Showing 75001 words to 78000 words out of 168813 words

Chapter 26 - YARIMA SUHAIL COMPLETE BY SIS NERJA'ART .txt

08 Aug 2024

100528

kuma cikin zuciyanta tace bayan basonki yakeba bai damu da ke ba to akan me zaiyi kishinki? Jinjina kai tayi k'wallah duk ta cika mata ido tace hakane kuma, wayarta tad'auka takira safiya nan tashaida mata da ta tafi gida.




Yarima ma zama yayi saman cushin d'in parlournsa yadafe kai hango zarah da wannan mutumin abokin shaheed yayi sai murmushi yake ma zarah, da k'arfi zuciyansa tabuga jingine kansa yayi tare da lumshe idonsa dan shima ya san yayi namijin k'ok'ari da bai d'au matakiba akansa kuma bayason zarah tad'auka ko ya fara damuwa da ita ne, bugu da k'ari a gaban idonsa aka aiwatar da komai babu ta yarda za'ayi yazargeta.
Ahankali yaja tsaki cikin ransa yace toh wai ma akan me zan damu? Gefe guda na zuciyansa yace dole kadamu tunda akwai aurenka abisa kanta.
Kiran sallar magrib ne yasa yamik'e yanufi toilet dan yad'auro alwallah.




wajen k'arfe tara zarah na shirin kwanciya safiya tashigo, kallonta zarah tayi tace kar dai kicemin yanzu kika dawo?
No tun d'azun muka dawo ina cikin gida wajensu mamina, kinsan wani abu?
Girgiza kai zarah tayi.
Wani guy ne yatambayeni wai dagaske kina da aure, inkuma baki da aure toh please inbasa number d'inki, bansan lokacin da nazaro idoba nace karufa min asiri kar kaja prince yasa arufeni, ai matarsa ce.


Shima guy d'in bakiga yadda yarikiceba wai wlh bai d'auka matar aure bace kuma matar prince ya ce dan Allah inbaki hak'uri wlh da ya sani da bazai miki maganaba, kuma ya ce zai samu prince yabasa hak'uri nace ai da kuwa hakan ya fi.


Murmushi zarah tayi tare da kwanciya tamaida idanuwanta tarufe cike da kewar yarima ammah ko bakomai ta d'anji sanyi a ranta da tasakashi a idonta, nan itama rahma takwanta.




Gimbiya sumayya kallon yarima tayi da yake kwance ita kuma tana gefensa tace yarima Allah ya taimaki 'yan matan wajen nan da basuzo wajenkaba dan na lura da kallon da suka dinga yi maka wlh da sunzo da sai munyi bala'i.
Shine katafi ban saniba saidai nawaiga naga bakanan, kuma fa ko lik'i baka shigo kayi masuba.




Murmushi kawai yarima yayi tare da rungumota jikinsa, dasauri sumayya takallesa tace a gajiye fa nake yau, yarima kallonta yayi sannan yamaida idanuwansa yalumshe ganin haka yasa sumayya tagyara kwanciyarta ahaka bacci yayi awon gaba da su.




Ranar juma'a safiya jan zarah tayi sukaje part d'in ummi ammah zarah kasa sakin jiki tayi cikin dangin yarima daga uhm sai uhm-uhm daga k'arshema tattarawa tayi tadawo turakarsu.




Da dare duk inda zaka nufa a cikin masarautar shirin tafiya dinner akeyi, mutane duk sun saka material sunyi kyau.


sumayya tare da rahma sukaje shago akayi musu shiri suka fito gwanin kyau musamman ma amarya rahma.




Wajen 8:30pm zarah tagama shirinta cikin anko d'inta tufke gashin kanta tayi sannan tasaka head d'inta tayi gwanin kyau kallabin tayafa a kafad'arta sannan tazura takalminta tad'auki hand bag d'inta tana fitowa sukayi kici6is da safiya da wata 'yar uwarta tsaye sukayi suna kallonta itama kallonsu tayi fuskarta d'auke da murmushi tace masha Allah 'yan mata kunyi kyau sosai.
Haba Mrs yarima wlh bakiga yadda Kikayi kyau ba kamar kece amaryar.
Uhm zaki dai fara tsokanata ne da kika saba.
Safiya kallon 'yar uwartata tayi tace dan Allah iman ya kika ga matar prince?
Murmushi iman tayi tace wlh tayi kyau sosai ji nake daman ma nice ita.


