Showing 36001 words to 39000 words out of 59977 words

Chapter 13 - BABANA DA MIJINA BOOK COMPLETE Fertymerh Zarah --.pdf

Unknown   

22 Mar 2025

4481


'Fulani tace boyar Allah tabani tausayi Wlhy, fatyma batada matsala a rayuwarta Duk Wanda ya
xauna da Ita xaiji daďi,

Dr Deen na tsaye hannuwansa sarqe a qirjinsa yana saurarensu, idanuwansa xube akan
fuskarta, komai bai ce ba,

Fiye da minti talatin kafin ta farfado, da addua a bakinta tana buďe idanuwanta hawaye na
soma xubo mata,

Sai suka taru akanta dukkansu suna bata baki, rarrashinta suke tare da fahimtar da Ita wasu
abubuwa game da irin Wannan dake faruwa,

Sai taji xuciyarta tayi sanyi ita matsalarta Kada a xargeta akan wani abu amma tayi alqawari a
xuciyarta kome xai faru a asibitin baxata qara leqa labour room ba, baxata qara taimako ba
iyakarta duba patient,

Bayan kowa ya fice ďakin ya rage ita da Dr Deen, sai ta dafe kanta da hannunta duka biyu tana
tuna abinda ya faru a ďaxu, ďagowar da xatayi suka haďa ido dashi yana kallonta sai da
gabanta na faďi, tayi qarfin halin mgn,


'Likita ya haquri? Ya sauke numfashi bayan ya ďauke idonsa akanta,

'haquri mun gode Allah fatyma, shima yaron ya koma ai, ta dubesa a razane,

'shima ya rasu? ya gyada Kai yana kallonta,

'Subhanallah, Wayyo Allah, Allah ya gafarta masu ya baka haqurin rashinsu ya musanyama da
mafi alheri,

Yasa yatsa ya ďauke guntuwar kwallah yana kallonta,

'I have no one in my life, babana kawai, no mother, no wife, no child, no brothers an sister, only
my father and family,

Ta sauke ajiyar xuciya kanta a qasa batasan dalilinsa na gayamata wannan ba sai dai a
xuciyarta tana tausayamasa,

Daga wannan bai qara cewa komai ba ya fice daga ďakin, itama fitowa tayi ta nufi office ďinta
kayanta ta ďauka ta fice daga asibitin gaba ki ďaya,

Ranar Sa'eed ya xo gidan, sun jima suna hira haďe da gayamasa matsalolin da take fuskanta a
ynxu asibiti, yace xai tayata addua itama ta dage.....


Baba yayi neman tedy bai gantaba hankalinsa yayi matuqar tashi domin matsafarsa ce aciki
wacce da Ita yake bata ba'a ganinsa a duk sanda xaiyi wani sharri, ba shiri ya jewa sima da
bayanin batan tedy ďinsa, ta ďauki wata ta basa,

Tun daga lokacin yasa ido sosai akan gidansa dan ganin mai masa shige da fice a ďakinsa,

Fauxie Kuwa kwata kwata ta manta da tedy da ta boye a under bed ďinta bata qara bi ta kanta
ba,

Some months.....

Cikin Iman ya shiga watan haihuwa, duk wani so, kulawa da gata ba Wanda bata samu daga
Deedah, yadaina fitar dare kullum yana tare da Ita komai shi ke mata, shi ke kaita asibiti kuma
shi ke daukota,

Soyayya suke mai cike da kulawa a tsakaninsu,duk burinsa na kan cikin a ynxu ita kanta Iman
tasan Deedah yafi ta son cikin,

Duk wannan abin da ake ciki baba bai taba sanin Iman Nada ciki ba, shi rabonsa da Ita har ya
manta, saboda sun daina bincike akan ta ynxu qananan yara yake satowa yana kawowa sima
tun lokacin da matar ta ganesa a asibiti bai qara shiga ba,


