Showing 42001 words to 45000 words out of 83141 words
Chapter 15 - Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel By Nana M Sha'aban .txt
Hafsa wallahi! wallahi!! wallahi!!! Kin ji na rantse miki ko, mu kan mu ba mu san da bikin ba, sai da muka zo gidan Hajiya Mama sannan" Fizge hannun Amatullahi tayi daga jikinta ranta a b'ace ta ce "daman baku yi niyyar na zo ba, tunda ranar ma a school babu yadda ban yi da ku ba, a kan ku shiga mota a kai ku gida ku ka k'i, kuma lokacin da ku ka hau adaidaita Yaya Safwan ya bi hanyar da ku ka bi, sai gani na yi kun bii hanyar gida anan na tabbatar kawai daman bakwa buk'atar cigaba da mu'amalarmu".
Khadijatullahi jikinta yayi sanyi dan kuwa ta san bata kyautawa k'awarta ta ba domin ita ce da laifi Amatullahi babu ruwanta nan, rik'e hannun Hafsan tayi lokacin da ta juya zata fita, ta juyo da niyyar fizgewa sai ta ga Khadijatullahi ce kuma tana tsoron karta fizge ta je ta fad'i tunda cikinta yanzu ya tsufa sosai ya kai wata takwas, "me zaki ce min ke kuma?" Hafsa ta fad'a cike da masifa, "ki yi hak'uri dan Allah wallahi ba wai da niyya mu ka yi miki haka ba, kuma Amatullahi kwata-kwata ba ta da laifi ni ce nake da laifin dan mana k'aunar abin da zai sake had'a ni da wani namijin na tsane su, ba na son ganinsu, amman bikin Aunty Murja wallahi kamar yadda besty ta ce ba mu san dashi ba mu ma sai da muka zo ake fad'a mana, kuma lokacin ya ri ga ya k'ure shiyasa ki yi hak'uri".
Hafsa tayi shuru tabbas ita ma ranar sai da ta raya wannan abin a zuciyarta cewa Khadijatullahi ba ta son ganin maza shiyasa ta k'i shiga motar "Shikenan ya huce" Hafsa ta fad'a tana murmushi, murmushin su ma suka yi gaba d'ayansu.
Aliyu ne ya shigo gidan idanuwansa a kan Khadijatullahi duk ya ji abin da suka fad'a zuciyarsa ta shiga bugawa magana Khadijatullahi ta girgiza shi ba ma shi kad'ai ba har da su Hajiya Mama domin kuwa sun san Jabir shi ne silar da yasa Khadijatullahi ta tsani maza, "Assalamu alaikum" Ya fad'a har lokacin idanuwansa na kan Khadijatullahi, amman ita tun da ya shigo ta kawar da kanta domin kuwa wata iriyar muguwar tsanar Aliyun take ji saboda tsananin kamannin Jabir da take gani a fuskar Aliyun ji take kamar Jabir d'in ne.
Suka amsa masa sallamar amman ban da Khadijatullahi d'akin Hajiya Maman ta shige tayi kwanciyarta, "ko me ya kawo shi nan, banza kawai" Tayi maganar zuciyarta kamar zata fashe saboda tsanar maza da tayi mata katutu a cikinta.
Hafsa da Amatullahi kuwa k'arasa suka yi suka zauna Hafsa ta gaisar da Hajiya Mama cike da girmamawa Aliyu ma ya gaishe da ita ya zauna kusa da ita suna yin hirarsu irinta jika da kaka, Hafsa kuwa hira suka shiga yi su da Shahida,Nihal da Amatullahi, zuciyar Amatullahi ta karkata a kan ta je ta ga wace wainar ake toyawa a gidansu domin kuwa ba ta k'aunar ace Lado da Inna Larai sun shirya, tashi tayi tana cewa "Sisters zan je na dawo yanzun nan","ina zaki je besty" Hafsa ta tambayeta.
"Ginin da na fara yi ne nake tsoron kada ya ruguje" Hafsa ta gane abin da Amatullahi take nufi dan haka ta fashe da dariya tana fad'i "gaskiya ne besty, gwanda ki je ki duba shi kar ya ruguje duk aikinki ya dawo baya" Khadijatullahi da take cikin d'aki tana jin su ita ma dariyar take yi sosai har suna iya jin dariyar Hafsa ta ce "Ahhh besty ke ma dole ki yi dariya, tana tsoron kar ya ruguje aikinta ya dawo ba, kin san fa besty akwai ta da iya tsara gini mai kyau","Ai kuwa dai kam" cewar Khadijatullahi.