Ku dai kukasani da tsokanarku, tana fad'in haka tawuce tanufi part d'in yarima tabarsu nan suna ta binta da kallo.




Zarah tana shiga lokacin yarima yana zaune saman 3 seater yana kallo, ahankali tayi sallama, juyowa yarima yayi yakalleta saida gabansa yafad'i ganin wani irin kyau da tayi, Zarah ma tsura masa ido tayi sanye yake cikin dakakkiyar shaddarsa coffee colour ya yi mata wani irin kyau, sun dad'e suna kallon juna sannan yarima yajanye idonsa yamaida ga TV, zarah ajiyar zuciya tasafke sannan tace barka da hutawa.
yauwa yarima yace batare da ya kalletaba.
Ahankali tace dan Allah zan tafi wajen dinner d'in.
Juyowa yarima yayi yakalleta sannan yace bazaki jeba.
Marairaicewa zarah tayi tace dan Allah kabarni
Wani irin kallo yarima yayi mata sannan yace kije kihad'o min coffee.
Zarah aje jakkarta tayi tafita tana turo baki ko da takoma part d'inta kallon su safiya tayi da suke jiranta tace bari tayi sauri tahad'a ma yarima coffee.
Sukace toh, nan tayi sauri tashiga kitchen tad'aura.




Bayan tagama d'auka tayi tanufi part d'insa tana shiga mik'a masa tayi, sannan tace dan Allah toh intafi?
Yarima kallonta yayi tana ta turo baki sannan yace na fad'a miki bazakijeba, juyawa zarah tayi zatabar d'akin cike da jin haushi.
batare da ya kalletaba yace kisamu waje kizauna.
Kujerar da take opposite d'insa tazauna ta cika fam,
A hankali yakai cup d'in bakinsa yana sha.
Wayartace tafara ringing saida takalli yarima da yake kallonta sannan tayi picking tace safiya kutafi kawai bazan samu damar zuwaba, tana fad'in haka takashe wayarta,
Sun dad'e a zaune zarah duk ta k'ule ji take daman yabarta tatafi part d'inta ko baccine tayi.


Har wajen goma saura suna Zaune a haka, Kiran wayan shaheed ne yashigo a wayarsa murmushi yayi sannan yayi picking yace ya dai ango?


A chan 6angaren shaheed cike da k'ulewa yace dallah malam katafo kawani bar mutane suna ta jiranka.
Ta6e baki yarima yayi yace ai bance ajiraniba.
Kar dai kacemin bazaka zo ba? Cewar shaheed
Yarima yace ni ban fad'aba malam.
Toh mujiraka kenan?.
Uhm zan gani, yana fad'in haka yakashe wayarsa gaba d'aya gudun kar ak'ara kiransa.
Zarah da tunda yafara wayar kafesa tayi da ido har yagama ahankali tace toh saidai muzauna gidan tare.


Kallonta yarima yayi yace me kikace?
Dasauri tagirgiza kai tace ba magana nayiba.
Murmushi yarima yayi sannan yacigaba da shan coffee d'insa.


Zarah duba time tayi ganin har 11 ta kusa sannan tamaida kallonta ga yarima tace bacci nake ji inje inkwanta?
Yarima batare da ya kalletaba yace zaki iya shiga kikwanta.
Zarah turo baki tayi tace a nan?
Yarima komawa yayi yakwanta a saman kujerar tare da d'aukar remote yacanza channel.












