Showing 75001 words to 78000 words out of 82977 words
Chapter 26 - MIJINA SIRRINA COMPLET BOOK BY UMMI AISHA.txt
dakin, dakinshi yaje ya shirya mintuna kadan sai gashi ya shigo, tana gaban mirror tana saka dan kunne bayan tayiwa fuskarta kwalliya,
Ta cikin mirror din ya nuna mata rubutun dake gaban rigarsa, rubutun ta kalla _Yes I did it_ shine abinda aka rubuta, murmushi tayi masa wanda ya ratsa zuciyarsa har yakasa hakuri saida yakai ga bata tukwici ta hanyar shanye gaba daya jan bakin da ta shafawa lips dinta,
Duka ta dan kai mishi akirji ta harareshi,
"Biyani jan baki na..."
Saida yasake tsotson bakin nata sannan yashafa mata wani yana yi mata gwalo,sake shagwabewa tayi nan ya dauketa cak yayi falo da ita,
Sallar azahar suka yi tare sannan suka ci abinci, matseta yayi tsam ajikinshi yau gaba daya ya hanata ko fita nan da can, ko part din hajiya yahanata lekawa, duk inda tayi yana biye da ita kamar wani jela har dare yayi,
Yau ko yar hirar ma da suka saba yi bai barsu sunyi ba saboda fitinarshi, ita nadiya duk yagama isarta,
Da safe da zazzabi yatashi, dariya nadiya tayi,
"Maganinka, anfada maka haka akeyi? Kabi komai asannu kaki"
Kallonta yayi yatashi zaune,
"Dariya kike yimin ko baby? Dariya ko? Nagode.."
Tashi yafara kokarin yi nan tahanashi tashige cikin jikinsa tana murmushi,
"Yi hakuri didi na, wasa fa nake yimaka, anjima zakaji zazzabin yatafi ai, sannu"
Daga mata kai yayi, haka yawuni bai fita ko compound din gidan ba har yamma sai lokacin yaji jikinsa yayi masa daidai sannan zazzabin ya sauka, wanka yayi yasa kananan kaya na hutawa,
Kan doguwar kujera yahau ya kwanta ya tasa kanshi da cinyar nadiya, yar hira yake yimata kadan kadan yana lalubarta,
Dabara tayi masa tace yatashi suje su gaida hajiya, tashi yayi suka fita zuwa part din hajiyan, suna zuwa sukaga anty siyama sunzo itada yaranta guda biyu da zee din amadi,
"Lahhh anty dan waken zagaye akayi mana yau?... "
Amadi yafada yana rungume yaran ta,
"Dama na jira ku fito ne, kun san ba ashiga gidan amare kai tsaye... Ko ba hakaba anty amadi??"
Murmushi yayi ya kalli nadiya nan tayi saurin wucewa tabarshi,
Saida suka gaggaisa sannan suka dunguma suka koma part din su amadi, nadiya ko kallon zee batayi ba bare su gaisa,
Abaya amadi ya tsaya, yana ganin Anty siyama tawuce yajawo nadiya, ita dinma dayake tana son bawa zee haushi bata ki ba harda su bashi kiss akumatu,
Su anty siyama sun dan jima sannan suka tafi nadiya sai cewa take abar mata yaran suyi kwana biyu amma fur amadi yaki yace a'a angonci yake yi, anty siyama kam jan yaranta tayi tace itama bazata barsu ba dama.
Babin rayuwa mai dadi suka bude domin itama nadiyan yanzu tafara sonshi wanda ita kanta bazata ce ga lokacin data faraba,
Komai tare suke gudanarwa shiyasa suka shaku da juna sosai,saida sukayi sati uku agida suna gudanar da soyayya sannan suka fara fita.
