Showing 72001 words to 75000 words out of 82977 words
Chapter 25 - MIJINA SIRRINA COMPLET BOOK BY UMMI AISHA.txt
yayi ta haye bayanshi yafara zagaya falon da ita.
Saida yaji yagaji sosai sannan ya zame ya kwanta tareda birkitota kanshi, ajikinshi ya rungumeta sosai yafara lumshe ido alamun bacci ga mamakinta kuwa mintuna kadan taji ya fara ajiye ajiyar zuciya ahankali yana fitar da numfashi cikin nutsuwa alamun bacci,
Zama taci gaba dayi ajikinsa har na tsawon wani lokaci kafin ta janye jikinta takoma dakinta, wanka ta sake yi tasha kwalliya, tunowa tayi da tunda tazo bata leka dakin dake opposite da nataba dan haka batare da bata lokaci ba ta nufi dakin,
Komai nacikin dakin sak irin natane sai ko kala da ta banbanta domin shi wannan milk and coffee colour ne kayan ciki,
Akwatunan kayanta tagani ajiye agefe guda nan farin ciki yakama ta,bude akwatin taje tayi ta dauko wata atamfa Holland dark green mai zanen buta ajiki ta saka,
Sarka da dan kunne da bangles tasa ta koma falo wurin amadi yana nan ayanda tatafi tabarshi yanata shakar baccinshi,
Kan doguwar kujera tahau ta mike tana bin falon da kallo, komai na gidan amadi yafi na gidan kabeer kyau da haduwa sannan shi kansa kabeer din amadi yafishi kyau da gogewa irinta gayu, ta tabbata Allah ne yayi mata zabi har yabata amadi domin ya maye gurbin kabeer bawai iyawarta ko dabarar ta ba,
Ita dinma baccin ne yadan fara daukarta sama sama sai kuma taji motsin mutum ajikinta, bude idonta tayi ahankali nan taga amadi yana aika mata da tsadadden murmushi mai sanyaya zuciya da kashe jiki,
"Baby kinyi kyau...." Bai kai ga barinta tayi magana ba yakai lips dinshi kan nata,
"Shine kika tashi baki tasheni ba ko.."
"Ai naga bacci kake"
Mikewa yayi ajikinta, yana shakar kamshin da jikinta yake fitarwa, ganin lokacin salla yakusa yasashi tashi yaje yayi wanka yasake kaya yafito,
Sallar la'asar suka yi sannan suka tafi part din hajiya domin gaidata,
Ba karamin murna hajiya tayiba lokacin data gansu, har kasa nadiya ta tsugunna ta gaisheta shi kuma amadi sai wata shagwaba yake zubawa hajiya kamar wani yaron goye,
Basu suka bar part din hajiya ba sai bayan sallar isha, yau ma kamar jiya shine ya timaka mata tayi komai sannan ta kwanta sai lokacin shikuma yaje ya shiryo yadawo dakinta, rungumeta yayi yana shafar kanta,
"Baby yau dai bazaki yi bacci da wuriba dan haka kiyi min tatsoniya.."
"Ni ban iyaba.." Tabashi amsa,
"Ni na iya bari inyi miki.."
Tatsoniya yashiga yi mata wanda tun tana amsawa har dai yaji tayi shiru alamun tayi bacci, addu'a yayi musu ya lullubesu, gaba daya kasa baccin yayi sai tunane tunane kala kala dake addabar zuciyarsa.
Haka suka kasance har na tsawon kwana biyar, kullum hajiya ke aiko musu da abinci har nadiya tafara girki da kanta sannan idan tayi sai ta zubawa hajiya nata daban a kula akai mata,
Iya soyayya amadi yana nuna mata, komai tare suke yi dashi baya barinta tayi ita kadai.
Fitowarta daga wanka bayan tagama aiki ta zauna tayi kwalliya, towel dinta ta sauke domin saka kaya,
Burum amadi yashigo kamar wanda aka koro,
"Ahmad menene haka.." Tafada batare data jiyo ba,
"Baby abu nake nema yi hakuri..."
