Showing 51001 words to 54000 words out of 80263 words
da yana yin aikinka wasu abubuwa ba za ka iya gudanarda su da kanka ba, in fact Daddy naga momma tana kula da ita sosai.
Ajiyar zuciya Daddy ya yi ya ce "please.....Sultan idan ina magana ta arziki ka daina sako min mommanka, wallahi ko sunanta banaso ji.
Cike da mamaki Aliyu yake kallon mahaifin nashi kafin ya nisa ya ce "Daddy kun sami matsala ne da ita...?
Ba ko d'aya kawai dai banaso zancenta mu ajiye shi a gefe, muyi wani.
Shikenan Daddy wane country kake tunani a fita da ita sai na nemo muku visa....?
Nayi magana da Dr Williams ya ce akaita Indian saboda suna da kwararun likitoci kwakwalwa.
Ba matsala Daddy yaushe kake so tafiyar...?
Nan da two weeks shima a dalilin inaso naje Lagos, da na dawo sai muyi tafiyar.
Ba damuwa ka barmin komai a hannuna.
Cewar Aliyu yana mai mik'ewa tsaye ni zan wuce Daddy daga nan suleja zan wuce na kwana biyu banje gidan gona ba, jiya ma Abbas ya kirani yana gayamin abincin kifi ya k'are.
Allah ya tsare ya kai ka lafiya.
"Amin Daddy ka kula da kanka banda yawan tunani.
Murmushi kawai Daddy ya yi yana jin k'aunar d'an nashi na yawo a sassan jikinshi.
Abinda Daddy baisani ba tun daga lokaci da suka fara magana momma tana la6e, duk firar da ta wakana atsakaninshi da Aliyu akan kunnenta saida taji motsin fitowar Aliyu ta ruga da gudu ta 6oye cikin curtain saida yafita sannan tafito daga ma6oyarta.
***----*****-----****
Barrister A tana dawowa daga raka Aliyu ta tattara plates d'in da suka yi amfani ta shiga kitchen ta wanke, tana kammalawa ta zari Hijabinta tafito compound adaidai baranda da tasaba tsayuwa tayi tsaye tana kallon shige da fice na mutanan gidan can ta hango Sa'eed yana ba flowers ruwa, wani gajere tunani tayi ta nufi wajenshi yana ganinta ya runsuna ya gaidata ta amsa tana d'an siriri murmushi "Sa'eed idan ka kammala aikinka ka sameni a garden I have some important matter to discuss with you.
Duk da ya tsorata da jin farucinta bai bari fuskarshi ta nuna hakan ba, sai cewa ya yi okay ma'am.
Ta juya ta nufi garden ta zauna tana jiran zuwanshi bata jima da zama ba sai gashi ya zo, kujerar da ke facing d'inta ta nuna mishi please have a seat!
Ya zauna yana d'ari-dari ka saki jikinki Sa'eed tambayar da zan maka tana da matukar muhinmmanci.
To ma'am Allah yasa ina da amsar tambayar naki.
"Amin!
Tafad'a had'e da yin shiru na wani d'an lokaci ta nisa had'e da cewa Sa'eed I trust you completely shine dalilin da yasa na kira ka anan.
Sa'eed!
Yes ma'am!
me kasani akan mahaukaciyar da ke cikin gidanan....?
Wacece ita menene matsayinta anan gidan?
Shiru ya yi na few seconds saboda haka barrister A bata katse mishi shiru nashi ba, sai ma tayi amfani da shiru nashi tana karantar yana yinshi.
"Asanyayye Sa'eed ya d'ago saida ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce "ma'am gaskiya ba komai nasani akanta ba zan ba ki labari iya abinda nasani, saboda ban wuce ten years da fara aiki a gidanan ba wani abu yafaru akan idanuwana wani kuma nasamu labari daga bakin wasu ma'aikata da suka rigani zuwa gidan
"Kaman yanda nasamu labari Hajiya Maryama ita ce uwargidan Alhaji M Ardo, tsawon shekaru 28 kenan da ta had'u da wannan lalura, doka ce agidanan ba'a bari ma'aikaci ko d'aya ya kusancin koda baranda flat d'inta ne, duk yawan mutane da ke gidanan idan kika cire Hajiya Zaituna ba wanda ke shiga wurinta.
Ni kaina ina mamaki wane zunubi ta aikata da yasa mijinta ya wofitar da ita har haka.