Da dare ta fito kitchen ďauke da plate na nama, fauxie na bayanta da tedy a hannunta, ta xauna

itama ta xauna kusa da ita,


'anty shi baby kullum sai yaci nama ne?
'Tace eh,
'tor anty ki sammin,
'a'a na baby ne kaďai wannan, ba kinci naki ďaxu tare da yaya ba, ta tunxure baki idanunta
sunyi rau rau kamar xatayi kuka, iman ta ďan dubeta ta gefen idanunta,

'crying baby, kina taba jin baby yayi kuka Kuwa ? ta girgixa kanta tana kallonta,

'idan kikayi kuka ma baxai fito ba, shikenan bakida jariri, tayi Saurin goge fuskarta,

'anty yaushe xai fito? Iman ta miqa mata sauran Naman tana faďin,
'ya kusa fitowa ai,
'anty idan na mutu kiyimin sadaka, wai inji malam ana yiwa Wanda ya mutu sadaka,
'tor idan ni na rigaki mutuwa fa?
'nima xn miki sadaka anty,
'ai nafiso ki mutu kibarni dan Idan na mutu bansan ya rayuwarki xata kasance ba, bnsan inda
xaki xauna ba,
'anty inda yaya xan xauna ko inda Amira,
'oh oh mutuwa ba ynxu ba fauxie, fata ta gari sai naga aurenki da sultan,
'anty ni bana sonsa yaya nakeso, iman ta dubeta,
'da gaske fauxie, ta gyada Kai tana kallonta,
'kinga shi yaya yana siyamin ice cream, chocolate, biscuits, tedy, yana daukana,
'tor shima sultan xai maki haka fauxie in banda abinki me xakiyi da mijina ai ya maki tsufa,
'anty ni banason sa yaya nakeso,
'ke Kinsan miye so ne? tayi shiru tana kallonta,
'kinga kin tadamin Kwaďayin ice cream ďauko min a fridge,
'babu shi na shinye,
'kiramin Suleiman yaxo ya siyomin, fauxie ta fice da gudu bata jima ba sai gata ta dawo,
'anty bayanan..
'ďan lami fa?
'duk ba kowa a gidan baba, ta duba agogon hannunta 9pm,
'ďauko min hijab ďina da makullin mota kixo muje...

Da gudu ta haura Sama taje ta ďauko sai tsalle takeyi,
'anty kema kina shan ice cream ashe,
'bani xnsha ba baby xai sha,
'baby ya iya sha ne anty,
'sosai ma.... ta buďe motar ta shiga itama fauxie ta shiga,
[22/03, 7:05 p.m.] Pherty: Sanda suka isa gurin siyarda ice cream ďin, tana daga cikin
Mota ta baiwa fauxy kuďin taje ta siyo, tana kallonta daga cikin motar sai tsalle take Acikin

shagon, ta sauke ajiyar xuciya dai dai lokacin da sukaji Kukan harbin bindiga, ta soma waige
waige kamar mai neman wani abu, ta juya tana kallon fauxy dake tahowa da baqar Leda a
hannunta sai Kuma taga ta tsaya tana kallon wani gu, ta sauke glass ďin motar da sauri tana
mata mgn,
'what are you waiting for Fauxy?
'lah anty... ta juyo tana kallon Iman, ta daka mata tsawa,
'kixo mubar gurinnan, da gudu fauxie taje ta shiga motar ta rufe ta juyo tana kallon Iman dai dai
lokacin da take tayar da mota,

'anty naga yaya da bindiga tare da wasu mutane, taja wani uban birki tana kallonta xuciyarta na
bugawa,

'qarya kikeyi bashi bane,
'Allah anty naganshi, yana xaune a motar can ta nuna mata da yatsa,

Iman taja motar xuwa inda ta nuna mata, ta ganshi da waya a hannunsa yana latsawa, a
gabansa bindiga ce ajiye, ta juya tana kallon mutanen dana shiga ďayan shagon da bindiga a
hannunsu,

ďagowar da Deedah xaiyi suka haďa ido da ita, fauxie na ganinsa tayi waving hannunta tana
murmushi,

'yaya.... , iman taja motar da qarfi, hankalinsa yayi matuqar tashi ya fito daga cikin motar tuni ta
fice,

