Showing 90001 words to 93000 words out of 168813 words

Chapter 31 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt

08 Aug 2024

100532

kar kice haka dan Allah kifad'amin abinda yake faruwa nayi alk'awali zan taimaka miki.


Zarah kallonta tayi cike da gamsuwa da maganar jakadiya sannan takwashe duk makircin da akeyi mata tafad'a ma jakadiya,


Jakadiya jinjina kai tayi tace wannan ba aikin kowa bane sai na gimbiya sumayya,
Zarah cike da mamaki tace yanzu kina ganin itace zata yi min haka?
Jinjina kai jakadiya tayi tace tabbas itace dan nasan wacece gimbiya sumayya da mahaifiyarta fiye ma da haka zasu iya yi.


Zarah share hawayen fuskarta tayi tace toh wlh zan iya hak'ura da auren inkoma gidanmu.


A'a gimbiya kar kice haka bai dace kikaraya ba, mu munsan halinsu, kuma sumayya da kikaga yarima ya aura toh auren had'ine ba auren soyayya bane sukayi.


hatta shi kansa yarima da kike gani akwai abinda mahaifiyar sumayya take k'ullawa akansa wanda ita kanta sumayya bata saniba.


Zarah ido tazuba mata cike da mamaki.


Jakadiya tacigaba da cewa akwai wani lokaci da dada ta aikeni wajen sultana sadiya, lokacin da nashiga parlour bakowa har na juyo zan baro d'akin najuyo magana k'asa-k'asa a bedroom d'in sultana sadiya tsaye nayi lokacin da najuyo tana cewa so take gimbiya sumayya tahaihu idan yaron yafara wayau tanaso tabi kowace hanya dan ganin ta kawar da yarima inyaso mijinta abashi rik'on k'warya kafin jikan nata yagirma daga baya yazama shine sarkin gari, ta san idan yahau toh sai yadda taso mulkin gidan zai tafi, dan ta tsani mahaifiyar yarima taso ace itace tahaifi d'a namiji Wanda zai gaji garin ba mahaifiyar yarima ba, ina jin haka cikin sauri nafito nabaro part d'in gudun kar taganni dan nasan idan taganni toh bazata ta6a barinaba.




Zarah cike da rud'ewa tace daman haka matarnan take? Toh shi yarima baisan halintaba ya amince ya auri d'iyarta.


Murmushi Jakadiya tayi tace tabbas yarima yasan kad'an daga cikin halayyarta dan tun yana k'arami idan yaje part d'inta wahalar dashi take dan akwai lokacin da tata6a watsa mai ruwan zafi, tagargad'e ni da idan nafad'a ma wani sai tayi sanadiyar barina aiki, kasancewar nikad'aice lokacin da abun yafaru.


Toh ba'a gane taba? Cewar zarah.
Eh toh, yarima yana da wani irin hali wanda ba komai bane yake iya bud'e cikinsa yafad'aba wannan halinsane tun yana k'arami, kuma na tabbata shi kansa yana sane da abubuwan da tayi masa kawai dai ya sharene,
indai wajen makircine toh kala-kala matarnan ta iya dan ina tunanin dasa hannunta sumayya takeyi miki wad'annan abubuwan.


Zarah jingine kanta tayi cike da jin tausayin mijin nata, Jakadiya tace ranki yadad'e kigode ma Allah da basubi ta wata hanyarba dan ganin sun kawar da ke, koda basubin boka ammah sun san makirci kala-kala.


Jinjina kai zarah tayi cike da mamakin halin su sumayya, ahankali tace duk makircinsu basu isa suyi abinda Allah bai nufa ba, kuma ina neman kariya daga ubangijina, saidai bansan yadda zanyi inshawo kan yarima yafahimceniba.




