Showing 111001 words to 114000 words out of 168813 words
Chapter 38 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt
tsufa kuma daga inda kika fara haihuwa yara duk sai sun rikitaki bakida lokacin kanki, kuma mijinki zaiyi baya da ke.
Sai a lokacin sumayya tayi magana tace zinat kifahimceni wlh yarima yana son haihuwa.
Tsaki zinat tayi tace kefa matsalata dake kenan baki ganewa, kinsan daga inda kika fara aje 'ya'ya komai zaibi ya jagule miki mijinkima zai fara tunanin k'ara aure dan gaba d'aya zaki gunduresa, kibari kawai sai shekara mai zuwa lokacin kin tara abinda kika tara na dukiya a lokacin mijinki yana muradin 'ya'yan sosai toh zakiga rawan kai wajensa dan bazai k'ara yarda yayi nisa da ke da babynkiba, indai kuma kina tunanin cikin wannan bagidajiyar yarinyar ne toh kidaina tunani kikwantar da hankalinki dan da nazo zai tashi aiki.
Sumayya cike da gamsuwa da maganar zinat tace hakane saidai yanzu ummah ta yi fushi da ni bansan ya zanyiba.
Dariya zinat tayi tace kar kidamu zan fad'a miki yadda zaki shawo kan yarima da ummah.
Sumayya murmushin jin dad'i tayi tace nagode sosai zinat saisa nake k'ara sonki.
Dariya zinat tayi tace bakomai baby nima kinsan ina sonki sosai insha Allahu nan da upper week zan shigo garin, Sumayya wani irin farin ciki taji ta dabaibayeta tace kai baby ammah wlh naji dad'i kuma nayi murna, ji nake kamar injawo lokacin yayi.
Dariya zinat tayi tace kai baby gaskiya naga alama kinyi missing d'ina sosai, yanzu dai bari inje bank zan yi miki depositing d'in wasu kud'i idan nagama komai zan kiraki muyi magana.
Sumayya ciki jin dad'i tace ohk dear sai najiki.
Yarima koda yakoma part d'insa tisa files d'in yayi gaba yana kallo ya kasa cigaba da aiwatar da komai, tausayin zarah ne da nadamar abinda yayi mata suka kamasa, dan tabbas ya san zarah ta cika mace ta gari tunda tana d'auke masa buk'atunsa kuma har ta amince tayi renon cikinsa abinda 'yar uwarsa ta jini takasa, tunowa yayi da wulak'ancin da yakeyi mata tsaki yaja tare da dafe kansa yace ya akayi hakan ya kasance? Tabbas nasan zarah fushi take da ni, ji yayi duk ba dad'i dan haka yamik'e yafito yanufi part d'inta.
Yarima ahankali yatura k'ofa yashiga ganin babu kowa parlour yasa direct yanufi bedroom d'inta.
Zaune yahangota saman gadonta ta buga tagumi, zarah juyowa tayi takallesa wani irin dad'i taji a ranta sannan tajanye idonta daga kallonsa,
Yarima tsaye yayi yana k'are mata kallo ta d'an rame, duk sai yaji ba dad'i,,,ahankali yataka yanufi inda take daga gefen gadon yazauna,
Kallon zarah yayi da tad'auke kanta tak'i kallonsa tabbas ba k'aramin fushi take da shiba, hannu yakai yarik'o nata gabad'ayansu wani irin shock sukaji a jikinsu yarima runtse idonsa yayi ahankali yafurta zarah....shuru yayi maganar ta lak'afe a mak'ogoronsa dan baisan ta inda zai faraba.
Har a lokacin fuskar zarah a d'aure take kuma bata juyo takallesaba tana dai saurare taji abinda zai ce mata,
Chan k'asan mak'oshinsa kamar wanda akayi ma dole yace please kiyi hak'uri.