_Comments_
*nd*
_Share_














_Sis Nerja'artโœ๐Ÿป_
๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘


_*YARIMA SUHAIL*_

๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘๐Ÿ‘‘






_*Written By~Sis Nerja'art*_






_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_




https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/


*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ยฎ*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE ๐Ÿ˜˜ HEART TORCHING โค TEARS OF SORROWS ๐Ÿ˜ญ CURDLES ๐Ÿ™‚ GIGGLES ๐Ÿ˜ AND MARRIEGE THINK๐Ÿ’‘
*JUST GIVE US FOLLOW....*โœ”




_Wannan page d'in mallakinkine *Ummu Rahma* marubuciyar *'DAN GARGAJIYA* nagode sosai da kulawarki agareni Allah yabarmu tare_




*PAGE* 3โƒฃ9โƒฃ


Zarah zamanta tayi nan tafara gyangyad'i saida taji baccin yana cinta sosai sannan tamik'e tana turo baki tashiga bedroom d'in yarima,


Har ta kwanta saman gadonsa sai kuma taji bata iya yin bacci haka dan haka tatashi saida tacire kayan sannan tashiga toilet d'insa cikin sauri tayi wanka tafito d'aure da towel, saida tatsane jikinta sannan tafara tunanin abinda zata sanya, raba ido tafarayi daga k'arshe da taga ba yadda zatayi yasa taja tsaki tace nasan halinsa ina iya zuwa zan fita yayi min wulak'anci
saman gadon tahau takwanta tare da k'udindine jikinta da blanket bata kawo komai a rantaba takashe gloves ahaka bacci yad'auketa.




Wajen 12 yarima yakashe kallon yatashi yashiga bedroom kunna gloves d'in yayi tare da kai kallonsa a bed d'insa zarah k'udindine take tana baccinta hankali kwance murmushi yayi sannan yacire kayansa yawuce yashiga bathroom


Bayan ya fito shiryawa yayi sannan yakashe gloves d'in yakunna marar haske sosai yaje yakwanta gefen zarah,


Zuba mata ido yayi yanayin yadda take bacci tana burgesa, ya dad'e yana kallonta sannan daga baya yajanyo blanket d'in zai rufa shima, zaro ido yayi ganin yadda jikinta yabayyana dan gaba d'aya towel d'in ya rabu da jikinta, k'irjinta yazuba ma ido yana kallo sannan daga baya yaruntse idonsa yana jin wani iri a jikinsa, duk yadda yaso yadaure kasawa yayi ahankali yabud'e idonsa tare da yaye dukkan blanket d'in.


Rungumota yayi jikinsa zarah baccinta kawai take hankalinta kwance ahankali yafara zagaye hannuwansa a jikinta daga k'arshe yamaida yakwantar da ita sannan yacigaba da wasa da kowane sashe na jikinta,


Zarah cikin bacci taji kamar wani abu yana bin jikinta dan ji tayi kamar ana mata tafiyar tsutsa, dak'yar tabud'e idonta tare da safkesu akan yarima da yake a k'irjinta,


Zaro ido tayi tare da d'aura hannunta a kansa tana nema taturesa muryarta tana rawa tace pppplease yarima kadaina,


Yarima duk yafita hayyacinsa ahankali yad'ago kai yakalleta da narkakkun idanuwansa batare da yayi mata magana ba yahad'a bakinsu yafara kissing d'inta, inda hannuwansa suke yawo a kowane sassa na jikinta nan da nan Zarah tamik'a wuya dan dama ita kanta tasan tayi missing d'insa.




Sun dad'e suna abu d'aya har Zarah tagaji ammah yarima bai k'yaletaba saida yagaji dan kansa sannan yabarta.


Zarah tana turo baki takalli yarima da yake kwance idanuwansa a lumshe yana maida numfashi tace shine katasheni daga baccina? Chan k'arshen gado takoma takwanta tare da janyo blanket tarufe jikinta ita kanta wani irin sanyi takeji a ranta fuskarta d'auke da murmushi a haka bacci yayi awon gaba da ita.




Yarima ma yadad'e a haka shi kansa yasan yana cikin farin ciki dan ji yake kamar yau yafara sanin Zarah, ahankali yabud'e idonsa yakalleta chan k'arshen gado ta k'udundune jikinta, jawo wayarsa yayi yaduba time lokacin 1:50am.