"Abinda zai ba ki mamaki ma'am tsawon shekaru goma da nayi agidanan banta6a gani wani ko wata daga danginta ko na mijinta da suna ya zo ganinta ba.
"Barrister A ta sauke zazzafar ajiyar zuciya ta talla6e kumatunta da hannayenta, ta ce "Sa'eed anaka hasashe me ya kawo wannan rashin kulawa da Maryama take fuskanta daga bangare biyu mijinta da danginta...?"
Meyasa kuma iya Momma ce kadai ke shiga flat d'inta...?
"Sa'eed ya nisa had'e da juyawa ya kalle hagu da damarshi saida ya tabbatar da ba wani ido, sannan ya ce ma'am maybe yana da alak'a da labarin da maigadi Daniel ya ta6a bani.
"Wane irin labari....?
Cewar barrister A cikin k'osawa.
A yanda Daniel ya labarta min ya ce Hajiya Zaituna asiri tayi ma Alhaji M Ardo shiyasa baya kulawa da Maryama kuma yana zargin ita ce silar haukacewa Maryama, saboda akwai wata rana da nurse d'in da take kula da Maryama ta zo dubata ya yi la6e ta window ya ga lokaci da nurse d'in take yi ma Maryama wata allura wacce ba ko shakka batada nasaba da ciwonta, ya ce lokaci da aka yi mata allurar yana kallon yadda ta dinga gurnani tamkar ranta zai fita, daga bisani tayi bacci ma'am duk yadda kike tunani wannan murd'ade al'amari ya wuce da saninki gidanan tamkar gidan Rina ne komai nashi ya sha bamban da sauran gidaje.
"Shiru barrister A tayi kanta ya dau zafi ba k'aramin rud'ani ta shiga ba ta sauke ajiyar zuciya yafi a kirga da kyar ta k'irk'iro murmushin dole ta ce "Sa'eed nasan za ka yi mamaki yadda nake maka wad'annan tambayoyi na yarda da kai Sa'eed shiyasa na za6e ka don ka warware min wannan al'amari, idan har da gaske momma ce silar haukar Maryama ni kuma na dau alk'awali sai nayi silar dawowa da ita cikin hankalinta, kuma sai na daidaita tsakaninta da Daddy wannan alk'awalina ne.
"Nima ina goyon bayanki hundred percent ma'am idan kina buk'atar wani taimako daga gareni ashirye nake da na taimaka.
"Nagode Sa'eed indan buk'atar hakan ta taso zan nemi ka kuma wannan ya zama sirri atsakaninmu.
"Karki damu ma'am insha Allah ba wanda zai ji wannan sirri daga gareni.
Cewar Sa'eed yana mai kallon fuskar barrister A.
Shikenan Sa'eed za ka iya tafiya.
Nima nagode ma'am ya karashe magana had'e da mik'ewa tsaye ta bishi da kallo har ya 6acewa ganinta sannan tayi ajiyar zuciya, ko ta wane hali dole ta nemi Baaba laraba tasamu wasu information daga gareta.
"Mik'ewa tayi ta koma flat d'inta da zumar daga baya zata nemi Baaba laraba.
A bangaren momma kuma tana gani ficewa Aliyu ta koma bedroom d'inta ta kira Jarumi a waya ta bashi labari abinda ke faruwa, sosai ya harzuk'a har tana jiyo hucinshi kaman zai kama da wuta.
Ranshi a 6ace matuka ya ce "Abinda nakeso da ke Zaituna ki bi kowace irin hanya ce ki hanawa barrister A shiga flat d'in Maryama, shigarta wurin zai iya 6ata mana plans da sauri shi kuma M Ardo ki barni da shi ni nasan ta yanda zan bullo mishi.
Bai tsaya jin ta bakinta ba ya yi hanging up.
***"""***"""****
Around 9:20pm Aliyu ya shigo gida Saidai fuskarshi ahad'e ba fara'a ko k'adan ba kaman yadda ya fita da safe ba.
Tana mishi sannu da zuwa ko inda take bai kalle ba, balle ya amsa mata ya ra6a ta gefenta ya haura sama, ta bishi da kallo baki sake tayi shiru tana tunani laifi me tayi mishi da zai mata haka, iya saninta har suka rabu batasan ta mishi wani laifi ba ko bayan tafiyarshi ya kirata a waya kuma ko awayan lafiya qalau suka rabu.
