Showing 12001 words to 15000 words out of 82977 words
Chapter 5 - MIJINA SIRRINA COMPLET BOOK BY UMMI AISHA.txt
sai ya dauko mata hoton gidan awayarsa yakawo mata tagani, gida kam ya tsaru babu karya kamar a turai domin gidane irin tsarin na turawa.
Saura kwana daya afara shagalin biki mahaifiyar kabeer ta aikowa da nadiya wani kayataccen leshi mai tsadar gaske a dinke tace tasa ranar kamu, ita kam nadiya koda yaushe aranta tana jin cewar tayi sa'ar uwar miji mai sonta da kaunarta,
Ranar kamu ba karamin kyau nadiya tayiba tafito sosai domin wani leshi ne ajikinta golden da gwaggwaro shima golden sai takalmi da jaka,
Nadiya tayi kyau iya kyau nan aka kwashesu zuwa wani hall wanda acan za ayi shagalin kamun, daf da za atashi angwaye suka zo nan kabeer yakasa rufe bakinsa sai fara'a yaketa faman zabgawa yasha wani yadin boyel brown da hula sai kamshine yake tashi ajikinsa, hotuna kam da video sun shasu babu adadi har su kabeer din suka tafi nan taron ya watse kowa ya koma gidansa yayinda su nadiya da sauran dangi sukuma suka koma gida.
Washe gari da misalin karfe 2 aka daura auren kabeer da nadiya akan sadaki dubu 30 kamar yanda waliyyinsa ya bayar wato mahaifin nadiya, shikuma mahainsa yayiwa nadiya walinci, ana tashi daga wurin daurin aure suka wuce wurin walimar da abokanshi suka shirya masa nan akaje aka debo su nadiya ita da kawayenta,
Yau dinma nadiya ba karamin kyau tayiba cikin wani jan leshi gashi an lullube jikinta gaba daya da lifayya wadda daga ganin adon dake jikinta kasan naira tayi kuka,
Wa'azi aka gudanar awurin walimar sannan akaci aka sha, ango shima ba abarshi abaya ba wurin zuba kyau domin wata lafiyayyar farar shadda yasha wadda taji dinki mai tsada,
Karfe hudu aka tashi daga walimar aka maida su nadiya gida, suna zuwa gida suka tarar da har anfara harhada kayan da za akai nadiya dasu domin abba yace ana yin sallar mangariba aje akaita,
Ai kuwa nadiya najin haka sai kuka nan mama tazo ta kama hannunta suka nufi falon abba,
Nan suka zauna tanata gursheken kuka,
"Nadiya kiyi hakuri kidaina kuka kinji domin kowacce mace hakace take faruwa da ita arayuwarta mutukar wannan ranar tazo, nidai abinda zance miki shine kiyi hakuri kibi mijinki sau da kafa kiyi masa biyayya,ki zama mace tagari mai rufa asirin mijinta, ina miki addu'ar Allah yabaki rayuwa mai dadi agidan mijinki yasa ta silarshi ki shiga aljanna, Allah yayi miki albarka"
"Amin amin, sannan kuma banda kazanta nadiya, banda rashin kunya, banda biye makota ana gulma, banda tona asirin miji, duk abinda yasaki kiyi abinda ya hanaki ki hanu, Allah yayi miki albarka yabaki yaya nagari" mama ta dora bayan abba yagama, nan mama ta kamata ta maidata inda ta daukota, da kuka da komai nadiya tasamu tayi wanka ta fito ta shirya lokacin har yan daukar amarya sunzo dan haka babu bata lokaci aka fita da ita aka saka a mota aka nufi gidan mijinta da ita lokacin ba afi karfe 7 nadare ba,
Suna zuwa kuma aka fara shirye shiryen tafiya dinner, angama shiryata kenan ango ya shigo cikin wani sky blue din yadi marar kauri, itama kuma dama shigar blue tayi nan suka bada kala,
Sai faman murmushi yake yimata amma ita duk idonta yayi ja saboda kukan da tasha gwanin ban tausayi, hannunta ya kama suka fita yana yimata magana ahankali,
"Menene yasaki kuka yanmata na? Ko kukan rabuwa dasu mamane? Kiyi hakuri kinji ai baku rabuba zaki rinka zuwar musu.."