Yau juma'a da misalin karfe 9 nasafe nadiya na kitchen tana shirya musu breakfast,
Amadi ne yashigo yana mika daga shi sai gajeren wando da riga armless milk colour amma duk da haka ba karamin kyau yayiba kamar badaga bacci yatashi ba,
Rungumeta yayi ta baya tareda kashe gas din datake girki,
"Didi meye haka?" Tafada tana harararshi awasance,
"Zo muje kiji, magana zamuyi.."
Bata musuba tabishi zuwa cikin bedroom dinshi, zaunarta yayi agefen gado shima yazauna yana facing dinta,
Yadauki mintuna masu tsawo yana kallonta batare da yayi magana ba,
"Didi menene? Kafada min mana"
Idanuwanshi ya lumshe nan kyawunsa yasake bayyana,
"Baby kina sona?"
Kallonshi tayi cikin rashin fahimta,
"Meya faru?"
"Kawai kibani amsa.."
Kai ta daga mishi,
"Ehhh ina sonka"
Ajiyar zuciya yasaki,
"Baby kiyi hakuri da abinda zan sanar dake ahalin yanzu, idan kabeer yadawo yace yana son ki koma gareshi zaki amince?"
Hankalinta ne yasoma tashi ta kalleshi,
"Haba didi, inkoma wurin kabeer inyi me bayan inada kai ahalin yanzu, meya kawo wannan maganar?"
"Baby zaki koma ga kabeer nanda dan lokaci takaitacce, yau ranace wadda zan fito infada miki gaskiyar koni waye... Yau zan bayyanar miki da wani labari wanda ke baki saniba..."
Hannuwanta da suka fara rawa ya rike yana kallonta, gaba daya jikinta rawa yake kamar mazari alla alla take taji abinda zai fada mata domin hankalinta yatashi mutuka,
"Didi ka sanar dani, me yake shirin faruwa ne?"
Kallonta yayi ya sunkuyar da kai,
"Nadiya nasan ada bakya sona kuma bakya kaunata, to ni dinma ban aureki dan kisoni ba domin inada wacce take sona kuma zan aurota mu zauna nan bada jimawa ba, ni dama na aureki ne kawai domin inyi taimako guda daya.. "
Idanuwa ta zaro tana kallonshi, tuni goshinta ya jike da gumi duk da sanyin ac din dake kadawa, wannan shine bazata, bakinta yana rawa tace,
"Didi taimakon me? Dalilin wanne taimako ka aureni?"
Nikaina Ummi Shatu tambayar da take makale akan fatar bakina kenan,haka kuma masu karatu nasan kuna bukatar wannan amsa....
*_Ummi Shatu_*👌🏻
*MIJINA SIRRINA...!*🌹
_(Labarin k'auna)_
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
® *HASKE WRITERS ASSO.*
_Home of expert & perfect writers_
_Ina mika sakon gaisuwa da babbar murya ga masoyan anty amadi musamman wadanda basa son rabuwarshi da nadiya, anty amadidi yagaisheku kyauta, haka duk wata wacce page 69 ya girgizata ko ya taba zuciyarta to ummi Shatu tabata page 70 kyauta tukwici agareta,sannan masoya kuyi hakuri kuma kuyi min uzuri domin littafin mijina sirrina labarine wanda yafaru agaske bawai kirkirar labarin nayi narubuta ba dan haka banida damar canjashi dole yanda yafaru haka zan rubuta saiko yan abubuwan da baza arasa ba, masu yimin text da masu kirana da wadanda suka nemi contact dina basu samuba duk nagode da kokarinku sannan ina gaisheku aduk inda kuke..._
*Ke din ta dabance maryam qaumi, hakika banda kamarki kawata, Allah yabarmu tare,*
*70*
aishaummi.blogspot.com
*G*aba daya jikin nadiya karkarwa yake yana rawa, so kawai take taji labarin da Amadi yace zai sanar da ita wanda ita bata saniba,
"Didi karka yimin haka, amadi idan ka yaudareni kayi wasa da zuciyata har nafara sonka bayan ada ba sonka nake yiba wallahi sai Allah yayi min sakayya..." Tafada idanuwanta sunyi jajur kamar gauta amma bata bar hawaye ya disa daga idanuwanta ba,
"Kiyi hakuri nadiya, nima ba ason raina zan barki ba sai dan babu yanda zanyi,
Abune wanda yazama dole sai nasanar dake, dan Allah ki nutsu ki saurareni sannan ki yarda da kaddarar data riski rayuwarmu adaidai lokacin da muka shaku da juna, muka aminta da juna, zuciyoyinmu sukai tarayya awuri guda..."
