Showing 15001 words to 18000 words out of 82977 words
Chapter 6 - MIJINA SIRRINA COMPLET BOOK BY UMMI AISHA.txt
haka nadiya ta zabga tagumi tana tunanin makomar rayuwarta.
Cikin wannan hali suka yi sati biyu koda yaushe idan kabeer yasa kafa yabar gidan da safe baya dawowa sai karfe 10 nadare, tunda akayi bikinsu basu taba zama da nadiya sunyi hira na minti daya ba, sai dai idan har fad'a zaiyi mata,
Koda yaushe ita kuma tana kokarin nuna kulawarta agareshi domin tana yimasa waya taji yanda ya wuni wani lokacin ya dauka yana tsaki wani lokacin kuma yaki dauka,
Tana zaune taci kwalliya amma gani daya zaka yimata kasan cewar akwai abinda yake damunta yaya kabeer ya shigo, lokacin karfe 5 na yamma,
Abinci ta kawo masa ya zauna ya danci ya tashi ya shiga cikin daki, wayarsa da yabari afalon ne tasoma kara nan nadiya ta dauka da niyyar kai mishi ai kuwa sai gashi ya fito, fautar wayar yayi yafara yimata fada,
"Uban waye yasaki ki daukar min waya? Danme zaki taba min waya? Karki kuskura nasake ganinki kin taba min wayata..."
Yana gamawa yawuce fuuhhhhh yakoma daki mintuna kadan yazo yawuceta yabar gidan daga nan bai sake dawowaba sai 11 nadare.
Haka rayuwar nadiya da yaya kabeer ta kasance koda yaushe babu dadi, tsakaninta dashi babu kulawa, babu magana mai dadi, babu tausasawa, babu nuna soyayya babu komai, kullum cikin yimata fada yake, idan ta kirashi awaya ya hauta da fada idan bataci abinciba ta jirashi yazo yayita fada da haka har suka debe watanni biyu da bikinsu, mai karatu acikin watanni biyun nan nadiya bata da wani labari mai dadi wanda zata bayar dangane da rayuwar aure, ko kadan bata san dadin aureba sai sabanin haka,
Kasancewar bata cikin kwanciyar hankali yasata ta rame ta kanjale domin kullum cikin kuka da damuwa take, lokacin da takai kimanin watanni uku babu kadan mama tazo mata,
Tsayawa mama kawai tayi tana kallonta saboda ganin irin yanda ta rame ta zabge, ita mama da atunaninta zata zo ta iske nadiya tayi kiba ta hada jiki amma sai taga sabanin haka sai dai batayi magana ba domin tayi zaton ko dai har nadiyan tasoma laulayi ne,
Nan mama ta kusan wuni agidan amma abin mamaki harta taho bata ga kabeer ya koma ba,duk sai bata kawo komai aranta ba saboda tasan irin soyayyar dake tsakanin kabeer din da nadiya.
Acikin satin da mama tazo itama maman su yaya kabeer tazo taga gida, sosai mamanshi keson nadiya domin har kayan makulashe ta kawo mata irinsu alawar madara, gullisuwa, tsami gaye,yashin madina, hanjin ligidi da sauransu haka ta kawo matasu cikin leda viva,bata jima dayawa ba tatafi,
Tun daga nan nadiya bata sake ganin kowa nagida ba sai dai mamanta kullum tana kiranta su gaisa da ita sannan ta hadata da kannenta su gaisa haka kuma duk satin duniya sai mama ta turo mata kati na dubu daya ko na 750 dama shi yaya kabeer babu ruwanshi da batun wayarta ko wani abin bukatarta kullum da safe da zarar ya kada rigarsa yafita sai dare.
Haka nadiya taci gaba da zaman hakuri zaman da babu komai acikinsa face damuwa da bacin rai har ta debe watanni shida lokacin dai ya kaita gidansu sau daya haka itama yakaita tagaida mamanta sau daya daga nan sai dai su waleeda suzo mata a weekend su wuni shiyasa har burin zuwan weekend take domin abba yana kawo mata su, duk ranar da suka zo wuni take cikin farin ciki shiyasa bata barinsu su tafi sai dare yayi.
Cikin wannan yanayi nadiya tafara amai wanda abisa dukkan alamu na laulayin cikine, kabeer ko ajikinsa babu abinda ya dameshi,
Lokacin ma da ya shigo ya isketa tana aman kallonta yayi yace,
"Ke cikine dake ko?"