Wannan maganar ta su ta saka su Hajiya Mama a rud'ani har Amatullahi tayi musu sallama ta fita, da Hajiya Mama ta gaji ta tambayi Hafsa "me take nufi da kar gininta ya ruguje?" Nan Hafsa ta fad'a musu abin da take nufi da hakan, Nihal da Shahida dariya suka saka sosai har da hawaye "Ai daman na fuskanci sister ba k'aramar 'yar drama ba ce" Shahida ta fad'a "wallahi kuwa other half" Hajiya Mama dai girgiza kai kawai tayi Aliyu kuwa yana son yin dariya ya basar, suka cigaba da yin hirar ta su.
*'BANGAREN INNA LARAI,LADO DA KUMA AMATULLAH*
Cikin sauri sauri ta k'arasa gidan tana saka kanta a sauron gidan ta ji muryar Inna Larai tana cewa "dan Allah kayi hak'uri mana Lado tunda ya ce a wannan satin zai turo kud'in sai ka tsaya satin idan ya huce ka ga bai turo ba, sai ka fad'i duk abin da zaka ce, tunda dai kasan k'aryar da nayi masa cewar ginin d'akina ne ya fad'i na gyara ban bada kud'in ba, kai ma kasan zai turo kud'i" Amatullahi tayi wani irin murmushi "lallai kam da ace ban dawo ba, da tuni ginina zai ruguje, amman yanzu na dawo zan d'ora daga inda na tsaya" Tayi magana a zuciyarta.
Shiga gidan tayi ko kad'an ba ta nuna ta ji abin da suke fad'a ba, ta saki wani irin murmushi tare da cewa "sannunku da hutawa Inna, my love nayi missing d'inka" Tayi maganar tana kallon Lado fuskarta tana nuna alamun tsantsar damuwa.
Lado ya k'ak'alo murmushin dole ya wanzar a kan fuskarsa "nima haka my love" Ya fad'a tare da mikewa tsayi yana cewa "zan fita waje na d'an sha iska my love ki kula da kanki" Yana gama fad'ar haka ya fita ransa a b'ace shi sam baya k'aunar yi wa Amatullahi magana kuma duk Inna ce ta jaaa masa gashi ta zamar masa k'arfen k'afa.
Ita kuwa Amatullahi d'akinta ta shiga tayi wanka, sannan ta fito wata doguwar ce a jikinta blue tayi mata matuk'ar kyau tamkar dan ita aka yi rigar, fita tayi daga gidan ta nufi gurin mai kiran waya ta biya shi kud'in sannan ya bata wayar ta saka number babanta sannan ta matsa chan nesa da mai kiran wayar domin kar ya ji abin da zata ce, ring d'aya biyu ya d'aga tare da yin sallama "Assalamu alaikum" ta amsa masa sallamar "Wa'alaikumussalam Babana Amatullahi ce","Allah sarki yarinyata nasan kinyi kewar babanki ko?" Yayi maganar cike da jin dad'in kiran da tayi masa "Eh babana nayi kewarka sosai da sosai kullum sai na ji dama nima ace na dawo gurinka mu dinga yin aikin tare","Allah sarki yarinyata karki damu na kusan dawowa insha Allahu na zo na ganki" Amatullahi ta ce "to Baba Allah ya dawo da kai lafiya","Aamin ya Allah" Sai kuma Amatullahi ta numfasa ta fara kora masa jawabi "Babana na ji wai Inna ta kira ka a kan cewa ginin d'akinta ya ruguje, ta kirawo mai gyara an gyara bata bada kud'in gyaran ba","Eh wallahi gobe ma nake shirin turo mata da kud'in dan ta biya shi kud'insa" Amatullahi ta ce "to wallahi Baba k'arya Inna take babu wani ginin da ya ruguje, so take ta damfare ka, kuma idan ka na tunanin ba gaskiya nake fad'a ba zaka iya zuwa ka duba ka gani da kanka" Shuru Malam Shu'aibu yayi domin a duniya babu abin da ya tsana irin kayi masa k'arya, gwanda ka fito fili ka fad'a masa gaskiyarka "Kin tabbatar babu ginin da ya ruguje","wallahi Baba da gaske nake yi maka" Amatullahi ta fad'a cikin fara'a, kashe wayar Malam Shu'aibu yayi ransa duk a b'ace kuma ya k'uduri niyyar ba zai bata kud'in ba kuma ko ta kirasa ba zai d'auka ba, Amatullahi kuwa mayarwa da kiran wayar tayi da wayarsa sannan ta shiga adaidaita ta nufi gidan Hajiya Mama.
