Showing 87001 words to 90000 words out of 164763 words
ta runtse idanunta gam dan zoben take gani a idanunta yana aman kudi zoben aljanu, bude gate tayi tafita dawani irin azababben gudu daidai kan wata mota Lexus ta danno yana shirin horn azo abudemai gate, ganin fuskar dabazai taba mantawa ba ko amafarki daure da towel kafafunta ba takalmi idanunta akulle dan gaban gidansu akwai manya manyan Street light bauuu sun haska ko ina yasa da sauri ya kashe motar yabude door yafito yana gyara zaman suit din jikinshi bude kofar gate dinsu yayi ganin babu kowa a compound yasa yawaiga da sauri ganin tana gudu yasa da sauri yabi bayanta, daidai tana shirin shiga titi yawani irin fizgo hanunta tadawo baya yariketa gam yana binta da kallo ganin idanunta a rufe ruf jikinta nawani irin rawa. "Mama Mama, Mamaaaaa! " tasake kwalama mamansu kira yasa ya jijjigata tareda kiran sunanta. "Amatullah" ko kadan kwanyanta baya aiki a lokacin sai kiran Mama Mama mama take ta datse idanunta gam, da hannu daya yarike ta yacire black jacket din jikinshi dake kamshi sosai ya daura mata akan kafadarta ya jijjigata tareda kiran sunanta. "Amatullah look, look, hey relax is me, open your eyes menene?" jin murya kaman ta Aadil sama sama yasa ahankali tabude idanunta dasuka kankance jikinta na rawa, Sanye yake da farin long-sleeve shirt wuyanshi daure da nicktie gashin kanshi a kwance yay wani irin mugun kyau yana rike da ita gam gam yana kallonta ganin ba lafiya tattare da ita, fashewa tayi da kuka sosai tafada jikinshi ta rungumeshi tace "My Aadil you are back" cirota yayi daga jikinshi da sauri fuskarshi adaure yace "where are you running off to daure da towel batakalmi ba hula are you okay" rikeshi tayi gam jikinta ya dauki ruwa tana kokarin sake shigewa jikinshi yahanata tace "som....something in...a..dakin" luuuu tayi baya zata sume da sauri yariketa ya dauketa yay hanyar gida da ita, bude gate yayi mai gadi yafito mugun kallo ya watsamai yace "bakasan aikin kabako how can be our security idan baka taking note of who goes in and out of this house eh? Anyway banda time dinka call Mami for me kace ta taho da Dr" yay hanyar shashin su Hamida dauke da Hamidan, bude kofar dakin yayi wani hadadden kamshin turaren wuta yadaki hancinshi kwantar da ita yayi akan kujera yatashi yay hanyar dining dan daukan bottle water dayagani daidai lokacin Mami da big Mum dasu Baffa da Suleman suka shigo dan duk suna tare ana maganan Abie inda yakai Aadil Mai gadi yace suzo Hamida ba lafiya, da sauri Mami takaraso ciki da gudu tana kallon fuskar Hamidan tace "maiya sameta Aabid? Kafafunta butu butu haka, wat happen son?" bude bottle water yayi yace "i don't know Mami dawowa na kenan naga tafito daga gate da gudu ahaka idanunta akulle i was trying to talk to her kuma saitai passing out" karban ruwan Mami tayi da sauri tana surutai. "na shiga uku wai meke faruwa ne ni Maryama" shafa ruwan tayi a fuskarta wani irin ajiyan zuciya Hamida tayi tabude ido tana kallon duka dakin, ahankali Mami tace "Hamida na kinajina?" kallon Mami tayi saikuma tajuya tana kallon duka yan dakin kafin idanunta ya sauka kan Aabid dayay folding hand akirji yana kallonta tashi tayi azubure tafashe da kuka tafada jikin Aabid tace "take me out of this place kaji My Aadil akwai wani abu adakin chan, akwai wani abu yanata girma am scared ka kaini wurin Mama dam Allah ku kaini wurim Maman mu da Kaka" takire Aabid gam, da sauri Suleman yace "to kodai tanada aljanu ne? " komawa bayan Aabid tayi tarikeshi gamgam jikinta narawa tace "abun na dakina chan bedroom pls take me out of here, zai fito yakamani i carried it dazu" tafashe da kuka sosai da sauri Mami ta tashi zatai magana Baffa yadaga mata hannu bayan yagama nazarin Hamidan yace "kubarta yarinya mai natsuwa haka dole akwai abinda ya firgitata bakuga bata hayyacinta ba, Sulemanu kumuje muduba dakin mugani" da sauri Suleman yace "to Baba" big Mum tace "ku dauko adduna incase maciji ne ko kunama" hararanta Baffa yayi yace "babu reptiles agidan nan ana fumigation ai" sukai hanyar dakin harda su Mami Aabid zai bisu