Riga ta saka sannan ta juya tana kallonsa yana bincike acikin drewar din gadonta,
"Wai me kake nema?"
"Wani sim pack da nashigo dashi nan jiya"
Murmushi tayi tajuya takarasa shiryawa sannan ta dauko sim pack din ta nuno masa,
"Ka ganshi nan amma tunda kashigo min daki batare da excuse ba bazan baka ba..."
Tsalle yadaka sai gashi agabanta, daga shi sai short nicker babu ko riga,
"Yi hakuri baby bazan sake ba.."
Yace da ita tareda langabe kanshi,juyawa tayi zata matsa daga wurin yayi gaggawar rikota,
Hannuwanta ta boye abaya bayan ta matse sim pack din atafin hannunta, janta yayi zuwa jikinshi yana kallon fuskarta,
Gam tarike sim pack din tahanashi turata baya yayi tafada kan gado yabita nan yafara kokarin kwatar sim pack din,
Sun dade suna burgima akan gadon kafin ya rufe bakinta da nashi, difff sukayi daga shi har ita sai ko numfashinsu dake cin karo da juna wurin fita,
Sun debe lokaci mai tsawo cikin wannan yanayi, amadi ne yafara sassauta rikon da yayi mata, tashi yayi jikinsa a mace ya fita daga dakin, sim pack din da bai dauka ba kenan yakoma dakinshi ya kwanta rub da ciki akan gado, ajiyar zuciya yake ta faman saki ahankali yana jin wata irin matsananciyar bukatar nadiya a wannan lokacin,
Saida yadanji nutsuwa sannan yatashi yashiga wanka,
Itama acikin yanayin mutuwar jiki yatafi yabarta, ahankali take sauke numfashi har numfashin nata ya daidaita, kasa fita tayi dan haka taci gaba da zamanta acikin daki har amadi ya shigo,
Blue din t shirt ce ajikinsa sai farin jeans, batare da ya karasa wurinda takeba yayi mata magana yana murmushi,
"Baby abinci...." Yafada cikin shagwaba, tashi tayi ta sauko daga kan gadon tazo zata wuce ta gefenshi, sim pack din dazu ta mika masa batare data yi magana ba, karba yayi yana murmushi,
Koda sukaje dining dinma domin cin abinci nan dinma wani sabon yanayin ne yarinka ziyartar su,
Akoda yaushe hakace take faruwa tsakaninsu, satinsu uku da tarewa yan gidansu nadiya suka zo harda mama ganin gida, wuni suka danyi mata sannan suka tafi,da kuka suka rabu itada twins dinta kamar wata yarinya haka ta zauna tana kuka, rarrashinta amadi yafara yi,
"Yi hakuri baby, tunda babu twins ai gani..."
Jin batayi shiru ba yasashi manna bakinsa kan nata, shiru tayi batare data shiryawa hakan ba,nan yashiga rarrashinta a aikace bada bakiba,
Daren ranar dakyar amadi yasamu bacci, tunani yafara yi aranshi kodai yadaina zuwa dakinta ne saboda kullum awahale yake barci sannan koda rana ne idan suna tare hakanne ke faruwa shikuma baya son karya alkawarin da ya daukar mata,dan baya baya yafara da ita, ko zuwa kusa da ita yadan rage to amma kuma shakuwar da ta dade da shiga tsakaninsu ita ke hanashi nisantarshi domin ko yawo bai iyaba kullum daga wurin aiki sai part din hajiya sai ko gida, koda yaushe suna kusa da juna sannan komai tare suke yi, ko makaranta sukaje basa iya rabuwa, daga yaji baiji motsinta ba zai lalubota awaya ko ita ta kirashi, haka daya baya iya cin abinci batare da daya ba wannan sabonsu ne,
Irin zaman da suka cigaba da yi kenan, kullum tare suke tafiya wudil su dawo tare, aikin gidan tare suke yi, girki, shara, wanke wanke,cin abinci komai tare suke gudanarwa,wannan dalilin ne yasa suka shaku mutuka.