Jakadiya tace kar kice haka ranki yadad'e kuma baidace kiga laifin yarima ba tunda duk baya makircinsu da suke miki baiyi tasiriba a garesa ammah a yanzu kiduba kiga har da sunansa da naki aka had'a kinga ai bakowa bane zai iya k'in yarda, yanzu dai abu d'aya zakiyi shine nake tunani kamar zai taimaka wajen ganin kin ku6utar da kanki, zarah kallon Jakadiya tayi tace wane abune please kifad'a min.




nan Jakadiya tace kice yatambayi guards d'insa sufad'i Wanda yashiga da baya nan tunda ke kince baki shigaba,
Zarah tace anya kina tunanin zai amince?
Eh insha Allahu ai ya aminta da su yasan bazasu ta6a yi masa k'aryaba,


Zarah jinjina kai tayi tace nagode sosai jakadiya, hak'ik'a kin taimakeni a lokacin da nake buk'atar taimako nakekai kukana ga ubangijina,


Jakadiya tace kar kidamu gimbiya har cikin raina nake jinki dan kece kikafi dacewa da yarima ba sumayya ba kuma ina fatan yakasance kece zaki fara aje mana magajin yarima.




Zarah saida gabanta yafad'i dasauri tagirgiza kai tace kar kice haka, sumayya ita tafi dacewa tahaihuwa da yarima.


'Yar dariya jakadiya tayi tace tuni tayi watsi da damanta koda haka mahaifiyarta taci buri itama ammah a yanzu k'addara ta riga fata,


Zarah cike da mamaki take kallonta tace ban fahimci abinda kike nufiba?
Murmushi jakadiya tayi tace kar kidamu dasannu zaki fahimta nan ba da dad'ewaba, jakadiya tana fad'in haka tamik'e tare da d'an rissinawa tace nabarki lafiya ranki yadad'e.




Zarah d'aga kai tayi tace nagode sosai jakadiya saidai ince Allah yabaki ladar abinda kikayi min.


Jakadiya murmushi tayi tace kar kidamu ai yi ma kaine, nidai fatana kirik'e sirrin maganar da nafad'a miki.




Zarah murmushi itama tayi tace insha Allahu babu wanda zai san maganar nan bayan mahaliccinmu sai ni da ke.


Jakadiya tace nagode, nan sukayi sallama tafita, zarah tsaye tayi tana tunani cike da jinjina ma sumayya da mahaifiyarta sannan daga baya tawuce tashige bedroom d'inta takwanta, nan hawaye suka cigaba da fita daga idonta tana tunanin hukuncin da yarima zai yanke mata akan laifin da ba ita ta aikata shiba, fashewa tayi da kuka tace ya ubangiji kakawo min d'auki, kuka tayi sosai saida taji kanta ya fara ciwo sannan tadaina haka taita juyi saman gadon daga k'arshe bacci yayi awon gaba da ita.






Yarima bayan zarah ta fita zama yayi saman gadonsa tare da dafe kansa cike da takaici, mamakin zarah ne yakamasa dan baita6a tunanin haka daga garetaba tun daga yanayin tarbiyarta, ya dad'e zaune yana jinjina lamarin dan abun ya d'aure masa kai sosai dan idan ya ce ba ita bace toh wanene zaiyi hakan?, tsaki yaja cike da takaici sannan yakwanta abu guda yatsaya masa a rai kalmar da tafurta ta nima ina da wanda nakeso, haka kalmar yaita jinta a kunnensa tana masa yawo har daga k'arshe bacci yad'aukesa..






