Showing 60001 words to 63000 words out of 82977 words
Chapter 21 - MIJINA SIRRINA COMPLET BOOK BY UMMI AISHA.txt
data dabaibayeshi.
Washe gari da safe nadiya ta sake kiranshi da sabon sim din da ta siyo nan yaki dauka tayita kira amma bai dauka ba daga karshe sai ta tura masa da massage cewar ita masoyiyarshi ce kuma sonshi take, ko takan text din baibi ba bare ya turo mata da reply,
Hakura tayi ta rufe sim din tunda taga alamun kamar bazai kulaba ai kuwa bai kula dinba shi duk da bai san wacece ba bata burgeshi ba domin mace daya ce kacal ke burgeshi a duniya itace nadiya kuma ya rigada ya mallaketa,
Kiranta yayi awaya lokacin tana kitchen tana soya miya, fadeela ce takawo mata wayar tana yimata surutu,
Karba tayi ta kara akunnenta,
"Baby yakike?"
"Lfy lau"
"Yau banji kiba, kina lafiya?"
"Lafiya lau"
"Ya twins dina?"
"Lafiya"
"Me kikeyi yanzu?"
"Aiki nake"
"Nikuma kin ganni nadawo gida duk agajiye da ace kina kusa da kinyi min tausa ko?"
"Uhmm" tafada tana juya miyar da takeyi,
"To yanzu me zaki bani duk da bakya kusa?"
Shiru tayi batayi magana ba,
"Baby"
"Na'am"
"Kice you love me"
"Dan Allah kayi hakuri basai nafada ba"
"Why? Gaskiya bazan hakura ba har sai kin fada sannan kiyi kissing dina.."
"Ka manta jiya ko?" Ta fada afili amma acikin zuciyarta cewa take "babu abinda zanyi maka bare ka cika min kunne da wannan shakuwar taka da ajiyar zuciya"
"Baby yi mana ina jinki.." Taji yafada a marairaice,
Daga murya tayi tace "na'am mama, to gani nan"
Jin haka yasashi rabuwa da ita saboda a tunaninshi mama ce ke kiranta,sallama yayi mata ya kashe wayar anan ta ajiye wayar taci gaba da aikinta. Tun daga wannan lokacin duk sanda ya kirata aikin da yake sakata kenan amma sai taki sai taji yana neman barinta da Allah sannan sai tayi amma kuma da zarar tafara zataji ya dameta da ajiyar zuciya ko shakuwa shiyasa ma bata son ta rinka biyeshi tana yimishi abinda yasata din,
Daren yau kam akalla sai da ya shafe awanni biyu yana wannan shakuwar,duk rashin tausayinta akanshi yau sai da taji yabata tausayi wanda bata san dalili ba,
"Sannu Ahmad.."
"Yawwa baby"
"Kasake shan ruwa"
"To baby"
Tana jinshi yana shan ruwa amma koda ya shanye sai yaci gaba da shakuwar, dakyar yasamu ya daina,
"Baby da zaki yarda da na turo miki kudin jirgi kin biyoni"
"Ka manta alkawarin da kayine? Idan na biyoka me zanyi maka?"
Ajiyar zuciya ya saki mai karfi,
"Kuma fa hakane, sorry mantawa nayi"
Jin yadaina shakuwar yasashi yi mata sai da safe ya katse wayar.
Akwana atashi har amadi ya kwashe watanni 8 a kasar london wanda yanzu har yafara lissafin dawowa,ita kam nadiya basu koma makaranta ba saboda yajin aiki da aketa gudanarwa,duk abin baiyi mata dadiba domin bata son ta tare bata gama makaranta ba,
Shiryawa tayi ta tafi sumaila gidan umman sumaila bayan ta sanarwa da amadi dama shi ba hanata fita yakeba daga tace zataje wuri kaza zaice adawo lafiya babu ruwanshi da yimata kulle,
Lokacin da taje gidan umman sumaila, umman murna tayi sosai da ganinta saboda dama tanada niyyar zuwa ranon itama domin kayan gyaran da tasa aka tanada musamman saboda nadiyan,tunda takai kanta kuwa nan umman ta shiga tula mata abubuwa, wasuma bata taba saninsu ba bare ganinsu,
Shikuma dan nacin nata akoda yaushe yana tareda ita a waya, ko abinci yake ci sai ya kirata kome yake yi sai ya kirata,
Sabon sim din da ta saka domin kiranshi kuwa harma ta daina kiran saboda baya dagawa ita abin har daure mata kai yayi.