Kasancewar yau weekend ne duk suna gida shida ita, farcenta yagyara mata ya kankare mata shi, itama tagyara masa nashi,
Part din hajiya yatafi ita kuma ta shiga kitchen ta sauke girkin da ya kammala na rana,
Daga ita sai wata yar farar yaloluwar riga iya cinya,dakinta takoma ta kwanta akan gado tafara tsifar kitson dake kanta, tun tanayi har tagaji ta kwanta sai bacci,
Ahaka amadi yashigo ya sameta, gefen kanta yaje yazauna ya dora kanta akan cinyarshi yafara yi mata tsifar, har yagama bata tashi ba yana kokarin zameta yatashi ne yaga ta bude ido,
"Baby kin tashi? Nayi miki tsifa saura abu daya.."
"Me?" Ta tambayeshi,
"Wanke gashi.."
Baj jira amsarta ba ya ciccibeta sai bathroom, ajiyeta yayi ya debo man wanke gashi kala kala yasoma wanke mata,
Rigarta ya sabule,
"Saura wanka.."
Rigar tarike, "nidai a'a"
"Wallahi sai nayi miki wanka yau.."
Jin abinda yace yasata kyaleshi ruwa ya sakar musu akansu, ganin yafara zare rigarshi yasata saurin lumshe idonta,
Sai da yayi musu wanka tas shida ita amma yakasa daina saba mata soso da sabulu, sunfi awa daya dakyar ya iya daura mata towel ya ciccibeta zuwa cikin dakinta, idanuwanshi sun gama sauya kala jikinsa duk babu kuzari amace,
Akan gado ya shimfidar da ita, ita dinma tana jinta cikin wani irin wahalallen yanayi domin dure duren umman sumaila yau kam sunce sai anfitar dasu, har wani hajijiya takeji da hajijiya tana daukarta banda murdawar da mararta tafara yi kamar wacce zatayi period,
Jin ya ajiyeta yana kokarin tafiya yasata bude lumsassun idanuwanta wadanda ke jike jalaf da ruwa sunyi wata kala tadaban,
Hannunshi ta riko......
_Sakon fatan alkhairi gareki mamu Allah yaraba lafiya..._
*_Ummi Shatu_*👌🏻
*MIJINA SIRRINA...!*🌹
_(Labarin k'auna)_
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
® *HASKE WRITERS ASSO.*
_Home of expert & perfect writers_
_Fatan alkhairi ga masoyana masu karanta labaraina aduk inda suke, wannan shafin kyauta ne agareku,duk wata masoyiyar Ummi Shatu wannan shafi natane... Ina alfahari daku_
*69*
aishaummi.blogspot.com
*J*uyowa yayi yana kallonta, ganin irin kallon da yake yi mata yasata saurin lumshe idanuwanta,
Dawowa yayi zuwa gaban gadon ya tsugunna yana rike da hannunta jikinsa yana digar da ruwa,
"Baby ya akayi..?" Ya fada acan kasan makoshinsa,
Ita maganar ma gaba daya bata jin zata iya dan haka tayi shiru sai sake matse hannunshi da tayi cikin nata,
"Baby..."
Yasake kiran sunanta domin yana son gasgata abinda zuciyarshi ke raya mishi,
Mikewa yayi nan taja hannunshi, ajikinta ya samu masauki ya daga kanshi yana kallonta, bakinta takai bisa nashi,
Dakyar ya iya raba bakinsa da nata,
"Baby kin amince? Bazaki zargeni da laifin karya miki alkawari ba..?"
Kai ta daga masa, cikeda farin ciki hadida doki yafara warware towel din dake nade ajikinta.