A chan 6angaren sumayya kiran sultana sadiya tayi tana yin picking bata bari tayi ko sallama ba cikin jin dad'i tace ummah na aiwatar da komai kuma ina tunanin nasara a cikin aikin namu, daga chan 6angaren sultana sadiya dariya tayi tace gaskiya naji dad'i daughter ai ina fad'a miki ta ruwan sanyi zatabar gidannan dan makirci kala-kala babu Wanda ban iyaba idan akayi wani baiyiba sai acanza wata hanyar, cikin jin dad'i sumayya tace saisa nake k'ara sonki ummana dan duk abinda nakeso kema kinasonsa na rabbata yanzu yarima zai zama nawa ni kad'ai.
Murmushi sultana sadiya tayi sannan tace kar kidamu d'iyata farin cikinki shine nawa, saisa nake burin kihaifo min jika wanda zai gaji masarautar nan ammah kinkasa fahimtar inda nadosa, Indai kinsan kina yin planning toh kitaimaki kanki kidaina tun kan waccan munafukar tafara haihuwa,
Gaban sumayya saida yafad'i dan bata ta6a yin tunanin hakaba, ahankali tace hakane kuma ummah insha Allahu bama zata haihuba zata bar gidan.
Sultana sadiya tace na dai fad'a miki kirufa ma kanki asiri kidaina.
Cikin shagwa6a sumayya tace toh ummah na ji.
Uhm Allah yasa dagaske, cewar sultana sadiya.
Ameen ummana.
Yauwa toh yanzu kikwanta kiyi bacci dare keyi.
Toh ummah ko mi kenan sai kinjini, nan sukayi sallama suka kashe wayoyin.
Sumayya fad'awa tayi saman gadonta cikin murna tace yes nasan zuwa gobe waccan munafukar zata koma kongon gidansu, ahaka tayi bacci cike da farin ciki.








Cikin dare zazza6i da ciwon kai suka tashi zarah daga baccin da take nan taita juyi saman gadon daga k'arshe k'asa tasafka takwanta, ciwon cinta yake babu wanda zata iya kira dan ko hannunta kasa d'agawa tayi daga k'arshe, tana nan tana juyi ahaka aka kira sallar asuba.




Har aka gama sallah akan kunnenta ammah takasa tashi dakyar tasamu tamik'e tana dafa bango har tashiga toilet, saida tahad'a ruwan d'umi tayi wanka sannan tad'auro alwallah daga zaune tasamu tayi sallah sannan talalubo paracetamol tasha, nan saman darduman tayi kwanciyarta har saida gari yafara yin haske sannan tamik'e tajanyo alkyabbarta tasaka, cikin rashin k'warin jiki tafito duk wanda yaganta ya san batada lafiya, ko da kuyanginta suka gaisheta hannu kawai tad'aga musu taku take dak'yar tana dafa bango tana tsayawa tahuta ahaka ta isa part d'in yarima.


Tana murd'a k'ofar bedroom d'in yarima tsaye tayi tare da jingine kanta jikin k'ofar tana maida numfashi,


Yarima da daidai lokacin yasafka daga saman gadonsa tsaye yayi yana k'are mata kallo ko da cikin fushi yake da ita ammah hakan bai hana yaji wani iriba da yaganta cikin yanayin.


Zarah ahankali tatako tamatso kusa da shi, yarima d'aure fuska yayi yace meyakawoki wajena? Ko wani abun kikazo kik'ara shirya min?


murmushin k'arfin hali tayi sannan ahankali tace nasan kana jin haushina akan abinda yafaru, shuru tayi nad'an lokaci sannan tace ammah dan Allah ina neman alfarma guda,
saida takalli cikin idonsa sannan tacize le6e cike da dauriya tace kataimaka kayi bincike kafin kazartas da hukunci, katambayi guards d'inka sufad'a maka wanda yashigo part d'inka da bakanan dan ni wlh duk jiya ban shigoba sai dare, k'wallah ce tacika mata ido tace bawai na ce kar kad'auka ba ni bace sannan kuma ban hanaka d'aukar matakiba idan kagane niceba kawai ina tunatar da kai ne kar kayanke hukunci batare da kayi bincikeba, a kullum addu'a ta Allah yabayyanar da gaskiya bazan ta6ayin bak'in cikiba idan hakan yazama k'arshen tarayyarka da ni, saboda ni nasan gaskiya bata k'arewa saidai k'arya tak'are,


Yarima cike da mamaki yake kallonta koda ya san har cikin ransa ya san maganganun da tafad'a gaskiya ne ammah hakan baisa yanuna a fili ya aminceba, zarah dafe kanta tayi ahankali tace na barka lafiya juyawa tayi tana fara tafiya nan jiri yakwasheta tayi baya zata fad'i.




cikin sauri yarima yatarota tafad'o jikinsa, ahankali yafurta ya salam, saboda wani irin zafi da yaji jikinta saikace zafin garwashi, rikicewa yayi yama mance da abinda yafaru cike da damuwa yace zarah daman bakida lafiya? Me yake damunki? Lokaci guda yajero mata tambayoyin duk ya rud'e.


