Showing 1 words to 3000 words out of 347556 words

Chapter 1 - KARAN DAFI COMPELET BOOK By Zainab Makawa.doc

22 Sep 2025

632

??ࡱ?>?? =Z????????????? ?
?
? ?
?
????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????V?

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F[WordDocument????1<0Table????????'Data
???????????????????? P?(24KSKS?1<??????????!?!?!?!!#!?,?$
?!??&?&?&?&?&?& ?&?&?&$#??%*??!?!?&?&?!?!?!?!?&?%?#!?%?&#!?&?%#!?&?&?!#! ?^`????^Normal d??,CJmH sH nHtH_HOJPJQJ^JaJhA`????hDefault Paragraph Font$mH sH nHtH_HOJPJQJ^J?i`????? Normal Table0:V 4?4?l4?4?la?6 $mH sH nHtH_HOJPJQJ^J(k`????(No List ?*>Vb?z???? L#=nUTn?yp??KARAN DAFI ?
YAFI DAN DAWA AMAFANI ?


ZAINAB IDRIS MAKAWA ?


????????

1??
DASUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI YAN UWA MUSULMAI INA MAKU SALLAMA IRIN TA ADDININ MUSULUNCI GODIYA DA YABO YA TABBATA GA ALLAH DA SHUGABAN MU ANNABI MOHAMMAD S,A,W
NAGODEWA ALLAH DAYA BANI WANAN DAMAN DON NA GABATAR DA WANAN LABARIN AGAREKU YADDA MUKA FARA LAFIYA UBANGIJI ALLAH YA NUNA MUNA KARSHENSA LAFIYA AMIN.
LITTAFIN KUDINE GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DARI BIYAR KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE RAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

Wanan labarin sadaukarwane ga duk wani dan masarautan AUNA da suka gabata ubangiji Allah yakai haske a kabarin su amin wa yanda suka rage Allah ya basu ikon cikawa da imani amin.