tasake fashewa da kuka tana rikeshi tace "don't leave me kaji Aadil" juyowa yayi ya kalleta kafin ya dauke kai ganin she's not okay, ihun su Big Mum dayaji dakuma salatin su Baffa kowa nakiran sunayen Allah yasa da sauri yay hanyar bedroom din yana rike da hanun Hamidan gudun karta kara fita, kutasawa yayi ta tsakakanan su Big Mum dayaga jukunansu narawa duk suna kallon dakin ya kutsa kai ya shiga dakin, chak ya tsaya kyam jinin jikinshi ya tsaya kyam, ganin abinda tunda yake aduniya baitaba ganiba, wani katoton huge zobe yagani akasan dakin yana aman kudi yan dubu daidai sababbin kudi nafita daga bakin zoben, kudin sun cika kasan dakin har wasu sun soma hawa kan gadon sunyi himm, daidainan Abie ya buga kofan falo ya shigo dakin rai abace Aadil biye dashi.
_hello lovelies, due to high demand na next page am introducing VIP readers, in bakison suspense kinason kiji next page always koda yaushe all you need to do is subscribe for VIP and be my VIP readers, for those interested all you need to do is pay 1k, for more enquiry 07012181461, chat me up and know more. I love you 😘_
51.....
_karki karanta in baki biyaba in kika karanta ina binki bashi pay anan or pay achan_
_Zaki tura 300 kota card kota bank sai nai adding dinki a group din danake posting, 3107021073 first bank aisha Muhammad, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461, you can also send MTN card to watsapp number na 07012181461_
_masu fitarmin da book kuda Allah_
Hanyar bedroom Abie yayi ganin babu kowa afalon straight cikin fushi yana daga murya yace "ina take zoki barmin gidana, mai bakin jini, mai kashin tsiya daga auroki kindawo mana bala'i" Hamida dake baki bakin kofar bedroom dinne tafara juyowa jin hayaniya da sahun tafiyan mutane, tana ganin Abie tareda Aadil daya fara tsalle zaiyo kanta gabanta yawani irin mummunan fadi sabida wani mugun kallo da Abie yake mata kaman zai chaka mata wuka, batasan lokacin data rike hanun mutum din dataji kusada itaba, hanun big Mum takama tarike gam da
sauri big Mum ta juyo jin anrike mata hannu ganin Abie da Aadil da yarike gama yasa tace "Baban yan biyu yauwa zokaga ikon Allah" daidai lokacin Baffa daya gama kiran liman din masallaci dan d whole scene looks spiritual da jinnish ya kalli Suleman da Muhammadu dasuke kafe a tsaye suna ganin abinda basu tabaganiba aduniya yace "kuje ku shigo da liman koma menene wanan abin ayar Allah yau zata kona manashi" da sauri suka jujjuya suka fita daga dakin ganin Abie a corridor rike da Aadil dayake kokarin fizge kanshi yana kuka yasa sukace "jeka gani kaima Abdullahi, abin mamaki" matsawa Mami databi Abie da kallo asanyaye tayi ganin yafara tafiya big Mum ma ta matsamai suka bashi wuri abakin kofan, sakin hanun Aadil yayi ganin yakaraso kuda da Mami da wani irin gudu Aadil yay wani irin tsalle ya rungume Hamida data makale ajikin big mum yace "oyoyo My Hamida" fashewa da kuka tayi sosai ajikinshi ta kankameshi tama kasa magana but she just miss him, jin muryan Aadil yasa Aabid yajuyo da sauri hada ido sukayi da Aadil daya rungume Hamida yana mata kuka ahankali itama tana kuka, ganin Aabid acikin daki yasa yasaki Hamida da sauri yawani irin ware manyan idanunshi yace "Bid" wani irin tsalle yayi ya shigo dakin batare daya lura da komiba yay wani irin jumping ya rungume Aabid kaman zai kadashi yace "oyoyo Bid" kyam idanunshi suka sauka akan ring din dake aman kudin har lokacin daidai lokacin Abie shima ya shigo cikin dakin, yanda gabanshi yafadi saida dan gajeren fitsari yazubomai daga wando yana tuna warning din OZo aranan da akabashi zoben kudin nan. "koda wasa karka bari zoben nan yay aman kudi agaban idanun wayanda basu taba shan jini ba, danka na zoben nan, karka bari zoben nan yay amai agaban mutanen daba yan gidaba, ka kiyaye, ka kiyaye idanu mashan jini ne kadai aka yarda su kalli zoben nan alokacin dayake baka kudi, idanun masu tsarki wanda suke gauraye da jini kadai sukeda ikon ganin lokacin aman kudin zoben nan, kariga kasan ranan dayake aman kudi sanan kariga kasan lokacin dazaima aman kudi ka kiyaye Tursoso, kakiyayeee".