Ba zarah ba hatta shi kansa yarima da yayi maganar saida yaji wani iri dan a karo na biyu da zarah taciri tuta yaimata abinda bai ta6a yi ma waniba bayan iyayensa shine kalman hak'uri,
Zarah fizge hannunta tayi tamik'e cikin sauri tanufi toilet, yarima kiran sunanta yashigayi ammah ina tuni ta shige nan tamaida tarufe,
Cike da takaici yarima yadafe kansa da hannuwansa biyu shi kansa ya san tabbas ba k'aramin 6atama zarah rai yayiba a karo na farko da yaji haushin kansa ya kamasa dan gaba d'aya zuciyansa zafi take masa.
Ya dad'e zaune saida yayi kusan 30minutes ganin batada niyan fitowa yasa yamik'e jiki babu k'wari yafita yabar d'akin.
Zarah tunda tashiga toilet d'in kuka tashiga rerawa ita kanta batasan tak'amaiman dalilin da yasa take kukanba, saida taji fitar yarima sannan tawanke fuskarta tabud'e k'ofan tafito tahaye saman gadonta takwanta tana sheshek'ar kuka.
Shi kansa yarima duk ji yayi ba dad'i dan gaba d'aya ji yake komai ya kwancemasa duk wanda yakallesa sai yasan yana cikin damuwa, koda yakoma part d'insa key d'in motansa yad'auka yafita yabar gidan yaje gidan gona.
A saman 3 seater d'in da take parlourn yakwanta gabad'aya shi kansa ya rasa gane tak'amaiman abinda yasa duk yacanza dan wani iri yakejinsa daga k'arshe kallo yakunna nan yazauna yana kallon wrestling.
A nan yayi sallar isha'i sannan yakama hanyan gida.
Koda yakoma gida, part d'in zarah yakallah har zai wuce nasa sai kuma yaji baya iya wucewa dan haka yafasa yanufi part d'inta, a parlour yasamu kuyanginta zaune baibi ta gaisuwar da sukeyi masaba yawuce yanufi bedroom d'inta.
Lokacin zarah tana kwance saman darduma tana tasbihi, k'amshin turarensane da taji yasa tagane ya shigo d'akin, cikin sauri tamaida idanunta tarufe kamar mai bacci,
Yarima tsaye yayi yana kallonta dan duk atunaninsa baccin takeyi, ahankali yatako ya iso inda take duk'awa yayi yad'auketa yanufi gado da ita.
Koda yakwantar da ita zama yayi gefenta ahankali yazare mata hijab d'in da take jikinta sannan yazuba ma fuskarta ido ganin yadda tayi fayau da ita.
Zarah ahankali take safke numfashi kamar irin na masu bacci, tana jinsa yakai hannu yad'age mata rigar da take jikinta nan yashiga shafa cikinta, duk'ar da kansa yayi yai kissing d'in cikin sannan yagyara mata rigarta yajanyo blanket yalullu6eta.
Mik'ewa yayi yanufi k'ofa koda yabud'e saida yajuyo yakalleta sannan yafita tare da rufe mata k'ofan.
Zarah tana jin fitansa tabud'e idonta, yaye blanket d'in tayi tamik'e taje tamurza ma k'ofanta key sannan taje tayi wanka tayi shirin baccinta takwanta.
Yarima ma koda yakoma part d'insa wanka yayi yashirya sannan yahau saman gadonsa yakwanta, ina nan bacci yace baisan batunba, haka yaita juyi, nan zarah tacigaba da fad'o mai a rai ko ya runtse idonsa ita kad'ai yake gani duk yadda yaso yajanye tunaninta a ransa kasawa yayi, yarima ya ja tsoki ya fi sau goma a lokacin, sai daga baya yasamu bacci yad'aukesa.
____________
Dasafe bayan yarima ya gama shirinsa yana shirin fita sai ga sumayya ta shigo d'akin, kallo d'aya yayi mata yad'auke idonsa nan gabad'aya fara'ar da take a fuskansa tagushe.
Sumayya bata damu da yanayin da tagansaba zuwa tayi tazauna gefensa cikin kwantar da murya tace please yarima kayi hak'uri kayafemin abinda na aikata insha Allahu bazan k'araba na daina.