Shiru yayi na dan lokuta yana kallonta wanda shi dinma idanuwanshi sun kada sunyi jajur kamar gauta,
Jin yayi shiru yakasa magana yasata kallonshi da jajayen idanuwanta, idanuwanshi akasa suke yakasa koda kallonta,
Yau nadiya jinta take kamar acikin mafarki take, gaba daya nutsuwarta bata tare da ita,
"Ka fada min abinda zaka fada min ina sauraronka.." Tace dashi bakinta yana rawa da jikinta gaba daya,
"Nadiya kabeer ne yasani in aureki,
Mun hadu dashi ne akasar misra lokacin hajiya bata da lafiya an kwantar da ita, shikuma ban san uzurin da yakaishi ba, anan mukayi sabo dashi har takaimu ga kulla alkawarin taimakawa juna,
Nadiya ba auren kisan wuta nayi dake ba..."
Katseshi tayi cikin karaji,
"Karya kake macuci azzalumi, idan ba auren kisan wuta kayiba me kayi..?"
Kwalarshi taje taci tana girgizashi,
"Ina tambayarka idan ba auren kisan wuta ba me kayi? Kafada min abinda kayi.."
"Nadiya wallahi nafi karfin nayi auren kisan wuta, kin san dai munada kudi bare kice ko dan kudi nayi, inada ilmi bare kice dan neman wani abu nayi ko dan jahilci, inada duk wani abu wanda dan adam yake nema acikin rayuwa..."
Kukan data fashe dashi shine yakatse maganar da yake yi,
Kifa kanta tayi ajikin gado tana kuka,kafin ta dago ta rungumeshi tana fadin,
"Ni bana son kabeer yanzu kai nake so, meyasa zaka koya min sonka bayan kasan ba son gaskiya kake yimin ba...?"
"To ai kinki bari inyi miki bayani sai faman kuka kike..."
"Wanne bayani zaka yimin? Bayan kaci amanata.."
Zame hannuwanta yayi daga jikinshi ya mike zuwa wurin bedside drewar nan ya bude ya ciro wata zungureriyar takarda wadda dama da alama yajima da tanadarta,
Ajiye mata takardar yayi akan hannunta yafita daga dakin, dafe takardar tayi tana kuka batare data dauka ta karanta ba,
Kukanta taci gaba dayi bata ko motsa ba daga inda yatafi yabarta, tsabar kuka idanuwanta duk sun kumbure sunyi jajur, kanta kuwa kamar zai fashe da ciwo ga yunwa da take faman damunta domin bataci komai ba,
Haka tawuni a durkushe tana kuka, shikuwa amadi abisa dukkan alamu ma baya cikin gidan sai yamma yadawo da misalin karfe 3,
Dakin da yabarta aciki yaje ya bude yashiga, har lokacin tana sulale awurin taci kuka tagaji tana jan numfashi dakyar,
"Baby wai har yanzu baki bar..." Ganinta ayashe akasa yasashi kasa karasa maganar da yasoma,
Agaugauce yaje inda take yadagata zuwa jikinsa,
"Baby... Baby..."
Bude idonta tayi tana ganinsa tasake fashewa da kuka gamida kara rungumeshi,
"Dan Allah didi kace ka janye sakin da kayi min, wallahi ina sonka, bana son kowa yanzu sai kai,kaine MIJINA SIRRINA..."