Zarah dak'yar tabud'e idonta tare da dafe kanta da yake sara mata, cikin muryar kuka tace kabarni inma mutuwa nayi babu abinda yadameka, wlh abinda akeyi min ya fi wannan ciwo kabarni kawai inmutu kowa yahuta, k'ila idan namutu zaka yarda da magana ta,
Yarima cike da rud'ewa yace kidaina cewa haka zarah, kifad'amin abinda yake damunki,


Zarah turesa tashiga yi cikin kuka tace ni kabarni wajen mamana zanje nasan su zasu fahimceni tunda sunsan abinda zan iya aikatawa da wanda ba zan iyaba.




Yarima rungumeta yayi a jikinsa yace kidaina cewa haka zarah, baisan lokacin da yayi su6ul da baka yace nima na yarda da ke.
Zarah idanuwanta suna lumshe batare da ta bud'eba tace dagaske ka yarda da ni?
Shuru yarima yayi yana mai nazarin maganar sai kuma chan yace eh.
'Dan guntun murmushi tayi sannan ahankali tace nagode.
Chak yarima yad'auketa yad'aurata saman gadon yakwantar da ita, wayarsa yad'auko yakira Dr feedoh (babbar likitace ta 6angare mata da take aiki a hospital d'insa) bayan sun gaisa yace kizo gida kisameni, cikin sauri tace toh ranka yadad'e, kashe wayar yayi tare da kallon zarah da taketa cize le6e tana girgiza kai daga ganin yanayinta kasan tana jin jiki, sannan yace ina zuwa, yana fad'in haka yafita
wajen guards d'insa yaje suna ganinsa duk suka duk'a suka kwashi gaisuwa,
yarima hannu kawai yad'aga musu sannan yakallesu d'aya bayan d'aya..........














_Comment_
*nd*
_Share_












_Sis Nerja'artโœ๐Ÿป_
๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘


_*YARIMA SUHAIL*_

๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘






_*Written By~Sis Nerja'art*_






_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_




https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/


*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ยฎ*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE ๐Ÿ˜˜ HEART TORCHING โค TEARS OF SORROWS ๐Ÿ˜ญ CURDLES ๐Ÿ™‚ GIGGLES ๐Ÿ˜ AND MARRIEGE THINK๐Ÿ’‘
*JUST GIVE US FOLLOW....*โœ”




_Wannan page d'in mallakin kine maman fodio hakik'a ke masoyiyace ta gaskiya saidai ince Allah yabar k'auna_




*PAGE* 4โƒฃ6โƒฃ




Kallonsu yayi d'aya bayan d'aya sannan yace jiya bayan na fita zarah ta shigo part d'ina?


Gaba d'aya shuru sukayi suna tunani sai chan d'aya daga cikinsu yace gaskiya bata shigoba,


Yarima ido yazuba mai sannan chan yace toh ko akwai wanda yashigo?
Nan ma shuru sukayi, Yarima yace kuyi tunani dai.


Chan sai suka kalli juna sai suka eh toh ranka yadad'e gimbiya sumayya ta shigo bayan magrib, gaskiya inba itaba babu wanda yashigo.