Dak'yar yasamu yamik'e jikinsa ba k'wari yashiga bathroom dan yatsarkake jikinta.




Bayan ya fito komawa yayi yakwanta tare da juya mata baya fuskarsa d'auke da murmushi ahaka bacci yayi awon gaba da shi.




Zarah ko da yarima yatayar da ita tayi sallah tana ganin ya tafi masallaci tasaka kayanta tafito takoma part d'inta, tama yi tunani safiya nan takwana ammah sai taga bakowa, saida tatsarkake jikinta sannan tad'auro alwallah tazo tayi sallah.




Bayan tagama saman gadonta tahau tayi kwanciyarta ahaka bacci yayi awon gaba da ita.




Wajen 10 safiya tatashe dak'yar Zarah tatashi dan ji take baccin bai ishetaba, kallon safiya tayi tace kekuma yaushe kika shigo?


Dariya safiya tayi tace tun d'azun nashigo ina parlour jin shuru baki fitoba yasa nashigo, Zarah maida idanuwanta tayi talumshe tace please safiya kibarni inyi baccina.


Janye blanket d'in da Zarah take rufe da shi safiya tayi tace ank'i d'in tunda kinje kunsha love da prince shine har yanzu baki tashiba,


Zarah tunowa tayi da darensu na jiya nan tabud'e idonta tana murmushi tace toh ina wuranki?


Hararta safiya tayi cikin wasa tace aikam dai daruwana tunda kika hana babban abokin ango zuwa dinner, mutane suna ta nemansa.
Da munsa rai tare zakuzo sai mukaji shuru ashe kina nan kin rikitamana prince dan tunda naga gayun da kikayi nasan dak'yar idan prince zai iya barinki kitafi batare da wani abuba


Ta6e baki Zarah tayi tare da tashi zaune tace kinsan dai halin yarima indai yasa kansa toh babu wanda zai iya hanasa dan haka nidai bani nahanasa zuwaba daman chan baiyi niyaba.


Safkowa tayi taje tashiga toilet tayi wanka bayan ta fito zama tayi tatsantsara kwalliyarta sannan tad'auko super English blue colour tasaka nan tamurza d'aurin kallabinta, sark'arta ta gold tasaka nan kyaunta yak'ara fitowa.






da k'arfe biyu daidai aka d'aura auren rahma da shaheed, auren da mutane dayawa suka hallara.




Saida su zarah sukayi sallar azuhur sannan suka shiga cikin gida da yake cike da jama'a.
Safiya jan Zarah tayi suka shiga part d'in sultana sadiya dayake a chan rahma tazauna,


A parlour suka tarar da sultana da sumayya sai wasu abokan sultana sadiya a zaune suna hira.
Cike da girmamawa su zarah suka gaishesu, nan abokan sultana sadiya suka amsa ammah banda ummah da sumayya da suka had'e rai.


Safiya ce takalli sumayya tace Aunty sumayya ina adda rahma?
Ta6e baki sumayya tayi tare da cewa kin bani ajiyartane?
Safiya murmushi tayi tace yi hak'uri dan naga tare kukene saisa natambayeki.
'Daya daga cikin k'awayen ummah ne tace kai sumayya miye nabak'ar magana? Kikasani ko k'awayen amaryane?


yamutsa fuska sumayya tayi tace nasan baku gane wacchan ba? tanuna zarah
Eh gaskiya bamu santaba wacece ita?


Ummah ce tace toh wacece banda munafukar kishiyarta.
'Daya daga cikin matan ne tace tace wlh sumayya banga laifinkiba toh waima ubanmi tazo yi mana a nan?
Sumayya tsaki taja tace gulmar da tasaba ko?


Safiya da zarah tsaye suke suna kallon ikon Allah , k'arama zarah da bata wani damuba dan tasaba da wulak'ancinsu Ummah.