Kulli nafsin za,ikatul mau sai innalillahi wa inna alaihim raji,un kalman da wasu ke fada ke nan a gidan hankali tashe yanzun nan fa muka gama magana da ita a waya itace,ma ta dama muna koko da safen nan muka karya dashi ta sallami yara zuwa boko amma yanzu ace muna wai ta rasu babu ita a duniyan nan kuma.
Kaico mu masu kayan kaico muna yawo da kaya a saman kan mu bamu sani ba ashe da ajali muke yawo wazai daurawa safiya mutuwa yanzu don Allah matar da ko ciwo yana da wuya tayishi amma yanzu ace itace nan kwance.
Irin surutun dake tashi daga cikin gidan ke nan a wurin mata dake shigowa daya bayan daya suna cika gidan da jimame a lokacin .
Wanda mafi yawa bakunan makwabtansune da suka shigo don jin kururuwan mutanen gidan nasu lokaci guda a cikin tashin hankali .
Tunda ta karyo kwana take hango taron mutane daga can kofan gidan mijin yar nata ta hango ya fito motarshi da sauri ya kutsa kai zuwa cikin gidan nasu.
Tafe take saye acikin uniform din makaranta mai launin farin riga da farin hijjabi sai blue wando ta goyo school bag dinta a bayanta gefenta kuma yayan yar natane biyu dake biye da ita suma kalan kayan nasu irin natane saidai akwai bambanci a wurin dinkin uniform din duk da kala dayane da zai nuna maka a makaranta daya suke karatu a lokacin.
Da sauri sauri gudu gudu suka karasa kofan gidan inda mutanen wajen suke cikin jimame kowa a wajen cikin yanayu mara dadi yake zaune wasu a tsaye jikin mota.
Ciki na fada ina bin kowa na gidan da kallo wanda mafi yawansu duk makwabtan unguwan da mukene suka cika gidan alokacin.
Kai tsaye dakin anty Safiya na nufa inda ban tsaya tunanen komai ba na fada dakin kai tsaye lokaci guda inda na hangota a kwance an gilma ta tsakiyan falon nata har an mata sutura yadda addini ya tanada ga musulmi idan yayi shahada.
Anty na fada da karfi lokacin wata aminiyar anty din da muke kira da maman baby ta riko hannuna tana fadin Bantu kiyi hakkuri Allah ya karbi anty ki yau bayan tafiyan ku makaranta.
Yanzuma Allah ya nufa sai kunga gawan nata har aka kai wanan lokacin ba a kawar da ita ba yi hakkuri kinji bintu ta fadi sunan nawa da kyau kamar yadda yake kafin dan anty safiya din ya canza min suna daga bintu zuwa bantu da kowa yanzu yasan ni da bantun .
Anty don Allah ki tashi maman baby kicewa anty ta tashi son Allah kice min karyane antyna tana raye bata mutu ba kamar yadda mama ta mutu ta barni.
Riko hannayena tayi cikin kukan da itama yazo mata din tana rugumeni a jikinta a daidai lokacin ne kuma yaran biyu na anty suke tabani cikin kuka don a furgice suke da ganin mutane sun cika muna dakin har wajen dan barandan mu da muke shan iska a wajen.
Muna ji muna gani saiga maza sun shigo suna fadin na cikin dakin su gyara zamu shigo mu dauki gawan yanzu nan nayi wani irin kururuwa ina fadin wallahi ba mai daukar min anty anty ba gawa bace barci takeyi don Allah kubar muna ita kada ku dauke ta.
Wani mai lafazin ustazaine naji yana fadin subbahallahi ku kama yarinyar ma duk yawan ku bamai mata nasiha zaku ajeta a nan tanawa gawa kururuwa haka.
Lokacin ne naji maman baby ta damkeni zuwa kuryan dakin anty iya abinda na sani ke nan ban kara sanin a inda nake ba kuma a lokacin.
Har akakai anty makwancinta bansan inda nake ba sai yammane na falko na gani a dakin maman baby dake zaune ita da wasu mata suna mayar da ba,asin mutuwan antyn namu.
Kaina dago naga yaran kwance a barin jikina dukkansu biyu sunyi barci a lokacin a jikina a hankali na mike ina gyara masu kwanciya.
Lokacin maman baby ta dago tana fadin kingasu sunki kwanciya a nan din dole sai a kusa dake ni yaran ma sukafi ban tausayi wallahi.
Ban kulata ba sai faman dan waige waigen da nakeyi ina duban hijab dina don har lokacin uniform dinane saye a jikina tunda abin ya faru naji maman baby na tambayan wani abune kike nema Bantu.
Nace hijjab nake nema naje gida kada anty tayi muna fada sai naga sun kalli junansu kafim ita maman baby din tace ki zauna har su dawo unguwa sun fitane da babanku shine ta barku a nan ku kwana.
Jin abinda ta fada yasa na kara dago kai na kalleta don nasan koda fita ya kamasu nice dai ai ake bari a gida yau kuma sai suce ta barni a nan.
Wai ya akayi har nazo nan din ban sani ba haka na koma na zauna a dan darare na fara tunanen dalilin zuwan mu gidan mama baby din a lokacin .
Naji muryanta a kaina tana fadin karbi wanan kisha bantu dama ai baki da lafiyane yasa baki gane komai ba na dai karbi maganin na hade don yadda kaina ke ciwo a lokacin.
Ban jima da shaba sai wani itin barci mai nauyine ya daukeni har ban san a inda nake kwance ba a lokacin nan falonta muka kwana har ita din.