Wani birki da taja sai da fauxie na faďi qasan seat, ta ciro wayarta ta Kira Suleiman haďe da
gayamasa inda take, ji tayi baxata iya driving ba, qafafunta rawa suke dama gasu a kumbure,
sai ta fito daga cikin motar tana kallon titi ita kanta batasan a wane hali take ciki ba,

'anty meyasa kika fito, kina jiran yaya ne, bata kula taba,
'anty kixo muje gida, nan ma bata kulataba,

Tana gurin tsaye Suleiman ya iso akan mashin, yabiya mai babur kana ya nufeta,

'gani hajiya, ta miqa masa key ďin mota,
'qarasa dani gida, ya karbi key ďin ta xagaya gidan baya ta shiga motar,

Sun fara tfy ya dubi Fauxiya sai ta wangale masa baki tana dariya shima dariya yayi mata,

'kagani mun siyo ice cream nida anty, ta nuna masa,
'eyye ashe xamu sha tare,
'ka Kira yaya ya siyoma naka yana can da bindiga a hannunsa,

Iman ta ďago ta kalleta sai taji Suleiman na faďin,
'sai kace nice ke, ni naki dai xn sha, ta fara dariya....

Suna isowa gida Iman ta fice, sulaiemn yaja hannunta sukayi bangaren baba,

'jeki ďebo kuďi kafin baba ya dawo, xnje na siyo mai insa a mashin gobe muje yawo har inda
qawarki Amira,

'da gaske,
'e mana,
Ta shiga tana murmushi ta ďebo kuďin, sai ta ďauko wannan kwalbar da tagani ranar, tare da
wata tukunya mai Jan kyalle akai,

Tana fitowa tabashi kuďin ya cusa aljihunsa ya rakata har gida kana ya fice yana murna,

Tana xuwa dakinta ta nufa ta ajiye kayan kana ta nufi ďakin Iman ga mamakinta sai ta sameta
tana kuka sosai,

'anty meyasa kike kuka? Kuka take sosai Kamar ranta wannan dalilin ya Sanya fauxie kuka,
suna haka Deedah ya shigo da qatuwar akwati a hannunsa, ya ajiyeta gefe kana ya nufi Iman
jikinsa a sanyaye,

'kiyi haquri ki yafemin Iman, na Karbi laifina nagaji da boye maki,

Ta dubesa da idanunta jawur, har wani qullewa mararta keyi,

'ka dade kana cutar dani Deedah, haram nake ci nake sha nake kwanciya acikin haram, ya
katseta da sauri,

'bana ciyar dake da haram Iman, tun kafin na aureki nake wannan sana'a, ta xare ido sosai tana
kallonsa xuciyarta na bugawa,

'amma Wlhy duk share ďin da ake bani ban taba sanya shi acikin kuďin halal ďina ba, kingansu
nan sune acikin akwati nake tarawa a yau na kawo dan ki yarda dani,

'babu wata sauran yarda tsakanina dakai Deedah, baxan iya yafe ma ba baxan iya cigaba da
xama dakai ba tsawon lokutta da dama kana cutar dani, ka sake ni Deedah, ta fashe da kuka
sosai,

Hankalinsa ya tashi ya juya yana kallon fauxie, ice cream take sha hankalinta baya kansu,
Kukan Iman har cikin xuciyarsa yake jinsa sai ya tsinci kansa shima yana Kukan,

'Iman inayin sata ne badan na so ba, na fara ne sanadiyar ummata da bata lfy domin na
siyamata magani, bayan mutuwarta na nemi aiki ban samu ba saboda banida ko Naira da xn
bada a Samomin aiki, oga nas ya sanyani wannan aikin ta dalilinsa na shiga wannan harka,
bayan na sami aiki na nemi na fita sukamin baraxana da rayuwata, na cigaba da xama dasu
badan naso ba amma Wlhy Iman ban taba amfani da duk kuďin da Muke robbery ake rabawa
ana bani nawa, kingansu duka acan, halal ďina ne a account ďina kuďin albashina, duk abinda
ke gidannan da kuďi na nasiya, saboda ke tsawon watanni nan nadai na bibiyarsu nake
xaunawa dake, sai na fahimci suna harin rayuwarkine suna so su kasheki saboda xn bar fashi
ta dalilinki, yau ma dana bisu tsautsayine bn fita daga motar ba, Ina bibiyarsu ne saboda ke
bana son Abinda xai sameki idan suka fahimci nadaina fashi, believe me Iman wallahi bana
fashi yanxu na dade da shiriya tuntuni, ki yafemin Iman Kada ki rabu dani kodan yarona dake
jikinki....

