Showing 45001 words to 48000 words out of 82977 words
Chapter 16 - MIJINA SIRRINA COMPLET BOOK BY UMMI AISHA.txt
hakan yabata mamaki,
"Autana kuka? Kuka kamar ba namiji ba, haba auta yi shiru akan auren ne? Indai aurene za ayi maka daina kuka"
"Hajiya amma kinaji ai yaya yace wai sai dai inkoma makaranta amma bazai yimin aure yanzu ba, ni babu karatun da zan koma wallahi har sai anyi min auren nan"
"To ya isa ai nace za ayi maka ba shikenan ba"
"Hajiya tunda yaya yace bazaiyi ba ai nasan bayi min zaiyi ba"
"Ai ni nace za ayi maka kama daina damuwa akan wannan kaji, share hawayenka"
Jin hajiya ta goyi da bayansa sai yaji hankalinsa ya kwanta zuciyarshi tayi sanyi nan ya saki jikinsa saboda yasan yanzu bashida matsala,nan takama hannunshi zuwa kan dining.
Washe gari da safe bayan sun gama yin breakfast yaseen ya kalleshi,
"Na turo maka link din da zaka cike foam din makarantar da zaka koma ka duba email dinka"
"Yaya baki nayiba amma nifa bazan koma karatu ba har sai nayi aure.."
Azuciye yaseen ya tashi zaiyi kansa Anty siyama tayi gaggawar shiga gabansa,
"Yaron nan naga alamun duka kake so inyi maka wallahi, ni kake fadawa cewar bazaka koma karatu ba har sai kayi aure? Kai har wani karatun kirki kayi? Masters din da kayi shine har kake ganin karanka yakai tseko? Mata nawane masu masters yanzu, banza shashasha"
"Nidai ko secondary gareni ya isheni inyi aure,kuma indai ba lalata yaran mutane akeso infara ba to abarni inyi aure"
"Karka fasa kaje kayi duk abinda zakayi" yaseen ya fada azuciye,
"Kai yaya amadi wai bakinka bazai yi shiru ba?" Anty Dija ta fada,
"Anty ai ni ba rashin kunya nake yi masa ba, ni kawai aure nake so, wallahi idan har banyi aure ba komai yana iya faruwa..."
"Auta tashi kaje" hajiya tace da dashi saboda jin yana kokarin yimusu tabargaza,
"Matsalar yan auta kenan wallahi basu da kunya ga shegiyar shagwaba" anty hameeda ta fada,
"Ai wanda kikaji kadanne nifa daga cemasa baya yawo sai cemin yayi wai to zai fara zuwa hotel da clubs yana hutawa" anty siyama tafada tana dariya,
"Zanyi maganinsa ai, wallahi karatu zai koma nanda wani month din.."
"Yaya abinda nakeso dakai tunda yaron nan ya nuna auren yake so to muyi masa saboda mu kare masa mutunci sannan mu karewa kanmu, domin indai bamu yimasa aure ba kuma yana so to fa shaidan bazai barshi ba zai ta ingizashi daga karshe azo ashiga halin da ba aso,dan haka kayi hakuri muyi masa auren tunda yanuna yanada bukatarsa kuma karatu yace zai koma amma sai anyi masa aure" hajiya tace dasu tana rikeda kumatunta,
"To hajiya shikenan za ayi kamar yadda kikace amma kifa tuna shekarun yaron nan kwata kwata 28 ne kacal fa ko 30 baiyi ba" inji yaseen,
"Ehh babu komai mudai yimasa shikenan mun fita hakkinsa" hajiya tabashi amsa,
"To shikenan hajiya"
Akan haka suka tsaya na za ayiwa amadi aure amma har lokacin yaseen bai huceba haushin amadi yakeji saboda duk barazanar da ya dade yana yimasa akan cewar babu shi babu kula yanmata amma shine sai da ya kula su.
Amadi kuwa duk da bai san abinda su hajiya suka tattauna ba bayan tafiyarsa hakan bai saka yaji son auren nadiya ya ragu acikin ranshi ba shi yanzu ne ma yake jin wani shaukin sonta acikin zuciyarshi,wayarshi ya dauka ya kirata, fitowarta kenan daga wanka kamar ba zata daga ba ta daure ta dauka,
"Baby nah.., ya jikin?"
"Da sauki"
Shiru yayi yana sauraren muryarta har yaji tayi shiru,
"Yanzu me kikeyi? Uhmmm?"
Sai da yafi minti miyar da tambayarta sannan tabashi amsa,
"Abu nake yi?"
