Showing 33001 words to 36000 words out of 82977 words
Chapter 12 - MIJINA SIRRINA COMPLET BOOK BY UMMI AISHA.txt
abada kaga kuwa idan hakane to babu amfanin naci gaba da saurarenka.."
Bata sake jiran abinda zaice ba tayi gaba abinta zuciyarta na zugi,
Kamar yadda zuciyar nadiya ke zugi da radadi haka ta amadi shima ke zugin tana yimasa radadi,
Kan kujerarshi yakoma ya zauna yana tunanin abinda ke damun nadiya,
"To Kodai yarinyar nan tanada aljanu ne?" Ya tambayi kansa domin aganinshi idan ba mai aljanu ba wacece zatace bazata yi aureba har abada,
Ya dade zaune a office dinsa abun yanata damunsa sannan yatashi ya tattare kayansa ya rufe office din yafita.
Ita kuwa nadiya abubuwan da ta fadawa amadi tsakaninta da Allah tafada domin har cikin zuciyarta abinda tafada gaskiyane, sam yanzu bata da burin sake aure kwana kusa sannan ta cire soyayya aranta bata tunanin zata sake son wani da namiji domin tunda dan uwanta jininta yaci amanarta ya ha'inceta gani take babu kuma wanda bazai yimata haka ba,
Yanzu ta dade da sakawa ranta cewar ba ita babu soyayya sannan ai ba a saran mumuni sau biyu a rami guda daya.
Amadi cikeda damuwa yabar makarantar yafita yana tuki yana tunanin nadiya amma ko da wasa kalaman da ta farfada masa basusa yaji sonta ya ragu daga cikin ransa ba shi yanzu ne ma yake jin cewar yafara sonta,
Koda ya samu ya karasa gida, da lokacin kwanciya baccinshi yayi wayarta yayita kira amma taki dagawa,daga taga shine sai taki dauka daga karshe sai ya tura mata da text massage,
_pls peak my call, just to hear your voice please.._
Sai da yasake kira fiyeda sau biyar sannan ta daga,shiru tayi lokacin da ta daga wayarma taki magana,
"Nadiya, dan Allah kiyi min magana.."
Kememe tayi taki amsawa, shiru shi dinma yayi kamar yadda tayi suka bar kstinshi yanata konewa,
Sunfi minti 20 ahaka taki tayi magana shikuma yaki kashe wayar yana jiran yaji tayi magana yaji muryarta ko zai ji sanyi acikin ransa,
"Nadiya.." Yakira sunanta ahankali wanda kanaji kasan damuwace aranshi domin muryarshi har tayi wani irin sanyi kalau,
Jin yana neman matsa mata yasata amsawa saboda so take yayi ya kashe wayarsa domin tanada uzuri amma ita ko kadan bata jin zatayi nadama ko dana sanin wannan abun da tayiwa amadi domin itama abaya bataji da dadiba shiyasa yanzu dole ta dauki matakin hana sake komawa gidan jiya.....
*_Ummi Shatu_*๐๐ป
[7/28, 7:00 AM] Ummi A'isha๐๐ป: *MIJINA SIRRINA...!*๐น
_(Labarin k'auna)_
*_BY_*
_*UMMI A'ISHA*_
ยฎ *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & Perfect writers)_
*38*
aishaummi.blogspot.com
*S*ai da yayi fiyeda mintu biyu da kiran sunanta sannan ta amsa,
"Ina ji.."
"Nasan kina ji ai.."
Shiru tayi sanin bazata sake magana ba yasashi cigaba,
"Yaushe kike free inzo in ganki?"
"Babu rana"
"Meyasa?"
"Saboda ni karatu nazo yi ba soyayya ba"
Dan shiru yayi na tsawon wasu sakanni,
"Nasani, nima bance soyayya kika zo yiba.."