Ita nadiya dai bata yi magana ba saboda tasan tana bude bakinta to fashewa da kuka zatayi dan haka taja bakinta tayi shiru,
Iya kawatuwa wurin dinner din ya kawatu yasha decoration blue colour,nan aka fara gudanar da abinda za ayi gadan gadan,
Daga nadiya har kabeer sunsha ruwan nairori wasu ma masu yimusu likin ita nadiya ba saninsu tayiba kawai dai tasan gayyar kabeer ce musamman ma wasu yanmata wadanda suka daddage sunata zubar musu da ruwan nairori,
Karfe 12 aka tashi daga dinner din aka kwashi mutane zuwa gida, nadiya ita da kawayenta suna motar musty shine yakaisu gida yana zuwa yace kawayen su fito zai mayar dasu gidansu nan suka yi masa caaaah wai bazasu tafiba sai anbasu kudin siyan baki, cheque din 20,000 ya rubuta musu yabasu sannan suka yarda suka hakura suka fito bayan sun gama tsokanar nadiya wacce ke lullube ta tukunkune agefen gado tana risgar kuka...
*_Ummi Shatu_*๐๐ป
[7/16, 7:29 AM] Ummi A'isha๐๐ป: *MIJINA SIRRINA...!*๐น
_(Labarin k'auna)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
ยฎ *HASKE WRITERS ASSO.*
*16*
~~~Sai da akayi kamar mintuna ishirin da tafiyarsu zarah maina tafara jiyo karar mota alamun yaya kabeer ya karaso gidan,
Sake gyara mayafinta tayi ta lulluba tana sauraren shigowarsa minti kadan kuwa sai gashi ya shigo hannuwansa dauke da ledoji manya guda biyu,
Ajiye ledodin yayi ya karasa wurinda take ya zauna akusa da ita yana murmushi,
"Yanmata nah.."
Shiru nadiya tayi takasa ko motsi ganin haka yasashi dagota zuwa jikinsa,
"Kidaina kukan haka kinji? Maza tashi kije kiyi alwala kizo muyi salla"
Batayi musuba ta mike taje ta shiga toilet din dake cikin dakin tayi alwala tafito tazo ta iskeshi yana jiranta nan yajasu salla sukayi sallar nafila raka'a biyu kamar yadda sunnah ta koyar,
Ledodin da ya shigo dasu yajawo ya bude ya fito da gasasshiyar kaza da snacks da drinks masu mutukar sanyi, "yan matana jeki kitchen ki dauko mana flate da wuka da cups.."
"Yaya kabeer ban san inda kitchen din yakeba.."
Jin abinda tace yasashi murmushi ya tashi dakansa yaje ya dauko yadawo ya zauna,
"Ga kaza zoki ci kinji yanmata na"
Duk da cewar nadiya najin yunwa sosai amma sai taji bazata iya cin kazar ba saboda kunyarshi dan haka ta jijjiga kai cikin dashewar murya tace,
"Nakoshi.."
Jan kazar yayi gabansa ya zage yafara cin abarsa batare da ya sake magana ba nan nadiya ta sake jin daci aranta saboda halin ko in kular da ya nuna mata,
Tana kallonsa yagama cin kazar ya dauki juice yasha ya mike,
"To tashi muje ki kwanta.."
Tashi tayi yabi bayanta zuwa kan lafiyayyen Italian bed din da aka kafa mata acikin dakin.
