Showing 135001 words to 138000 words out of 168813 words

Chapter 46 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt

08 Aug 2024

100536

bace zata gansa batare da taji ya burgetaba, dan rannan mijina ya fad'amin a hospital har 'yan mata sun fara shige masa dan ma baibasu fuska saisa suke yin baya da shi.


Ajiyar zuciya zarah tasafke tace toh ya zanyi Aunty jamila jin dad'inama da baya kulasu ammah ni kaina indai zai fita hankali baya kwanciya sai yadawo kuma dai gashi badaman ayi masa kulle.


Dariya jamila tayi tace kinjiki da wata magana wai kulle, kedai kicigaba da addu'a Allah yakare miki mijinki.
Ameen y rabb,,nan zarah taje tahad'o breakfast tadawo tazauna tana yi suna hira.


Bayan sun gama a tare suka shiga kitchen suka had'a lunch sannan zarah tawuce part d'insu tayi wanka tashirya.


Wajen k'arfe ukku gabad'ayansu parlour suka dawo suka zauna suna kallo suna hira jefi-jefi har akayi sallar la'asar ammah su yarima basu dawoba, jamila kallon zarah tayi tace mutanen shuru basu dawoba.
Uhm wlh kau Aunty jamila nima tunanin da nake kenan Allah dai yasa lafiya.
Ameen y rabb,,,cewar jamila, suna cikin haka sai ga su yarima sun shigo da sallamarsu.


Juyowa sukayi suka kallesu tare da amsa musu sallamar sannan sukace sannunku da zuwa.


Amsawa sukayi,
jamila ce tace tun d'azun muna ta jiranku ammah shuru.
Dr mu'az kallon yarima yayi sukayi murmushi sannan yace munje neman auren prince ne dan cewa yayi yanaso ya auri 'yar garin nan,,,yak'arashe maganar tare da kallon zarah da tacika tayi fam.
Jamila ma kallonta tayi tace laahhh my har da kai ake had'a baki dan ak'aro ma gimbiya abokiyar zama? Gaskiya ni ban goyi bayankuba.
Zarah saboda bak'in ciki kamar tad'aura hannu saman ka tafasa ihu,
Yarima murmushi yayi yace toh ya aka iya tunda ina so, yanzu dai bari inshiga ciki ind'an watsa ruwa, batare da ya kalli zarah ba yawuce yashige yana dariya ciki-ciki.


Murmushi mu'az yayi yace sorry gimbiya kar kiga laifina prince ne yaimin dole saisa nabisa mukaje,
Jamila k'unshe dariyarta tayi tace ku dai kukasani nidai ina bayan gimbiya.


Zarah shuru tayi kamar ruwa ya cita ta ma rasa abinda zatace,
Nan dr mu'az yashige yana dariya ciki-ciki.
kallonta jamila tayi tace ranki yadad'e kitashi prince fa na chan yana jiranki.
cike da k'ulewa tace Aunty jamila toh me zanyi masa.
Rik'e baki jamila tayi tace haba Zarah banyi tunanin jin haka daga garekiba ai na d'auka ko da ma kishiyarce bazata firgitakiba tunda kinsan kinriga kin zarce mata, kinga tashi kije kitaimaka ma mijinki nima kinga tafiyata.


Zarah ba dan tasoba tamik'e tanufi part d'insu lokacin da tashiga bedroom tsaye taga yarima gaban dressing mirror yana shafa da alama daga wanka yafito.


Tsaye Zarah tayi tana kallonsa, shareta yayi yai kamar baimasan tana wajenba, bayan ya gama ta gefenta yazo zai gifta yawuce sai a lokacin ya kalleta ta cika tayi fam, danne dariyarsa yayi Sannan yace kekuma fa?


Ai zarah kamar daman jira take yayi magana nan tafashe da kuka,,,,da mamaki yake kallonta yace Allah yabaki hak'uri daga tambaya sai kuka? Toh indai tambayarce toh nadaina nan yawuce yai tafiyarsa yabud'e wardrobe.