Daga nan shiru ta sake yi masa taki magana, agogon dake kafe a bangon dakinsa ya kalla, karfe 12 saura yan mintuna kuma tun 10:40 ya kirata,
"Shikenan saida safe.."
Tun kafin yakarasa ta katse wayar kittt, ko kadan baiji ciwon abinda tayi masa ba bare har ransa ya baci, asalima shi dadi yaji da yasamu zarafin jin muryarta a wannan dare.
Washe gari da safe ma bai iya hakura ba haka ya kirata amma bata dauka ba, ganin yayi mata 2 miss called bata dauka ba yashi hakura saboda yayi tunanin ko ta shiga lecture ne tunda lokacin 10:30 nasafe,
Barinta yayi tayi lectures tagama sai wurin karfe 5 nayamma sannan yasake kiranta, yanzun ma dai dakyar ta dauka tayi shiru,
"Kin fito daga lectures din..?"
"Uhm..." Tabashi amsa wanda kanaji kasan ta dolece,
"To sannu"
Shiru tayi masa nan suka cigaba da zaman kurame, ko tari babu wanda yayi acikinsu fiyeda mintina 20,sai can tayi magana,
"Ina son zanje nayi uzuri"
"Adawo lafiya" shine kawai abinda yace tayi hanzarin katse wayar, ko kadan bata son taci gaba da kulashi balle har takamu da sonshi yazo ya wulakantata kamar yadda yaya kabeer yayi mata,shiyasa bata jin zata sake yin soyaya acikin rayuwarta domin tayi tun tana yar karama daga karshe bata ci ribaba kuma bata samu alfanu ba to me zaisa yanzu ta sakeyi alhalin ta mallaki hankalin kanta,
Ko kusa abinda tayiwa amadi da yamma bai dameshi ba bare ya hanashi kiranta da daddare, sake kiranta yayi bayan ya kwanta yayi shirin bacci,
"Bakiyi bacci ba baby..?"
Yafada ahankali, shiru tayi bata amsa ba dama shi dinma yasan ba amsawar zatayi ba dan haka ya kyaleta bai matsa dole sai tayi magana ba maimakon hakama sai kawai yajawo iPhone dinshi ya kunna ya hau Facebook ga wayar kuma makale a kunnenshi yasa earpiece,
"Ko kina jin bacci?"
"Eh inaji" tafada cikin kaguwa domin alla alla take yace sai anjima,
"To kwanta kiyi baccinki basai kin kashe wayar ba saboda ina son naji ko kina yin minshari..."
Jin yafadi haka yasata cewa, "banida charge sai anjima"
Tun kafin ya amsa ta katse wayar ta kasheta gaba daya ta tura karkashin pillow, wannan dalilinne ma yasa washe gari taki kunna wayar gaba daya saboda kar amadi ya dameta dama kuma tafara tunanin sake layi saboda shi.
Tun safe yake kiran wayarta akashe har wurin 1, kawai sai yaji hankalinsa yatashi bazai iya hakura ba har sai yaje wudil ya gano lafiyarta,
Hajiya tana falo idonta sanye cikin glass tana karanta littafi mai tsarki sai gashi yafito cikin bakar t shirt mai gajeren hannu da blue din wando,
"Hajiya zanje wudil yanzu nadawo.."
Dagowa hajiya tayi ta kalleshi,
"Autana lafiya? Inji dai kalau?"
"Hajiya lafiya lau, ba jimawa zanyiba"
"To ai bakaci abinci ba ka zauna magajiya ta karasa abinci kaci sai ka tafi"
Girgiza kai yayi, "a'a hajiya barshi kawai sai nadawo.."
Tashi hajiya tayi takama hannunsa, "to kaga tunda bazaka jiraba zo ka cinye guntun farfesun nan maza.."
Babu yadda ya iya haka yabita zuwa kan table, nan ta mika masa bread da farfesun hanta guntun wanda sukaci da safe, tana tsaye akansa har saida ya cinye sannan ta mika masa tissue da ruwa tana fadin,
"Yawwa kaga ai yanzu sai nafi yarda da cewar sai kadawo sannan zaka ci abincin.."