*'BANGAREN SAFNA*
Tun ranar da ta ji labarin cewar Safwan da Hafsa sun shirya kuma yanzu soyayya suke yi, kuma ta fuskanci duk irin abubuwan da take yi a gidan dan ta kuntatawa Safwan d'in sam bai dameshi ba, nuna mata ma yake yi kamar bai san tana yi ba, hankalinta ya tashi zuciyarta ta shiga yi mata zafi, ta shiga neman hanyar da zata bi ta mallake Safwan d'in ita kad'ai kuma ta cusa masa tsanar Hafsa a cikin zuciyarsa amman kwata-kwata ta gaza samun hanyar, kullum cikin kuka gashi kuma kamar k'ara ruru mata wutar son Safwan d'in ake yi a zuciyarta, yau ma kamar kullum tana zaune a falo tana shan kukanta.
Safwan ya shigo falon domin ya manta wata takardar wad'anda suka siya kaya kuma ake binsu bashi, kallon Safna yayi cike da tausayi tabbas shi kansa ya san Safna tana sonshi sosai, amman kuma Hafsa ita ma tana matuk'ar son shi bai san a cikinsu waya fi son shi ba wannan Allah ne kad'ai yasan hakan, har ya huce sai kuma ya dawo domin bai zai iya barinta cikin yanayin da take ciki ba a yanzu.
Zama yayi a kusa da ita tare da kama hannunta yana murzawa, kamar jira take ta fad'a jikinsa tare da fashewa da wani irin kuka ta k'ank'ameshi kamar wanda aka ce mata idan ta cika shi guduwa zai yi, shi kuwa Safwan shafa gashin kanta ya shiga yi a hankali yana bubbuga bayanta "Yi shuru babyna ba na son kina yin wannan kukan, yana ta da min da hankali sosai","Ba ka so na yanzu, ka fi son Hafsa duk irin abin da nake maka baya burgeka shi ne zaka k'ara aure" Tayi maganar cikin kuka "Wa ya gaya miki cewar ba na sonki, na fi son Hafsa, kuma ke a tunaninki saboda na gaji da ke ne shine zan k'ara aure, ke sanin kanki ne, Hafsa tun kafin na aureki muke tare da ita 'yar uwata ce" Ya saka hannu ya d'agota yana share mata hawayen fuskarta sannan ya cigaba da cewa "Ina sonki sosai Amaryata","da gaske" Tayi maganar cikin farin ciki, kai ya gyad'a mata alamar "eh" sannan ya cigaba da cewa "ko da na auri Hafsa matsayinki ba zai tab'a chanzawa ba, saboda ke ce ruhina ita kuma ita ce rayuwata" Murmushi tayi tana mai jin farin ciki a zuciyarta.
Yanzu kam ta fara samun sassauci a kan zafin da take ji a zuciyarta, sambatarta yayi a kuncinta yana fad'ar "Baby nayi mantuwa ne, shiyasa na dawo zo muje ki ta ya ni d'auko takardar","to" Ta fad'a tare da mik'ewa hannunsu yana rike da na juna suka shiga d'akin ya d'suki takardar sannan ta rakashi har bakin motarsa zai shiga motar ta rumgumeshi ta baya "Baby ka tafi da ni" Murmushi yayi sannan ya juyo ta dora kanta a kan k'irjinsa "Baby ina kishinki sosai ba zan iya tafiya da ke office ba, saboda akwai maza sosai" Murmushi tayi tare da janye jikinta daga na shi tana cewa "To shikenan baby yau da wuri zaka dawo amman ko?" Kai ya gyad'a mata alamar "eh" ta marairaice fuska cikin shagwab'a tace "to k'arfe nawa zaka dawo?","6:00pm dai dai" Nan ta fara kukan shagwab'a "gaskiya ni ban yarda ba, k'arfe 4:00pm na ke so ka dawo","to rigimammiyar matata yadda kike so haka za'ai zan dawo k'arfe 4:00pm insha Allah zan yi kok'arin ganin na gama aiki da wuri" Dariya tayi sosai tare da cewa "to a dawo lafiya" Mota Safwan ya shiga ya ja har ya fita daga gidan Safna tana d'aga masa hannu.