Ko inda take bai kallaba yashareta,
Sumayya marairaicewa tayi tace dan Allah kayafemin na yi maka alk'awali wlh bazan k'araba.
Wani irin kallo yarima yawurgamata sannan yace sumayya duk abinda kika za6a ma kanki daidai da ke ne, bana bak'in cikin hakan,
Shuru yad'anyi na lokaci kad'an sannan yace a tunaninki mata nawa suke bibiyata, mata nawa duk'awa suna rok'ona sukeso in auresu? Ke kin samu dama saisa kike yadda kikeso, hanya yanuna mata yace tun kan mutuncinki ya ida zubewa a idona tashi kifita kiban waje.
Sumayya kallonsa tayi taga babu alamun wasa a fuskansa dan haka tayi sauri tamik'e, tsayawa tayi gabansa tace please yarima ka.....wani irin kallo yawatsa mata cikin sauri tajuya tafita tabar d'akin.
Binta yayi da kallo cike sa takaici dan gani yake duk ita taja zarah take fushi da shi, tsaki yaja sannan yamik'e yad'auki wayansa da key d'in mota yafito.
Part d'in zarah yawuce dan yadubata saboda baya jin dad'in fushin da take da shi.
yana shiga zaune yatarar da ita a parlour saman cushin ta ci kwalliyanta tana sanye cikin english wears riga da skirt ta tufke gashin kanta, gabanta cup d'in coffee ne aka d'aura saman table.
Yarima tsaye yayi yana kallonta dan gabad'aya taso tarikitasa da yaganta, zarah d'ago kai tayi suka had'a ido saida gabanta yafad'i cikin sauri tajanye idonta daga kallonsa dan ita kanta saida tasamu tasaita nutsuwanta.
Takowa yayi yazo inda take zaune daga gefenta yazauna gab da ita nan yazuba mata ido, sharesa zarah tayi tad'auke kanta gefe kamar batasan da zamansaba.
Yarima ma janye idonsa yayi daga kallonta nan sukayi shuru gabad'ayansu, ganin batada niyar yin magana yasa yarima yace ke baki iya gaisuwaba?
Zarah d'aure fuska tayi kamar ba zatayi maganaba sai kuma chan tace ina kwana?
Shuru yarima yayi kamar bai jitaba saida yayi kusan minti d'aya sannan yace ya kike?
Ta6e baki zarah tayi sannan tace lafiya,,,,,tana fad'in haka tamik'e zatabar wajen.
Cikin sauri yarima yajanyota tafad'o jikinsa, ido suka zuba ma junansu zarah cikin sauri taruntse idanunta, yarima cigaba yayi da kallonta sai chan yakai hannunsa yashafi k'ashin wuyanta, ahankali kamar mai rad'a yace baby bakison cin abinci duk kin rame.
Zarah shuru tayi tak'yalesa tana ji yatura hannunsa cikin rigarta yana shafa cikinta tare da kwantar da kansa saman k'irjinta, su dukansu cikin wani irin yanayi suka shiga
Zarah ce tafara dawowa cikin hayyacinta dan haka tabud'e idanunta tanemi taturesa ganin ta kasa yasa tafashe mashi da kuka,
Cikin sauri yarima yad'ago yakalleta yace lafiya?..
Cikin kuka tace ni kakyaleni.
Yarima batare da ya yi maganaba yasaketa nan cikin sauri tamik'e tashige bedroom d'inta.
Yarima binta yayi da kallo har tashige nan yamaida kansa yajingine da kujera haushi da takaicin kansane yakamasa, daga k'arshe mik'ewa yayi jiki ba k'wari yawuce yabar part d'inta.