"Menene shi? Fada min sai inzo in tayaki"
Shiru tayi masa har sai da yasake maimaitawa, "daga wanka na fito zan shirya, sai anjima"
"Dan Allah tsaya kiji, karki kashe dan Allah, kinga da ina kusa nine zanyi miki wankan,nine zan shiryak..."
K'ittt ta kashe wayar acikin zuciyarta tana mamakinsa dama haka yake shima, afuska kamar salihi ashe ashe, shika A ne,
Murmushi yayi saboda shi kansa bai san lokacin da ya soma sakin layiba.
Kwana uku da tsayar da maganar yiwa amadi aure yaseen yasake tarasu yafara tambayar amadi wacece yarinyar da yake so,
"Sunanta nadiya"
"A ina gidansu yake?"
"A rano suke"
Dukkaninsu mamaki ne ya kamasu saboda sun zaci zaice a abuja sai sukaji sabanin haka,
"Good, wacece ita sannan waye mahaifinta?"
"Mahaifinta babban dan kasuwa ne sannan yana aiki a state government, ita kuma dalibata ce a KUT amma bazawara ce ta tab'a aure kuma tanada yara biyu"
Atsorace yaseen ya kalleshi yayinda yayunshi Mata suka hau salati da sallallami,
"Auta bazawara?" Hajiya tace dashi cikin mamaki,
"Anty amadi bazawara fa kace, kanada hankali kuwa?",anty Dija ta fada cikin zaro ido,
"Da hankalina anty, ai ba haramun bane, ni wallahi ita nakeso kuma ita zan aura"
"To kuwa bazaka aureta ba koda kuwa zaka mutu, kaji yaro da shashanci, sai kace marar mafadi? Karasa wacce zaka so sai bazawara?" Yaseen yafada cikeda mamaki,
"Gaskiya auta nima anan ban goyi bayanka ba, kaje ka sauya shawara saboda nima bazan goyi bayan da ka auri bazawara ba, ai sai ta rinka yi maka wayo.." Hajiya ta dora nata jawabin,
"Hajiya..."
"Kai tashi ka fita daga nan, tashi ka fice ko inzo inyi ball dakai.." Yaseen yafada azuciye, tashi amadi yayi ya fita hankalinsa yakai kololuwar tashi, ransa kuwa idan yayi dubu to ya b'aci.....
*_Ummi Shatu_*👌🏻
[19/08, 7:22 p.m.] Ummy Aysha: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
_(Labarin k'auna)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
® *HASKE WRITERS ASSO.*
*49*
aishaummi.blogspot.com
*K*o gabansa dak'yar yake gani saboda tsananin damuwa da b'acin rai, dakinsa ya shiga ya zauna zuciyarsa tana faman yimasa zugi da zafi, gaba daya yama rasa abinda zaiyi kuka ko me? Tagumi yayi jikinsa sai tsuma yake,
Gaba daya babu wanda ya goyi bayan amadi ya auri bazawara har hajiya wannan karon taki bin bayansa, anty siyama kuwa cewa tayi ai ga kanwar mijinta nan zee dake mutuwar sonshi a aura masa ita kawai anan ne kuma hajiya bata bada goyon baya ba tace adai kyaleshi yasake nemowa da kanshi.
Tunda amadi ya shiga daki bai fitoba su hajiya sunyi tsammanin ko fushin ne har lokacin bai huce ba ashe ba haka bane zazzabi ne mai zafi ya rufeshi dan haka babu shiri ya kwanta ya lulluba da bargo, yana nan kwance har la'asar tayi ganin bai fitoba yasa hajiya lekawa dakin nasa nan ta hangoshi kwance cikin bargo,
Hankali atashe hajiya taje gaban gadon tana kiransa, "auta..!!! Auta na, meya sameka?"
Jin jikinsa tayi zafi zau lokacin data yaye bargon,
"Baka da lafiya shine baka fada min ba auta? Meyasa?"
Kamar hajiya zatayi kuka ta fita ta kira yayunsa nan ta taho masa da abinci da magani, kamar karamin yaro haka ta sakashi agaba ta bashi ya dan ci yasha magani, wani irin ciwo kansa yake yi masa kamar zai bar gangar jikinsa.