Daga nan bai sake magana ba yayi tafiyarsa yawuce ciki yabarta tana faman kwarara amai,
Satinta biyu tana zazzabi atafe daga karshe zazzabin ya kwantar da ita, nan ya dauketa yakaita asibiti likita yana dubata yace cikine da ita na wata biyu, ga mamakinta sai taga yana murna harda bawa likita tukwici, daga nan ya daukota suka dawo gida bayan ya biya ta kasuwa ya siyo mata fruits su lemo da ayaba da makamantansu,
Tunda suka dawo gida kuma yarage fada da masifar da yake yimata yafara dan kula da ita, komai tace tana so baya k'i shiyasa lokaci kankani tayi kyau tayi kiba saboda hankalinta ya dan fara kwanciya,
Yanzu abu dayane ke damunta shine wayar da yaya kabeer ya tsiri yi acikin kowanne dare, koda yaushe ta bude idonta sai tajiyoshi yana waya, kusan kwana yake yana yin waya da wadda bata san ko wacece ba, bayaga haka kuma ko wacce safiya ta Allah sai yafita da sassafe yana tafiya inda bata san ko inaneba,
Wannan dalilinne yasa yau ta daura aniyar tambayarshi inda yake zuwa, tana kwance afalo ya shigo lokacin misalin karfe 9 nasafe, akusa da ita ya zauna nan ta yunkura ta tashi dakyar,
"Yaya kabeer wai ina kake zuwa da sassafe ne?"
"Nadiya shamsiyya nake zuwa nake kaiwa makaranta, baki Santa ba ko? Yar kanwar mamace to shine aka kawota gidanmu dan tayi karatu.."
"Amma yaya kabeer fisabilillahi sai kaine zaka rinka kaita makarantar? Kullum fa da karfe 6 kake fita, haba dan Allah, gaskiya nidai wannan abun yana bata min rai.."
Mikewa yayi yashiga cikin daki baiyi magana ba, nan ran nadiya ya baci domin tagane cewar tsakaninsa da shamsiyyan akwai wani abu, tana ganinsa yazo ya sake fita bayan yayi shirin office,
Tagumi ta zabga tayi shiru, wayarta ce ta soma kara nan ta dauka taga bakuwar number ce,
"Assalamu akaikum"
Daga daya bangaren aka amsa sallamarta tana jin muryarsa ta ganeshi ba kowa bane face yaya Kamal dan gidan wan mama wanda suke zaune agarin tofa....
*_Ummi Shatu_*๐๐ป
[7/17, 8:23 AM] Ummi A'isha๐๐ป: *MIJINA SIRRINA...!*๐น
_(Labarin k'auna)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
ยฎ *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of experts writers)_
*20*
~~~Nan suka fara gaisawa cikeda zumudi domin rabonta dashi tun tana JSS lokacin da yake zuwa gidansu hutu, Allah ya hada jininta dashi sosai,
Hirace ta barke tsakaninsu nan yafara tambayarta ya rayuwar auren nasu, tsakaninta da yaya kamal babu boye boye sannan ayanda take jin zuciyarta sam bazata ji sauki ba har sai ta amayar da abinda ke cikin zuciyarta dan haka ta fara zayyane masa damuwarta tun daga washe garin ranar da aka kawota har yau,
Hakuri kamal yafara bata cikeda tausayinta,
"Nadiya kiyi hakuri, ki dauki Dangana sannan kisani komai na duniya mai wucewa ne sannan babu abinda yake dawwama a duniya,
Dadi baya taba dawwama haka shima wuya da damuwa basa dawwama,
Farin ciki baya dawwama kamar yanda bakin ciki baya taba dawwama,
Kisakawa ranki cewar ibada kike yi domin zaman aure ibadane haka kuma abayan kowanne tsanani to da akwai sauki haka alqur'ani ya sanar damu,
Kiyi hakuri kici gaba da yiwa mijinki biyayya karki gaji sannan karki daina,
Kidauka cewar bautar Allah kikeyi sannan aljanna kike nema kin san kuwa samun aljanna ba abune mai sauki ba dole sai ansha wahala sai anshiga damuwa,
Haka kuma kamar yadda baki taba fadawa kowa ba saini to kiyi hakuri kisake daurewa karki fadawa kowa wannan maganar domin sirrinki ne keda mijinki ta shafa kinji..?"
"Naji yaya kamal.."