"Maybe ko awaje ne aka 6ata mishi rai to ni miye laifina da laifin wani zai shafe ni..?
Tafad'a a k'asan zuciyarta har tayi niyyar ta share shi sai kuma tafasa, ta haura steps tanufi bedroom d'inshi ta murd'a handle had'e da sallama ya amsa mata adak'ile shima ya amsa ne saboda sani darajar sallama da ba zai amsa mata ba, ko inda take bai son kallo don haka ya juya mata baya yana cire kayan jikinshi da sauri ta nufi bathroom ta dauko mishi bathrobe ta mik'a mishi mtsss....ya ja mata tsaki had'e da ra6ata ya shiga bathroom sai kuma ya lek'o da kanshi sounding very angry ya ce "kada ki kuskura na fito na sameki a d'akina daga haka ya rufe k'ofa, ya barta tsaye turuss...tana kallon k'ofar bathroom jin saukar ruwa yafara wanka yasa tafice for the first time da taji tausayin kanta ya lullu6eta da ta tuna da irin zazzafar soyayyar da take mishi bata ankara ba taji saukar hawaye akan kumatunta, da saurinta ta sauka k'asa ta shiga kitchen ta jingina bayanta a kitchen cabinet tasa kuka mai cin rai she is totally confused, me tayi ma Aliyu zai mata wannan wulak'anci.
Da ada ne zata iya daurewa a yanzu kam ba za iya ba, saboda yariga ya saba mata da kulawarshi da soyayyarshi, idan ya ce zai juya mata baya ba ko shakka zata iya susucewa ko kuma tayi 'yar k'aramar hauka.
"Ta kasa jurewa ta share hawayenta tafito ta zauna a dining table, tana jira ya fito cin abinci tafi 10 minutes a zaune amma ba Aliyu babu labarinshi, tana gani haka tagano nufinshi ko abincin nata ba zai ci ba.
Zata iya jure komai daga gareshi amma ba zata iya jure ya kwana da yunwa ba ta tashi da sauri tanufi upstairs.
Jeeddah Aliyu
[7/27, 12:18 AM] Jiddah Aliyu: *DA D'UMID'UMINSU DAGA ALK'ALUMA SHIDDA NA KUD'I NE IDAB KANA SO SAI KA TUNTUBE WANNAN NUMBER*
0813943903
*SAI KA TURA SHEDAR BIYANKA GA WANNAN NUMBER*
08166177830
*ZA KA IYA TURAWA WANNAN NUMBER KATIN MTN*
08039424298
*SHEDAR BIYANKA KATINKA GA WANNAN NUMBER*
07084161619
DA D'UMID'UMINSU DAGA ALK'ALUMA SHIDDA
*JIDDAH ALIYU*:-```GIDAN RINA```
*A'ISHA DANSABO*:-```BURIN ZUCIYA```
*KHADIJA AHMAD KDEEY*:-```DA CIWO A ZUCIYATA``
*RAHMA MUH'D RUFA'I NALELLE*:- HAYATUDEEN
*SLIMZY*:- IZZATA
*SAFIYA GALADANCHI*:- TANA K'ASA TANA DABO
*GIDAN RINA*
*31*
Ahankali ta murd'a handle k'ofar ya bud'e ta danna kai, ta hango shi zaune akan resting chair ya lankwashe k'afarshi d'aya akan chair d'in, yayin da d'ayan k'afar take k'asa ya saka laptop atsakiya yana operating bud'e k'ofar da tayi yasa ya d'ago afusace ya ce "whats the hell are you doing in my room...?
Banace banaso ganinki ba me ya dawo da ke...?
"Tuni idanuwanta suka ciciko da hawaye she can't take its anymore ji take kaman ta d'ora hannu bisa kai ta dinga ihu, cikin rawar murya mai dauke da alama so yi kuka ta ce "Yalla6ai I'm sorry...ni bansan laifi da nayi ma, ba don Allah daure ka fad'amin laifi da nayi maka na rok'eka gafara.
"Ke dallah rufemin baki I can't wasting my precious time akanki don haka kifita ki bani wuri.
Kuka ta fashe da shi tana fad'i "Ba zan fita ba koda za ka kasheni Yalla6ai haba don Allah meyasa za ka dinga treating dina haka..?