Safiya ce tace haba bayin Allah daga tambaya sai cin mutunci? Sumayya cikin 6acin rai tace ke safiya kikiyayeni ko ranki ya6aci.
Ta6te baki safiya tayi tace Allah yabaku hak'uri sannan takama hannun zarah suka wuce wani room da taga wata abokiyar rahma ta shiga.


A chan saman gado suka hango amarya zaune taci k'walliya tasha kyau har ta k'oshi, gefenta k'awayentane suka zagayeta sunata hira.




Safiya jan zarah tayi sukaje suka zauna bakin gadon.
Zarah fuskarta d'auke da murmushi tace sannunku? ina wuninku?
Gabad'ayansu suka amsa sannan tacema rahma amarya kinsha kyau Allah yabada zaman lafiya.
Murmushi rahma tayi sannan tace Ameen nagode sosai,


'Daya daga cikin 'yan matan amaryace tace gimbiya wannan ma friend d'inki ce?
Girgiza kai rahma tayi tace matar Bro ce.
Kallonta sukayi sukace ba dai yarima ba?
Shi man amaryarsace 2 months kenan yanzu da aurensu, cewar rahma.


Gabad'ayansu suka juyo suka kalli zarah d'aya daga cikinsu tace ashe matansa biyu, masha Allah gaskiya tana da kyau sosai kamar prince.
Wata tace saisa baya kallon mata ashe yasan ya aje mata kyawawa a gidansa.
Sai tayita haifo mana kyawawan yara, cewar safiya.
Zarah da kanta yake sunkuye d'ago kai tayi tagallah ma safiya harara.


Dariya safiya tayi tace daga fad'in gaskiya sai harara?
shuru zarah tayi tak'yaleta, tanajib wasu daga cikin 'yan matan suna ta maganar yarima har taso taji haushi, sai daga baya suka canza hira.


Saida sukayi sallar la'asar sannan suka fito sukaje part d'in dada basu wani dad'eba suka koma na ummin yarima nan suka zauna suna hirarsu.


Saida akayi sallar magrib sannan aka d'auki amarya aka kaita gidanta da yake kusa da masarautar, zarah cikin motarta sukaje gidan amarya, kowa saida yayaba tsari da kyaun gidan anzuba mata gaya na'azo agani dan room nd bedroom 3 akayi mata, nan akaita santi daga k'arshe kowa yayi Allah yabada zaman lafiya sannan aka watse aka bar amarya da wasu abokanta.




Shaheed kallon yarima yayi da yake shirin barin gidansu yace haba yarima yanzu kana nufin bazaka rakani wajen amaryataba?
Harararsa yarima yayi yace akace maka dole sai naje? Idan su muhammad sukaje ai ya wadatas,
Cike da jin haushi Shaheed yace shikenan duk yadda kayi daidaine daman jiya k'in zuwa dinner kayi.
Wai kai baka ganin rahma k'anwace agareni akanme zan dinga shige muku.
Ta6e baki Shaheed yayi yace nikuma abokine wanda bakada kamarsa, toh laifine dan kaje?
Rik'o hannun yarima yayi yace please yarima kataimaka karakani d'akin amaryata.


Murmushi yarima yayi yace toh shikenan naji jeka ka ida shiryawa kazo muje dan ni yau dawuri nakeson komawa gida saboda agajiye nake.
Shaheed yace angama ranka yadad'e.






Wajen k'arfe tara suka raka Shaheed gidansa, Tunda suka shiga d'akin da amarya take yarima bai d'aga kai yakalli kowaba dannar wayarsa kawai yake, nan abokansu da na amarya sukaita tsokanar ango da amarya, duk yadda wasu sukaso yarima yayi magana ko sunsamu shiga ammah baiyiba dan nunawa yayi kamar baisan da zamansu, nan aka k'ara yi musu nasiha sannan suka tashi sukabar gidan,
yarima yana shirin shiga motarsa saiga wasu mata biyu sun iso cikin kwantar da murya sukaimasa sallama.
Rik'e yake da murfin motar ya amsa musu ciki-ciki.
Ahankali d'aya tace dan Allah in bazaka damuba munaso kayi dropping d'inmu.
Ta6e baki yarima yayi sannan yace ba hanyarmu d'ayaba kudaije wajen wad'anchan su k'ila hanyarku sukayi.
Matan kallon juna sukayi sannan d'aya tace toh please zamu iya samun phone number d'inka?
Wani irin kallo yarima yayi musu sannan yashiga motarsa yaja yabarsu nan tsaye.
A k'arshe saidai suka koma wajen sauran abokan ango suka shiga motocinsu Cike da takaicin abinda yarima yayi musu.