ta dubi cikin nata kafin ta maida kallonta garesa,
'I can't forgive you Deedah, cikin ma bana so, I hate you Deedah baxan iya xama da barawo ba,
meyasa ka boyemin tuntuni .....

'please Iman, wallahi am not among them yanxu, tuntuni na tuba na daina, dan Allah karki rabu
dani,

Ya tsugunna gabanta yana roqonta, ta tureshi tana kuka sai ya saketa, baxata iya xama dashi
ba, ransa ya soma baci ganin yanda ya qasqantar da kanshi gareta yana roqarta yasan abinda
xafi amma ya kamata ta duba masa ta yafe masa,

Kamar daga Sama taji muryar fauxie,
'anty me yaya yayi maki? suka juya suna kallonta,
'anty kiyi haquri, iman ta ďauke kanta gefe, fauxie ta matso gareta,
'anty malam yace ka xamo Mai yafiya a gurin mutane kaima a wajen Allah Mai laifine,
'kinji anty, please forgive him,
'shut up banxar yarinya, me kika sani a rayuwa, ko kin san tsawon lokacin da ake cutar dani,
maxan nan guda biyu sun min illah a rayuwata, *Babana da mijina*, bama kamar Deedah dana
daukeshi abokin rayuwata, ta dalilinsu na kamu da cutar hawan jini, jin daďina ragagge ne da
kai Ahmed, baxan iya cigaba da xama da barawo ba ka sakeni,
Wannan kalma ta barawo tana baqanta xuciyarsa,

'gwanda xama da barawo akan xama da matsafi fatyma, tayi masa wani kallo,

'Waye matsafi Deedah?
'Oho maki.... taja guntun tsaki,
'kabani takarda ta nace,
'baxan iya sakin ki ba Iman, kiyi haquri mucigaba da rayuwarmu a tare cikin so da kulawa kamar
yanda muke a ynxu, mu kula da yaronmu da xaixo bada daďewa ba,

'I can't Deedah, I hate you, kafita rayuwata, ba ruwanka dani idan ba haka ba cikin ma xn illata
shi xn kashe kaina Deedah....,

Hawaye sosai ke fitowa daga Idanunsa, Ashe akwai ranar da Iman xata iya rabuwa dashi, iman
xata iya gayamasa Kalamai masu xafi haka, to menene sauran jin daďin sa idan har xata iya
kashe kanta saboda shi? ya dubeta,

'Am so sorry, xn fita rayuwarki kamar yanda kika buqata, inason rayuwarki da ta yarona, Ina
sonki da gaske idan ke bakya sona, baxaki iya xama dani a kowane hali ba ki rufamin asiri, xn
tafi na barki ki yafemin ki Kuma kulamin da cikina, Idan Kuma kinji wani abu ya sameni daga
baya kece sanadi, ya juya yana sharar kwalla komai bai dauka nashi a gidan ba sai akwatin da
ya shigo da Ita ta kuďi,

Fauxie ta diro xata bishi Iman ta riqeta,

Kalamansa ke mata yawo a kwakwalwa tafi kowa son mijinta, bacin raine daya mata yawa a
xuciya but she truly love her husband, ta tashi da sauri tabi bayansa,

Fitowarta gidan yayi dai dai da ficewarsa daga cikin gidan cikin motarsa, ta soma kwala masa
kira, Ina ya riga ya fice,

Tana tsaye bakin gate ďin hasken Mota na Haske mata jiki,

Yaja wani birki cikin tsananin tsoro da mamaki,

'Iman yake gani da ciki, yaushe tayi ciki yaushe ya girma haka, Sam bashida lbr shida Sima.......