***
K'arfe 8 nasafe nadiya ta farka duk jikinta sai faman yimata ciwo yake saboda gajiyar biki wacce ta hadar mata da gajiyar da yaya kabeer ya tara mata adaren jiya,
Dubashi tayi amma baya cikin dakin nan ta yunkura dakyar ta sauka daga kan gadon ta shiga toilet tasamu tayi wanka ta fito in banda yunwa babu abinda takeji nan tayi salla ta shirya ta zauna tayi tagumi tana jiran dawowarsa amma shiru babu alamunsa,
Ganin har karfe goma da rabi tayi bai dawoba gashi tana jin rsananin yunwa yasata tashi taje ta dauko guntun snacks din da ya bari adaren jiya tafara ci tana ci tana hawaye saboda bakin cikin rashin ganin yaya kabeer,
Ita abinda yasata kuka ma shine yasan irin yanayin da yatafi ya barta aciki maimakon ya tsaya ya tarairayeta yabata kulawa ya taimaka mata ya nuna mata soyayya kamar yadda kowacce amarya take samu daga angonta washe garin ranar da aka kaita amma ita yayi tafiyarsa yabarta bata samu wannan kulawar ba,
Sannan ko acikin littattafan da take karantawa tana jin irin zumudin da angwaye keyi tareda nunawa amarensu soyayya amma ita sam bata samu haka ba, da kuka tagama cin snacks din ta tashi tafita tana tafiya dakyar, gidan tabi ta ga yanda aka tsarashi dan kyau kam gida yayi kyau sai dai fatan Allah yasa tasamu farin ciki mai dorewa acikinsa,
Ganin dagaske yaya kabeer baya cikin gidan yasata komawa falo ta zauna zuciyarta nata tunanin inda yatafi, "kodai abinci yatafi siyo mana?"
Nan ta zauna ita kadai har yan gidansu suka zo su waleeda da yan uwan mama, ananne ta dan sake taji dadi ana jimawa kuma sai ga yan gidansu yaya kabeer dauke da kulolin abinci,mintuna kadan sai ga kawayenta suma nan taji tasamu saukin damuwar dake addabar zuciyarta,
Gidanta cika yayi sosai da mutane nan kawayenta suka sata ta sake yin wanka tasha kwalliya domin yan unguwa sai shigowa ganin amarya suke yi,
Wuni guda cur babu kabeer babu alamunsa sannan ko waya bai yimata ba dadi daya taji shine kawayenta da kannenta har dare suka kai agidan sai daf da sallar isha sannan suka tafi, nan kuma tsoro ya tisata agaba sa'arta daya ma da akwai wuta,
Atsorace taci gaba da zama acikin gidan har karfe 9 nadare sai lokacin taji karar mota alamun dawowar yaya kabeer....
_Gaisuwa ga masoya masu bibiyar labarin hakika kune abin alfaharina...._
*_Ummi Shatu_*๐๐ป
[7/17, 8:23 AM] Ummi A'isha๐๐ป: *MIJINA SIRRINA...!*๐น
_(Labarin k'auna)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
ยฎ *HASKE WRITERS ASSO.* _(home of expert writers)_
*17*
_Wannan shafin nabaku shi kyauta k'awayen arziki, Cwt Kausar luv, Besty phertymah Xarah, Fido sodangi k'awata tareda dukkanin d'aukacin masoyanku masu sonku suna bibiyar rubutunku akoda yaushe...._
~~~Tashi tsaye tayi ta karasa bakin kofar falon domin taroshi amma koda taje sai tayi turus saboda ganin irin kallon da yayi mata,
"Yaya kabeer sannu da zuwa.." Tace dashi jikinta asanyaye,
"Yawwa..." Shine kawai abinda yace yabi ta gefenta yawuce batare da yasake koda kallonta ba,
Tamkar gunki haka nadiya ta zama sai ido da tabishi dashi,
Abubuwa biyune suke daure mata kai ahalin yanzu, nafarko fitar sassafen da yayi ko tashi bai bari tayiba sannan tunda ya fita bai dawo gidanba sai yanzu, sannan yanzun ma da yadawo babu fara'a babu magana mai dadi kenan da saninsa yatafi ya barta yayi biris da ita ko waya bai yimata yaji yanda ta wuni ba tunda yafi kowa sanin acikin yanayin da yatafi ya barta,