***
Abangaren kabeer kuwa al'amura sun fara sauki domin tunda su fati da A'isha sukaje suka ga halin da yake ciki suka koma suka sanarwa da mama da abbansu daga mama har abban babu wanda ya kula maganar domin sunce sun dade da cireshi daga sahun yayan da suka haifa,
Kuka A'isha da fati suka shiga yi suna rokon su abban amma basu sauraresu ba daga karshe saida maganar taje kunnen abban su nadiya da umman sumaila, taruwa sukayi gaba dayansu suka tattauna tareda bawa juna hakuri tunda dai kabeer dansu ne babu yanda zasuyi sannan hannunka baya rubewa kace zaka yanke ka yar, dan haka yazama wajibi su tsaya su taimaki rayuwarsa su rabashi da asabe ko zai samu damar fita daga halin hau'ula'in da yake ciki tunda dai Allah ya rufa asiri ta sanadiyarsa zumunci bai rabu ba,
Dakyar aka samu Abba da mama suka sauko suka yarda da abinda yan uwa suka fada, nan aka dukufa ka'in da na'in wurin rokon Allah tareda yin sadaka akai akai domin Allah ya raba kabeer da masifar da yake ciki,
Cikin ikon Allah hankalinsa yafara dawowa jikinsa tun da ya kyalla ido yaga asabe agidansa hankalinsa yatashi domin bai san ya akayi ma har ya aureta ba, jinsa yake kamar wani sabon mutum wanda ya shafe shekaru aru aru cikin halin lalurar tabin hankali, jinsa yake kamar dogon barci yayi mai tsawo sai yau ya farka,
Tamkar zautacce ya zama sai faman kiran nadiya yake, nan hankalin asabe yayi kololuwar tashi domin bata tsammaci aikin boka na kududu zai karye da wuri ba,
Cikin dare kabeer yaketa aikin zuba mata masifa yana zaginta yana cewa sai tabar masa gidansa, ina nadiya? Wannan tambaya yayi mata ita tafi sau dari cikin wannan dare,
Daren ranar basu runtsa ba saboda tashin hankali, zagi kuwa asabe ta shashi agun kabeer yafi akirga sai kiranta da karuwa yake,
Lokacin da asuba tayi yafita salla lokacin ne tasamu damar kiran kawarta teemah ta zayyane mata abinda yake faruwa nan teemah tabata shawara, sosai taji dadin shawarar teemah kuma tayi na'am da ita,
Shi kuwa kabeer yadade yana addu'a a masallaci domin yaushe rabonsa ma da zuwa masallacin? Shi kansa bazai iya tuna lokacin ba domin tunda asabe ta shigo cikin rayuwarsa komai nasa ya lalace,
Yana fita daga masallaci yaje ya figi mota sai gaidansu, ganinsa sassafe yasa mama cikin tashin hankali domin tayi zaton ba kalau ba,
Kuka yasata agaba yafara yi yana neman gafararta tareda rokon cewar ta yafe masa,
Mama cewa tayi ta yafe masa duniya da lahira, cikin wannan hali abba yashigo ya riskesu shi dinma gafararsa kabeer ya nema yana kuka hawaye bibbiyu akan kumatunsa,
Dukkaninsu iyayen nasa sun yafe mishi amma Abba yabashi shawarar cewar ya tsaya yadage da addu'a sannan indai yana son ya zauna lafiya to ya zama dole yarabu da asabe, shiru yayi yana goge hawayen fuskarshi domin dama ko abba bai fada ba yanada wannan tunanin na sakin asabe,
Har karfe 10 tayi yana gidansu tareda iyayen nasa suna dorashi akan hanya mai bullewa, 10:30 ya tashi ya tafi da niyyar zai dawo gidan anjima,
Koda yakoma Gida tun daga get ya hade rai domin yau so yake ya nunawa asabe cewar tayi babban kuskure amma kuma koda yashiga cikin gidan sai me??
