Showing 162001 words to 165000 words out of 168813 words

Chapter 55 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt

08 Aug 2024

100542

fa tana nan?
Batare da ta juyoba tace eh bismillah kazauna bari inmata magana, tana fad'in haka tawuce tanufi part d'in ummi tasanar da ita zuwan bak'on sannan tafito tawuce room d'inta.


ummi koda tafito cikin jin dad'i tace oyoyo yau ga salim mutanen agadaz dakansa ya kawo mana ziyara.


Murmumushi wanda takira da salim yayi tare da d'an zamowa daga kujerar da yake zaune yace ummi ina wuni.


Lafiya lou salim ya gida da mutanen gidan dafatan kowa yana lafiya.
lafiya lou ummi.
masha Allah toh ya k'arin hak'uri? Ayi dai hak'uri ban samu nadawo ba bayan sadakar ukku, ni ina ji tun ma lokacin rabona da agadaz.
Alhmdllh ummi ai bakomai.
masha Allah toh Allah yajik'anta, Allah sarki khadija mutuniyar kirki Allah dai yasa ta huta, ina yaran naku ina fatan suna lafiya?
Duk suna lafiya.
toh masha Allah, Allah yaraya mana su,


Ummi kira tashiga k'walah ma sumayya, fitowa tayi sanye da hijabi a jikinta tace ummi gani.
murmushi ummi tayi tace sumayya wannan shine bak'on nawa matsayin yaya yake a wajen su yarima kije kisa su kuyanga zinnira sushurya masa abinci.
Kallon bak'on tayi da a yanzu ma yatsareta da ido ahankali tace sannu da zuwa ina wuni?
Murmushi yayi yace lafiya lou ya gida?
Batare da ta bashi amsaba tawuce taje tabada umurni akawo masa abinci daganan tawuce wajen dada.






Cika masa gabansa akayi da abinci iri-iri ci yake ammah gabad'aya hankalinsa yana ga k'ofa.


Bayan ya gama kallon ummi yayi yace ummi wai ina prince? Kinsan bana k'asar akayi bikkinsu shi da rahama.


Murmushi ummi tayi tace duk suna nan lafiya lou yanzu ma zaka ganshi dan na fad'a masa zakazo, ina fata dai ka dawo k'asarka ta haihuwa kenan bazaka koma india ba, haba salim mutuwa ai bata wuce kowaba yakamata ace zuwa yanzu ka cire khadija aranka tunda wanda yabaka ya kar6i kayansa shekara biyu da wani abu fa kenan yanzu, kadaure kayi aure karik'e 'ya'yanka ukku wajenka suma sutaso hannun iyayensu, dan su yaya munir hankalinsu ba a kwance yakeba basuda buri dayawuce suga ka saki ranka ka canza aure, d'azun koda yakirani a waya cewa yayi ink'ara kwatanta maka, kaifa salim ba yaro bane kai yakamata kakwatanta ma wasu.


Ajiyar zuciya salim yasafke yace insha Allahu ummi zanyi aure dan a lokaci guda wata ta fara canza min tunani.


Cikin jin dad'i ummi tace masha Allah wace me sa'a ce haka?


Dariya salim yayi yace ummi kuma a wannan garin naku daga zuwana yau d'innan.
Gyara zama ummi tayi tace salim fad'amin inda take insha Allahu zanje dakaina insami iyayenta.


Dariya salim yayi yace ummi kima kwantar da hankalinki ba wata bare bace nidai fatana Allah yasa ba matar aure bace.
Toh Alhmdllh tunda 'yar gida ce wacece ita?


Duk'ar da kansa yayi alamun jin kunya sannan yace ummi ba wata bace face wadda nagani nan wlh ummi tunda nashigo taburgeni Allah dai yasa batada aure.


Murmushin jin dad'i ummi tayi tace in na fahimceka sumayya kenan kake nufi?
Eh ummi ita indai zaku bani ita toh wlh na amince zanyi aure.