"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un..." Shine kawai abinda ta iya furtawa taje kan kujera ta zauna hawaye nata faman ambaliya akan kumatunta,
Tunani daya takeyi Allah yasa ba irin wannan mummunan zaman zasuyi ita da yaya kabeer ba, burinta daya Allah yasa bazai sauya mata daga yaya kabeer dinta mai sonta mai kaunarta mai damuwa da ita akoda yaushe ba,
Kukan zuci taci gaba dayi har na tsawon wani lokaci nan ta tashi ta bishi cikin daki ga mamakinta akwance ta sameshi yanata faman daddanna wayarsa wadda da alama chaten yakeyi,
A dan nesa dashi ta zauna tana kallonsa,
"Yaya kabeer lafiya kuwa yau ka tashi tun sassafe ka fita baka dawoba sai yanzu..?"
"Lafiya lau" ya amsa mata atakaice,
Dan shiru tayi nawani lokaci sannan tasake magana,
"Yaya kabeer ga abinci can nakawo maka?"
"Ke dan Allah ki kyaleni idan ina jin yunwar ai zan fada miki haba, ke wacce irin yarinyace kin tisani agaba sai surutu kike yimin? Kin tambayeni ina natafi dasafe kinzo kuma kina sake yimin nonsense question.."
Binsa da kallo kawai nadiya ta tsaya yi saboda yadda ya fututtuke yana balbala masifa kamar wacce ta watsa masa wuta, ko a mafarki akace mata yaya kabeer zaiyi haka bazata taba amincewa ba amma sai gashi azahiri tagani,
"Allah yabaka hakuri yaya kabeer.." Tafada idonta cikeda kwalla,
Tashi tayi tawuce taje ta dauki zani ta shiga bathroom tayi wanka ta fito tazo ta shirya tasaka kayan bacci ta kwanta,
Bata san iya adadin lokacin da ya kwashe yana chaten dinsa ba.
Yauma kamar jiya haka tasake tashi da ciwon jiki, jikinta duk yayi tsami amma koda ta duba gefenta sai taga wayam babu yaya kabeer babu alamunsa,
Zama tayi akan gadon tana tunani, to wannan wacce irin rayuwace? Dama haka auren yake? Miji sam bazai zauna agidansa tare da matarsa ba,
Nan da nan hawaye suka fara zubowa daga idanuwanta ita sai yanzu tagane dalilin mama da kullum idan tatashi yimata fada akan aure take cemata tayi hakuri domin gaba daya auren babu komai acikinsa face hakuri to dama wannan hakurin ne?
Share hawayenta tayi ta tashi ta dingisa zuwa cikin toilet tayi wanka tafito tayi salla ta shirya ta fita falo gidan babu komai na abinci sai ko danye sannan gas dinma ba aduro ba gashi babu kalanzir idan risho tace zata kunna, in banda yunwa babu abinda takeji,
Tana zaune afalo taga an kawo wuta nan taje ta jona electric cooker ta dora indomie ta dafa ta zo falo ta zauna taci tana gamawa ta tashi ta gyara gidan tasake yin wanka,
Tana daki tana kwalliya taji sallamar yan gidansu nan tafita cikeda murna domin su waleeda ne da sauran yan biki sukazo yimata sallama saboda ayau zasu tafi,
Ba karamin dadi tajiba nan ta hanasu waleeda tafiya tace sai yamma tayi hakane saboda tana son ta ragewa kanta zaman kadaicin da zata yi, daidai lokacin sallar azahar suma kannen kabeer suka zo gidan, nan suka zo mata da abinci wainar shinkafa da miyar agushi wai inji mama,ita dai nadiya tasan tayi sa'ar uwar miji amma abisa dukkan alamu batayi sa'ar mijiba,
Nan suka wuni dasu fati da su husna kannenta sai mangariba sannan suka tafi ai kuwa suna tafiya ta shiga damuwa domin gidan tsitttt yake sai ita kadai kwal kamar mayya.