Dagudu zarah taje tarungumesa tabaya tacigaba da kukanta.
shuru yarima yayi yana jin kukan nata yana ta6a har cikin ransa,
ganin baida niyar yin magana yasa zarah cikin kuka tace menakeyi maka da kakeso kayi aure? Dan Allah indai wani abu nakeyi maka kafad'amin wlh zan daina,
juyowa yarima yayi yakalleta yaga haik'an take ta kukanta, murmushi yayi yace zarah ni na ce kinmin wani abu?
Girgiza kai tayi tana mai cigaba da kukanta.
tallabo fuskarta yayi yace kuma ni kikaji nace aure zanyi?
Nan ma Girgiza kai tayi.
murmushi yayi sannan yace tsokanarki fa daman mu'az yake dan yaga yadda zakiyi sai kuma gashi ya gani.
Zarah fad'awa tayi jikinsa tana cigaba da kukanta, dariya yarima yayi yace lallai ashe matar tawa tana tsoron kishiya ai na d'auka da jaruma nake zaune.
Duka zarah takaimasa a k'irji cikin kuka tace kai ko? Wlh ban yarda sai na rama,
dariya yarima yayi yace toh nidai bani nayi maganar ba.
'Dago kai zarah tayi takallesa tare da tsagaitawa da kukan da take tace ina sonka sosai akanka ba abinda bazan iyaba idan mace tara6eka ji nake wani iri sumayya ma dan ba yadda na iya nasan idan nace zanyi kishinta toh banyi ma kaina adalciba.


Murmushi yarima yayi yace aiko sai kinyi hak'uri dan yarima mijin mace hud'une.


Turo baki zarah tayi tace insha Allahu a haka zaka tsaya ba k'ari.
Dariya yayi yace lallai yarinya sai kinji ana gud'a ankawo min amaryata sabuwa gal.


Harararsa tayi cike da k'ulewa tace ai nima d'in gal aka kawo maka ni,
K'unshe dariyarsa yayi sannan yace toh ni mekikaji na ce?


Marairaicewa zarah tayi tace dan Allah kayi hak'uri akan abinda nayi maka jiya insha Allahu ba zan k'araba, wlh bana jin dad'i inga kana fushi da ni duk sai inji wani iri.


Goge mata hawayen fuskarta yayi yace kar kidamu ni ban rik'ekiba daman ai ke bakya laifi.


Murmushi zarah tayi tace ka dai fad'a dai kawai nidai yanzu kashirya muje kayi lunch dan nasan ka kwaso yunwa.
Toh ranki yadad'e yadda kikeso haka za'ayi.
dariya zarah tayi tace au abun harda tsokana?
uhm ni na isa intsokaneki,


nan zarah tataimaka mashi yashirya sannan suka fito inda suka tadda su mu'az suna zaune suna jiransu.


Ganinsu yasa mu'az yakyalkyale da dariya yace prince har ka gama lallashin?
Harararsa yarima yayi yace tunda ka had'aba.
Zarah duk'ar da kanta tayi cikin jin kunya.
jamila tace ammah dai nasan saida akasha da-ga kafin kashawo kanta.
Murmushi yarima yayi yace baby toh gaki gasu kisan zaman da kike dasu dan so suke suga ank'ara miki kishiya.
Turo baki Zarah tayi tace kabarni da su ai insha Allahu dagani ba k'ari ni kad'ai na isheka ko?
Dariya sukasa mata dan yanayin yadda tayi maganar ya basu dariya, yarima murmushi yayi yace kekad'ai fa kin isheni baby.


nan suka wuce dining suna dariya, zarah ganin tsokananta suke yasa tasharesu nan sukayi lunch, bayan sun gama nan taja yarima suka koma part d'insu sukaita shan love d'insu












_Comment_
*nd*
_Share_












_Sis Nerja'artโœ๐Ÿป_
[5/3, 9:52 PM] Sis Naj Atu: ๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘


_*YARIMA SUHAIL*_

๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘






_*Written By~Sis Nerja'art*_






_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_




https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/


*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ยฎ*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE ๐Ÿ˜˜ HEART TORCHING โค TEARS OF SORROWS ๐Ÿ˜ญ CURDLES ๐Ÿ™‚ GIGGLES ๐Ÿ˜ AND MARRIEGE THINK๐Ÿ’‘
*JUST GIVE US FOLLOW....*โœ”




*PAGE* 6โƒฃ2โƒฃ






*BAYAN WATA DAYA*


Zarah cikinta ya girma sosai dan a lokacin watansa takwas da ta zauna k'afafuwanta har kumbura suke, lalla6ata kawai yarima yake dan indai yana gida baya bari tana komai saidai shi yayi mata.




Yau ma kwance take saman cinyarsa suna kallon wani series film, d'ago kai tayi takallesa tace my dan Allah kataimaka kakira min su mama mugaisa kaga har yanzu bamuyi waya da su ba.


Kallonta yarima yayi batare da yayi magana ba, ganin haka yasa zarah tace ammah Indai kaga da matsala toh kabarsa kawai.


janyo wayarsa yayi yace ai dolema inkirasu dan nasan hali yanzu kin fara min kuka.


Murmushi zarah tayi tace karufa min asiri kai ai d'an alalla6ane ranka yadad'e inba hakaba yanzu mutum ya amsa query.


Hmm haka dai kikace, yanzu dai bari inkirata mugaisa, nan yarima yakira mama cikin girmamawa yagaisheta, bayan sun gaisa nan yamik'a ma zarah.


Cike da jin dad'i zarah tace hello mamana,
Daga chan 6angaren mama tace zarahta.
Murmushi zarah tayi tace ina wuni mama?
Lfy lou zarah, ya gidan,,cewar mama.
Lafiya lou mama nayi missing d'inku kwana biyu.
Daga chan 6angaren mama tace aikam dai zarah kun 6oye, ai muna neman wayanki bata shiga.
Zarah d'ago kai tayi takalli yarima da hankalinsa yana wajen T.V sannan tace eh wayarce tasamu matsala saisa, ina fata duk kuna lafiya ina abbanmu da su yaya rauda?
Mama tace babanku baya nan saidai su rauda, ai muna ta kiranki mufad'a miki munkoma sabon gida.


Wata irin k'ara zarah tayi cike da murna tace Alhmdllh gaskiya naji dad'i Allah yasa alkhairi, Allah yatsare sai munzo ganin gida.


Dariya mama tayi tace Ameen y rabb, toh Allah yakawoku lafiya.


Ameen mama, aba su yaya rauda mugaisa.


Nan mama tabasu sukasha hira har suna cewa zasuzo dan sun fitar da anko d'in bikkin Aysha, nan zarah tace a'a kar suzo dan sun d'anyi tafiya ammah idan sun dawo zata nemesu, sun dad'e suna hira sannan sukayi bankwana suka kashe wayar cikin jin dad'i.


Mik'ama yarima wayarsa tayi tace ka gama min komai nagode sosai my soulmate,
Murmushi yarima yayi yace toh yanzu hankali ya kwanta ko?


Girgiza kai zarah tayi tace har yanzu da saura, hankalina bai ida kwanciyaba.


Kallonta yarima yayi yace toh menene yayi saura?


Marairaicewa tayi tace dan Allah kakira ummi mugaisa da ita ko tasamu sauk'i a ranta dan nasan duk inda ummi take yanzu bata cikin kwanciyar hankali.




Nan da nan fara'ar da take fuskar yarima tagushe gabad'aya damuwa tabayyana, shuru yayi baice ma zarah komai ba.


Ganin haka yasa zarah tace dan Allah kataimaka koda minti biyune mugaisa da ummi.


Da mamakinta sai gani tayi ya janye mata kai daga saman jikinsa nan yamik'e yashige bedroom.