Sai da mai gadin ya rufe kofar san ta nufi falon zama tayi a kan kujera ta lumshe ido tunda dai Safwan yace ita ce ruhinsa ai shikenan yanzu dai ta san ita ma tana da matsayi mai girma a gurinshi kuma ta san abubuwan da Safwan yake so da wanda baya so dan haka ta haka zata bi ta kwace mijinta ko da kuma Hafsan ta shigo ba ta isa ta fi ta a gurinshi ba dan ta san ba lallai ne ita ta san abubuwan da yake so da wanda baya so ba, murmushi tayi sannan ta tashi ta shiga gyara gidan wanda yayi kaca-kaca, nan gidan yayi kyau ta shiga kitchen nan ma ta gyara shi sannan ta dawo falon ta kwanta kafin k'arfe uku tayi ta dora girki ta san wajen hud'u ta gama sai ya dawo ya ci abincin da zafinsa.
*'BANGAREN GIDANSU JABIR*
Da sassafe Aunty Murja ta tashi dakyar tana dafa bango cikin sand'a take tafiyar dan kar ta tashi mijin nata daga bacci, shi kuwa Alhaji Mansur tun lokacin da ta tashi shi ma ya farka wani irin farin ciki ne ya kama shi tabbas tun kafin aje ko ina Murjanatu tana shayar da shi zumar soyayya wacce ya gaza samunta a gurin Hajiya Asiya kitchen ta shiga dan d'akin har da kitchen a cikinsa komai akwai a cikin kitchen d'in dan haka ta fere dankalin turawa ba tare da ta yanyanka shi ba, ta fasa kwai ta saka masa tattaruhu da albasa da su maggi da curry ta shiga tsoma wannan dankali tana soyashi har ta gama ta saka ta wani kwanon kas ta fito dashi ta ajiyeshi a kan teburin ta koma kitchen d'in ta dora ruwan tea ta saka masa citta,kanin fari da masoro sannan shima ta zuba a flask ta d'aukoshi ta ajiye kusa da wannan kwanon dankalin, toilet ta shiga tayi wanka sannan ta had'a masa ruwan wanka ta fito ta shirya cikin wata atamfa kofi colour d'inkin riga da siket tayi kyau sosai zama tayi kusa da Alhaji Mansur d'in dan ta tashe sa yayi wanka ya ci abinci kada ya makara gurin aikinsa.
Kallonsa wata iriyar kunyarsa take ji tun jiya, murmushi tayi tare da shafar fuskarsa, idanuwansa ya bud'e ya zuba su kanta suka had'a ido tayi saurin saka hannuwanta ta rufe fuskarta tana dariya, tashi yayi zaune ya jawo ta jikinsa yana kok'arin cire hannuwanta daga fuskarta, Hajiya Asiya ta banko kofar d'akin da k'arfi idanuwanta suka sauka a kan su ganin Aunty Murja a kan cinyar Alhaji Mansur shi kuwa ya rumgumota jikinsa suna ta kokawa wani irin ihu ta kwalla.
Babu wanda ya ji ihun domin kuwa kowa yana d'akinsa kuma akwai tazara mai yawa tsananin d'akin Abba da sauran d'akunan, Aunty Murja ta bud'e ido k'irjinta sai bugawa yake amman a fili ba ta nuna tsoro ko fargaba ba, ta shiga kok'arin tashi daga jikin Alhaji Mansur d'in amman bai ba ta izinin yin haka ba, ya rumgumeta sosai dan ko motsi ma bata iya yi, Hajiya Asiya zuciyarta kamar zata fashe "to tsohuwar 'yar bariki ke har kin isa har kina da matsayin da zaki zauna a jikin miji, to wallahi yau sai kin gammace da baki auri Mansur ba" Tayi maganar cikin yanayin tashin hankali.
