ta zuba ma waje d'aya ido tana kallo, daga gefen gadon yazauna tare da dafe kansa yana tunanin lamarin sumayya dan gabad'aya ta gama ficce masa a rai, wayoyinsa yakashe gabad'aya dan ya san dole sai memartaba ya nemesa dan dama gudun kar amaido masa aurenta yasa yaimata saki ukkun.
Zarah ruk'o hannunsa tayi cikin muryarta da tadashe saboda kuka tace tunanin me kakeyi?
Kallonta yarima yayi cike da tausayi yace in kaiki asibiti adubaki ko?
Girgiza kai zarah tayi tace babynka lafiyarsa lau dan basu samu sun ta6asa ba nikuma ciwon jikine kuma nasan zan warke insha Allahu.
Yarima d'aura hannunsa yayi saman fuskarta
07, February 2025
Shuraihu Usman
jjjjj