Komai an hargitsa shi baya bisa ka'ida, fuskarshi ahade yashiga falonta nan dinma anyi kaca kaca dashi, haka bedroom dinta ma amma kuma ita bata nan, nan yashiga dubata amma babu ko alamarta, ganin babu wasu muhimman kayanta ya tabbatar masa da cewar bata gidan, gaba daya ta tattare kayanta da nasa masu amfani ta gudu.
Zama yayi cikeda takaici gamida dana sani mai tsanani tareda bacin rai dake faman ziyartar zuciyarsa, in banda tafarfasa babu abinda zuciyarsa keyi, sannu ahankali wasu hawayen nadama suka fara bin kumatunsa,
Yadade zaune yana kukan takaici kafin ya iya tashi, yama rasa abinda zaiyi domin idan yace zaibi asabe mc to bai san ta inda zai fara nemanta ba domin ko yaje jos zaiyi wuya yaganta,
Sake rufe gidan yayi yafita ya nufi masallaci domin har azahar ta kusa, daga can gidansu yasake komawa nan ya zauna tareda su mama, mama sai nasiha take yimasa tana yimasa fada akan rayuwa domin ko yanzu yaga darasi irin na kaidin mata.
Sai dare yabaro gidan yakoma nasa, kasa bacci yayi sai aikin tunani, can karfe 2 nadare yaji alamun dirgowar mutane cikin gidan, ta window yaleka nan ya hango mutane guda hudu da bakaken kaya hatta fuskarsu rufe take da bakin abu, mai gadin gidan yaga suna kokarin daurewa dan haka yayi gaggawar neman wurin buya.
Cikeda da sand'a hannuwansu rikeda bindigogi suka shiga dakin nasa amma neman duniya sunyi basu ganshi ba, ko ina na gidan saida suka caje tsaf amma babu kabeer,
"Ya oga yakamata fa mu ware tunda bamu ga wannan gayen ba, kar asuba tayi mana anan.."
D'aya daga cikin yan fashin ya fada,
"Haka za ayi zaki bari nakira waccar mata..." Ogan yafada yana latsa wayarshi, mintuna kadan yakara wayar a kunne,
"Ya kun kasheshi..?"
Asabe mc ta tambayeshi ta cikin wayar,
"Ai bamu ganshi ba, da ace mun ganshi da tuni mun dade da hallakashi.."
Dan shiru yayi yana saurarenta kafin yace,
"Shikenan bari mu faso.."
Juyawa yayi ga yaranshi, "ya kuzo mubar gidan nan kun san tafiyar mu mai nisa ce.."
Basu kara bi takan mai gadin ba suka kama katanga suka tsallaka bayan yan mintuna kuma yaji sun sake dawowa sun dauki motarsa kwaya daya wacce tayi saura, duk abinda yake faruwa akunnen kabeer ne domin yana makale cikin rizabuwa yana jinsu, dama rizabuwar babu ruwa yanzu aciki ita yabude yashiga ciki ya buya,
Duk da yaji tafiyarsu amma bai iya fitowa ba har saida asuba tayi, duk yabi yahada zufa,
Mai gadi yaje ya kunce wanda duk yajigata.
Gari yana wayewa kabeer ya sallameshi sannan shima ya hada duk kayanshi wadanda sukayi saura wanda yasan zai bukata ya kulle gidan yanufi gidansu,
Al'ajabi sosai su mama suka shiga domin abin al'ajabine wai asabe mc tasa ana farautar rayuwar kabeer, tun daga wannan rana yakoma gidan da zama, gashi babu aikin yi nan yashiga fafutukar neman wani,
Duk da yanajin kunyar abban nadiya da mamanta haka ya daure ya cije yaje gidan ganin yaransa, yaji dadin yanda aka karbeshi babu wanda ya nuna masa koda afuska, tun daga ranar yasamu wurin zuwa, kusan kullum sai yaje gidan yaga yaransa.