Murmushi yayi acikin ransa yace "no body will be like mother.."
Afili kuma yace "to hajiya sai nadawo,bye.."
Fita yayi ya tasamma wudil cikin lokaci kankani sai gashi acikin makarantar,class rep din su nadiya yakira domin har lokacin ita wayarta akashe take,
Cewa yayi yaturo masa nadiya, office dinsa yaje ya bude yashiga,
Yayi kamar minti 10 da zama sai gata ta shigo bayan tayi knocking,
Fes ya sauke idanuwansa akanta, tana sanye cikin pink din doguwar riga tayi rolling da farin mayafi dan madaidaici,
Ahankali ta bude bakinta tayi sallama takarasa ta zauna akujerar dake gaban tebur din amadi,
Kallonta yayi kafin yayi magana,
"Meyasa kika kashe wayarki?"
"Saboda ina da lectures kuma banson adameni.."
Murmushi yayi ya lashi pink lips dinshi,
"To kidaina kashe waya, is better kisata a silent akan ki kasheta gaba daya,
Saboda idan ankira anji akashe sai ayi tunanin ko ba lafiyaba, kinga ni yanzu ina zaman zamana agida kika saka nataso nataho saboda tun safe nake kiranki amma wayar akashe shiyasa nazo naga meya faru.."
Cikeda mamaki ta kalleshi nan suka hada ido, ita abin nasa kamar almara take ganinsa, yanzu kenan yana nufin purposely itace dalilinsa na zuwa wudil yau?
"Tunda naganki kina lafiya shikenan yanzu kinga sai nasamu damar gudanar da duk abubuwan da zanyi.."
Ita dai nadiya shiru tayi tana tunanin wannan kaddara, wannan wanne irin sone Allah ya jarrabi amadi dashi akanta bayan ita kuma ba sonshi zatayi ba,
Kallonta kawai yake yi batare da yasake yin magana ba kamar yadda ita dinma batayi magana ba,sai hade rai da tayi ta bata fuska taci magani,
Sun dade ahaka kafin yace shikenan taje tatafi shima tafiya zaiyi, batayi magana ba ta tashi ta fita,
Murmushi yayi sannan yatashi yafita ya rufe office dinsa,
Kafin yamma har yakoma gida, yana kan dining yana cin abinci bayan hajiya tatashi ya kira nadiya,
Ajiyar zuciya yayi saboda jin ta bude wayar tata amma har yakaraci kiranshi yagama bata dauka ba, sai text ya tura mata cewar yaje gida lafiya.
Haka al'amarin nasu ya kasance koda yaushe yana kiranta awaya amma idan ta dauka sai dai tayi masa shiru kudinsa yayita tafiya abanza amma wannan bazai hanashi sake kiranta idan anjima ba,
Yau kam ranar lecture dinshi ce, lokacin da ya shiga class yi yayi kamar bai san tana ajinba yayi lecture dinshi yagama, yana tsaye agaban stand ya dauki wayarshi yafara latsawa bayan ya gama lecture din yana jiran questions daga daliban,
"Kizo office ina son ganinki.."
Shine abinda ya tura mata, din din, taji shigowar text nan taga shine tana budewa taga abinda ya rubuta, bata yi reply ba saboda dama batayi illa dai kawai kallonsa da tayi taga ya maida hankali wurin yiwa wani dalibi da yayi masa tambaya bayani,
Bata fuska tayi saboda tasan duk kyawun yaya kabeer amadi yafishi, sannan yafi kabeer wayewa yafishi komai na rayuwa, to kabeer ma da bai kai amadi kyau ba yayi wannan tururuwar yan matan bareshi, sannan yaya kabeer da bai kaishi ajiba yayi mata wannan kwarya kwaryar wulakancin to inaga amadi?