Wani irin race da zuciyarshi Abie yafara yasa yaji saliva bakinshi ya bushe gabaki daya zaiyi magana, yana kokarin magana amma maganan taki fitowa sai iska yake fita. "ahhh, huuuu"....
Ahankali Aadil yasaki Aabid yamike tsaye kanshi narawa sosai miyau nazuba daga bakinshi, kafe zoben Aadil yayi da ido yana kallon kullutun jikin zoben yaga yakawo wuta a jan wuta a idanunshi, kanshi yagani ajikin kullutun amma dan karamin shi, yana cikin keji an rufe, ganin Aadil karami yayi yarike karfen kejin yana girgizawa yana mai magana directly. "free me, free me kafin yagama aman nan, ninekai dasuka shanye, nine brain dinka dasuka shanye, free meee nowww, yakusa gamawa" wani irin juyawa idanun Aadil sukayi sama gabaki daya kafafunshi su lankwashe, duk dakin babu wanda ya lura dashi asandare yay baya ya zube akasa gabaki daya asume akan kudaden, ihu Hamida tayi ta shigo dakin da gudu kafin ta iso Aabid ya dagashi afirgice ya rungume kanshi a kirjinshi Mami ma ta shigo daidai nan su Muhammad suka shigo da limam dawasu malamai guda biyu alarammomi, dago kai Aabid yayi ya kalli Hamida data tsaya gefe takasa zuwa kusada shi tafashe da kuka sosai tana kallon Aadil datake so ta taba amma takasa sabida yanda Aabid yarikeshi, kallan Mami Aabid yayi yace "Mami take her to your room ta nemi hijabi tasaka please" tashi Mami tayi takama hanunta suka fita daga dakin Mami ta karbo mata hijabi
.
_karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi, pay anan or pay achan_
_this book is for sale, just 300 naira zaki turo ta 3107021073 first bank aisha Muhammad, idan baki da account u can send MTN card, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461_
Shiga malaman sukayi suna kallon abinda ke faruwa da karfi liman din ganin yanda baban zobe ke fitar da kudi yafara karanto addu'a. "Bismillahil lazi la yadurru ma' ismihi shai'un fil-ardi wa-laa fil-samaa'i wa huwas Samee'ul Aleem" yakaranto addu'an yana tsugunnawa yakai hanunshi kan saman idanun Aadil dake hanun Aabid yabude idanun yana ganin yanda idanunshi suka juya sama baka ganin bakin ko kadan, jinin jikinshi yasha batare dayay magana ba ya kalli sauran malaman dake tareda shi, hakan yasa daya daga cikinsu yakalli baffa yace "muna bukatan ruwa a gora Alhaji danka kodai aljanu sun shafeshi kokuma da sihiri ajikinshi" gyara zama limam yayi yana kallon zoben dayake fitar da kudi har lokacin yafara karatun al Qur'ani, sauran malaman suka zauna kusa dashi suka jonashi suna karantowa atare da karfi sosai kaman zasu fasa dakin da zakin murya, wani irin girma zoben yakarayi kaman an huramai iska, Suleman Big Mum tarike gam dan wani irin tsoro taji tanaji kowani mutum na dakin tambayoyine fal aransu daga ina zoben nan yake? Daga ina tayaya yazo dakin nan?