Nan yaci gaba da bata shawarwari akalla sai da suka shafe awanni yana yimata nasiha gamida bata hakuri tareda tausar zuciyarta akan taci gaba da jurewa gamida hakuri,
Ko ba komai taji dadin shawarwarin da yaya kamal yabata tareda bada hakuri domin idan abu yana damunka kasamu wanda ka fadawa har yabaka hakuri dadi kakeji koda bai baka komai ba.
Nan taci gaba da rainon cikin da yake tareda ita shikuma kabeer bai fasa halinshi na daka sammako ya fita da sassafe ba wai shamsiyya yar uwarsa yake kaiwa makaranta sannan ga wayar dare da ya kware akanta kamar gwauro marar iyali,
Juyi nadiya tayi nan tajiyo muryarsa kasa kasa afalo yana maganganu ahankali wanda daga ji wayar tasa yake yi, yunkurawa tayi ta tashi dakyar ta fita falon nan ta hangoshi akwance cikin kujera kamar ba dareba sai wayarsa yake,
"Yaya kabeer..."
Juyowa yayi tareda katse wayar yana cewa "i will call you back latter..."
Tashi yayi yana kallon nadiya,tamkar zai hauta da duka haka yayi yabude babin masifa,
"Menene? Acikin tsohon daren nan zakizo kina kirana, me zanyi miki? Ba tambayarki nakeba, nace uban me zanyi miki, wannan wanne irin rashin mutunci ne, da rana ba abar mutum ya hutaba haka da daddare ma baza abarshi ya hutaba.."
"Haba yaya kabeer, yanzu me yayi zafi da zaka fara fada da daddaren nan, ni idan nice na bata maka rai kayi hakuri, gani nayi abinda kake yi bai daceba sannan bai kamata ba, ya za ayi ni ka baroni acikin daki sannan kazo nan ka zauna kana waya, idan wayarka zakayi ai sai kayi da rana tun kana waje amma bawai sai kadawo cikin gida..."
Katseta yayi cikin wata irin tsawa,
"Ke karki kuskura kiyi min iyayi kin gane ko,kece ma zaki tsara min yanda zan rinka gudanar da rayuwata?, saboda gaki uwata ko? To bari kiji.."
Bai karasa ba yaga ta rike cikinta tareda faduwa akasa nan da nan yaga tafara murkususu jini yana bin kafafuwanta, iya tashi hankalinsa kam ya tashi domin yana mutukar son cikin dake jikinta nan yaji ya shiga rudu,
Dakyar ya iya kokarin daukarta yakaita cikin mota yanufi asibiti da ita wanda yake can gaba dasu kadan,
Cikin wani daki aka sata nan likitoci suka yi cahhhh akanta suna dubata daga karshe dai sunaji suna gani babu yanda zasu iya cikin dake jikinta ya zube,
Kabeer yayi mutukar bakin ciki lokacin da yaji cewar cikin ya zube, nan ya zauna acikin asibitin har gari ya waye sannan ya tafi gidansu yaje ya sanarwa da mamanshi, hankali tashe mama ta bishi zuwa asibitin bayan tasaka A'isha ta hadowa nadiya tea da sauran kayan karyawa,
Tunda mamanshi taje itace take kula da nadiya domin tana mutukar sonta ko kadan bata son damuwarta shiyasa kullum cikin yimata hidima take, karfe 8 daidai yaje ya dauko A'isha da shamsiyya zuwa asibitin ita nadiya sai yau taga shamsiyyan ma domin akomai tasan tayiwa shamsiyyan nisa amma da yake namiji ba dan goyo bane shine yaya kabeer yake neman fifita shamsiyyan akanta,
Nan sukayi mata sannu mama ta taimaka mata ta tashi ta hada mata tea sannan ga farfesun kayan ciki da soyayyen kwai ta bata taci takoma ta kwanta, sai da wurin karfe 11 sannan yaje gidansu nadiya yafada nan mama ta rude ta shirya tatafi asibitin amma da taje sai taji hankalinta ya kwanta saboda tasamu maman kabeer na kula da nadiya,ita nadiyan ma lokacin bacci takeyi, nan su mama suka shiga gaisawa tareda jajantawa juna.