Yauma kamar Jiya yaya kabeer bashi yadawo gidan ba sai da misalin karfe 10:30 lokacin nadiya har bacci ya dauketa akan kujera tana zaune ta kifa kanta akan hannun Kujerar da take kai....
*_Ummi Shatu_*๐๐ป
[7/17, 8:23 AM] Ummi A'isha๐๐ป: *MIJINA SIRRINA...!*๐น
_(Labarin k'auna)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
ยฎ *HASKE WRITERS ASSO.*
*18*
~~~Sai da yafi minti 20 da dawowa sannan nadiya tafarka nan tsoro ya sake kamata domin duk a zatonta bai dawoba amma kuma tana jiyo kamar motsi acikin dakinta,
Tashi tayi tanufi hanyar dakin tana magana "waye..?"
Shiru taji dan haka ta sadada ta shiga, tana shiga taga yaya kabeer ne yake tsane jikinsa yafito daga wanka,
"Yaya kabeer kaine kadawo ashe.. ?"
"Nine" yabata amsa, sanin yanda suka yi jiya yasata yin shiru bata sake magana ba, nan itama taje tayi wankan ta shirya ta kwanta,
Tunani ne ya mamaye zuciyarta saboda gaba daya yaya kabeer ya bata mamaki bata taba tsammanin cewar irin wannan rayuwar zasuyi dashiba, ita a zatonta irin rayuwar soyayyar da ake rubutawa acikin littafi zasuyi ashe abin ba haka bane sai yanzu tagane cewar rayuwar datake karantawa a littafi tasha banban da abinda ke faruwa azahiri amma ita bata fahimci hakanba sai yanzu,
Da wadannan tunanin bacci yayi awun gaba da ita, kasancewar tasamu tayi isasshen bacci yasata tashi da wuri domin ta riga kabeer tashi, Salla tayi ta zauna tana karatun alqur'ani har yaya kabeer din yatashi,
Gaisheshi tayi bayan ya idar da salla nan yace ta dora masa ruwan zafi tace babu gas kuma babu kalanzir,
Fita yayi can sai gashi da gas din da kayan tea yazo ya ajiye mata nan taje ta kunna wuta ta dafa masa ruwan zafin sannan ta dafa ruwan tea, wanka yayi ya fito yasha tea din akaro nafarko da yaci wani abu agidan,
Yana kammalawa ya kada rigarsa yafita bai sake waiwayar gidanba hatta kayan miya sai aike yayo mata,
Jalop din taliya da shinkafa tayi ta zuba a food flaks ta ajiye taje tayi wanka, tana fitowa taji wayarta na kara nan taga mamace murna sosai ta shiga yi ta dauka suka gaisa nan mama ta harhadata dasu waleeda dasu amir suka gaisa sai da suka gama gaisawa da kowa sannan mama takoma gefe,
"Nadiya ai babu matsalar komai ko? Naji tunda aka kaiki baki kiraniba sannan baki kira abbanki ba"
"Ehh mama wallahi wayar tawace babu kudi.."
Dan dam mama tayi sannan tace "to shikenan, ina kabeer din ko ya fita?"