Abie ko kyafta ido bayayi yay kokarin dazaiyi yay magana yakasa kaman wanda aka dinkemai baki yana kallon yanda zoben ke kumbura yana kumbura yana kumbura.
Ayoyi daban daban suke karantawa suna fuskantar zoben wani irin girgiza zoben yafara yana rawa rawa kaman abinda ke shirin fashewa kafin tuss yawani irin fashe ya tarwatse, kumfane yafara fita daga bakin Aadil jikinshi na girgiza kaman mai ciwon farfadiya yana mikewa yana bankarewa da sauri Aabid dake rike yana neman fizgemai yace "innalillah, Malam my brother meke faruwa dashi" cigaba da karatu malam yayi batare daya amsa Aadil ba, wani irin girgiza dakin yafara kaman saukan aradu hakan yasa malaman suka kara karfin karatu suna kiran Allah, rike Baffa Muhammad yayi gam yayi dakin na kara yana making sound kaman sound din guguwa, wutan dakinne sukai kara suka fashe tareda tarwatse wa dakin yay duhu dumdun abunku dadama darene kara karfi karatu malaman sukayi Aabid ya rungume Aadil da jikinshi ke rawa sosai har lokacin miyau nafita daga bakinshi yana zuba awuyanshi.
Wani irin bulluwo Ozo yayi da kwarangwal dinshi jikinsu na hayaki sosai ta bango, magana sukaji kaman daga sama maikama da murya irin ta abumai tsoratarwa. "Tursoso kanagani ana konamu kai shiru bakace komiba, Tursosooo!" yakira sunan Abie cikin wani irin fushi tone, tundaga silin gashin Abie nakai har zuwa karkashin tafin kafarshi rawa yake jin muryan Ozo, cikin wani irin yanayi na daburcewa da rashin sanin mai yake fadi yace "O...Ozo the g..great bansan cewa anan nabar zobena ba hala danazo inajan Aadil ne yana fada dani shine zoben yafita daga hannuna, Ozo dan Allah karafumin asiri kayakuri" Abie yakarashe maganan cikin tone din kuka, waya Baffa yaciro tsabagen son ya gasgasata me kunnuwanshi suka gama jiyemai ya kunna flash kaman dukansu sun hada bakine gabaki dayansu harda Aabid wayoyinsu atare suka ciro suka kunna flash light dakin yay haske bauu duk suna kallon Abie da idanunshi yay kuri alamun mara gaskiya sunyi jajir kirjinshi nawani irin bugawa gabaki daya yay wani iri yana kallon Ozo da kwarangwal dinshi dake jikin bangon dakin jikinsu na hayaki while malaman na karatun su har lokacin batare dasun yankeba, wani irin kara Ozo yayi ya buga karfen hanunshi sabida konewan dayakeyi yace "bazaka hanasu konamu ba Tursoso" da sauri Abie kaman mahaukaci ya tsugunna yanajan gwuiwa ya zagayo tagaban malaman yace "kuwa Allah, kuwa Allah nace baniba kudena karatun nan zan fadi muku komi, kunga ran Ozo the great yariga yabaci, inhar kuka konashi kashe Aadil zaiyi, wlh, wlh, billahillazi la'ilaha illahuwa kuruwan Aadil na tareda shi, kai rayuwan Aadil gabaki dayanta ma yana wurinshi, shine ya shanye rayuwan Aadil ya shafemai kwakwalwa, shine ya zamad da Aadil abinan dakuke gani, inhar baku denaba mutuwa zaiyi, zuge jinin Aadil zaiyi tass" babu wanda bai girgiza ba dajin kalaman Abie ba, shiko Abie ko kadan bai damuda wanan ba yasan dukansu babu abinda suka isa sumai, yanada kudin da zai iya kullesu dukansu, yanada kudin dazai iya batar dasu aduniyan nan gabaki daya anemesu arasa, sanan yanada kudin da zaije daganan harbangon duniya inyanaso yaje just to free his self daga shame and talk of the town. Wani jarababben tsawa Ozo yadakamai karfen hanunshi yay haske yace "bazaka hanasu ba Tursoso" da sauri Abie yasa hannayenshi ya rufe bakin limam kaman zaiyi kuka yace "kudena konamin Ozo, Ozo ne rayuwata, shine