My wattpad Phertymerh1

*Babana da mijina*


©Fertymerh Xarah


32


*Dis page is for you Muhammad saleem & Maryam kaumi*

Hasken dana dallare fuskarta ya sanyata juya fuskarta gefe ba shakka baba bane tasani
Shikadai xai iya mata haka duk gidan, tasan ma'aikatan baxasu gwada mata hakan ba,

Bai shigo ba kuma bai kashe fitilar motar ba, mamaki da kaďuwa ya sanyasa kasa motsi sai
kallo yake binta dashi,

Ganin abin bamai qarewa bane sai taja qafafunta da kyar har nauyi suke mata ta koma cikin
gidan,

Wayarta ta ďauka tana kiran Deedah amma yaqi ya ďauka daga baya ma sai taji ya kashe
Wayar gabaki ďaya,

Hankalinta yayi matuqar tashi sai take danasanin abinda tayi masa, tana son mijinta so bana
Wasa ba, tana yi masa wani irin so marar misaltuwa bataso taganshi cikin wani hali ballantana
irin Wannan da taganshi ya fita a ynxu, ta duba fauxie har tayi barci sai ta gyara mata
kwanciyarta haďe da cillar da tedy dake Kan gado,
Baba Kuwa da kyar ya qarasa yayi parking ya fito, da sauri ya shiga cikin gida kai tsaye ďakin
tsafinsa ya nufa yana neman tedy ďin sa domin ya bata ya jewa sima da wannan sabon al'amari
daya gani a tare da fatyma,

Amma Kuma sai me? Wayam babu, hankalinsa ya tashi domin baxai iya bata ba dole sai da Ita
kwata kwata hankalinsa bai bashi rayuwarshi dake cikin kwalbar da tukunyar matsafarsu bata
gurin ba shi dai yaga wannan tedy ďin,

Sai xufa yake yayin da babbar rigarsa tayi masa nauyi, ya cire ya cillata gefe hankalinsa tashe
ya fito yana kiran Suleiman cikin ďaga murya,

Suleiman Kuwa tuni ya fice daga gidan, yaje kashe kuďin sa bashida wata damuwa bayan su,

Jin shiru ba alamarsa baba ya tara duka masu aikin gidan tun daga security masu girki, shara,
wanki da guga mata da maxa dake gidan ya tambayesu Waye ya shiga ďakin bayan fitarsa,

Ba Wanda yasani hassalima ba Wanda ya gani saboda bamai xuwa bangaren sa idan ba
Suleiman ba domin shine Mai Kula da wurin Kuma ba Wanda yaga shigarsa Sannan baya xaton
Suleiman xai shiga wurin domin ya ďauka Suleiman nada amana ne bayada bincike kosa ido
akan Abinda bai shafesa ba,
Ya tattarasu ya korasu daga falon ya cire hularsa yana firfita da Ita sai xufa yake hankalinsa a
matuqar tashe tunaninsa yakasa bashi Wanda xai shiga ďakin ya ďaukar masa kaya,

Iman Kuwa sai faman juye juye take ta kasa barci jikinta na bata ba lfy ba Deedah ďin ta take
gani a duk sanda ta rumtse idanuwanta, Ina ya shiga Ina yaje wane hali yake ciki meyasa bai
dawo gida ba she don't know...

Daga ita har baba basu rumtsa ba kowa da saqe saqen xuciyarsa.....


Deedah Kuwa bayan barinsa gidan wata qatuwar takarda ya ciro daga cikin akwatin, baya
mantawa Duk inda yasan yayi fashi yakan rubutu ya ajiye kuďin da oga nas ya bashi a inda
suka yi fashi xaiyi alama ya rubutu ga kason da aka bashi, Allah ne shaidarsa bai taba cin kuďin
ba bai Kuma taba sha'awar yin sadaka dasu baisan dalilinsa na tariyar kuďin ba haka kuma ya
kasa sanyasu a account ďinsa, sai ynxu ya gane dalili wato ya maida kuďin inda ya karbosu, is
too late akwai inda baxai iya xuwa ba akwai inda yayi masa nisa, the best thing for him is to
seek

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login