Kasancewar autane shalele kowa sai da ya nuna damuwarsa akan rashin lafiyar amadi nan aka manta da batun maganar auren da yace zaiyi amma shi abin yana nan acikin ransa, har dare yayi dukkaninsu suna dakinsa ana hira shikam yana kwance kansa akan cinyar hajiya tana shafar kansa kamar wani jariri,
Lokacin da yaga kowa yafice sai iya hajiya yasamu damar yimata magana,
"Yanzu hajiya kun k'wammace inje inyi zina akan ku aura min wacce nake so? Hajiya idan fa bakuyi min auren nan ba tunda ina son yarinyar nan kuma ace itama tana sona to fa shaidan zai iya ribatarmu mu aikata abinda bashi kenan ba,saboda zamu rinka ganin ai tunda baza abarmu mu mallaki junanmu ba gara mu aikata komai, amma idan har kuka amince na aureta hajiya kun taimakawa rayuwata sannan kun tamaka mata itama, kuma ni banga abin gudu a auren bazawara ba tunda annabinmu ma da ita yafara alhalin shima bai taba yin aure ba, dan Allah hajiya kiyi min wannan alfarmar a matsayinki na mahaifiya ta, ku barni na auri nadiya.."
Shiru hajiya tayi na wani dan lokaci sannan ta shafi sumar kansa,
"To autana kabari zan duba Nagani kasan nafi kowa sonka shiyasa bazan taba bari wani abu ya cutar dakai ba, zanyi maka istihara nagani idan har aurenka da ita alkhairi ne Allah ya tabbatar idan kuma ba alkhairi bane Allah ya sauya maka da wacce tafita alkhairi"
"Yawwa hajiyata, insha Allah ma alkhairi ne.."
"Allah yasa haka"
Sallama hajiya tayi masa ta tashi tafita ta ja masa kofar, shiru amadi yayi yana tunanin nadiya acikin ransa, shi ko zai koma karatu to yafi son sai andaura aurensa da ita saboda gani yake muddin ya tafi bai aureta ba to kafin yadawo wani ya aure masa ita.
***
Kallon asabe kabeer yayi zuciyarsa cike da jin haushinta nan ya fincike hannunta daga jikin kwalar rigarsa amma bata hakura ba sai da ta sake cakumar wuyar rigar tasa,
"Sakeni.., sakeni nace ko jikinki ya fada miki yanzun nan.." Yafada cikin karaji, maimakon ta sakeshi sai jan rigar tasa tayi ta ketata nan ya rufeta da duka itama tana ramawa amma da yake karfinsa da nata ba d'aya bane yasa yayi mata lilisss, zaginsa ta hau yi tana cewa dole dai sai ya zauna da ita ko yana so ko baya so,
Cikeda bakin ciki yaje ya sauya kayan jikinsa yabar gidan, kusan koda yaushe hakace take faruwa, kullum acikin fada suke ta zageshi tass shikuma ya nada mata na jaki, shi kansa idan ya zauna sai ya rasa gane wacce irin musiba ce ta sauka akansa, nadiya ce ta fado masa nan kuma yaji hankalinsa ya sake karkata agareta take zuciyarsa tafara aiyana masa wani abu...
***
A b'angaren nadiya kuwa tun tana fushi akan fadan da mama tayi mata har ta hakura ta ware amma bata taba sanin cewa Abba yayi magana da amadi akanta ba,
Yau da safe misalin karfe 9 amira tazo ta kirata tace taje Abba na kiranta, fita tayi daga cikin bargonta ta dauki hijab dinta ta nufi falon Abba,
Yana zaune shida mama ya kammala karyawa,
Zama tayi ta gaidashi, cikin fara'a ya amsa sannan ya dubeta duba irin na maganar da za ayi mai muhimmanci ce,
"Nadiya wannan yaron Ahmad tun yaushe yake zuwa wurinki?"
Gabanta ne ya fadi ras rass domin jikinta yafara bata cewar Abba maganar aure zaiyi mata,
"Abba bamu dade tareda shi ba kuma ni wallahi bani nafada masa gidanmu ba haka kawai naganshi yazo.."
"To nadiya in banda abinki ai mai sonka shi yake zuwa Inda kake,sannan agaskiya ni na yaba da nutsuwar yaron wannan dalilinne ma yasa nabashi dama domin ya turo magabatansa ayi maganar aurenku tunda kedai yanzu ba karamar yarinya bace.."
Hawaye ne suka fara bin kumatun nadiya wanda takasa magana,
"Kiyi hakuri nadiya nasan ke mai biyayya ce sannan mai hakuri ce akan komai, to yanzun ma wannan biyayyar taki da nasanki da ita zaki yimin ki auri wannan yaron domin nagari ne, nasan abaya kinyi mana biyayya kin auri kabeeru wanda bakiji dadin zama dashi ba to yanzu kuma insha Allah zakiji dadi ko dan biyayyar da kike yimana.."