Cikin jin dad'i ummi tace toh sumayya dai ta ta6a aure ammah a yanzu basu tare sa mijin nata Indai har kana sonta tsakani ga Allah toh nikuma insha Allahu zan sameta muyi magana.


Shima Cikin jin dad'i yace wlh ummi ina sonta kuma zan kular muku da ita, da gobe naso inkoma ammah a yanzu na canza ra'ayi har sai ta amince sannan zan bar garin nan.


Jinjina kai ummi tayi alamun gamsuwa sannan tace toh Allah yashige mana gaba.
Salim yace Ameen.


Koda yarima yashigo zama yayi sukasha fira cikin jin dad'in ganin d'an uwannasa kuma babban yaya dan dama tun yana karatu a india ummi tahad'ashi da shi.
Yarima fita sukayi tare suka zagaya gari yanuna masa wurare sai dare suka dawo gida.






Bayan sallar isha'i sumayya zaune take ta gama shirin bacci tana duba wasu addu'o'i.
Ummice taturo k'ofan tashigo tare da yin sallama.


Murmushi sumayya tayi ta amsa mata tare da fad'in sannu da zuwa ummi.


Yauwa daughter nan tazauna bakin gadon tare da kallon sumayya tace daughter daman bakiyi bacci ba?
Eh ummi ammah yanzu nake shirin yi.
Ohk ya yi kyau ammah inaso kitaimaka kiban aron hankalinki zamu d'anyi magana, gyara zamanta sumayya tayi tace toh ummi.


Ummi ma fuskantarta tayi tace sumayya aganina yakamata ace wannan lokacin kinyi aure indai kina da wanda kikeso yake sonki saidai idan babune shine sai kizauna har sai Allah ya kawo.
Murmushi sumayya tayi cikin jin kunya sannan tace ummi ai har yanzu babu wanda mukeson juna.
Murmushi itama ummi tayi sannan tace toh sumayya Allah yakawo, sai kuma tayi shuru kamar metunani sai chan tace am yauwa sumayya d'azun salim ya tuntu6eni akan maganarki ya nuna min yana sonki sosai indai zaki bashi dama sai yagabatar miki da kansa.


Gaban sumayya saida yafad'i cikin damuwa tace ummi ya za'ayi in amince masa daga ganinsa ba irina bane ko kin mance abubuwan da na aikata kuma fa doctor ya ce ba zan ta6a haihuwa ba taya kike tunani zai iya aurena,,,,tak'arashe maganar hawaye suna zuba daga idanunta.


Ummi cike da tausayinta tarungumota jikinta tace sumayya kidaina cewa haka tunda kin tuba ai Allahu gafururrahim ne, sannan da kike maganar haihuwa kikwantar da hankalinki nasan salim Indai yana sonki toh zai iya aurenki ahaka dan shima yana da yara ukku marayu da mahaifiyarsu ta mutu tabari shekara biyu da wani abu kenan kizauna kiyi tunani ko ma ince zuwa gobe kibashi dama kuhad'u kuyi magana dan jibi yakeson barin garin, ammah Indai baiyi mikiba kar kiji komai kisanar da ni kinji ko?


'Daga kai sumayya tayi nan ummi tamik'e tace kikwanta kiyi bacci kar kisa damuwa a ranki kinji ko?
Ahankali tace toh ummi.
Murmushi ummi tayi tace sai dasafe dota.


Bayan ummi ta fita sumayya zama tayi taita tunani akan maganar ummi ta dad'e ahaka sannan dagabaya takwanta tai bacci.




Wanshe kare wajen 11am bayan ta gama breakfast fitowa tayi parlour dan tayi kallo, zaune ta tadda mutum shi kad'ai yana kallo, ganinta yasa salim yazuba mata ido, sumayya bataji dad'in had'uwarsuba ahankali tace ina kwana? Amsa mata yayi fuskarsa d'auke da fara'a.
Juyawa tayi zata koma room d'inta nan taji muryarsa ya ce please sumayya in ba damuwa kiban dama yanzu muyi magana.