Idanuwanshi ne suka cicciko da kwalla, kinkimarta yayi ya dora akan gado yakwanta ajikinta,
"Baby wai tun lokacin da natafi kike awurin nan baki tashi ba?? Meyasa zaki yimin haka?"
Jin jikinta yafara daukar zafi yasashi tashi arazane ya riketa,
"Baby zazzabi? Zazzabi zakiyi? Ko inyi miki wanka?"
Girgiza masa kai tayi alamun a'a, mintuna kadan jikinta ya gauraye da zafin zazzabi kamar garwashi,
Hankalinsa ba karamin tashi yayiba, Dr Salaha yayi azamar kira, yana gama kiranta yakoma jikinta ya kwanta yana jijjigata kamar jaririya,
Duk yarasa inda zai tsoma ransa yaji dadi ganin halin da take ciki,
Zuwan Dr salaha ne yasashi mikewa daga kan gadon yaje ya shigo da ita,
Duba nadiya tayi tabashi maganin da zai bata idan taci abinci sannan ta jona mata karin ruwa,
Sallama yayi da dr salaha ta tafi shikuma yakoma kusa da ita ya zauna yana shafar gashin kanta, har fuskarta ta dan fada saboda tsabar tashin hankali,
Ta dan jima tana bacci sannan ta farka, idanuwanta ta bude taga amadi akusa da ita yana rike da hannunta, jin tayi dan motsi yasashi tashi zaune yana kallonta,
"Baby kin tashi? Inkawo miki abinci kici kisha magani?"
Kai ta daga masa idonta dauke da kwalla, ruwan dake hannunta ya cire mata saboda yakare, sauka daga kan gadon yayi ya fita zuwa kitchen,
Bai wani bata lokaci ba sai gashi yashigo dauke da filet da cup,
Dankali da kwai da sos ya zubo mata sai dan ruwan tea acikin cup, zaune ya tadata yafara bata dankalin abaki tana ci, kallonsa kawai takeyi idonta cikeda kwalla,
Girgiza mata kai yayi yana rikeda hannunta guda daya,
"Baby meyasa baki nutsu kin karanta takardar da nabaki ba, da kin karanta da duk haka bata faruba saboda nasan zaki fahimci abinda nake nufi kuma zaki gane komai acikin sauki.. Dan Allah kiyi hakuri karki yi kuka, kidaina kwallar nan haka"
Goge mata kwallar yayi yaci gaba da bata dankalin tana ci, saida taci da yawa sannan yabata ruwan tea din tasha yabata magani tasha har lokacin jikinta akwai zafi amma dai taji saukin ciwon kan da yaketa azazzalarta kuma ciwon da jikinta yake yi mata shima ya dan ragu,
"Zanyi wanka kuma banyi salla ba.."
Tafada muryarta adashe, ahankali ya dagota ya riketa ajikinshi yazuge zip din rigar jikinta ya cire mata rigar, shi dama baijin kiwar daukarta akoda yaushe dan haka ya dauketa cak yayi toilet dinshi da ita,
Ruwa mai dan dumi yatara mata yasata aciki yayi mata wanka amma dakyar ya iya controlling kanshi,alwala yayi mata bayan yagama yimata wankan ya daura mata towel dinshi ya fita da ita, agefen gado ya zaunar da ita sai faman binshi da ido take yi, fita yayi zuwa dakinta ya dauko mata kayan da zata saka,
Wata jar doguwar riga mai mutukar kyau ya dauko mata, rigar bata da kauri dayawa sannan kuma irin mai mannewa ajikin mutum dinnan ce sannan anjera wasu duwatsu ajikinta,
Pant da bra ta karba tasa da kanta sannan yazira mata rigar yafesa mata turarenshi na axe, daga zaune tayi salla tana idarwa ya mika mata wannan takardar ta dazu, gabanta ne yasake faduwa ta daga ido tana kallonshi zuciyarta tana yimata wani irin suya wato dai amadi yadage sai ya rabuda ita ko?,
"Kiyi hakuri ki karba ki karanta baby..."