Washegari duk da maganin danasha nice na fara tashi kamar yadda na saba agidan antyna zan tashi in fara kuna gas insa muna ruwan zafi kafin na shiga nayi sallah in fito i fara hada muna breakfast da zamu school ko a karya a gidan dashi.
In ka debe kwanakin nan da banjin dadi don haka nake kwana da wani irin zazzabi a jikina kamar ba zan kai safe ba wani lokaci.
Motsinane ya tayar da maman baby din data dan samu barci zuwa asuban ta falko ta ganni take fadin bantu lafiya na ganki a tsaye nace naji anyi kiran sallah ne ina son in hada gas na dora muna ruwane.
Tace koma ki kwanta nan ai gidana kuke har yanzu baku koma gidan antyki ba tukun na koma kiyi barcin ki in lokaci yayi zan hasa maku wutan ai ta fada cikin tsigar lalashi a gareni.
Komawa nayi na kwanta har lokacin maganin yana aiki a kaina don haka barcinne ya dauke ina kwantawa ban falko ba sai wajajen karfe takwas da rabi na falko da kuka don na tuno da abinda ya faru dana bude ido na ganni a gidan maman baby kwance .
Sai abindaya faru jiya ya fado min a rai tiryan tiryan wai anty safiya data kawoni nan fatakwal ta rasu idona runtse a hankali sai hawayen bakin ciki daya fara zubo min a fuskana.
Da kyar ta lalasheni na tashi nayiwa yaran wanka na nima nayi ta bamu kayan su muka saka don bata yarda mun koma gida ba a lokacin.
Shadayan rana maman baby ta shigo dakin da muke zaune ni da yaran antyna ta kalli abincin data aje muna na karyawa taga bamuci ba take fadin haba Bantu idan baki sake jikinki ba ta yaya yaran nan suma zasu sake jikinsu.
Kin kai shekuran da zaki san duk mairai namaci ne kowa zaman jiran ta yakeyi a nan da kika ganmu ko yanzu ko anjima ko yau ko gobe kamar dai yadda tazowa yar uwanki garemu a bazata.
Ke nan da gaskene antysafiya ta rasu ta barmu da jamil da jamila don Allah kice min a, a ko zanji saukin abinda nake ji a zuciyana yanzu.
Tace bazan rudeki ba Bantu yanzu hakama mutanen garin ku suna hanyan zuwa nan din ance sun kusa karasowa nan din kinga ki tashi ku danci wani abu a cikin ku ko dan yaran nan kada suzo kuma abu ya kara jagulewa gareku.
Hawaye nake sakewa far far far a hankan na jawo dan kula mai kalan green dake gefen katifan da muke kwance na bude shimkafa da wakene da miya sa salad da aka zuba sama duk ya langabe ya dafe a lokacin don zafin kulan abincin daya sauka mashi.
Kallon gefen da yaran suke kwance nayi na dan dago jamil naji jikinshi da zafi a lokacin dago kai nayi na kalli maman baby din cikin bata fuska nake fadin jikinshi yayi zafi kardai ciwon nasane yake son tashi na fada a sanyayye ina kallonta.
Ko kuma maraicin uwa ya fara dukansa ba don rashin uwa aiba wasa bane tundai ga yaro karami haka irin jamal da jamila ai kinsan dole ya bukesu.
Tayar da yaron nayi na rugume a jikina lokaci guda ina shafa masa kai ina fadi kasa kasa jamal tashi kaci abinci kaji mu koma gida wurin anty.
Jin hakan yaron ya mike zaune yabi jikina ya kara lafewa nasan zafin da jikin nasa ya farane ya sakashi hakan.
A hakan kuma na fara debo abincin a hankali nayi bissimillah na fara bashi da kyar ya karba dan dama ita jamilan batayi min gardama ba take dan karba kadan kadan tana wasa.
Inda sabo na saba don tun haihuwansu har tasowan yaran nice dai mai masu komai dani suka saba ko banza dani kuma suka bude idanunsu fiyema da mahaifan nasu duk ko a lokacin shekaru goma sha biyu ke nan a duniya ina karama sosai a duniya amma na iya kula da duk wani laluran yara na iya komai na fanin gida da duk wata mace zatayi a gidan ta a lokacin.
Kowa a layin namu ya sanda hakan duk wani laluran gidan anty na nice meyin sa don har ka shigo ka fita zaka samu idan muna gida ina aikina hankali kwance kamar wata babba dani.
Iyakar anty shine kwanciya tana karatu ko kallo hatta kwanon ko kofi idan sun ci abu ko sunsha da an aje zan zo na dauka na kawar dashi ko yaushe ka shigo gidan namu tsab yake yana kamshi saboda kwazona data tarbiyantan dani dashi.
Wanda wasu a lokacin suke ganin rashin imanin ta niko a wajena ban dauki wanan komai ba don ina jin dadin zama da antyn nawa a hakan don bata da hayanita ko mugunta a gareni amma mutane suna fadin wai hakan ai muguntane a gareni don ko wata yar aiki babba ba zata gwada min komai ba a lokacin.
Antyna bata rageni da komai ba haka kuma abinda nakeso shi zanyi a gidan nasu mijin anty yaya Habibi kamar yadda anty take kiransa kowa ma ya dauka hakan habibi habibi shi ba mazaunin gida bane yana wurin sana,an shi ta mai da yakeyi sai darene yake zama damu a gida wani lokacin ma har muyi barci bai dawo gidan ba.
Yana can wurin neman hakak dinshi na duniya sai mune a gida da antyna da yaranta koda ya dawo lokacin matarshi kadai yake dashi dana wasu tsabgoginshi na gida idan ya gama ya kwanta.