Gyara na musamman umman sumaila ke yimata baji ba gani, ita duk ma tagaji da dure duren da ake yimata gashi umma ta hanata tafiya, ita da taje da niyyar sati uku saida ta shafe fiyeda sati shida har saida akace an janye yajin aiki sannan umman ta kyaleta ta tafi amma tace zata rinka yi mata aike kuma lallai lallai duk abinda aka kai mata tayi amfani dashi,
Tana komawa gida tafara shirin tafiya makaranta saboda Allah Allah take yi tagama makarantar kafin amadi yadawo amma tasan hakan ba mai yiyuwa bane tunda shi yanzu saura watanni biyu kacal yadawo.
Sai da ta tanadi komai na bukata sannan ta tafi wudil can dinma dai da kayayyakin umman sumaila ta tafi wadanda yanzu har ta saba dasu,
Kan karatunta ta mayar da hankali sosai, koda wanne lokaci amadi yana kiranta, wata rana ai fada wata rana ayi dadi kun san halin mutuniyar taku da taurin kai, amadin ne kadai ya iya da ita saboda shi mai hakuri ne sannan bashida riko domin ko fadan akayi ba ayin minti biyar zai sake kiranta nan zai shiga lallashinta yana bata hakuri koda kuwa shi dinne da gaskiya, yawancin fadan ma shine mai gaskiyar amma sai yayi hakuri ya dauki laifin ita yabata gaskiyar yayita rarrashinta yana bata hakuri har sai ta hakura, ita kanta ta san yana tsananin sonta kawai dai zuciyarta ce har yanzu bata sauko ba daga fushin baya.
Yau da gobe babu wahala awurin Allah domin amadi har ya kammala abinda yaje yi yafara shirye shiryen dawowa, wani boutique yashiga ya rinka jibgowa nadiya sexy dress, duk kayan da ya siyo mata babu wanda zata iya sakawa ta fita koda tsakar gida sai dai adaki domin kayane na garari,
Koda wasa bai fada mata dawowarshi ba shiru yayi mata, kullum yana yi mata waya kamar yadda ya saba amma ranar da zai dawo sau daya ya kirata daga nan sai bata kara jinshi ba.....
*_Ummi Shatu_*👌🏻
*MIJINA SIRRINA...*🌹
_(Labarin k'auna)_
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_
_Kuna ina? A'isha chuchun gaye, A'isha Dansabo, A'isha Gambo, A'isha (Maman khadija),A'isha (mom minal) wannan shafin nakune takwarorin Ummi Shatu.._
*61*
aishaummi.blogspot.com
*K*asancewar shigowar yamma yayi sai bai samu zarafin kiranta da wuri ba,
Yana ajiye jakarshi ya nufi part din da aka gina musu shida nadiya domin baya son asamu kuskure daga yanda ta zana,
Part din ba karamin kyau yayiba amma babu abinda aka zuba na furnitures, yanda nadiya ta zana haka akayi shi babu abinda aka sauya,
"Wowwww.." Yafada bayan ya zira hannuwanshi acikin wandon jeans dinshi,sai da yabi ya dudduba ko ina sannan yafito yakoma part din hajiya,
"Autana ina kaje ne inata nemanka, kazo kayi wanka kaci abinci mana"
Hajiya dake tsaye cikin falon ta fada,
"Hajiya part din baby naje nagano, bana sone ayi mata ba yanda ta zanaba asamu problem, amma naga komai yayi daidai.."