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'artโ๐ป_
๐๐๐
_*YARIMA SUHAIL*_
๐๐๐
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ยฎ*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE ๐ HEART TORCHING โค TEARS OF SORROWS ๐ญ CURDLES ๐ GIGGLES ๐ AND MARRIEGE THINK๐
*JUST GIVE US FOLLOW....*โ
*PAGE* 5โฃ4โฃ
Ahaka yarima yaje wajen aiki ammah kwata-kwata baida kuzari, Dr khalil shi kansa saida yalura da yanayin yarima,,,,,ko da yatambayesa abinda yake damunsa yarima banza yayi dashi yak'yale, kan dole Dr khalil yaja bakinsa yayi shuru dan ya san kome zaiyi toh bazai samu amsar tambayarsaba.
Zarah koda tashige bedbroom d'inta saman bed d'inta tafad'a tashiga tacigaba da kukanta wani irin son yarima ne yake fizgarta daga gefe guda kuma haushinsa takeji,,, ahaka tasha kukanta saida taji yunwa tana niyar yi mata illah sannan tamik'e taje wanko fuskarta tafita tad'auki coffeenta tasha.
Sumayya koda yarima yakoreta daga part d'insa bata wani damuba sosai cikin ranta cewa tayi na zan hanyar da zan 6ullo maka,,,,daga nan wucewa tayi tatafi turakar iyayenta.
Tana shiga a parlour ta tarar da sultana sadiya kishingid'e tsakiyan kuyanginta suna ta yi mata hidima, ganin sumayya yasa suka zube gabad'ayansu suna kwasar gaisu sumayya ko kallon inda suke batayiba ganin haka yasa cikin sauri suka ficce daga parlourn gudun kar suyi laifi.
Sultana sadiya tana ganin sumayya ta shigo nan tahad'e fuska babu alamun fara'a ko kad'an a tare da ita.
Sumayya jiki ba k'wari tazo tazauna gefenta ahankali tace ummana.
Sultana sadiya batare da ta kalletaba tace me yakawoki wajena.
Sumayya fashewa tayi da kuka tare da fad'awa jikin sultana sadiya, shuru sultana tayi tak'yaleta.
Cikin kuka sumayya tace ummah dan Allah kiyi hak'uri wlh na daina.
Sultana sadiya sai a lokacin ta kalleta tace sumayya kikyaleni kawai tunda bakyajjn magana kije kawai na sallamaki wajen wad'anda kike jin maganarsu.
Sumayya Cikin kuka tashiga girgiza kai ahankali tace ummah wlh ina jin maganarki akasine kawai aka samu kuma insha Allahu na daina bazan k'araba, dan Allah kiyafe min wlh duk na zubar da pills d'in.
Sultana sadiya cike da tausayin d'iyartata tashiga d'an bubbuga mata bayanta kad'an cikin sigar lallashi tace toh shikenan sumayya na hak'ura ammah dan Allah kidaina irin haka kinsan idan labari yajema su dada bazakiji da kyauba ke kinsan ko mahaifinki yaji sai kashinki ya bushe.
Sumayya share hawayen fuskarta tayi cikin jin dad'i tace insha Allahu ummah ba zan sakeba.
Murmushi sultana sadiya tayi tace yauwa d'iyata, yanzu sai kije kisamu kilallashi wanchan miskilin mijin naki ko shima ya safko, Allah yaimiki albarka.
Ameen ummana, insha Allahu zan k'ara bashi hak'uri....nan tazauna sukasha hira da ummah cike da jin dad'i sannan daga baya tayi mata sallama tafito tanufi turakarsu dada dan tagaisheta.
koda tashiga fuskarta d'auke da murmushi taduk'a tagaishe da dada,
Cikin jin dad'i dada ta amsa mata nan sumayya tazauna gefen dada tana murmushi tace 'yar tsohuwa me kika ajemin?
Ido dada tazuba mata tace me fa zan aje miki bayan gakinan kinyi 6ul-6ul da ke kin koma d'imemiya wai mi wanchan miskilin yake d'irka miki?
Dariya sumayya tayi tace wlh dada hutune kawai,,,dada cikin rashin yarda tace kodai mun samu k'aruwane?