Tsaye tayi tai shuru batare da ta juyoba, ahankali yak'ara cewa please.


Juyowa tayi batare da tayi magana ba tadawo tazauna bisa d'aya daga cikin kujerun da suke parlourn.
Salim tashi yayi yakoma bisa kujerar da take saitinta yazauna, kallonta yayi da take wasa da yatsun hannunta yai murmushi sannan yace hajiya sumayya ina fata dai ummi ta yi miki bayani akan komai.


Shuru sumayya tayi, ganin haka yasa yace toh ammah duk da haka bari ink'ara miki bayani da kaina agaskiya sumayya tunda naganki jiya naji k'aunarki ta shiga raina, ina sonki tsakani ga Allah idan kin amince sai kiban dama in nuna miki irin son da nake miki dan ni har ga Allah aurenki nakeson yi.
Batare da ta d'ago kantaba tace ummi bata fad'a maka na ta6a aureba?
Kar kidamu indai wannan ne toh ba matsala dan nima na ta6a aure shekara tara kenan rasuwa matata khadija tayi muna da yara ukku, Al-ameen shine babba shekararsa takwas sai Amina shekara shidda sai autansu Sadiq shekara ukku, indai har kin amince zaki zauna da marayu kikasance uwa agaresu toh insha Allahu bazaki ta6a samun matsala daga garemuba zamu zauna da ke tsakani ga Allah, dan ni tun mutuwar matata ban ta6a tunanin zan k'ara son wata maceba ammah sai gashi cikin k'anganin lokaci na fad'a tarkon sonki.


Cikin tausayi sumayya tace Allah sarki Allah yajik'anta su kuma Allah yaraya su,
Ameen nagode saura inji daga gareki.
Sai a lokacin tad'ago kai takallesa tace ammah fa ni bana haihuwa zaka iya zama da ni ahaka.
Murmushi yayi a karo na biyu sannan yace kar kidamu sumayya ni naji na amince ina sonki kuma muna da su Sadiq gasunan zan mallaka miki su sugama 'ya'yanki halak malak.


Sumayya har cikin ranta taji dad'in maganar da yayi ko bakomai itama yanzu zata fara sabuwar rayuwa....murmushi tayi masa a karo na farko sannan tace kabani lokaci zanyi tunani.


Marairaicewa yayi yace please kitaimaka kizartas da hukunci yau dan gobe nakeson barin garin saboda wani aiki da nabaro kinsan 'yan kasuwa.


Shuru tayi nad'an lokaci sannan tace shikenan zuwa anjima zaka ji ni.
Murmushin Jin dad'i yayi yace toh Allah yasa inji alkhairi.
Ameen tace tare da mik'ewa zata wuce d'akinta har ta fara tafiya yakira sunanta, a nutse tajuyo takallesa,
Marairaicewa yayi yace please ataimaka atausaya min kar ayanke min hukuncin da ba zan iya d'aukaba.
Yanayin yadda yai maganar ya bata dariya nan tajuya tashige d'akinta.




A ranar taje tasamu ummanta tafad'a mata maganar da sukayi da salim, sosai sultana sadiya tanuna farin cikinta tace na tabbata sultana bilkisu bazata ta6a za6a miki abinda zai cutar da keba koda salim d'an uwantane kuma jiya sun shigo tare da yarima mungaisa na yaba da hankalinsa, Indai ya yi miki toh ki amince ki auresa.
Cike da gamsuwa da maganar mahaifiyartata tace toh ummah nagode sosai Allah yaza6a abinda zaifi zama Alkhairi
Ameen sultana sadiya tace nan suka d'an ta6a hira da d'iyartata sai bayan azuhur sannan sumayya takoma part d'in ummi.


Bayan sallar la'asar sumayya ta shaida ma salim ta amince sosai yanuna farin cikinsa tare da yi mata godia, nan suka zauna sukasha hira sama-sama dan rabin hirar duk shi yakeyinta, musanyar number waya sukayi.