"Ohhh autana da rawar kai kake, tunda ka dawo ai sai akawo maka ita ku tare kowa ya huta"
"Yawwa hajiya dan Allah kisa baki nanda 2 weeks ta tare.."
"To shikenan autana, yanzu dai shiga dakinka kayi wanka kafito kaci abinci, nayi maka mutumin naka wato tuwo"
"Woohhhhh" yafada harda dan tsallenshi sannan yawuce dakinshi.
Nadiya kuwa koda taji amadi shiru bata kawo cewar yadawo ba kuma bata kirashi ba, har dare yayi shiru bata jishi ba,
Bayan ta kwanta ne misalin karfe 9 sai ga kiranshi koda ta duba ba number din waje bane dan haka taji mamaki ya kamata,
"To shi wannan ya haka?" Ta tambayi kanta tareda kara wayar acikin kunnenta,
"Baby.."
"Uhmm"
"Shine ko ki nemeni ko bayan kuma kinji ni shiru"
"To ai nasan lafiya kake tunda najika shiru"
"Hakane, to nadawo dazu, yaushe zaki zo yimin sannu da zuwa?"
"Kadawo?"
"Wallahi nadawo baby"
"Sannu da dawowa"
"Yawwa yaushe zaki zo kiyi min sannu da zuwa? Ko nine zanzo?"
Shiru tayi tana tunani,
"Sannu da zuwa kuma? Bayan wanda nayi maka yanzu"
"Haba baby yanzu ai ba sannu da zuwa kika yimin ba, idanuwana fa suna bukatar ganin fuskar matata ko kin manta yau rabona dake 11 months da yan kwanaki akai? Allah ina son ganinki.."
"To yanzu ya kakeso ayi?"
"So nake kizo gobe, zan turo driver ya daukeki, wallahi son ganinki nakeyi"
"Allah ya kaimu goben idan banida uzuri da yawa to"
"Insha Allah ma bakida shi baby"
Dakyar dai yasamu ya dan lallasheta ya shawo kanta harta amince cewar zataje din nan yayi mata sallama ya katse wayar saboda bacci yakeji.
Washe gari kuwa koda ya kirata saida ta gama jan ajinta sannan tace yaturo drivern, shidai ta inda take so tanan yake binta, lallabata yakeyi saboda baya son taki amincewa da zuwan,
Wurin 12 daidai na rana suka karasa gidan, iya hajiya ta tarar a babban falonta ita da mai aikinta, hajiyan tana sanye da glass a idonta suna shirya bit,
A kunyace nadiya ta shiga cikin falon,cikeda murna gamida soyayya hajiya ta tarbeta,kai idan ba sani kayiba bazaka taba cewa hajiya surikarta ce ba saboda irin tarbar arzikin da tayi mata,
Lokaci kankani aka cikata da kayan marmari gamida kayan jika makoshi, jin bataji motsinshi ba yasa ta fara kiranshi awayarta amma kuma wayarshi akashe,
Ta jima zaune afalon itada su hajiya lokaci lokaci hajiya tana dan yimata hira har tsawon mintuna 20,
"Autan yana dakinshi yanata faman bacci tashi ki shiga" hajiya tace da ita tana murmushi,
"Wai dama komawa yayi?" Mai aiki ta tambayi hajiya tana dariya,
"Kema kuwa ai kin san halin auta da shegen baccin safe sai yakai azahar yana baccin nan, aida ya fito sake komawa yayi.."
Ita dai nadiya tana zaune bata tashiba har saida hajiya tasake ce mata ta shiga sannan ta tashi akunyace ta nufi dakin nasa,
Ahankali ta bude ta shiga,nan wani kamshi mai dadi ya doki hancinta wanda ya gauraye da sanyin air condition din dake sanyaya dakin,dakin ya tsaru mutuka kamar dakin mace,
Kwance ta hangoshi akan gadonshi daga shi sai gajeren wando da round neck t shirt sai sharar bacci yake yi abinshi batare da damuwar komai ba,
Karasawa tayi zuwa bakin gadon ta zauna, tashinsa tafara yi,
"Ahmad.... Ahmad" ta kira sunanshi ahankali,
Ko motsi baiyi ba bare yasan tanayi, hannu takai jikinshi tafara dan dukanshi,
"Ahmad..."