Juyo da fuskar Aunty Murja, Alhaji Mansur yayi suna kallon kallo wani irin murmushi yake sakar mata ita ma tana mayar masa da martani "meyasa ki ka je kika yi wanka ba tare da kin tashe ni mun yi tare ba" Abba yayi maganar yana kallon cikin idon Aunty Murja, ita kuwa duk sai ta ji kunya a wani b'angaren kuma ta ji babu dad'i domin Hajiya Asiya tana nan kuma ta san ta ji abin da ya ce mata.
"Ka yi hak'uri ba zan sake yin makamancin irin haka ba, na ga ka na bacci ne shiyasa" Ta bashi amsa domin ta san inda tayi shuru zai ji haushi, kuma yayi fushi da ita,ita kuma a duniyar nan ta tsani Alhaji Mansur yayi fushi da ita, dan ba za ta iya jurewa ba.
"To daga yanzu ba bacci ba ko mai kika ga ina yi indai zaki yi wanka ki tashe ni muyi tare","to insha Allahu zan yi yadda kace Yaya" A dai-dai kumatunta ya sumbaceta tare da k'ara rumgumeta.
Hajiya Asiya kuwa ta ji duk abin da suka ce, cike da b'acin rai ta ce "dabba kawai abin da ka iya kenan shashasha kawai wanda bai san meyake ba, kuma wallahi ba ka isa ba" Nufarsu tayi gadan-gadan ta d'auki wannan kwanon dankali ta bugashi a k'asa ya tarwatse gaba d'aya a k'asa, cikin zafin nama Alhaji Mansur ya tashi da niyyar yayi mata dukan tsiya.
Aunty Murja ta rik'oshi tana murmushi "dan Allah ka barta bai kamata daga tashinka ka fara da b'acin rai ba, kasan ba na son ranka ya dinga b'aci dan Allah ka kyaleta kaji Yaya" Wani irin mari Hajiya Asiya ta zabgawa Aunty Murja wanda sai da ta ji shi har tsakiyar kanta ai kuwa kafin ta sauke hannunta daga fuskar Aunty Murja ita ma ta ji saukar na ta marin a fuskarta wanda ya gigitata har sai da ta saki ihu, haka Alhaji Mansur ya finciketa har sai da suka isa bakin kofar ya hankad'ata ya mayar da kofar ya saka key.
Dawowa yayi gurin Aunty Murja tare da dafe gurin da Hajiya Asiya ta mareta sumbatarta yayi a gurin sannan ya rumgume abarsa tare da zama a kan gadon, a kan k'irjinsa ta kwantar da kan ta tare da fashewa da kuka, hankalin Alhaji Mansur yayi matuk'ar tashi ya rasa inda zai tsoma ransa ya ji dad'i d'agota yayi idanuwansa sun kad'a sun yi jajahur "Haba Murjanatu dan Allah ki taimake ni ki yi shuru ki dena kukan nan kin san ina sonki sosai ba na son ganin zubar hawayenki" Goge mata hawayen ya shiga yi amman wasu na k'ara zubowa cikin muryar kuka Aunty Murja take cewa "ni Yaya ba wai marin da tayi min ne yasani kuka ba, irin abin da ta ce maka ne yasani kuka" Murmushi yayi tare da cewa "to ki daina kukan nan ya isa haka,ai idan ita ta fad'a min maganganu da ba su dace ba, ke na san zaki faranta min rai ki sa na manta da abin da ta ce min".
Haka dai yayi ta rarrashin ta har tayi shuru ta raka shi ya shiga toilet dan yayi wanka ita kuma tana tsaye a bakin kofa tana jiranshi, yana fitowa ta tare shi da towel tana goge masa jiki dukka shima ya goge a cikin toilet d'in, ita ta zab'ar masa kayan da zai saka, sannan ta taimaka masa ya shirya ya fito a asalin angonshi ruwan tea d'in da ta had'e masa ta zuba masa ta bud'e fridge ta d'auko meatpie da cincin d'in da Hajiya Mama ta saka aka yi mata ta ajiye masa tare da cewa "ga wannan duk da nasan ba lallai ka koshi da shi