Da kallo zarah tabisa cike da tausayinsa, nan tamik'e tabi bayansa, saman gado ta tarar da shi kwance yayi pillow da hannuwansa, takawa zarah tayi taje tahau gadon takwanta daga gefensa tare da rungumesa cikin kwantar da murya tace kayi hak'uri mijina idan na 6ata maka rai, nima ba ason raina hakan yakasanceba kawai dai gani nayi yakamata ace koda sau d'ayane ka kira ummi dan nasan a yanzu duk inda ummi takasance toh hankalinta a tashe yake, ammah da taji kana cikin k'oshin lafiya na tabbata hankalinta zai kwanta,
Yarima maida idanunsa yayi yalumshe yana jin wani iri a ransa.


Zarah cigaba tayi da cewa kafini sanin yadda ummi takeji a game da kai, kana tunani ko da sau d'aya hankalinta zai kwanta alhali batajin ko muryarka?


shuru yarima yai yakyaleta kamar yaba banza ajiyarta.


Ganin haka yasa zarah tafashe da kuka tace shikenan kayi yadda kakeso tunda haka kaza6a idan namutu ba shikenan ba.


Yarima jin maganartata yayi har cikin ransa, rungumeta yayi tare da bud'e idanunsa yace zarah kidaina cewa haka insha Allahu bazaki mutu kibarni ba, indai ummi ce bari inkirata yanzu.




Zarah cikin jin dad'i tarungumesa tace nagode sosai mijina Allah yasaka da alkhairi.


Murmushin k'arfin hali yarima yayi yace Ameen dear, wayarsa yajanyo yalalubo number d'in ummi.








Ummi tun bayan tafiyar yarima bata samun kwanciyar hankali dan ko abincin kirki bataci, sultan Ahmad shi yake tsareta yake samu tana ci, kullum aikin d'ayane daga lallashi sai wa'azi ahaka tad'an safko tafara sakewa.


Yauma zaune take saman darduma tana lazimi, wayartace datake kusa da ita tafara ringing, ido tazuba ma wayar ganin sabuwar number ce kamar ba zata d'aukaba har saida takusan tsinkewa sannan tayi picking tare da yin sallama.




Yarima jin muryar umminsa yasa yalumshe ido yana jin wani irin nishad'i a ransa, nan Ummi taita magana ammah shuru.


Zarah ce tata6osa ahankali tace kayi magana.


sai a lokacin yabud'e idanunsa sannan yace hello Ummina.


Jin muryar yarima yasa sultana bilkisu tarikice tarasa mezatayi murna ko kuka, ai sai ji yayi ta fashe da kuka tace my son kaine? Shine katafi kabarni baka ko nemana? Ni miye nawa laifin da kagujeni, baka tunanin halin da zan shiga?




Yarima runtse idanunsa yayi yanajin wani irin d'aci a ransa, cike da tashin hankali yace ummina kiyafemin wlh ba ason raina hakan yakasanceba, kema kinsani ba zan iya zaman second d'ayaba batare da kina a rainaba.




Cikin kuka Ummi tace nasan haka my son dan Allah kadawo gareni ko nasamu sauk'in abinda nakeji a raina, kataimaka kazo inganka ko hankalina ya kwanta.




Yarima hawayene yaji suna zuba daga idanunsa, ahankali cikin muryar lallashi yace Ummi kikwantar da hankalinki muna cikin k'oshin lafiya, indai har kina kuka toh nima zaki sani inyi.


Jin haka yasa ummi tayi saurin tsaida kukanta tace nadaina my son, yaushe zakazo?


Karkidamu ummina very soon zanzo gareki kicigaba da yi min addu'an da kikasaba.


Murmushin jin dad'i sultana bilkisu tayi tace Allah yaimaka albarka kaida zuri'arka my son, a yanzu hankalina ya kwanta da naji kuna cikin k'oshin lafiya, kuma insha Allahu akowane lokaci zakucigaba da kasancewa cikin addu'ana, yanzu kuna ina?


Shuru yarima yayi nad'an lokaci sannan yace ummi muna nan cikin k'oshin lafiya.