Yarima jinjina kai yayi yace kun tabbata? Gabad'ayansu sukace eh ranka yadad'e.
Yarima baice komai ba yawuce yashige,
Koda yashiga parlour saman kujera yazauna tare da dafe kansa mamakin sumayya duk yacikasa ahankali yace idan na fahimta toh duk wani abu da yake faruwa toh dasa hannun sumayya a ciki, toh meyasa sumayya take yin haka? Meyasa takeso taga ta yi silar mutuwar auren zarah? Anya ba da sa hannunta aka zuba poison a abincinba? Wani huci yafitar mai zafi sannan yace koma me kenan da sannu gaskiya zatayi halinta ba zan zargetaba, yana nan zaune a wajen wayarsa tafara ringing ganin mai kiransa yasa yai picking tare da cewa Doctor kin iso?
Daga chan 6angaren tace eh ranka yadad'e gani a waje dogarawa sun hanani shigowa.
Yarima yace ohk, ba d'aya daga cikinsu wayar.
Toh ranka yadad'e, cewar doctor feedoh, nan tamik'a ma dogari d'aya waya, yana d'auka Yarima yace kubarta tashigo.
Jin muryar Yarima yasa yarissina kamar yana gabansa sannan cikin girmamawa yace toh ranka yadad'e angama.
Yarima kashe wayarsa yayi tare da mik'ewa yashiga bedroom d'in tsaye yayi bakin gadon yana k'are ma zarah kallo da gabad'aya ta galabaita, ahankali yazauna gefenta tare da dafa kanta yace ya jikin?
Gyad'amai kai kawai tayi,


Mik'ewa yayi yafito waje yasa d'aya daga cikin guards d'insa yaje yazo mai da doctor feedoh, cikin sauri yatafi.


Nan Yarima yadawo parlour yazauna yana jiransu, bayan minti biyar sai ga guard d'in tare da doctor feedoh sun shigo, duk'awa guards d'in yayi yace gata ranka yadad'e,
'Daga masa hannu yarima yayi,
Fuskarsa d'auke da murmushi yace u ar wlcm Dr.
Dr feedoh saida tazauna sannan tace thanks Dr, ya mai jikin.
Alhmdllh yace tare da mik'ewa yace bismillah mushiga daga ciki kidubata,
Ohk sir, cewar dr feedoh nan yarima yawuce gaba tana biye da shi har cikin bedroom d'insa, daga gefen da zarah take kwance yazauna, kallonta yayi da tazuba ma Dr feedoh ido, ahankali yace ga doctor nan zata dubaki.
Fuskar Dr feedoh d'auke da murmushi tace sannu gimbiya, ya k'arfin jikin naki?
Zarah ma d'an guntun murmushi tayi cikin k'arfin hali tace Alhmdllh.
Dr matsowa tayi tana fiddo kayan aikinta daga cikin jakka tace ranki yadad'e ko zaki iya fad'amin abinda yake damunki?
Zarah kallon yarima tayi da shima yatsareta da ido, shafa kanta yayi sannan yace kidaure kiyi mata bayani kinji? d'aga mai kai tayi alamun toh, yana fad'in haka yamik'e yace doctor bari inbaku waje.
Doctor feedoh murmushi tayi cikin girmamawa tace a'a ranka yadad'e kayi zamanka ka ga inda na6ace sai kataimaka min.
Murmushi yayi yace kar kidamu ai nasan aikinki, bakida matsala, yana fad'in haka yafita yakoma parlour


Yana fita doctor feedoh gefen gadon tazauna, fuskarta d'auke da murmushi tace ranki yadad'e kamar da me dame kike ji?
Ahankali zarah tabud'e baki tace zazza6i da ciwon kai.
Dr rubutawa tayi tace bayansu babu abinda kuma kikeji?
Zarah shuru tayi kamar tana tunani sai chan tace sai kuma yawan kasala da bacci, jinjina kai Dr tayi tace bayansu bakya tashin zuciya?
Girgiza kai zarah tayi.
Nan Dr tarubuta sannan tace toh kina cin abinci?
Ba sosai ba, cewar zarah.
Dr idon zarah d'aya taduba sannan tad'auko wata roba tamik'a mata tace ko zaki taimaka kiyo fitsari nan ciki, saboda akwai awon da nakeso inje yanzu inyo.