"To Abba" shine kawai abinda nadiya ta iya cewa sai ko hawaye dake faman bulbula daga idanuwanta,
"Allah yayi miki albarka nadiya, Allah yasa yaranki kema suyi miki irin biyayyar da kike yimana,kiyita hakuri kinji"
"To Abba"
"Allah yayi albarka,shikenan tashi kije.."
Tashi tayi tafita tana faman hawaye, tana zuwa daki ta zauna ta shiga kuka, kuka take sosai kamar wacce aka rafkawa mutuwa, ita bakin cikinta ma amadi fa ko ta bakinta baiji ba amma shine zai tafi wurin Abba kai tsaye kenan auren dole yakeso ayi mata ko me??
Ta dade tana rusar kuka kafin ta dauki wayarta ta tura masa text massage,
_Yaushe mukayi haka dakai, yaushe nace zan aureka da har zakaje wurin Abba kace zaka turo Manyanka,ka tab'a ganin inda aka yiwa bazawara auren dole? Ni nafada maka bana sonka ka rabu dani ko dole ne auren? Nidai kasani muddin na aureka to auren dole akayi min domin ban taba jin sonka acikin raina ba..._
Ganin massage dinta yasa amadi shiga cikin mamaki domin bata taba tura masa da text massage ba, yana karantawa yaji hankalinsa yatashi nan yayita kiran wayarta amma taki dauka daga karshe ma sai ta kashe wayar gaba daya, duk da cewa bashi da lafiya yana zazzabi haka ya figi mota ya tafi rano saboda fushin nadiya agareshi babban abune ko kadan baya son fushinta,
Karfe 11 nasafe ya isa kofar gidansu sai dai yau baizo da niyyar shiga cikiba domin kananan kayane ma ajikinsa ga zazzabi dake damunsa,
Wayarta ya kira taki dauka domin ta bude wayar lokacin, text ya tura mata cewar yana kofar gida tayi hakuri ta fito, dama kamar wadda take jira nan ta dauki hijabi ta fita afusace domin sai ta tsattsageshi sannan zataji dadi, kofar motar ta bude ta shiga yana zaune ya dora kansa ajikin sitiyarin motar saboda wahalar da yakeji,kansa ya daga ya kalleta yasake dorashi akan sitiyarin yana kallonta,
"Baby meyake faruwa ne, laifin me kuma nayi?"
"Au ba kasanma abinda kayiba kenan? Yanzu kayi min adalci da har zakaje wurin Abba ka kai kanka kace zaka turo ayi maganar aurenmu bayan bani nabaka wannan damar ba? Ka taba jin nace ina sonka bare har nace zan aureka? Ni ba sonka nakeba,wancan auren ma da nayi shima ba son mijin nakeba ko ahaka zan kare a auren mazajen da bana so basa sona? Ni shikenan bazanji dadin aure ba kowanne aure da akwai matsalar da zan fuskanta?"
Kallonta kawai yake yi da jajayen idanuwansa wadanda suka yi ja saboda wahalar zazzabi har lokacin kansa yana bisa sitayarin motar akwance, sai da yaji ta tsagaita daga masifar da take balbala masa sannan yayi magana cikin muryarsa mai masifar sanyi,
"Allah yabaki hakuri baby, wallahi bani nakai kaina wurin Abba ba, shine ya kirani yace inturo manyana amma kiyi hakuri, sannan idan kikace wai bana sonki bakiyi min adalci ba, da ace yanzu kin san halin da nake ciki saboda ke wallahi da sai kin tausaya min"
"Wanne so kake min? So ko sha'awa? Babu wani sona da kake kawai kai dai kana sone kasamu wani abu daban atare dani daga nan kuma wulakanci ya biyo baya.."
Murmushi yayi ya kalleta, "sha'awa fa kikace? Haba baby idan sha'awace ke damuna ba so ba ai da sai in nemi budurwa in magance sha'awata shikenan.."
"To koma dai menene bari kaji koda ace zan aureka sai munyi yarjejeniya dakai sannan sai kayi min alk'awai guda daya.."
Har lokacin fuskarsa dauke take da murmushi, jijjiga mata kai yayi, "yarjejeniyar me zamuyi sannan wanne alkawari kike so inyi miki? Zanyi miki shi ko na menene mutukar atare dani abun yake".