Ajiyar zuciya tayi tace masha Allah gaskiya naji dad'i toh ina d'iyar tawa?


Yarima waigawa yayi yakalli Zarah da tahad'e kai da gwiwa tana kuka k'asa k'asa, dafata yayi nan tad'ago kai yamik'a mata wayar kallonsa tayi, nan yai mata nuni alamun takar6a.


Bayan ta amsa muryarta tana rawa tayi ma ummi sallama, amsa mata ummi tayi nan Zarah ta gaisheta cike da girmamawa.


Ummi bayan sun gaisa, cikin sanyin jiki tace Zarah kiyi hak'uri da abinda yafaru mune muka ja miki.




Girgiza kai Zarah tashiga yi cikin sheshek'ar kuka tace ummi kidaina cewa haka *K'ADDARA CE* kawai taja hakan kuma har ga Allah ban ta6a tunanin kun cutar da ni ba koda sau d'aya, saidai abu d'aya nake tunanin kunyi min shine kun sama ma rayuwata farin ciki, baku k'yamaceniba a matsayina na talakka kun had'ani aure da d'anku, taya zan yi wani tunani nadaban akanku? Wlh ummi ku masoyanane nagaskiya ku iyayene agareni dan dani da 'ya'yanku duk d'aya kukad'aukeni,
K'ara fashewa da kuka Zarah tayi tace ummi wlh kun gama min komai a rayuwata tsakanina da ku saidai addu'a dan banda abinda zan biyaku.




Ummi Murmushin jin dad'i tayi tare da goge hawayen fuskarta sannan tace Allah yaimuku albarka Zarah, Allah yasafkeki lafiya mucigaba da addu'a insha Allahu memartaba zai safko daga fushin da yake kudawo gida.


Murmushi zarah tayi tace Allah yasa ummi,
Yarima zare wayar yayi daga kunnenta tare da switching off d'inta gabad'aya.




Zarah da mamaki take kallonsa da ya aje wayar tare da komawa yakwanta yamaida idanunsa yalumshe, saman k'irjinsa takwanta ahankali cikin muryar lallashi tace kayi hak'uri insha Allahu komai zaizo k'arshe.


'Dan guntun murmushi yarima yayi sannan yace niko zama na nan ya fi min dad'i koda sau d'aya bana tunanin komawa gidanmu, nidai burina iyayena susami kwanciyar hankali.




Da ido take binsa har yakai aya sannan tace kadaina cewa haka yarima koma me akayi maka yakamata ace ka hak'ura domin 'yan uwa dabansuke ba a iya canzasu, cikin dangine zakashiga kai rayuwarka kaji dad'i.




Murmushi yarima yayi yace naji yanzu dai aji da ni sarkin surutu.


Zaro ido zarah tayi tace anya zan iya? Kaga fa yanzu nayi nauyi.


Kar kidamu baby zaki iya nima ai ahankali zan miki dan banason wannan rakin naki.




shagwa6e fuska tayi kamar zatayi kuka tace au nice ma sarkin raki?


Dariya yayi sannan yace toh ai haka kike,


Uhm naji ai kaine baka tausayina.


Yarima yace au haka kikace? Toh shikenan bari kigani.


Zaro ido zarah tayi tace dan Allah kayi hak'uri da wasa fa nake.


Shareta yarima yayi nan yakwantar da ita, ganin tayi rau-rau da ido yasa yai murmushi tare da komawa gefenta yakwanta, kansa yana kallon ceiling.


Kallonsa zarah tayi ganin baida niyar yi mata komai yasa tace toh ka fasa?


Juyowa yayi yakalleta yana murmushi yace sarkin tsoro ni ba abinda zan miki daman.


Dukan wasa zarah takaimasa tace kai ko?
Dariya yayi yace ya na iya tunda Allah ya had'ani da matsoraciyar mata.


Uhm kaima kasan ni jaruma ce.


Nidai bansan komai ba ammah bari inyi just na 5 hours tanan zan d'an gane jarumtarki.