Jikinta yana rawa ta karba ta warware tafara karantawa, yana ganin haka yatashi yafita daga cikin dakin, cikin rawar jiki nadiya tafara karanta takardar kamar haka:
_Farawa da dunbin gaisuwa agareki yake kyakkyawa kuma mace mai mutukar daraja awurina, hakika nayi farin ciki mai tarin yawa kasancewarki mata agareni, nasan abinda nayi miki ban kyauta ba kuma na sanya zuciyarki acikin wani hali amma ina neman afuwarki abisa laifin da nayi, kisani nayi hakane domin auna adadin irin soyayyar da kike yimin, actually ayau ina cikeda farin ciki mai yawan gaske saboda jin da bakinki kince kina sona yanzu, wannan kalmar da kika furta min bazan barta tatafi abanza ba shiyasa na tanada miki tukwici mai yawan gaske, dafarko ki duba cikin bedroom dinki zakiga tukwici nafarko, tukwici na biyu kuma idan nadawo zaki ganshi, tukwici na uku kuma sai kin kammala karatunki zan baki shi, kiyi hakuri duk abubuwan da nafada miki dangane da kabeer wallahi ba gaskiya bane am joking,kisani babu wata mace da nake iya gani sai ke kadai, i luv u...._
Yours for Eva
didi
Tukwikwiye takardar tayi ta mike tana jin wani irin karfi ajikinta, dakinta ta nufa tana zuwa tabude ta shiga, akwatina set biyu tagani guda 24 masu dan banzan kyau pink and purple kowanne anrubuta A & N ajiki da manyan harrufa,
Kobata budesu ba tasan kayan ciki bana wasa bane,
Juyawa tayi tafita ta nufi falo saboda daya tukwici din dama yace sai yadawo,
Key din mota tagani ya ajiye mata akan center table din dake tsakiyar falon tareda yar karamar farar takarda,
_Baby kije waje kiga motarki..._
Shine abinda yarubuta ajikin yar takardar da ya ajiye mata zama tayi sharaff akan kujera batare data je taga motar ba,
Duk da cewar zuciyarta tayi sanyi amma har yanzu bugawa zuciyarta keyi bata daina ba ga ciwon kai, dafe goshinta tayi tana jiyo motsinshi a corridor,
Tana zaune acikin falo yashigo yasha jeans brown da blue din t shirt anrubuta awesome ajiki,
Zama yayi akusa da ita yana zuba kamshi fuskar nan sai annuri ne ke fita daga jikinta,
"Baby ga wayarki da na canja miki, kedin fa yar gatace..."
"Malam ni ka rike duk kayanka bana so, wancan dinma gara kaje ka kwashe abinka domin bana bukatarsu..."
Murmushi yayi yakai mata kiss ta tureshi batareda tabarshi yayi ba,
"Shiyasa akarshen takardar nabaki hakuri saboda kukan da nasaki,
Baby yanzu ke idan nace zan rabu dake sai kiyarda? Kisawa ranki cewar mutuwa ce kadai zata iya nasarar rabamu, idan har zan iya yaudararki ko naci amanarki ashe so karyane, da mutanen duniya sun daina yarda da kowa, da sun daina bawa kowa amana,
Abinda yasa kikaga na bullo miki ta wannan hanyar shine, ranar farko dana fara baiyanar miki da soyayyata agareki sai kika nuna min cewar bazaki taba sona ba har abada kuma da bakinki ma kin furta min hakan,
Har yanzu abun yana raina kuma yana damuna, zuciyata takasa tabbatar min da cewar kina sona ko kuma sabanin haka shiyasa nayi haka domin na samu tabbaci... Sorry baby"
"Kaga nifa yanzu duk wadannan kalaman naka bazasu yi tasiri ba agareni, sannan ina son kasani nima yanzu nadaina sonka..."