Girgiza kai sumayya tayi tace wlh dada banda komai.
Rik'e ha6a dada tayi tace sumayya kodai zakije asibiti aduba lafiyanki, tunda shi wanchan miskilin bai damu da hakanba.
Dada na je ance lafiya ta lau fa kawai dai lokacine baiyiba.
Ajiyar zuciya dada tasafke sannan tace toh Allah yanuna mana lokacin, Allah yasa ina da rabon ganin d'an cikinki.
Dariya sumayya tayi tace Ameen dada.
Ho 'yar nema ko kunyata bakyaji....cewar dada.
Dariya sumayya tashiga yi tace kunya ai ya wa-ne yanzu.
Dak'uwa dada tayi mata tace gidanku sumayya, ja ira kawai.
Sumayya tsagaitawa tayi da Dariya da take tace afuwan ranki yadad'e na daina.
Murmushi dada tayi tace toh ya wajen 'yar uwartaki ina fata tana lafiya.
Ta6e baki sumayya tayi tace inaji lafiya lou take.
Sakin baki dada tayi tana kallonta tace sumayya ban fahimcekiba? Kar dai kicemin baku zaman lafiya.
Sumayya k'wallah ce tacika mata ido tace toh dada ya zanyi yarinyar da bata k'aunata kullum batada aiki sai had'ani da mijina, ni me natsare mata da zata dinga min haka.
Dada da mamaki take kallon sumayya tace sumayya yanzu yarinyar nan da nake gani kamar babu ruwanta itace takeyi miki haka?
Hmm dada kenan kawai dai abar maganar dan in kikaji wasu abubuwanma da takeyi sai kinyi mamaki, ni yanzu babbar matsalata fushin da yarima yakeyi da ni kusan kullum sai ta had'amu.
Dada salallami tashiga yi tace na shiga ukku ni Asma'u, yanzu saboda Allah yarinya tazo tararar da ke gidan mijinki sannan tace zatayi miki irin haka?
Toh kibarni da yariman yadawo zan gansa idan shi bazai iya d'aukan matakiba a kai toh ni zan d'auka ko inhad'asa da memartaba tunda shi yana jin maganarsa.
Cikin jin dad'i sumayya tace yauwa Dadata ammah dan Allah kar kifad'ama yarima ni nafad'a miki dan wlh zai iya kakkaryani.
Cike da tausayin jikartata dada tace kar kidamu sumayya insha Allahu bazan ceba, kuma ko na ce ai bai isa yata6akiba dan ko dole inrama miki.
Cikin jin dad'i sumayya tace kibarsa kawai Dada ni zaman biyayya da hak'uri kawai nake da shi, duk abinda yayi min dan kansa, dan na ma fi ganin laifin wacchan munafukar matar tasa mai mugun hali.
Tsaki Dada taja tace kibarni da su kawai,
haka sumayya tazauna tayi ta 6ata zarah a wajen dada nan Dada tahau tazauna tana ta jimamin halin zarah.
Yarima koda yadawo wanka yayi yashirya sannan yad'anci lunch kad'an, yana gamawa fita yayi yanufi part d'in zarah dan kwata-kwata yanzu wani iri yakeji game da ita rashin zuwanta part d'insa ba k'aramin d'aga mai hankali yakeba.
Yana shiga bedroom d'inta daidai lokacin tafito wanka d'aure take da towel tana tsaye gaban dreesing mirror tana yin shafa.
'Dago kai tayi takallesa nan suna had'a ido tajanye fuskarta daga kallonsa, yarima tsaye yayi yana kallonta batare da yayi maganaba.
Tana gamawa tawuce tanufi wajen wardrobe d'inta tabud'e tad'auko kayanta, juyowar da zatayi sai ganin mutum tayi bayanta tsaye, k'ara d'aure fuska tayi ta ra6a ta gefensa zata wuce yarima jawota yayi tafad'o jikinsa yarungumeta,
K'ok'arin turesa tashiga yi nan yak'ara matseta a jikinsa ahankali yace wai ke meyasa kike min haka?