Kwanan nadiya takwas a asibitin aka sallameta bayan anyi mata wankin ciki nan Maman kabeer tace maman nadiya tatafi da ita Gida tunda likitoci sunce ta dan samu hutu banda aikin wahala, ita abinda yasa bazata tafi da nadiya gidanta ba tasan idan sunje bazata sake kamar gidansu ba amma idan gidansu ne zatafi sakewa,
Nan mama ta yarda suka tafi da nadiya bayan sun biya ta gidanta sunje sun daukar mata kayan sawarta, komawar nadiya gida ba karamin kwanciyar hankali ta samuba domin cikin sati biyu tayi kiba tayi kyau jikinta ya dawo saboda mamanta tana mutukar kula da ita sannan babu abinda takeyi daga kallo sai ko taci abinci ta kwanta, gashi yanzu babu damuwa babu bacin rai bp dinta ma da yahau ya sauka, babu abinda takeyi ko mama tagani tana aiki idan tace zata tayata sai taki, sai dai ta zauna tayita kallo idan kuma su husna sun dawo daga makaranta suyita hira suna sata dariya domin suna nan har yanzu da halinsu na sa'insa, idan yamma tayi kuma abba yadawo to bazai shigo haka ba sai ya tahowa da nadiya wani abu na kwadayi, yana dawowa kuma zasu tattara su koma falonsa hatta abinci tare za ahadu aci, ana ci ana hira shiyasa nadiya ta kwammace gara rayuwar gida sau dubu data gidan aurenta.
Yaya kabeer ma yana zuwa dubata lokaci zuwa lokaci sannan yana kawo mata abubuwan bukata, har nadiya ta Karaci zamanta agidansu tafara shirin komawa gidanta bata taba fadawa mama matsalarta ba ko kuma damuwarta ba duk da tasan tana cikin damuwa sannan babu wanda yafi cancanta da jin damuwarta sama da mahaiifiyarta amma bata taba sanar da mama ba, tasan ita babu wani jin dadi ko farin ciki kwaya daya da zata iya fada wanda tasamu agidan aure to ina dadin ma yake auren dako amarci ba asamu anyiba matsalolin rayuwa suka taru suka yimasa illa,
Watanta biyu agidansu sannan takoma gidan yaya kabeer bayan abba ya bata kudi har dubu hamsin yasaka mata acikin account yace idan tana da damuwa sai ta dauka tayi amfani dashi,
Tunda ta koma gidan yaya kabeer yasamu abinda yayi missing shikenan suka dawo yar gidan jiya, baya zama agida idan yafita tun safe sai dare, baya zama suyi hira da ita to bai zauna agidan bama bare suyi hirar, wayar cikin dare, fita sassafe kai shamsiyya makaranta, ita dai nadiya kawai zaman hakuri take nan tasake rarramewa, damma dai yaya kamal dan uwanta yana kiranta awaya koda yaushe yana kwantar mata da hankali, da haka kwanaki masu yawa suka shude nan tasake samun wani cikin tafara laulayi ganin haka yasa yaya kabeer fara bata yar kulawa saboda cikin da yake jikinta,
Kamar wancan lokacin yanzun ma tayi kiba tayi kyau saboda hankalinta ya dan kwanta, sannan kuma fitar da yakeyi sassafe zuwa kai shamsiyya makaranta ahalin yanzu yadaina wayar tsakar daren ce dai har yanzu yanayi,
Daga mamanta har Maman shi kowacce na taka muhimmiyar rawa wurin ganin sun bata kulawa domin kullum cikin yimata aiken kayan dadi suke, haka kawai zataga mamanshi ta aiko A'isha kanwarshi ta kawo mata abun kwadayi, ko kuma taga Amira kanwarta mama ta aikota, yanzu bata da damuwa sosai saboda shima yaya kabeer din yarage masifar da yake yimatay,nan hankalinta ya kwanta tayi kyau sosai kowa yaganta yanzu yasan tasamu kwanciyar hankali sabanin da.
Cikinta yagirma ya shiga wata bakwai sannan yayi kato kamar wadda zata haifi yaya hudu, karfe biyu da rabi na dare ta farka tana jin yunwa da kishin ruwa dama tunda cikin yafara girma take tashin dare cin abinci da shan ruwa, yaya kabeer tajiyo afalo yana aikin wayar tasa ta dare kamar yadda ya saba, nan ta yunkura dakyar ta fita falon ranta idan yayi dubu ya baci take zufa ta rufeta jininta yahau mutuka saboda dama ta dade da kamuwa da hawan jini nan hawan jinin ya tashi jikinta yahau rawa,
"Yaya kabeer..."
Takira sunanshi cikin radadin ciwo, saurin tashi yayi ya katse wayar amma kafin yakarasa wurinta har ta sulale ta yanke jiki tafadi cikin daukewar numfashi.......