*_Ummi Shatu_*👌🏻
*MIJINA SIRRINA...!*🌹
_(Labarin k'auna)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_
_Fatan alkhairi ga daukacin masoya masu bibiyar labarin.._
*50*
aishaummi.blogspot.com
*S*ai da ta hade rai sannan tace,
"Koda na amince munyi aure to ba zaka kusanceni ta karfi ba har sai da yardata da amincewata.."
Duk da cewar yaji maganar tata wata iri amma sai yaji tazo masa da sauki saboda bai zaci wannan maganar zata fada ba,
Shiru yayi yana nazari amma kuma zuciyarshi tana ta tausarshi ta hanyar cemishi,
"Tunda kana sonta kawai ka amince da kanta zata nemeka badai mace bace ai mata akwai rauni.."
Ganin yaki yayi mata magana yanata murmushi shi kadai yasata yin magana,
"Kai nake jira fa kayi magana"
"Ni ai na amince karki samu damuwa..."
Galala tayi tana kallonsa domin koda wasa bata dauka zai amince acikin sauki ba duba da cewar shi saurayine ba taba yin auren yayiba,
"Shikenan tunda ka amince amma kasani alkawari fa ka dauka.."
"Nasani.." Yabata amsa,
"Shikenan yayi kyau" tafada tana kokarin bude kofar motar domin fita,
"Baby zan samu maganin zazzabi agidanku? Wallahi zazzabi ke damuna yanzu ma ba kiji jikina ba"
"Za a iya samu bari naje na duba.."
Fita tayi yabita da kallo "baby riigima" yafada acikin zuciyarsa.
Paracetamol ta dauko masa sachet daya sannan taje falon abba ta dauko bottle watar guda daya marar sanyi tafito,
Yana nan kamar yadda ta tafi tabarshi haka ta dawo ta sameshi,mika mishi tayi yatashi ya karba ya balli maganin guda biyu yasha yana yamutsa fuska,
Sake kwanciya yayi ajikin sitiyarin, dukkaninsu sunyi shiru babu wanda yake cewa komai da haka har bacci ya dan fara daukarshi sama sama,
Juyawa tayi ta kalleshi da niyyar tayi masa sallama ta koma gida amma kamar da wasa sai taga wai yayi bacci, zuba masa ido tayi tana kallonsa, hakika duk inda ake neman cikakken namiji to amadi yakai matsalar kawai ita har yanzu bata sake dashi bane gudun kar akuma sake maimaita abinda yafaru abaya.
Sai da yashaki baccinsa ya more sannan ya bude idonsa bai zaci zai ganta ba amma sai yaganta zaune,
"Baby yi hakuri wallahi ban ma san time din da baccin ya daukeni ba"
Shiru tayi bata tanka ba dama kuma yasan ba tankawar zatayi ba,
"Bari naje na tafi.."
"Allah ya kiyaye hanya" tafada tareda bude kofar motar ta fita, ko akwalar rigarsa abin da tayi, tashin motarsa yayi yakara mai ya nufi gida.
Kwana biyu da faruwar haka hajiya tace masa ta amince ya auri bazawara mutukar hakan zai samar masa da kwanciyar hankali duk da bata so tayi nesa dashi,
Tara yayunshi hajiya tayi tace musu subar amadi ya auri nadiya kamar yadda yake so kuma itama yanzu taji auren ya kwanta mata arai, babu wanda yayi magana acikinsu saboda dama sun san hakace zata faru tunda dan gaban goshi ne.
Murnar da amadi yayi kamar zaiyi me, nan yaseen yace duk da haka dai zai koma karatu, amadi bai damuba saboda yasan idan har aka aura masa nadiya angama mai wahalar ko bata tare ba.
Lokacin da yayi mata waya yace manyanshi zasu zo bata yi wani murna ba shi kadaine kawai ke murna, nan ta kashe wayar ta ajiye gefe tana dan karamin tsaki,
"Anty nadiya nifa ina jiye miki wani abu guda daya, karfa yanzu yaya Ahmad kawai lallabaki yake sai kunyi aure yazo ya rama duk wadannan abubuwan da kike yimasa ko kuma yabari sai kin kamu da sonshi sannan ya rama koma har yayi doubling.." Amira dake gefe tana yin sak'a da kwarashi ta fada,
"Amira kenan idan har yayi min haka ko fiye da haka zan barshi ne da Allah kawai kamar yadda nabar yaya kabeer da Allah, nasan haushina kukeji kuna ganin kamar bana kyautawa Ahmad saboda abubuwan da nake yi masa, Amira shi so yanada wahalar gaske sannan duk zuciyar da ta samu kanta