Katseta yayi ta hanyar dora yatsanshi akan lips dinta,
"Ai karma kiyi wannan maganar, nida ke ahalin yanzu duk muna son juna dan haka babu amfanin mu tsaya muna wahalar da zukatanmu,
Kuma ma inbanda abinki baby tayaya zan iya sakinki alhalin na dandani zumar dake tare dake? Kin san kuwa yanda nake kishinki? Wallahi ko kinyi min laifi babba zaiyi wuya in inya rabuwa dake saboda ban son kisake komawa kabeer, ina bakin cikin kasancewarshi mijinki nafarko, naso ace nine nafara aurenki, da nabaki jin dadi marar yankewa wanda zaisa bazaki kara kallon wani namiji ba domin zaki rinka kallonsu a matsayin mata yan uwanki,amma duk da haka ai nasan yanzun ma nayi kokari.."
Kicin kicin tayi da fuska ta hade rai kun san mutuniyar taku akwai iya tsare gida,
"Nidai nafada maka, nima yanzu bazan zauna dakai ba gidan tsohon mijina zan..."
Saurin rufe mata baki yayi da hannunshi yajata jikinshi ya matse,
"Me zaki koma kiyi agidan wannan bakauyen? Wani baki mummuna dashi, ni haushinsa nakeji yagama sanin sirrina.."
"Karka kara zagar min uban yayana.." Tafada bayan tasake daure fuska, jijjiga kai yayi yana murmushi,
"Nidai bazanyi fada dake akan wannan kucakin gayen ba saboda nasan ba iya kyau kadai nafishi dashi ba hatta bawa mace nutsuwa nafishi..."
Shiru tayi masa tafara kokarin kwacewa daga rikon da yayi mata,
"Kin san Allah haushin wannan kabeer din nakeji, Allah yasa sai yamutu sannan zan mutu saboda kar na rigashi mutuwa yasake maye gurbina yahanani kwanciyar kabari"
Bata sake kulashi ba illa fuska data hade ta bata rai, hijabin jikinta ta cire ta koma kan carpet ta kwanta,binta yayi kasan ya jingina da jikinta yayi ruf da ciki asamanta,
"Baby bai kamata alkhairi yazama mugunta ba, ya kamata ki karbi tukwicin da nabaki hannu bibbiyu.."
Jin tayi shiru bata tanka masa ba yasashi birkitota ya shige jikinta, koba komai dai taji dadi da ba gaskiya bane abubuwan da yafada mata da safe,
Shareshi taci gaba dayi sai shan kunu take tana ciccin magani har yagaji yatashi yatafi part din hajiya, sanin tana fushi dashi yasa yaki dawowa saida dare yayi,
Lokacin da yafita akwatunan da ya ajiye mata taje ta dan dudduba wadanda zata iya domin kayan sunyi yawa ita kanta tasan kayan nan sun lashe dukiya mai yawan gaske domin akwatun english wears daban, na shadda daban, na less daban, na atamfa daban, na hijabai daban, na gyale daban, na inner wears, komai dai da akwatinsa, sannan ga wasu kit guda biyu cikeda gwala gwalai,
Tea taje tahada ta dafa indomie da kwai ta ci tayi wanka ta kwanta, ko rigar bacci yau bata tsaya sakawa ba saboda jikinta babu karfi,
Jin alamun tafiya ya tabbatar mata da dan rigimar ne yadawo, dakin yashigo yana sanye da kayan bacci,
"Baby yau da towel za ayi baccin?" Yace da ita bayan ya sunkuya yana leka fuskarta,
Fuska ta daure ta kalleshi,
"Menene haka?"
"Baby kenan, wai maimaikon kiyi murna amma sai faman fushi kike yimin har yanzu kinki hucewa.."
"Akan me zan huce? Ai nafada maka nima yanzu bazama zanyi dakai ba