*_Ummi Shatu_*๐๐ป
[7/19, 7:50 AM] Ummi A'isha๐๐ป: *MIJINA SIRRINA...!*๐น
_(True life story)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
ยฎ *HASKE WRITERS ASSO.* _Home of expert writers_
*21*
~~~Arude yaje inda take yafara jijjigata yana kiran sunanta,
"Nadiya, nadiya, nadiya.."
Jin bata amsaba sannan da alama bata yin numfashi yasashi cikin sauri ya mike ya fita arude domin dauko ruwan sanyi saboda abisa dukkan alamu suma tayi,
Bude idonta tayi tabishi da kallo domin dama suman karya tayi masa saboda taga alamun idan har batayi masa hakaba bazai daina wannan mummunar dabi'ar ta wayar dareba,
Tana jin alamun tahowarsa tayi saurin rufe idanuwanta tareda dauke numfashinta,yana zuwa ya kwara mata ruwan sanyi nan ta saki ajiyar zuciya da karfi ta bude idanuwanta cikin alamun galabaita,
"Nadiya ko zamu tafi asibiti..?"
Kai ta girgiza masa tana kallon duk yanda yabi ya rude domin ko kadan baya son ya sake rasa cikin dake jikinta,
"Bani abinci naci yunwa nakeji"
Cikin hanzari ya tashi yaje ya kawo mata ta karba ta fara ci, tun daga wannan lokacin tasamu yadaina yin wayar dare sannan zuwa kai shamsiyya makaranta ma da yakeyi yanzu yadaina saboda baya son asake samun matsala kamar yanda aka samu a wancan cikin,
Cikin kankanin lokaci nadiya tayi kyau tasake yin kiba saboda yanzu bata da matsalar komai kabeer yana kula da ita haka mahaifiyarsa itama tana iya bakin kokarinta wurin faranta mata rai.
Har cikin nadiya ya shiga watan haihuwa kabeer bai sake yimata wani abu wanda zataji daci acikin ranta ba domin yana mutukar son cikin dake jikinta,
Cikin dare nakuda ta kamata nan yashiga firgici ya kinkimeta suka tafi asibiti gaba daya yakasa samun nutsuwa yayi nan yayi can har aka samu ta haifi yaranta yan tagwaye mace da namiji, murna awurin kabeer abin ba acewa komai, kasa tafiya yayi sai acikin mota ya kwana, gari yana wayewa kuwa yaje yakaiwa su mama labari kafin kace wani abu tuni har asibiti ya dinke da yan uwa yan gidansu da yan gidansu nadiya, jariran tubarkalla bul bul dasu kyawawa domin yaya kabeer shima ba baya bane awurin kyau haka nadiya,
Kwanansu biyu a asibiti aka sallamesu suka koma gida, kayan da kabeer ya hado shida mahaifiyarsa abin ba amagana domin sun jibgowa mai jego ita da jariranta kaya na kece reni,
Abban kabeer da abban nadiya tare suka zo ganin jariran anan suke tambayar kabeer sunan da zai sawa yaran yace sunan mahaifiyarsu abban zaisa da sunan mahaifinsu wato usman da Habiba nan su abba suka yita sawa yaran albarka dasu kabeer din,
Adaki yasamu nadiya ya fada mata yanda sukayi dasu abba nan itama tabada goyon baya tace sai su rinka kiran yaran da nabeel macen kuma nabeela,
Shagali iya shagali kabeer yayishi awannan haihuwar, komai da nadiya ke bukata itada yaranta ya tanadar musu, ranar suna aka nadawa yara sunan Habiba da usman,
A washe garin suna kuma aka tafi da nadiya gida domin mamanta ta kula da ita tunda haihuwar farice sannan yara biyu,
Tunda ta koma gida ta sake samun kwanciyar hankali, yaya kabeer yana zuwa kusan kullum yana ganinsu ita da yaranta dahaka har suka yi watanni biyu agida a lokacin ne abba yace zaman ya isa haka ya kamata su koma gida nan nadiya ta hada komai nata ta shirya kabeer yazo ya dauketa suka tafi.
Komawarta gidanta nan ma babu wani bacin rai ko tashin hankali zamansu suke yi da kabeer lafiya babu wata matsala, dan uwanta kamal kuma kullum cikin kiranta awaya yake yana tambayarta yanayin zamansu da kabeer kullum hakuri da nasiha yake yimata yana nuna mata cewar shi zaman aure ibadane dan haka dole akwai jarrabawa acikinsa.
Kwantar da hankalinta tayi taci gaba da