Idonshi ya bude wadanda suka yi ja saboda tsabar bacci,
"Uhm uhmmm baby..." Yafada yana kokarin tashi zaune, bata ankara ba kawai sai ji tayi ya rungumeta,
Binta da kallo yakeyi sosai domin ba kadanba ta canja mishi, kamar yadda itama take ganin ya sauya sosai, dama shi farine sosai to farinshi na yanzu yafi nada sannan ya danyi yar kiba amma ba mai yawa ba,
Shi kam ganin nadiyan shi yayi ta cika sosai tako ina, wata atamfa ce kalar purple ajikinta,dinkin ya zauna daram ajikinta, riga da skirt, sannan tayi simple daurin dan kwali tana sanye da wani gyale shima purple colour,
Jikinta take kokarin janyewa bayan ta bata fuska,
Riketa yayi kam yana murmushi nan yafara kokarin lalubar bakinta amma taki tanata faman kawar da kanta, murmushi yayi,
"Baby nadawo zamu fara ko? Za afara yimin rowar da aka saba..."
Ganin taki yarda yasashi fara kissing din wuyanta, tureshi tafara yi har tasamu nasarar tureshi din ta matsa gefe,
Kallonta yayi fuskarshi dauke da murmushi baiyi fushi ba yasake matsawa kusa da ita nan ta matsa shima yasake matsawa,
"Dama dalilin da yasa kasa a daukoni kenan?"
"A'a baby ba dalilin kenan ba but kin san dai nayi missing dinki da yawa shiyasa..."
"To nidai gaskiya a'a.." Tafada tana zumbura bakinta,
"Baby pls karkiyi min haka.."
Dauke kanta tayi, ya bude bakinshi kenan da niyyar yimata magana yafasa saboda tarin da ya sarkeshi nan yafara yinshi babu kakkautawa,
Juyawa tayi ta kalleshi,
"Sannu"
Kai ya daga mata kafin yafara shakuwar da yasaba,
"Indauko maka ruwa?"
Hannunta ya kamo yajata jikinshi, yanzu kam maganar daru takare tunda taga halin da yake ciki, shiru tayi tai luf ajikinsa amma har lokacin wata irin shakuwa yake yi k'wat,
Bakinta ya luluba da nashi cikin doki abin mamaki ko minti daya ba ayiba taji yadaina shakuwar,
"Nikam yau nashiga uku kuma" tafada acikin zuciyarta,shikam amadi tunda har yasamu dama bai tsaya awuri daya ba.
Sai da yaji nutsuwarshi ta dawo mishi sannan ya kwantar da ita ajikinshi,
Hannunta Yakama acikin nashi,yafara yi mata rada akunnenta,
"Baby ga maganin shakuwar awurinki amma da zakice wai zaki dauko min ruwa..."
Murmushi ya sake yi yana kallon fuskarta, idanuwanta arufe fuskar nan gata nan dai babu yabo babu fallasa,shi gaba daya yarasa nadiya wacce irin macece wadda bata da saurin manta abu koda yake yasan sai ahankali zata manta da wulakancin kabeer har takarbi soyayyarshi domin dauriya da hakurin da tayi ba kowacce mace ce zata iyaba,
Kissing din wuyanta yayi sannan yafara jan dan kwalin kanta nan tarike hannunshi,
"Karka cire min dan kwali.."
"Saboda me?"