Zarah kar6a tayi tamik'e dak'yar, ahankali take tafiya har taje toilet d'in yarima, nan tayo fitsarin tafito tamik'a ma doctor, kar6a Dr tayi ta aje sannan tace ranki yadad'e kiyi hak'uri munason mud'an d'ibi jininki kad'an.


Zarah bata musaba tamik'a hannunta tare da runtse idonta nan Dr feedoh tad'ibi jinin sannan tamik'e tace bari inje inhad'o miki result d'in.
Gyad'a kai kawai zarah tayi.
Dr ko da tafito a parlour tasamu yarima kallonsa tayi fuskarta d'auke da murmushi tace ranka yadad'e munyi duk abinda yadace yanzu zanje inyi mata test zuwa anjima kad'an insha Allahu zan dawo da result,


Jinjina kai yarima yayi sannan yace toh bakomai Dr Allah yamaidoki lafiya.
Ameen tace sannan tawuce tafita.


Bayan ta fita yarima mik'ewa yayi yashiga bedroom d'in, kallon zarah yayi da take lumshe ido alamun bacci zatayi hannunta yaduba sannan yace baby bari ind'an sa miki drip,
Zarah batace komai ba, kalman babyn da yakirata da shi takemata yawo a cikin kunnenta dan wannan ne karo nafarko da yakirata da hakan,
Shima kansa yarima saida yaji wani iri ammah yashare nan yahad'a drip d'in yasa mata, sannan yawuce yashiga bathroom dan yayi wanka.




Lokacin da yafito zarah har tayi bacci dan haka yashirya sannan yakomo gefenta yazauna yana ganin yanayin yadda ruwan yake shiga jikinta.




Bayan awa d'aya sai ga Dr feedoh tadawo, nan yarima yabada izini abarta tashigo bayan ta shigo fuskarta d'auke da murmushi tace ranka yadad'e albishir nazo maka da shi kuma ina fatan samun goro daga wajenka.
Kallonta yarima yayi cikin rashin fahimta sannan yace albishir kuma?
Har a Lokacin fuskarta d'auke da fara'a tace eh ranka yadad'e.
Yarima yace ohk, ina jinki.
Dr feedoh kallon zarah tayi da tad'an bud'e idonta alamun ta farka tasakar mata murmushi sannan tace madam tana d'auke da juna biyu.
Yarima kalmarce yaji tana yawo acikin kunnensakamar a mafarki, Kallonta yake yace me kikace?
Murmushi Dr tayi sannan tace tana d'auke da ciki na tsawon wata ukku da rabi (14wks) kenan, nan tamik'a masa result d'in tare da takardar magani.
Yarima kar6a yayi ya duba sannan ya jingine kansa a jikin gadon tare da lumshe idonsa yana jin wani irin nishad'i a cikin ransa ahankali yace Alhmdllh, Allah nagode ma, nan yabud'e idonsa yasafkesu akan zarah da take kallonsa ammah bata gane abinda ake nufiba.


Kallon Dr yayi fuskarsa d'auke da murmushi yace nagode doctor tabbas kinmin babban albishir kuma dole inbada tuk'uici, ammah abun mamaki ya akayi har yakai tsawon wannan lokacin ammah ban ganeba?


Murmushi Dr tayi sannan tace kuma doctor kana saurin fahimtar na wasu matan ammah kai naka sai gashi cikin ikon Allah, Allah ya 6oye abunsa har tsawon sati goma sha hud'u (14 wks) sannan yabayyana kuma har da k'arin ba wani laulayi takeyi ba.




Jinjina kai yarima yayi tare da kallon zarah da idanuwanta suke rufe yace hakane, Allah shi yake ajiyarsa kuma sai ya so yake bayyanata, yana fad'in haka yamik'e yaje yabud'e wardrobe d'insa yad'auko cheque yacike sannan yazo yaba Dr feedoh yace ga goron albishir d'inki.
Dr feedoh d'an rissinawa tayi takar6a cikin jin dad'i tace

08, February 2025
Shuraihu Usman

jjjjj

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login