Koda akayi sallar isha'i haka yakirata sukasha hira saida yasan yadda yayi tad'an saki jikinta da shi har wajen k'arfe goma na dare suna tare.
Ummi taji dad'i sosai da taga sun amince ma juna.


Hatta memartaba, dada, sultan abbas, sultan ahmad aranar sukasan da maganar salim nan sukayi musu fatan alkhairi.




Washe gari saida suka k'ara gaisawa sosai da sumayya sannan yai musu sallama yakoma tare da yi mata alk'awali zai dawo ba da dad'ewaba, a mota koda yarima zai kaisa airport labarin sumayya kawai salim yake bashi shidai yarima saidai yayi murmushi nan yai musu fatan alkhairi shima.


Tun daga ranar soyayya mai k'arfi ta k'ullu tsakanin sumayya da salim dan ko da yakoma saida yasanar da danginsa nan suma sukayi murna tare da yi masa fatan alkhairi.
Kusan kullum sai ya bata yaransa a waya sunsha hira sosai da sumayya, ita kanta har mamakin kanta take dan bata ta6a tunani zata iya son waniba bayan yarima ammah sai gashi lokaci guda salim ya canzata.




_________________


A lokacin da cikin zarah yacika wata tara cif kulawa sosai take samu a kowane 6angare yarima ko bayaso yana nisa da ita ko da ace yana wajen aiki toh suna manne da juna a waya, bayan 30 minutes batare da ya kirata ya tambayi lafiyartaba.
Kuyanginta ma basu yin nisa da ita indai yarima baya nan dan idan yadawo yaganta ita kad'ai fad'a yake musu sosai, saidai idan bacci zatayi shine take sallamarsu takwanta.



_*BAYAN SATI BIYU*_


Zarah zaune take gefen yarima inda gabanta plate d'in apple ne aje ammah ba ci takeba kad'an-kad'an ta cije le6e, kallon yarima tayi da yake cike wasu files, rik'o file's d'in tayi nan yad'ago kai yakalleta, murmushi tasakar masa tace hearty ka aje hakanan kahuta man tun d'azun fa kaketa abu d'aya kaga dare ya yi kazo muje mukwanta zuwa gobe sai ka ida..


Shima murmushin yamaida mata sannan yace sorry baby ai na kusan gamawa gobe nakeso inje inyi submitting d'insu kiban minti goma kinji?
Kwantar da kanta tayi a kafad'ansa tace toh shikenan hearty ammah minti goma kawai nabaka,
Ohk angama ranki yadad'e.




Bayan ya gama kallonta yayi yace baby muje mukwanta.
Mak'e kafad'a tayi tace ni saidai kad'aukeni mutafi.


Hancinta yaja yace shikenan baby as you wish.


Koda sukaje bedroom Kwantar da ita yayi sannan shima yakwanta, juyawa tayi chan gefen tana murmushi bata ankaraba sai ji tayi ya rungumota ta baya, cikin kunnenta ahankali yarad'a mata baby yau guduna akeyi?
Juyowa tayi takallesa tare da marairaicewa tace bahaka bane hearty wlh ji na nake yau duk wata iri,
Kwantar da kansa yayi a k'irjinta yace baby daman tun d'azun da naga yanayinki nace bakida lafiya ammah kikace lafiyarki lau.
Shafa sumar kansa tayi tace ni lafiya ta lau hearty.
Toh bari ingani idan kina da lafiyar ganin ya d'age mata riga yasa tayi saurin cewa dan Allah kabarni kar kayimin komai.
Murmushi yayi yace toh sarkin tsoro ni ba abinda zanyi miki lafiyar babyna kawai zan duba.
Nan yashiga shafa cikinta tamaida idanunta talumshe tana jin sauk'in ciwon da takeji daman tana daurewane dan kar ta tayar mashi da hankali, ahaka bacci medad'i yai awon gaba da ita.