gatana, yabani abinda wanan mutumin marikina bai baniba dudda uwarshi tacemai yasoni sama da yaran daya haifa amma tana mutuwa ya manta da batun, Ozo ya soni ya fifitani akan duka members yan cult, shiko wanan tsohon yaranshi yafiso, suya sani baniba, dudda nafi yaranshi ilimi nafisu iya aiki, nafisu kaifin basira kullum ninake samamai customers da ciniki a kampani amma daya tashi raba motoci bai baniba yabama yaranshi, Ozo shiya bani kudi saisama har yarshi ta yarda zata aureni da bata aureniba ai, sanan Ozo ya zamaddani popular yabani fame akasanni globally aduka kasashen duniya, nazama babban mutum, kuduba fa duka abubuwan nan dayamin abu daya kawai ya nema awurina shine jinin dan farina, amma dana haifi Aadil nakasa badawa, nama Ozo daya sharemin hawaye butulci sabida yanda nake son Aadil, gadai yaron imbecile amma shine rayuwata duka, Allah ya jarabeni da masifaffen son Aadil, na roki alfarma Ozo yamin da sharadin duk cikin da Maryama zata kara samu tun kafin ahaifa zasu shanye duka, barin Maryama sau uku ba bari bane Ozo nabama yaran nawa tun suna cikin cikin uwarsu, dan Ozo ya chanchanci abinda yafi haka agareni ma, yamin komi a duniya, yaban duk abinda nabukata, inhar kundena konamin Ozo na zan baku ganamasgo manya manya na dollars guda dari uku na rantse da zatin Allah" yafada ahaukace, kabar da hanunshi limam yayi yacigaba da karatun da karfi dan maganganun Abie kara musu karfin guwiwa yin karatun more and more yayi, dole yau su babbaka matsafan nan da ayoyin Allah, su kawo karshen su sanan su kubutar da Aadil, wani irin haske karfen Ozo yafara ran Ozo amasifar bace, kwarangwal dinshi tafara rawa tana narkewa kafafunta sun narke suna diddiga kaman roba da akai melting da wuta, wani irin girgiza karfen Ozo yayi yana nishi yana kallon Aadil da Aabid da gudu Abie kaman zarare ya tube riga yay wani irin tsalle ya tare Aadil da Aabid ya karesu yace "dont kill my children Ozo, na rokeka idan akwai any atom of son dakake min aranka karka kashemin yaran nan, amma nabaka izini ka kashe kowane ne agidanan, kama kashesu gabaki daya banda asara, they're all bloodline but don't touch my children please Ozo, Ozo karka kashemin boys dina, Aadil baisan dadin asalin duniya ba, na tauyemai 30yrs of fresh life, kabarmin shi har lokacin da Allah ya kindayamai aduniya su cika karka kashemin Aadil Ozo na rokeka" wani irin hayaki ne ke fitowa daga bakin Ozo idanunshi na fitar da bakin ruwa, karfenshi na wuta sosai yana hayaki, ganin haka yasa Abie ya warware mazariyan wandonshi yace "Ozo kawa Allah karka kashemin yara, kai nace karka tabamin yarana fa, bakajina ne? Karka tabamin yara, Aadil zuciyata ne, karka tabamin yan biyuna, zanyi tsirara agaban duka duniya inhar bazaka kashemin yarana ba, karka tabamin yan biyuna Ozo" kana ganin Abie kasan ya haukace bil hakki dan maganganun dayakeyi basuda kan gado, daidai lokacin Hamida ta shigo dakin da gudu sanye da dogon hijabin Mami hankalinta atashe tana kallon fuskar Aadil dahar lokacin ke kulle bakinshi na fitar da yellowish kumfa tareda hancishi, mugun rudewa tayi batare data lura dasu Ozo ba tai wajen Aabid dake rungume da Aadil da mugun gudu tana kallon fuskar Aadil din ganin kaman yamutu daidai lokacin Ozo yasaki wutan tsafin karfenshi direct sai wutan tsafi yay saitin cikin Hamida ya shige, tsayawa Hamida tayi chak daidai ta karaso kusada Aabid ta mika hannu tana shirin taba kan Aadil