"Kawai"
Murmushi yayi, "baby rigima, badai kawai ba,ina son ganin kalar kitson dake kan matata ne"
"Ni babu kitso akaina"
"To zan gani haka"
Juyi tayi zata matsa daga jikinshi yayi saurin rikota ya mayar da ita,
"Baby dadina dake rikici kuma rikicin ma narashin gaskiya, inbanda haka nida mallakina amma ahanani?"
Saida ta zunbura masa baki sannan ta bude da niyyar yimasa magana, ruf ya rufe bakinta da nashi, neman kwacewa tafara yi amma kuma takasa dolenta ta hakura domin yau tasan ita takawo kanta gareshi,
Idonshi dake lumshe ya bude ya kalleta, mayar da kanshi yayi saman kirjinta ya kwantar yana sauke mata ajiyar zuciyar da yasaba yi mata awaya,
"Ka matsa zan tashi" tace dashi tana dan harararshi,
Baiyi mata magana ba illa kankameta da yasake yi,
"Nace ka matsa zan tashi.."
Nan dinma shirun yayi mata sai wata ajiyar zuciya da yake ajiyewa ahankali,
"Ai da nasan haka ne da bazan zo ba, daga zuwa na shikenan kuma kawai...." Hannunshi yakai ya rufe mata baki,ture hannun nashi tayi,
Baice da ita komai ba saida yagama sauke ajiyar zuciyarshi sannan yajuya kanshi akan kirjinta yana murmushi,
"Allah yabaki hakuri ya huci zuciyarki baby, karfa ki manta raboda dake shekara guda kenan kuma yanzu zuciya taga abinda take so take kauna sannan take bege bazata yi wani feelings ba?, wallahi wannan sakonnin badaga gareni bane daga zuciyata ne, ita keso itake muradi.."
Hannunshi yakai saman kirjinta nan ta buge hannun,yasake mayarwa ta sake bugewa yasake mayarwa ta kuma bugewa,
"Idan kika sake buge min hannu ban yafe miki ba har lahira.."
Ta inda yake cin galaba kenan idan ya hadata da Allah, tana ji tana gani dole ta rabu dashi tunda yace bai yafeba idan tasake buge masa hannu,
"Allah nan gaba ko kace inzo bazan zo ba" tafada kamar zata saka kuka,
Kiyi hakuri.." Shine abinda ya iya cemata, shiru tayi masa ta dauke kanta,
Har lokacin sallar azahar yayi suna nan tare ita dai nadiya duk yagama takurata, dan tureshi tayi,
"Dan Allah kabari ni fita nake son yi"
"Ina zakije inda yafi nan?"
"Wurin hajiya zanje.."
"A'a, ita hajiya babu ruwanta da dadewarki anan tunda tasan wurin mijinki kika zo sannan yadade bai ganki ba..."
"Nidai dan Allah kabarni intafi"
"To zan barki amma sai kinyi kissing dina sau 30"
"Gaskiya a'a" tace dashi tana zunburar baki,
"To narage miki kiyi guda 20"
"A'a"
"Allah sai kinyi, fara tun kafin mala'iku su fara tsine...."
Tashi tayi tana harararshi fuskarta babu fara'a, nan tafara abinda yace ta shiga kissing din bakinshi mai dauke da jajayen lips,
"Ai nayi sai anjima kaga tafiyata"
Daukar mayafinta tayi da dan kwalinta ahannu saida taje bakin kofa sannan ta tsaya tafara daura dan kwalin,
"Bari nataso..." Taji yafada ba shiri ta bude kofar da sauri zata fita, dariya taji yayi, toilet ya nufa yana cewa,
"To da wasa nake yimiki.."
Duk da haka dai bata koma cikin dakin ba falo tawuce wurinsu hajiya, hajiyan na kokarin tashi nadiyan tafito bedroom dinta ta shiga mintuna kadan ta leko tace nadiya ta shiga tayi salla.