Lokacin da taga ya kammala ya fita itama tashi tayi tafita tana tsakin matsantawa rayuwarta da amadi yake yi....
_Fatan alkhairi gareku masoya masu bibiyar labarin.._
*_Ummi Shatu_*๐๐ป
[7/29, 9:43 AM] Ummi A'isha๐๐ป: *MIJINA SIRRINA...!*๐น
_(Labarin k'auna)_
*_BY_*
*_UMMI A'ISHA_*
ยฎ *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_
_Sak'on fatan alkhairi ga yayata mai sona, (Maman meenal), Allah ya albarkaci rayuwarki da zuri'arki gaba daya, I dey over love you my aunty.._
*39-40*
aishsummi.blogspot.com
*B*in bayanshi tayi yana tafiya ahankali kamar wani marar lafiya,
Kusan atare suka karasa office din nan yabude ya shiga tareda bar mata kofar a bude saboda yaganta tana binshi a baya,
Barin kofar a bude itama tayi taje ta zauna ganin haka yasashi tashi da kansa yaje ya rufe kofar ya dawo ya zauna,
"Nadiya, wai har yanzu baki sauya ra'ayinki akaina ba? Har yanzu baki ji aranki cewar ni masoyinki ne na hakika ba?"
Kamar bazata yi magana ba sai kuma ta bude bakinta,
"Gaskiya banjiba, shiyasa nafada maka tun farko cewar ka hakura dani saboda bana jin zan soka.."
"Har yanzu bakya sona kenan..?"
"Bana sonka gaskiya"
Murmushi yayi,
"Nadiya kenan, nikuwa kina bani mamaki irin yadda kike fada min wai bakya sona kanki tsaye, ke ko yar karantawa ma babu, bakya tsoron nayi miki halinmu na lecturers in kadake?"
Shiru tayi bata amsaba,
"Shikenan you can go, sai munyi waya.."
Mamaki ne yakamata saboda ita duk tunaninta yayi fushi bazai sake bi takanta ba amma sai taji sabanin haka,
Tashi tayi tafita yabita da kallo ya tattara inasa inasa ya tafi,
Tun daga nan yaci gaba da yimata waya, text da sauransu, dai dai da rana daya basu taba yin hira ta minti dayaba sai dai kawai ta dauki wayar tayi shiru idan yagaji yace mata sai anjima ya kashe,
Text massage kuwa ko ya aiko mata bata yimasa reply, gashi da zarar ya kirata yaji bai sameta ba hankalinsa zai tashi nan zai bar duk abinda yakeyi yatafi ganinta, har sai yaganta lafiya lau sannan zai koma yaci gaba da harkokinsa,
Ita abin nashi mamaki yake bata saboda lokuta da yawa sai taganshi yazo makaranta idan tazo sai yace kawai ita yazo gani bawai wani uzurinne ya kawoshi ba, wannan abu yana mutukar daure mata kai amma koda ta tuna yaudara irinta maza sai take ganin ai wannan ba komai bane domin zasu iya yin fiyeda haka ma,
Ganin abin nashi bamai karewa bane yasata shirya yanda zatayi masa wanda tasan cikin ruwan sanyi zai rabu da ita, dakansa ma zai ce mata ya hakura,
Ranar da zai zo yayi musu lecture ya kirata da safe,
"Yawwa dama Ina son zamuyi magana dakai.."
"Inajinki, ai gani"
"Dan Allah dan annabi ka rabu dani.."
"Saboda me?" Ya tambayeta,
"Saboda ni ba sa'ar aurenka bace"
"Kamar ya kenan?" Ya bukata,
"Ni bazawara ce harda yara biyu, yarana har sun fara zuwa school, kai kuma kaga saurayine dan haka aurenmu bazai yiyu ba.."