Yarima ma gefenta yadawo yakwanta tare da rungumota jikinsa.


Cikin baccin ne taji kamar wani abu yana tsikararta firgit tayi tafarka tana jin wani irin ciwo tun daga cikinta zuwa mararta, ahankali tazame jikinta tasafko k'asa tazauna tana murk'ususu nan da nan tafita hayacinta sai hawaye, jin ciwon ba mek'arewa bane yasa tafara kiran sunan Yarima da yake baccinsa.


Cikin bacci yaji ana kiransa ahankali yabud'e idanunsa ganin zarah yayi a k'asa tana ta murk'ususu cikin sauri yasafko daga saman gadon yazo inda take tare da rik'ota cike da tashin hankali yace zarah lafiya?


Hawaye suna fita daga idanunta tajawo hannunsa tad'aura saman mararta, dak'yar tabud'e baki tace ciwo.
Cikin tashin hankali yace bari inzo muje hospital ina tunani haihuwar ce,,,tashi yayi yacanza kaya sannan yad'auko mata zane da hijab yasaka mata, jakkar da suka tanada ta haihuwa yad'auko cikin sauri yax'auko key d'in motarsa sannan yad'auki zarah yafito.


Guards d'insa k'arfan jakkar da take hannunsa sukayi nan suka take masa baya har wajen mota, a back sit yasakata sannan yabud'e mazaunin driver yashiga, kallon guards d"insa yayi yace kar su biyosa, wuta yaba motar tun kan ya isa gate yafara horn cikin sauri megadi yazo yabud'e masa yafita daga masarautar.




Gudu yake sosai cike da tashin hankali ga zarah da take kwance baya tana ta kuka da salati, cikin k'ank'anin lokaci ya isa hospital d'insa, tun kan ya isa yakirasu yasanar da su zuwansa dan haka suna isa yatarar da su suna jiransa nan aka fito da zarah cikin sauri aka turata zuwa labour room.




Dr leemah ce tatsaya kanta, yarima ko gefenta yatsaya yana taimaka mata cike da tausayin matar tasa, zarah ta sha wahala dan gabad'aya gidansu babu sunan wanda bata kiraba, yarima waje biyu yaraba hankalinsa da wajen lallashin zarah sai wajen ceto babynsa, cikin ikon Allah batafi minti sha biyar tana nak'uda ba tahaifo shantalelen d'anta, Dr leemah ce tayi saurin d'aukesa tamik'a ma wata nurse dan tagyarasa, inda yarima yakoma wajen zarah yana mata sannu batare da ya ga abinda aka haifar masaba.


Hawaye suna fita daga idanunta tana maida numfashi sama-sama ahaka dr leemah tagyarata.


Koda nurse d'in tagyara yaron Dr leemah tafara kar6ansa tana yaba kyaunsa tana cewa wannan prince ne sak yabiyo.


Sai a lokacin yarima yamik'a hannu yakar6esa murmushin jin dad'i yayi tare da furta Alhmdllh, nan yai masa addu'a da kiran sallah, zuba ma yaron ido yayi cike da so, zarah ahankali talek'o yaron da yake hannun yarima saida gabanta yafad'i batasan lokacin da ta furta masha Allah ba dan yaron kyakkyawane kamar daddynsa, kallonta yarima yayi yana murmushi yace kinga kyautan da ubangiji yabamu ko?


Itama murmushin tayi tace masha Allah yanzu nan ni na haifesa?


Yanayin yadda tayi maganar ta ba yarima dariya, murmushi yayi yace eh man kece, ammah ai da ni yake kama.


Itama murmushin tayi cikin jin dad'i tace saidai kai d'in dai.


Nan su Dr leemah suka taimaka mata tatashi tayi wanka, a cikin daren yarima yakira sultana bilkisu yashaida mata, da har ta ce gasunan zuwa asibitin nan yashaida mata ai ta haihu cikin k'oshin lafiya yanzu dan dare yayi ammah tun da asuba zasu dawo.