Amadi kam cikeda farin ciki yayi wanka ya fito yayi salla sannan yasa kayanshi ash colour din t shirt da yellow din rubutu ajiki manya anrubuta _FUN TIME_ sai yellow colour din trouser, hatta belt din da ya daura yellow colour ce, turarenshi na axe yafesa sannan ya fita, fitarshi tayi daidai da fitowar su hajiya itada nadiya,
Kan table suka wuce direct amadi sai kallonta yake yana yi mata murmushi amma ita taki koda kallonshi ne, hajiya diban abincin ta tayi a flate tabasu wuri ta nufi falo taje tayi zamanta tana kallon labarai a CNN,
Matsawa yayi kusa da ita ya dauki flate ya zuba musu jalop din couscous wanda yasha hadin kayan lambu yayi kyau sosai,
"Kaga ka kori hajiya daga nan" tafada tana kallonshi, dan lips dinshi ya lasa,
"Baby bani fa nakoreta ba, kawai dai tabamu wuri ne..."
Bata sake magana ba tayi shiru, abincin yafara diba yana bata shima yana ci amma yasha daru da rigimarta kafin ta yarda taci abincin, diba yake a spoon ya bata idan ta diba taci sai yaci wanda ta rage acikin spoon din,
Suna tsaka da cin abincin anty siyama tayi sallama zee kanwar mijinta na biyeda ita cikin wata shiga ta alfarma.....
_Get well soon luvly sister @Khairat Dandawaki_
_Fatan alkhairi agareki stylish bitch_
_Gaisuwa mai yawa ga duk masoyan anty amadi... Musamman kawata maryama qaumi_
*_Ummi Shatu_*👌🏻
*MIJINA SIRRINA...!*🌹
_(Labarin k'auna)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_
*62*
aishaummi.blogspot.com
*T*un daga nesa zee ta kafe amadi da ido tana kallonshi domin ba karamin kyau yayiba, yayi mutukar tafiya da hankalinta gamida tunaninta gaba daya cikin lokaci kankani,
Dan kallon nadiya tayi nan ta fahimci itace matar shi dan haka tayi saurin dauke idonta daga gareta ta mayarshi kan amadi,
"Anty amadi duri aketa yine haka?" Anty siyama tafada fuskarta dauke da fara'a tana faman karkada key din motarta dake hannunta,dago da kanshi yayi shima fuskarshi dauke da fara'a ya kallesu, saida gabanshi ya dan harba sakamakon ganin zee da yayi domin bai so ganinta ba kwata kwata a wannan lokacin saboda yasan zaiyi wahala idan batayi abinda zai b'ata mishi shirinshi ba,
Kallonta yayi sosai tayi kyau cikin wani dark blue din material dinkin doguwar riga, fuskar nan sai sheki takeyi saboda kwalliyar da tasha, kanta daure da wani hamshakin gwaggwaro, tamkar wacce zataje dinner ko kuma zaben sarauniyar kyau, dan mayafinta kuwa akafadarta guda daya kawai ta ajiyeshi batare da ta koda yafashi ba,
Saida yasakawa nadiya abinci abakinta sannan yayiwa anty siyama magana,
"Kai anty dan Allah, wai ya akayi kika daina fadin yayan ne.."
"Saboda kai ba yayana bane..."
"Sannu da zuwa anty siyama" nadiya tafada wadda maganarta ce ta katse hirar anty siyama da amadi,
"Yawwa amaryar mu, har anzo tarbar angon ne?"
Sunkuyar da kai nadiya tayi tana murmushi abinta cikin kunya,
"To ba dole ba, aini dan gatane.."
Dariya anty siyama tayi tajuya tawuce falo wurin hajiya, ita kuwa zee tana tsaye rikeda waya a kunnenta tana magana ahankali sai wani kashewa amadi ido takeyi,
Koda wasa bai nuna ya santa bama bare nadiya ta kawo wani abu acikin ranta, ci gaba da bata abincin yayi har suka cinye wanda ya zuba musu,
Cikeda yanga da jan aji zee tabar wurin itama ta nufi falo batare da tayiwa amadi magana ba,
Kallon nadiya yayi,