Shiru taji yayi dan haka tafara tunanin daga yau zasuyi bankwana dashi, bankwana na har abada,
"To kibari idan Nazo makaranta bayan mun gama lecture sai inganki ko 10 minutes ne"
"Ok" shine kawai abinda ta fada ta kashe wayar,
Kamar yadda yafada bayan yagama yimusu lecture tabishi zuwa office dinshi, kallonta ya jima yanayi sama da kasa yana son yagano banbancinta da budurwa amma yakasa, shi har yanzu kallon budurwa yake yimata,
"Kikace kin taba aure?"
"Ehh har inada yara ma guda biyu.."
Murmushi taga yayi ya kalleta,
"To ina babansu? Rasuwa yayi?"
"A'a rabuwa muka yi"
"May be saboda in sameki ne shiyasa Allah ya rabaku,rabona ne ya danne nashi..."
Mamaki maganarshi tabata nan takasa koda kwakkwaran motsi tayi shiru tarasa abinda zatace.
Zuba mata ido yayi yana kallonta shidai yasan bawai son nashine bata yiba akwai dai dalili mai karfi wanda bazai barta ta amshi soyayyarshi ba bawai dan baiyi mata ba, shida mata ke binsa suna cewa suna sonshi to tayaya ita da yace yana sonta da bakinsa zata ce bata sonshi,
"Indai akan cewa kin taba aurene sannan kinada yara yasa bakya sona ko kuma kike son kin amsar soyayyata to kisa aranki cewar yanzu ne ma nasake jin ina sonki fiye da yanda nake sonki ada, zan aure ki ahaka sannan zanci gaba da sonki ahaka..."
Dafe goshinta tayi tana al'ajabin wannan abu na amadi sai kace abin asiri, ga yan mata nan a makarantar kyawawa hadaddu masu aji amma duk yarasa wacce zai so sai ita?
"Kayi hakuri fa, ni sonka ne kawai banayi.."
Tashi tayi ta dauki jakarta har taje bakin kofa taji yace,
"Nikuma ina sonki sannan insha Allah sai na aureki.."
Bude kofar tayi tafita tana jin haushinsa saboda ita tagama dawowa daga rakiyar maza tasan mafi yawansu abinda yake bakinsu bashine acikin zuciyarsu ba, abinda yaya kabeer yayi mata kadai ya isheta example a rayuwa domin yasota awaje ya kaunaceta kamar zaiyi hauka amma daga ranar da aka kaita gidanshi tayi sallama da farin ciki ta shiga damuwa, rashin mutuncin da yayi mata ko wacce taje gidan miji babu budurci sai haka,
Shiyasa shima amadin zuciyarta takasa aminta dashi, takasa yarda da cewar son gaskiya yake yimata, dan haka tasaka aranta cewar bazata taba sonshi ba sai dai yayi yagama inyaso idan yaga babu riba sai ya hakura.
Shi kuwa amadi koda wasa baiyi fushiba sannan wai dan tace ta taba aure harda yara bai sauya komai na daga son da yake yimata acikin zuciyarshi ba, sai dai kawai yana jin kishin koma waye wanda ya rigashi auren nadiya sannan kuma yana yimishi kallon soko wawa marar tunani da har ya iya rabuwa da mace kamar nadiya,
Koda yatafi tun yana hanya bai karasa cikin kano ba yake kiranta yace mata yatafi amma bata dauka ba, packing yayi agefen titi yatura mata text,
_Baby natafi, ki dauki wayar kiji abinda zan fada miki please.._
Bayan yatura mata text din da yan mintuna yasake kiranta anan ta dauka tayi shiru kamar yadda ta saba,
"Baby.. Kina jina?"
"Uhm.." Shine amsar data bashi,
"Wai ko sayar min da muryar za ayine? Ko sai na siya sannan za arinka yimin magana.."
Tana jinsa amma tayi shiru bata yimasa magana ba,
"Shikenan dama kira nayi nafada miki natafi, yanzu ma haka ina hanya nakusa shiga cikin kano..."
