Showing 168001 words to 168813 words out of 168813 words
Chapter 57 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt
granny sultana.
Shafa kansa tayi tare da bashi peck a goshi tace toh shikenan my boy ina jiranka.
Shima peck d'in yabata a kumatu sannan tad'ago takalli yarima tace please hearty kar ka dad'e.
Kar kidamu baby zan dawo dawuri, hannu tasa tarufe ma Ameer ido sannan tayi ma yarima kiss a baki.
Murmushi suka sakar ma juna tace adawo lafiya my heartbeat.
Allah yasa baby nan tad'aga masu hannu har suka fita.
Take masa baya guards d'insa sukayi nan yasa Ameer a mota yace akaishi gidan shaheed sannan yawuce yagaishe da su memartaba da yake fama da ciwon k'afa bayan sungaisa yaje yagaishe da su ummi da sultana sadiya daga chan yawuce fada.
Wajen k'arfe takwas koda yadawo yatarar da zarah har tayi bacci nan yai shirin baccinsa sannan yahau gadon kallon zarah yayi da tabaje tana ta kwasar bacci ahankali yad'age rigarta yakai hannu yana shafa cikinta daga k'arshe yad'aura kansa saman cikin.
Jin abu samanta yasa tafarka daga baccin da bata dad'e da fara yinsaba, kallon yarima tayi tashafa kansa sannan tace hearty me kakeyi nan?
Murmushi yayi batare da ya d'ago kansaba yace ina gaisawa da baby na ne.
Zaro ido tayi tace wane irin baby?
Sai a lokacin yad'ago yakalleta yace Wanda yake manne a cikinki.
Karufan asiri ni banda komai.
Murmushi yayi yace taya kike tunani zan k'ara bari kisamu ciki batare da nagane ba, wanchan karen ma dande ban maida kaiba ammah ai naga alamomi kawai jin kai ne yahana intabbatar da hakan.
Ajiyar zuciya tasafke tace toh taya akayi kagane ina da ciki bayan ni kaina bansan da shi ba.
Rungumota yayi jikinsa yace baby ko kin mance ni doctor ne? Insha Allahu nan da wata shidda zaki haifo min wani babyn.
Zaro ido tayi tace nashiga ukku yanzu har ina da ciki wata ukku batare da na saniba?
Jan hancinta yayi yace toh kidai shirya ni d'in kinsan ba ma wasa bane.
Marairaicewa tayi tace toh ammah duka fa Ameer shekararsa ukku.
Toh ai ya ma kwana biyu ai na gama wasa duk bayan shekara biyu zaki dinga haihuwa Insha Allahu k'ara ma kishirya dan mijin nan naki yana da son yara, wlh zarah indai kece bazan damuba dan inaso inga kin haifar min yara kodan susamu irin tarbiyanki, dan halayyarki ce ta kirki tacanza min rayuwa, tabbas na yarda kud'i basu bane rayuwa, rayuwa medad'i itace aginata akan ilimi na addinin musulunci, duk kud'in mutum indai baida ilimi toh bai cika mutum ba yana da tauwaya a rayuwarsa, a kodayaushe ina k'ara gode ma Allah da yamallaka min ke a matsin matata tagari wlh wani lokacin har ji nake kamar ba zan iya rayuwaba in babu ke, zarah kece komai nawa, ina fata zaki cigaba da haifamin yara masu irin tarbiya da hak'urinki wad'anda duniya zatayi alfahari da su.
Rungumesa tayi kamar zata maidasa cikin ciki hawaye suna fita daga idanunta tace nagode sosai mijina Allah yabarmu tare, duk abinda kakeso toh nima shi nakeso dan ka riga ka zama ni nima nazama kai fatana Allah yabarmu tare har k'arshen rayuwarmu, ka gama min komai a rayuwata kaine silar dawowar duk wani farin ciki nawa, a kodayaushe bakina cikin yi maka addu'a nake dan addu'a ce kawai zanyi maka inbiyaka abubuwan da kakemin, kaduba kaga gidan da su mama suke zaune yanzu babba ne sosai kuma kai kamallaka masu, sannan duk wata sai ansafke masu kayan abinci, hatta su yaya rauda baka barsuba kullum cikin kyautata masu kake sannan.......cikin sauri yarima yasa hannu yarufe mata baki yace baby ya isa haka duk abinda nayi ma su abba cancantace tasa haka ko da ace bana aurenki zan iya yi masu fiye da haka, kukan ya isa haka dear indai ba so kike nima inyiba, cikin sauri tagirgiza kai tace a'a kar kayi,,,harshensa yasa yashiga lashe mata hawayen fuskarta bayan ya gama nan yashiga yi mata rad'a a kunne chan sai suka saka dariya gabad'ayansu, turesa zarah tashiga yi tace nak'i wayon naka ni kak'yaleni.
Rik'o hannunta yayi yace please dear kitaimaka min.
Tallabo kansa tayi tatura bakinta cikin nasa nan suka shiga kissing d'in juna kowa yana nuna ma d'an uwansa k'warewarsa cikin salon so daga k'arshe yarima suhail yajanyo blanket yarufesu.
_Laifin dad'i k'arewa_
_*Alhamdulillah* anan muka kawo k'arshen wannan novel mesuna *YARIMA SUHAIL* abinda muka fad'a daidai Allah yabamu ladar kurakuren da suke ciki Allah yayafe mana_
_Fatan alkhairi agareku dukkan masoyana naji dad'i kuma nagode ma Allah akan yadda wannan novel d'in yasamu kar6uwa sosai a wajenku_
_Duk wani wanda nata6a 6atamawa ina fata zai yafemin domin duk d'an Adam ajizine tsakanin harshe da hak'ori ma ana sa6awa balle tsakanin mutane, Allah yayafe mana gabad'ayanmu al'ummar musulmai_
_Daga k'arshe ina taya dukkan d'aukacin al'ummar musulmi murna akan wannan wata mai albarka da zamu shiga, ina fata Allah yabamu ikon shiga watan ramadan lafiya sannan yabamu ikon azumtarsa, ya ubangiji kasa muna daga cikin bayinka wad'anda zaka 'yantar a cikin wannan watan me albarka_
_Sis Nerja'art takuce a duk inda kuka kasance masoya,ππ_
_Comment_
*Nd*
_Share_
_Sis Nerja'artβπ»_
08, February 2025
Shuraihu Usman
jjjjj