Baban jamal yazo yana kofa yana son ganin ku mama baby ta fada tana tsaye a kan mu daga kofa dakin data saukemu a ciki kallon yaran nayi ina fadun wai daddy yazo zubur yaran suka mike.
Muka fito a tare dani yana zaune dashi da abokinshi Sani idanuwanshi sunyi ja jajir a lokacin kana mashi kallo daya kasan yana cikin matukar damuwa a tare dashi ba sai an tambaya bama.
Kasa na zube kamar yadda na saba gaidashi ina fadin ina kwana yaya ya dago kai da niyar amsa min sai kuka yana fadin Bintu yayanki ta tafi ta barmu ta tafi tabarmu babu wani alaman dake nuna zata wucene ta barmu a yanzu.
Kukan nima nakeyi yake fadin kiyi hakkuri fatima su mama nan hanya yanzun zasu karaso nan suzo su daukeku kunji.
Jin hakan yasa na kara karfin kukan da nakeyi din a lokacin don nasan rayuwata a yanzu saidai yadda Allah yayi dani ke nan don komawata gida a yanzu ba alheri bane gareni gaskiya.
Amma yaya zanyi dole in koma gida in zauna a gaban iyayye da yan uwa a yanzu duk da karancin shekaruna zuciyana ta dauki wanan abin ta dorawa kanta shine tunane na a yanzu.
Ya dan rugume yaranshi a jiki kuka yakeyi sosai a lokacin yayin da maman baby da abokinshi suke bashi hakkuri da kyar ya mike yana fadin idan suna son wani abu ina nan waje a fada min.
Nayi kuka sosai don matan dake zuwa gaisuwan a layin mu nan suke shigowa gidan maman baby suyi muna gaisuwan su tafi hakan yake sani kuka idan sunzo suna fadan halin antyn namu na alheri.
Ni kuma sai indinga jin kamar suna zuba min ruwan zafine a zuciyana suna kara sani a wani haline nake ji a jikina sai inta kuka wi wi wi a lokacin.
Karfe biyu daidai yan garin mu suka iso mama baby ta shigo tana fadin ina Bantu gama yan uwan naku can sun iso yanzu kai abjn tausayi fa naga wata mai kama da ita sosai halan mamantane ko kuma yarku gaskiya kamar yayi yawa kowa na fadan hakan.
Jin abinda take fada yasani zabura na tashi na kamo hannun yaran muka fito tana fadin ki tsaya suzo nan mana su sameku nace aa maman baby barin samesu can kada nayi laifi kuma a garesu dkn bansan ko suwaye sukazo ba.
An kabilun layin mu sai faman fadi suke min da Ayah sorry fa sorry for the lost bantu sorry wooo chaiiiii haka nake kada masu kai kawai ina wucesu a cikin kuka.
Gida ukune tsakanin mu da gidan maman baby din tun a kofa na sare ba yadda zanyi haka naja kafa na shiga dauke da jamila ina jaye da jamal rata rata zuwa ciki ni dai burina inyi tozali da wa yanda suka zo daga can garin namu a lokacin.
Suna zaune dakin yayi shiru na fado ciki da yar siririyar sallamata na fara arba da mama Laraba kishiyan maihaifiyan ya habibi a zaune tayi tagumi tana saurarenshi sai yayan mu Altine daga gefenta sai su gwaggo Jummai da mama sa, a su biyar ne maza biyu suka dauko mota tundaga kaduna zuwa nan din.
Inda fata yafi taushi nan ake zuwa wurin mama Sa,adatun na nufa kai tsaye na fada mata a jiki na fara rera kuka na tashin hankali haba Bintu kiyi hakkuri hakana mana kowa yasan keda baba kukai wanan rashin da yaran nan duk kukan da zamuyiwa safiya a yanzu bayan ku muke.
Mama Larabace ke fadin hakan a cikin hawaye tana kokarin goge hawayen nata dake gangarowa a fuskanta lokaci guda.
Da kyar suka samu na dan lafa daga inda anty Altine take zaune tace ke kirabamu da wanan kukan don Allah hakana muji da abinda ya damemu yanzu kinji.
Tana fada tana zaro min ido mama larbace tace haba Altine kubarta tayi abin kukane ai ya sameta yanzu ya samemu dai ta fada a hasale tana mikewa zuwa waje can ta zauna tana kuka sosai tare da fadin maganganu ciki ciki da ita tasan me take fada a lokacin.
Kai koma me kikeji ai shi kowa keji a yanzu komeye aisai ki bari har a koma gida amma ba anan garin mutane zakizo kina kokarin sayar muna da hali ba haka Altine gwaggo ta fada a sanyaye.
Balle ma wanan duk camfine ai ba mai kashe wani bayan Allah kwananta daine ya kare yau suke zaune lafiya da yar uwanta na fada masu don Allah su jaye wanan camfin ga yar nan da bata san ma me takeyi ba a yanzu.
A to idan basu jayewa sai suyi tayi ai hannun ka baya rubewa kayar don ya lalace kawai ayi imani da kwanan tane ya kare yanzu din shine zaifi ba a son bawa da camfi don Allah.
Ina ji ina gani a ranan aka hada kayan anty kaf a wuri daya yaya habibi ya samo babban mota da zata iya kwasan kayan hardamu duka aka kwashe mu zuwa gida kaduna cikin kuncin rai da kewan anty da nake ganin kamar unguwa ta tafi a lokacin ba mutuwa tayi ba yadda ake fada.
Wanda har lokacin nice komai na yaran nata don basu yarda da kowa a cikin saini kadai don haka nake manne dasu a jikina ko ina nake suna nan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login