"Ehh ya fita mama"
"To shikenan, ayita hakuri dai nadiya, zaman aure dan hakurine Allah yabaku zaman lafiya"
"Amin mama" nadiya tafada tana hawaye domin ita yanzu sai take jin cewar rayuwar gidansu tafi ta gidanta dadi domin da agidane da tuni yanzu tana can cikin kannenta yan uwanta suna wasa da dariya wani lokacin ma harda mama da abba acikin wasan amma nan gashi tazo rayuwarta atakure,
Sai da suka jima da mama suna hira sannan sukayi sallama ta ajiye wayar tazauna agefen gado tasha kukanta ta koshi ta share hawayenta tasoma shiryawa lokacin ba afi karfe 2 narana ba, tana gab da kammala shirinta taji karar shigowar text nan ta dauka ta duba tana budewa taga mamace ta turo mata katin waya har na dubu daya,
"Allah sarki mama.." Tafada idonta cikeda kwalla,
Falo ta koma bayan tayi salla tajona kayan kallo ta kunna tafara kallon wata tasha, tunowa da tayi cewar tana karantawa acikin littattafai tana jin irin yanda mata ke kulawa da mazajensu yasata daukar wayarta ta kira yaya kabeer,
Kamar bazai dauka ba sai kuma taji ya daga,
"Hello nadiya.."
Jin ya ambaci sunanta yasanya ta mamaki domin ada yanmatana yake kiranta amma yanzu tadawo nadiya,
"Yaya kabeer kana inane?"
"Ban gane ina inaba, sai kace wani yaronki zaki wani tambayeni ina ina? Menene? Me zanyi miki?"
Jikinta ne yafara rawa saboda jin masifar da yake yimata,
"Babu komai dama dai bugowa nayi inji lafiyarka.."
Bai sake bata amsaba ya katse wayar Kitttt,
Har lokacin da ya kashe wayar jikinta rawa yake domin fada yake yimata bil hakki da gaskiya,
Tagumi tayi tana rike da wayar tagagara koda motsi tana tunanin yanda yaya kabeer ya zama ahalin yanzu.
Wuni tayi acikin damuwa abincin ma bata iya ciba saboda ita kadaice masu zuwar matan ma yau babu wanda ya lekota dan haka tawuni sukuku har dare sai wurin karfe goma yaya kabeer ya dawo,
Sannu da zuwa tayi masa taje ta kinkimo abincin data dafa ta kawo masa,
"Yaya kabeer ga abincin.."
"Ke kinci?"
"A'a kai nake jira.."
"To danme zaki jirani? Agidanku mahaifiyarki tare kikaga sunaci da mahaifinki? Nace agidanku haka akeyi? Karki sake wani jirana akan abinci, idan kin dafa kayanki kici kawai basai kin jiraniba kin gane?"
Tsallake abincin yayi ya wucewarsa zuwa cikin daki yabarta sakare tana hawaye, jan abincin tayi ta dan tsakura a flate tafara ci tana hawaye har ta gama.
Washe gari da sassafe yace taje ta dafa masa ruwan wanka zai fita, nan ta shiga kitchen ta dauki ashana kenan ta hango wani murgujejen bera nan ta yarda ashanar tayi daki da gudu domin tana tsananin tsoron bera,
"Menene?"
"Yaya kabeer bera ne acikin kitchen din.."
"Akan beran zaki fasa dafa min ruwan wanka? Ke wacce irin sakarya ce marar sanin abinda ya kamata? Look kinga nifa bazan dauki wannan sakarcin na banza da wofiba..."
Bathroom ya shige ya doko kofar yanata bala'i, falo ta koma ta zauna, tana zaune ya fito cikin shirinsa nafita yasaka kai yafice bai ko kalleta ba.........
*_Ummi Shatu_*๐๐ป
[7/17, 8:23 AM] Ummi A'isha๐๐ป: *MIJINA SIRRINA...!*๐น
_(Labarin k'auna)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
ยฎ *HASKE WRITERS ASSO.*
*19*
~~~Bin bayanshi da kallo tayi sannan cikin damuwa tace,
"Adawo lafiya"
Bai amsata ba ya karasa ficewa,