Zaro ido zarah tayi tace karufamin asiri ai sai inmutu.


Kumatunta yaja yace ba zaki mutuba dear, maida kanta tayi saman k'irjinsa tace Allah yasa ina da rabon rayuwar,
Yanzu in namutu shikenan aurenka zaka sake kamance da ni,,,tak'arashe maganar kamar zatayi kuka.




Rungumeta yayi yana ji kamar ta soka masa mashi a mak'oshi da ta ambaci mutuwar, ahankali yace zarah kidaina cewa haka dan ni bana tunanin zan iya son wata bayan ki, ban ta6a son wataba sai ke.


'Dago kai tayi takallesa tace har sumayya?


Yarima ji yayi wani irin takaici da tsanar sumayya sun dabaibayesa musamman ma da yatuna halin da yasameta ita da k'awarta,,,cike da takaici yagirgiza kai yace sumayya auren had'ine akayi mana,
Zuba mai ido zarah tayi tace toh kai bakada za6in kanka mu dukanmu baka akayi?


Cike da k'osawa da tambayoyinta yajanyeta daga jikinsa yamik'e yace baby kin cika tambaya har kinsa kaina ya fara ciwo yanzu dai bari inje ind'anyi wani research a system,,yana fad'in haka yaje yad'auki system d'insa yakoma parlour.


Zarah da kallo tabisa cike da so da k'auna har yaficce, sannan tayi murmushi tare da janyo pillow tarungume a k'irjinta.


______________
Ummi bayan yarima ya kashe wayar ajiyar zuciya tayi dan har cikin ranta taji dad'i da taji d'anta yana cikin k'oshin lafiya kuma ta ji hankalinta ya kwanta, a ranar saida kowa yasan tana cikin farin ciki dan rabon da aganta a yanayin tun ran da yarima yabar gidan.






A 6angaren sumayya ko hidimarta kawai take koda tanajin ba dad'i akan mutuwar aurenta ammah zinat tuni ta fara mantar da ita damuwarta dan basuyin ko 2 hours batare da sunyi wayaba nan wata shak'uwa tak'ara shiga tsakaninsu, da ace za"a duba wayarta a lokacin blue films da pic's ne kawai cikinta da ta zauna part d'inta batada aiki sai kallo sai waya, wulak'anci ko k'aruwa yayi dan ma'aikatansu har ji suke daman bata dawoba dan gabad'aya indai zata fito toh sai ta hanasu kwanciyar hankali.


Sultana sadiya ganin hankalin sumayya ya kwanta yasa itama taji dad'i a ranta, hatta shi kansa sultan abbas koda ya nuna fushi yake da ita saida taje tasamu tabasa hak'uri sannan tasamu sauk'in mahaifin nata.




Yau ma kamar kullum kwance take tayi d'aid'ai a saman gadonta tana waya da zinat, inkaganta sai karantse da namiji take waya dan shagwa6a kawai take zuba mata akan tazo taimata ko sati guda ne.


Zinat tace anya baby kina ganin ba matsala ni fa ina tsoron abinda yafaru da farko yak'ara faruwa dan kinga wanchan mijin naki har tabbai yabarmin a jiki.


Ta6e baki sumayya tayi tace ke kema tunawa da shi ai wlh tunda yasakeni toh sai nayi silar rabasa da wannan tsinannar matar tasa.


Dariya zinat tayi tace baby har yanzu dai kina akan bakanki, yanzu dai kisaurareni end of this week zaki ganni.


Wani irin k'ara sumayya tayi tace dagaske kike ko wasa?


Dariya zinat tacigaba da yi, sai chan tad'an tsagaita dariyar tace kai baby zaki ciremin kunne, zan shigo man ammah anya ba a hotel zan safkaba, saboda ni a yanzu gidanku yafi k'arfina.


Cike da Jin dad'i sumayya tace bawani fin k'arfi, dan Allah kizo kawai wlh babu

08, February 2025
Shuraihu Usman

jjjjj

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login