Idan wayar da take hannunta tayi magana to itama tayi,
"Sai kinji ni anjima ko?"
"Uhm" dama amsar kenan koda yaushe uhm bata yimasa magana wadda tawuce wannan,
"To sai anjima" yafada tareda katse wayar yana murmushi.
Kamar yadda yafada mata cewar babu abinda zai sauya soyayyarta acikin zuciyarshi hakance kuwa ta faru domin kullum cikin yimata waya yake ko text amma sai ta gadama zata dauki wayar, idan text ne kuwa iyakaci ta karanta ta ajiye wayar babu amsa, a ka'ida sau daya zaije wudil a sati amma saboda ita sai yaje sau biyu ko sau uku saboda kawai yana son yaganta,
Rashin yimasa magana a waya kuwa idan ya kirata harma yasaba domin yanzu idan ya kirata sha'anin gabansa yake yi yana rike da wayar saboda yasan ba magana zatayi ba haka zasu bar credit din yayita tafiya a banza har zuwa lokacin da zai cemata sai anjima, ita kanta tana mamaki tarasa gane ko amadi wanne irin mutum ne wanda baya fushi, duk abubuwan nan da take yimasa rana daya bai taba nuna mata cewar yayi fushi ba gashi wani lokacin da gayya zata kashe wayarta ai yana jin wayar akashe zata ganshi a wudil,
Akwai wata rana da takashe wayar da daddare saboda tasan yasaba kiranta da daddare dan haka tun 8 takashe, 9 ya kirata yaji waya akashe, yasake kira yaji akashe adaren yafito zai tafi wudil nan hajiya ta hanashi tace koma menene yabari sai da safe saboda ita bata sonshi da tafiyar dare haka ya hakura yakasa bacci,
Ita kuma karfe 2 ta kunna wayar saboda babu wuta gashi tana son tayi karatu, ai tana kunnawa sai ga kiranshi,
"Dan naci.." Tafada aranta, daukar wayar tayi badan tasoba,
"Meyasa nakira wayarki naji akashe..?"
"Na kashe ne saboda ina son yin bacci da wuri.."
"Kin kashe kinyi bacci nikuma kin hanani bacci ko?"
"Kamar ya?" Ta tambayeshi cikin rashin fahimta,
"Saboda banji muryarki ba shiyasa nakasa bacci da tuni ma sai dai ki ganni a wannan daren hajiyace ta hanani tace dare yayi..."
"Ohhh" shine kawai abinda tace,
"Yanzun me zakiyi?"
"Karatu" tafada atakaice,
"To shikenan nikuma tunda naji muryarki yanzu bacci zanyi sai da safe"
"Uhm" tafada tareda katse wayar.
Haka amadi keta fama da nadiya akan tasoshi amma taki, har semester ta kare babu wata gamsasshiyar magana da tayi masa, ana igobe zata tafi gida sai da yaje makarantar yayi yayi da ita tafada masa dalilinta na rashin sonsa da batayi amma tayi shiru, address din gidansu ya tambaya nanma taki fada, tamkar kurma haka take zame masa dama duk lokacin da yazo,
Murmushi yayi ya saka hannunshi a aljihu ya dauko rafar yan dari bibbiyu ya dauki jakarta ya bude yasaka mata aciki,
"To ga kudin mota Allah ya kiyaye hanya saboda nasan idan nace zanzo nakaiki ba yarda zakiyi ba, amma ki shirya ganina agidanku akoda wanne lokaci.."
Ko kadan maganarsa bata dauketa da gaske ba domin tayaya zai san gidan har yaje? Sallama yayi mata yatafi ita kuma ta koma hostel takarasa shirya kayanta tafita cikin gari taje ta siyo kayan tsaraba tayiwa twins dinta siyayya sosai washe gari tatafi gida inda zatasha dogon hutu