Cikin muryar fushi ya ce "Duk wannan kuka da kike yi na munafuci ne you really disappointed me Amina, me nayi miki da za ki za6a ki wulak'anta min mahaifiya...?
"Kukanta ya tsaya cak...tasaki baki da hancinta tana kallonshi wato tanan momma ta 6ullo.
Ba shakka kuwa tayi nasara amma zata tabbatar ta rusa nasararta ta.
Da sauri ta durk'usa daf...da shi ta rik'o soft hand d'inshi ta matse anata tana massage palm dinshi ahankali, hawaye na kai da kawo akan kumatunta ta tausassa muryarta, ta ce "Kada Allah ya kawo min wannan bak'ar rana arayuwata da zan wulak'anta koda 'yar aiki mahaifiyarka ce Yalla6ai balle mahaifiyarka.
Idan har ni Amina zan iya wulak'anta mahaifiyarka to ashe kuwa zan iya wulak'anta tawa mahaifiya.
"Tun daga lokaci da tafara magana jikin Aliyu ya yi sanyi, shiru ya yi yana tuno wacece momma tun yana cikin zani goyenshi zai iya bada labarin halayyata, yafi kowa sani makircin mahaifiyarshi musanmman da ya tuna bataso aurenshi da Barrister A saboda haka zata iya bin kowace irin hanya don ta kawo 6araka atsakaninsu.
"Cikin sanyi murya ya ce "Mekika je yi flat d'in Maryama...?
Ba komai Yalla6ai kawai naga anbar flat d'in da dirty shine nasa housemaid su tsaftace, ni kaina bansan hakan zai jayomin laifi awurin momma ba.
To amma ni ba haka momma ta gayamin ba.
"Zaro idanuwa tayi tare da fad'i na shiga uku me ta ce da kai Yalla6ai...?
"Murmushi ya yi had'e da d'ago ha6arta yana kallon cikin idanuwanta, ya ce manta kawai banaso maimata zance, ni kaina banaso ki sake zuwa flat d'in wannan matar she's very dangerous zata iya cutar min da ke ba zan manta ba lokaci da ina k'aramin yaro na ta6a shiga flat d'inta kinsan me ya faru...?"
Cike da zumud'in son jin labarin ta girgiza kanta.
A wannan lokaci rufeta kawai ake yi a d'akin kwanata, tsautsayi yasa ni shiga wurinta tana arba da ni ta k'ank'ameni a jikinta kaman zata mayarda ni cikinta, ga wani irin gunji kuka da take yi da kyar aka cireni daga jikinta, tun daga lokaci momma ta hanani shiga wurinta da yake nima na tsorata matuk'a shiyasa har zuwa yau da nake ba ki labari k'afana bai sake shiga wurinta ba.
"Tagwaye ajiyar zuciya ta sauke ta rangwad'ar da kanta tana kallonshi ta ce "gaskiya Yalla6ai matar nan tana da ban tausayi ya kamata ku taimaka mata, tsawon shekara 28 tana rufe ba fa kwana 28 bane shekaru ne masu yawan gaske don kawai Allah yasa tana da saura kwanaki a duniya da tuni an shafe babinta a duniya.
Ta6e baki ya yi yana fad'i a kwananan Daddy zai fita da ita Indian, insha Allah zata sami lafiya.
"Yauwa Yalla6aina tashi mu je kaci abinci.
Mik'ewa ya yi yana murmushi suka sauko downstairs hannayensu sark'e da juna, suka nufi dining area d'aya daga cikin kujerun dining table taja mishi ya zauna ta dauki plate tayi mishi serving, sannan taja kujerar da ke facing d'inshi ta zauna tare da serving kanta, ahankali suke cin abincinsu ba ka ji komai sai k'arar spoons suna kammala cin abinci suka koma falo, tana zaune akan three sitter yayin da ya yi pillow da cinyoyinta sai fira suke abinsu kaman ba d'azu ya gama fushi da ita ba.
*****"""****"""****
*AFTER ONE WEEK [BAYAN SATI D'AYA*]
Tuni barrister A tafara aiki da Greatest Nigerian lawyer firm.
Team ne na kwararu lawyers the whole nigeria ake ji da su. kasancewarta kwarariya ta kuma san makamar aikinta yasa cikin k'ank'alin lokaci sunanta ya yi fice.