Harararsa zarah tayi tace wani abu kaga na yi maka?
Zuba mata ido yayi yana kallonta da mamaki sannan yace dan kinga ina lalla6aki saisa kike min yadda kikaga dama
Ta6e baki zarah tayi tace kar ma kalalla6ani indai nice na gama shiga sabgarku tunda daman sai kunga na shiga sannan zaku sami daman wulak'antani,,,,fashewa tayi da kuka tace ni duk abinda sumayya takemin me nata6a cewa shine ni kamar jira ake ko banyi mata wani abuba sai ace na yi toh ya kukeso inyi!!! tak'arashe maganar cikin d'aga murya.
Yarima shuru yayi yakasa magana sai chan yarungumeta a k'irjinsa tare da runtse idonsa yana jin wani iri a ransa,,,ahankali kamar me rad'a yace ix owk zarah, insha Allahu hakan ba zai k'ara faruwaba,
Zarah janye jikinta tayi daga nasa tawuce zatabar wajen, kallonta yarima yayi yace wai ke dan kin samu ina lalla6aki shine kike min haka?
Zarah juyowa tayi takallesa sannan tace toh ni me kaji na ce maka?
Yarima har ya bud'e baki zaiyi magana nan wayarsa tafara ringing,,,d'aukowa yayi yaduba ganin me kiransa yasa yayi picking tare da yin sallama.
Daga chan 6angaren dada amsa mashi tayi sannan tace toh dodo kazo yanzu ina son ganinka.
Yarima kallon agogon hannunsa yayi sannan yace yanzu kuma?
Cikin fad'a dada tace eh, inkuma bazakazoba saboda ka rainani toh sai infad'ama ubanka shi sai yasa kazo.
Yarima shuru yayi baice komaiba.
Jin ya yi shuru yasa dada tace ko bakaji abinda naceba?
Cikin k'osawa da maganar yace ganinan,,,,yana fad'in haka yakashe wayar ko inda zarah take bai kallaba yawuce yafita yabar d'akin
Zarah da ido tabisa har yatafi sannan tad'auki kayanta tasaka, cikin ranta ji take daman batayi ma yarima hakaba.
Yarima koda ya isa turakar su dada a parlour yasameta zaune tana jiransa, ko da yayi sallama ciki-ciki ta amsa masa, saman d'aya daga cikin kujerun yazauna cikin girmamawa yagaisheta.
Amsa masa dada tayi daganan d'akin yad'au shuru ba wanda yak'ara magana, ganin baida niyar yin magana yasa dada tace toh d'an nema watau shine kayi zaune baka ma jin zaka iya tambayata dalilin kiran da nakeyi maka.
Murmushi kawai yarima yayi batare da ya yi maganaba.
Dada gyara zamanta tayi ta fuskanci yarima sosai sannan tace suhail na ji abinda kakeyi ma 'yar uwarka kuma na gode ba ita kayimawa ba ni kayimawa.
Da mamaki yarima yake kallonta har saida takai aya sannan yace ranki yadad'e wani abu tace na yi mata?
Harararsa dada tayi tace kai kar kamaidani k'aramar yarinya ko ka d'auka duk abinda kukeyi mata kai da matarka bai dawowa a kunnena?
Yarima har ya bud'e baki zaiyi magana sai kuma yafasa nan yacigaba da dannar wayarsa da take hannunsa.
Nan dada tacigaba da cewa Toh bari kaji ko kaso ko kak'i sumayya 'yar uwarkace kuma za6inmu ce sannan wannan aure naku mutuwa kawai zai raba, ita wacchan matar dan kaga za6inka ce saisa kake ma 'yar uwarka wulak'anci son ranka kuma inaso kasani ciki Allah yake bayarwa kuma itama sumayya in da rabo zata haihu.
Yarima banza yayi mata kamar ba da shi
08, February 2025
Shuraihu Usman
jjjjj