***
Soyayya mai sanyi amadi ya shiga nunawa nadiya, ita kanta tasan tayi sa'ar miji domin komai nashi cikin nutsuwa yake aiwatar dashi sai dai abinku da sabin shiga dole sai ya nuna rawar kai,
Ita dariya ma yake bata amma bata samu zarafin yin dariyar ba har saida nutsuwarta ta dawo gareta,
Hannunshi takama tana dariya kasa kasa, idonshi ya bude ya kalleta yana sauke ajiyar zuciya ahankali,
"Baby dariya..." Yafada ahankali cikin sanyin murya yana kallonta,
Girgiza masa kai tayi tana kunshe dariyarta, jikinta ya matsa ya rungumeta yana gyara mata gashin kanta wanda yake ajike jalaf ya zubo ya rufe mata fuska,
"Baby Allah yayi miki albarka, Allah yasa ki haifa min twins..."
Kallonshi tayi ta mayar idanuwanta ta lumshe,
"Saboda baka san wahalar dawainiyar yan biyu ba ko shiyasa kake yimin fatan..."
"Meye wahalar aciki?" Ya katseta,
"Rainonsu.." Tabashi amsa,
"Zan tayaki.."
Yatsanshi yadora akan lips dinta ya hanata magana, wani sanyayyen kiss ya manna mata akumatu sannan yafara nuna mata soyayyar da yake mata akaro na biyu, sam bata yi yunkurin dakatar dashi ba domin shi bai taba aure ba yaune rana mai daraja agareshi,
Jinsa yayi acikin wata duniya ta daban wacce bazai iya fassara yadda takeba,
"Baby indai hakane amma kin dade kina cutar damu, meyasa baki bari mun samu wannan farin cikinba tun farkon auren mu... Kar Allah ya maimaita min rayuwar da, baby da batayi ba, yanzu ne nasan ni dan gatane cikakke..."
Rungumeta yayi yana jin sonta yana sake ratsashi,
"Amadidi tashi..." Yaji tafada,
"ba amadidi ake cewa ba, amadi zaki ce" yabata amsa idanuwansa arufe,
"To didi..."
"Meye kuma wani didi sai kace yaro..?
"Dafa? Koda yake yau ka dan fara girma ashe.."
Ya fuskanci tsokanarshi take yi shiyasa ya rabu da ita yana murmushi shi kadai,
"Kaida wa?"
"Muje inyi miki wanka.."
"A'a nagode..."
Ko saurarenta baiyi ba ya dauketa zuwa toilet,duk da itace ta nema da kanta saida taji ya isheta saboda wankan ma bai yiyuba, yau ta barowa kanta aiki,
Sai da aka dade iya dadewa sannan wankan yasamu suka fito yana goye da ita abayanshi.
Towel yadauka yafara goge mata jikinta dashi yana aika mata da murmushinsa mai sanyi,
"Baby.... Ince wani abu?"
"A'a karka ce"
"Saboda me?" Ya tambayeta yana yi mata murmushi, cumb ya dauka yasoma taje mata gashinta,
"Saboda nasan abinda zaka ce.."
"Taya akayi kika sani?"
"Nidai nasani dan haka basai kafada ba..."
Dariya ya danyi yalashi jan lips dinsa,
"Allah baby yau kin sa nazama kamar maye..."
"Shine"
Tabashi amsa bayan ta kwace cumb din, bai hakura ba yakoma bayanta ya zauna tareda rungumeta,
Rabuwa dashi tayi taci gaba da taje gashinta tana gyarashi,
Daure gashin tayi da blue din ribom ta mike taje ta dauko wata doguwar riga mai santsi yar kanti mai karamin hannu tasa,
Amadi ta kalla wanda ke zaune ya langabe kai yasa yatsanshi daya abaki, murmushi tayi,
"Wallahi yan auta dama sai ahankali, kalleka fa yanda kayi kamar wani dan karamin yaro..."
"Su kuma yan fari fa? Fada min su yasuke" yabata amsa bayan ya mike,
"Ai kasan dai yan fari sunfi yan auta ako ina..."
"Sharafffff malama.." Yace da ita tareda ficewa daga