Sosai ummi tanuna farin cikinta tare da addu'an Allah yaraya.


A nan hospital d'in su yarima suka kwana, tun asubar fari sultana bilkisu takira sultana sadiya tashaida mata sosai sultana sadiya tanuna farin cikinta inda tasa ma'aikatanta su d'aura ruwan wanka kafin su zarah su iso.


Dada ma koda taji labari murna tayi sosai har da hawayenta zataga jinin suhail d'inta shi kansa memartaba ya nuna farin cikinsa sosai,
Kan kacemi gabad'aya masarautar ta san da maganar haihuwar zarah.
gabad'aya su dada suka taru bayan sunyi sallar asuba suna jiran dawowarsu yarima cike da tsaguwa da son ganin babyn.








_Comments_
*Nd*
_Share_










_Sis Nerja'artโœ๐Ÿป_
[5/3, 7:55 PM] Sis Naj Atu: ๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘


_*YARIMA SUHAIL*_

๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘






_*Written By~Sis Nerja'art*_






_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_




https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/


*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ยฎ*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE ๐Ÿ˜˜ HEART TORCHING โค TEARS OF SORROWS ๐Ÿ˜ญ CURDLES ๐Ÿ™‚ GIGGLES ๐Ÿ˜ AND MARRIEGE THINK๐Ÿ’‘
*JUST GIVE US FOLLOW....*โœ”




_Sak'on gaisuwa da jinjinar bangirma agareku masoyana, nagode sosai da soyayyarku agareni, hak'ik'a kun nuna min kulawa sosai banda abinda zance maku saidai addu'a Allah yasaka da alkhairi Allah yabar k'auna.๐Ÿ˜๐Ÿ˜˜_


๐Ÿ’๐Ÿ’๐Ÿ’


_*Yayata ko ma ince Auntyna jiddah mumyn zarah bazan ta6a mancewa da keba a rayuwata ke d'in tadabance saidai ince Allah yabar wannan zumuncin namu๐Ÿ’ž*_


๐Ÿ’“๐Ÿ’“๐Ÿ’“


_~M.B.A nd Mu'az banda abinda zance maku saida addu'an fatan alkhairi๐Ÿคฉ~_


๐Ÿงก๐Ÿงก๐Ÿงก


```My dala dole ingaisheki kuma in jinjina miki da namijin k'ok'arin da kike Allah yabar k'auna๐Ÿ˜```


๐Ÿ’•๐Ÿ’•๐Ÿ’•


_Intelligent Writer's ni kaina bansan abinda zan ce ba akan k'warin guiwar da kuke bani saidai ince Allah yak'ara d'aukaka mana k'ungiyarmu ya albarkaceta, Allah yak'ara had"a kanmu gabad'ayanku na gaisheku, Aunty maryam Allah yaraya mana newborn baby muhammad๐Ÿฅฐ_


๐Ÿ’˜๐Ÿ’˜๐Ÿ’˜






_*S.A.N 4EVER na jinjina maku tagwaye ukku ku d'in na daban ne acikin zuciyata๐Ÿ˜๐Ÿ‘*_




๐Ÿ”š๐Ÿ”š๐Ÿ”š๐Ÿ”š๐Ÿ”š๐Ÿ”š




*PAGE* 7โƒฃ0โƒฃ




Yarima saida yai sallar asuba sannan yad'auko zarah suka dawo gida, staffs d'insa wad'anda sukayi night duty zuwa suka dinga yi suna tayasa murna,, a mota zarah da take rungume da babyn ido tazuba masa tana kallo cike da sha'awa, yarima da yake tuk'i juyowa yayi yakalleta yai murmushi har zaiyi magana sai kuma yafasa.


Lokacin da suka isa gida suna fitowa daga mota su dada da suke tsaye suka iso inda suke, sultana sadiya ce tafara kar6an babyn cikin jin dad'i tadubasa tai masa

08, February 2025
Shuraihu Usman

jjjjj

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login