Yarima ko da yakoma gida wanka yayi sannan yabi lafiyar gado yakwanta.


Zarah ko daman koda tadawo dak'yar tasamu tayi wanka takwanta batayi tunanin daman zuwa part d'in yarima ba dan agajiye take.


_Toh mudai saidai muce amarya rahma da ango shaheed Allah yabada zaman lafiya_






*BAYAN SATI 'DAYA* 'yan bikki duk suka watse zarah tayi missing d'in safiya dan 'yan kwanakin nan da sukayi sun saba sosai, yanzu saidai zaman kad'aici kuyangintane suke d'ebe mata kewa tahanyar bata labarai masu dad'i.




Yau kasancewar girkin zarah ne kwance take saman bed d'inta kanta yana kallon ceiling da alamu tunani take, ringing d'in wayantane yakatseta ganin mai kiranne yasa tasaki murmushi dan rabonta da yarima tun lokacin bikki, saida takusan tsinkewa sannan tayi picking, yarima baijira tayi maganaba yace kihad'o min coffee yana fad'in haka yakashe wayarsa, fuskar zarah d'auke da murmushi tamik'e tanufi kitchen dan ko bakomai tasan yau zata sakasa a idanunta.


Bayan tagama had'a masa hijab d'inta tasaka kasancewar daman har tayi shirin kwanciya,


Ahankali tabud'e bedroom d'insa tashiga yarima dasauri yad'ago kai yakalleta sannan yamaida kansa yacigaba da dannar laptop d'insa, zarah k'arasawa tayi kusa tashi tare da zama gefensa sannan tace ga coffeen.
Yarima batare da ya kalletaba yace ina zuwa,
Haka yabar zarah rik'e da cup har kusan 5 minutes sannan yakar6a,
Mik'ewa zarah tayi zata tafi, batare da ya kalletaba yace ina zakije?
Murmushi zarah tayi tace zanje inkwanta ne.
Ban baki iziniba, cewar yarima da yake dannar laptop.
Marairaicewa tayi tace wlh bacci nakeji.
Ko inda take yarima bai kallaba.
Zarah turo baki tayi sannan takoma tazauna,
Yarima tagefen ido yana kallon yadda take ta fushi.


Zarah ita kanta har tagaji da zaman cikin ranta tace lallai mutumin nan ya raina min wayau miyake nufi da ni ne? Chan kuma sai tayi murmushi tare da cire hijab d'inta nan gashinta yabazu kallon yarima tayi da ya aje cup d'in yana cigaba da dannar laptop, amsar laptop d'in tayi ta aje gefe, yarima binta yayi da kallo cike da mamaki Ahankali tafad'a jikinsa tare da rungumesa cikin shagwa6a tace please kazo muyi bacci kaga har 11 fa tayi.
Wani iri yaji a ransa ammah yadake yace kikwanta mana ni sai nagama abinda nake.
Zarah d'ago kai tayi tana kallon cikin idonsa ahankali takai bakinta cikin nasa yarima daman kamar jira yake nan yacafke nan suka fara rikita junansu sun dad'e a haka sannan zarah tazare jikinta takwanta tare da jawo yarima jikinta dak'yar yasamu yakashe gloves.




yau makara sukayi sallar asuba har saida gari yafara haske sannan zarah tafarka duba time tayi taga 6:15am zaro ido tayi sannan takalli yarima da yake kwance yana bacci har takai

08, February 2025
Shuraihu Usman

jjjjj

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login