"A hankali take tafiya tafito daga wuse zone magistrate court hannunta na dama rik'e da jakkar laptop d'inta, ta nufi parking space ta shiga motarta tayi reverse tafice daga harabar kotun, direct gida ta wuce tana gama parking tafito har ta nufi hanyar flat d'inta sai kuma tafasa ta nufi hanyar na Maryama, tasha magiya kafin Baaba laraba ta bud'e mata k'ofa bayan ta shigo saida tafara lek'awa d'akin Maryama, taga halin da take ciki sannan ta dawo falo wurin Baaba. falon ya dauki shiru na wani d'an lokaci kafin Barrister A ta kawo k'arshen shiru ta hanyar cewa Baaba ki yi hak'uri da ta k'urawa da nake miki wanda kusan kullum idan zan fita office ko na dawo sai na biyo flat d'inan ina miki magiya ki budemin k'ofa ga alama yau dai kin gaji da naci nawa, shiyasa kika bud'emin batare da korafi ba.
"Ajiyar zuciya Baaba tayi kafin ta ce ki yi hak'uri 'yar nan banida za6i da ya wuce na hanaki zuwa sasshe nan, yau dinma na yanke shawara na bude miki ki shigo saboda akan idanuwana Zaituna ta fita, yanzu ma ina shawartarki da ki yi gaggawa tambayata abinda kike so sani akan rayuwar Maryama ni kuma ashirye nake da na ba ki amsa.
"Murmushi barrister A tayi tare da gyara zamanta, ta ce "Baaba menene alak'arki da maryama...?
Tsawon wane lokaci kika dauka tare da ita...?
Me kuma kika sani dangane da ciwonta....?
"Saida Baaba ta gyara daurin d'an kwalinta kafin ta ce "Alak'ata da maryama ta samo asali tun shekara 32 da suka wuce abaya, na kasance 'yar aiki a wurin maryama.
Mijina ya mutu ya barni da marayu 'ya'ya har guda 4 mahaifina ya mutu mahaifiyata kuma makauniya ce sai tayo bara muke samu abinda mu ka ci saboda ba wani dangi da zai iya tallafawa rayuwarmu, saboda suma suna fama ne da nasu talauci.
"Asalina ni 'yar suru local government ce take cikin jahar kebbi, tsananin talauci ne ya kawo ni aikatau a garin Abuja wanda anan Allah ya had'ani da Maryama had'uwata da ita shine silar da rayuwarmu ta canza ni da zuri'ata, idan nace zan tsaya gayamiki irin dibin alkhairi maryama agareni wannan makirar mata zata dawo ta tararda ke anan.
"Haka ne Baaba sai ki hanzarta ni kaina banaso ta dawo ta tararda ni.
"Baaba tayi gyaran murya tare da cewa ciwon Maryama ya samu asaline alokaci da take dauke da juna biyu har na watani 6 sai kawai muka waye gari da ita a haukace, alokaci Alhaji ya nema mata magani daga bayane ya daina kulawa da ita kaman dai yadda muka waye gari da ita ahaukace, haka muka waye gari ba wanda ke tada koda zancenta ne.
"Tsananin tausayin rayuwar Maryama da d'inbin alkhairi da tayi min abaya yasa na za6e na sadaukar da rayuwata agareta, shiyasa duk tsawon wad'annan shekaru nake zaune da ita duk da a wasu lokuta Zaituna tana min barazana, ina da yak'ini tabarni na zauna da maryama ne saboda tasan ba wanda zai iya zama da ita sama da ni.
wannan shine kad'an daga cikin abinda nasani akan rayuwar maryama.
Baaba a labarinki kin ce Maryama tana da juna biyu shin ta haife shi idan kuma ta haifeshi ina abinda ta haifa...?
"Maryama ta haifi cikin jikinta 'ya mace sai dai bata zo da rai ba kaman yadda nasamu labari daga bakin Zaituna.
"Kina nufi lokaci da ta haihu ba ki tare da ita ne...?
Kwarai bana tare da ita saboda na tafi suru sakamakon rasuwar da mahaifiyata tayi.
"Numfashin Barrister A ta sauke kafin ta ce "Allah yajik'anta ya gafarta mata.
Amin!
Cewar Baaba.
"Barrister A ta Kalle Baaba ta ce "ki kwantarda hankalinki Baaba insha Allah maryama tayi kusan samu lafiya, a cikin kwanaki nan Daddy zai fita da ita k'asar waje.
"Murmushin takaici Baaba tayi had'e da