Showing 42001 words to 45000 words out of 82977 words
Chapter 15 - MIJINA SIRRINA COMPLET BOOK BY UMMI AISHA.txt
sai batayi maganaba illa kawai hannu data mika ta amshi wayar,yanda muryarta take asanyaye haka shima tashi muryar take sanyi kalau,
"Ya jikin naki?"
"Da sauki"
"To gani awaje nazo dubiya..."
Mamakine ya isheta saboda jin cewar wai yazo da wannan sanyin safiyar, amma koda ta tuno naci da juriya irin nashi sai taga wannan ba komai bane awurinshi,
"To ai ni bazan iya fitowa ba yanzu ma kaga akwance nake.."
Juyawa amira tayi ta fita saboda kiran da taji mama tana kwala mata daga cikin kitchen,
"To ya za ayi kenan?" Taji ya tambayeta, shiru tayi saboda bata san abinda zatace masa ba,
"Kodai injuya inkoma bakya son ganina?"
Nan dinma shirun tayi bata amsaba,
"Shikenan bari naje natafi.."
Dif taji ya kashe wayar tana kokarin juyawa ta gyara kwanciyarta kuma taji maganarsa atsakar gida suna gaisawa da mama,
"Ohhh wannan kowanne irin mutum ne shi oho, ban taba ganin mutum mai hakurin Ahmad ba.." Tafada acikin zuciyarta amma kuma tarasa dalilin da yasa har yanzu bataji tana sonshi ba domin ko maganar data fadawa yaya kabeer cewar zata auri amadin kawai tafada ne dan ta tura masa haushi amma bawai dan tana son amadin ba,
Tare da Amira suka shiga cikin falon inda nadiya ke kwance, hijab din dake jikinta ta sake gyarawa saboda rigar bacci ne ajikinta,
Wajen kanta yaje ya tsaya ya dafa hannun kujerar da kanta ke kai yana kallonta, tsabar naci irin na zuciyarshi sai yaji tayi masa yimasa kyau a wannan yanayin duk da fuskarta akode take babu kwalliya, idanuwanta arufe, dan sunkuyawa yayi,
"Baby...."
"Uhmm" ta amsa dakyar saboda bata son sunan nan da yake fada mata,
"Sannu..., jikinne?"
Kai ta girgiza masa,
"Kinji sauki?"
"Uhmmm"
"To Allah ya kara baki lafiya.."
"Amin.."
Haka yaci gaba da tsaiwa akanta ita kuma tana kwance ko bude idonta bata yiba bare taganshi sai dai kamshin daddadan turarenshi gaba daya ya cika mata hanci,
Sai da Amira ta shigo dauke da tiren abinci sannan tayi masa magana,
"Yaya Ahmad ka zauna mana.."
Wuri yasamu yaje ya zauna, yaci gaba da kallon gimbiyar wacce ke kwance jikinta lullube da hijabinta.....
_*Ummi Shatu*_👌🏻
*MIJINA SIRRINA...!*🌹
_(Labarin k'auna)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_
*Gaisuwa mai tarin yawa ga Dije uwar hawwa, Salma m,Maman humy,pheey tareda yan matan Amadi Zeebells & Fatima Dasuki,nagode Allah yabar zumunci...!*
*46*
aishaummi.blogspot.com
*Z*ama yayi akan kujera ya zubawa gimbiyar ido wacce ke kwance ta lulluba da hijabinta,
"Yaya Ahmad ga breakfast.." Amira tace dashi tana ajiye masa tiren agabanshi,
"Amira ita nadiya din taci abinci ne?" Ya tambayi amira muryarsa asanyaye,
"A'a bata ciba amma ai zata ci"
"To ai ita yakamata afara bawa baniba"
"Tom bari naje nakawo mata nata"
Fita amira tayi shikuma yaci gaba da kallon nadiya wadda ke kwance tana jin duk abinda ke faruwa,
Babu jimawa amira ta dawo rikeda cup mai dauke da ruwan zafi sai filet wanda aka doro soyayyen kwai akai,
"Anty nadiya gashi tashi kici.."
Ko motsi batayi ba bare asaka ran zata tashi,
"Anty nadiya..." Amira tasake kiran sunanta, tashi amadi yayi yaje ya karbi cup din da filet din dake hannun amira,
"Kawo amira jeki kawai.."
Bashi amira tayi ta juya ta fita, magana yafara yimata ahankali cikin sanyin muryarshi,
"Baby.."
"Uhm.."
"Tashi kisha tea din kinji.."
Shiru tayi masa sannan batayi ko motsi ba,
"Yi hakuri baby kitashi, ko bazaki iya tashiba?"
Sake yin shiru tayi har lokacin idanuwanta suna rufe,
"Tashi kinji.."
"Zan tashi"
"To tashi.."
Hijabinta ta gyara sannan ta tashi ta zauna sai lokacin ta kalleshi gaba daya haushinsa takeji saboda ya takurawa rayuwarta karfi da yaji yana neman ya rusa mata plan dinta da ta shirya,
Akusa da ita ya zauna ya mika mata tea din nan ta karba fuska adaure kamar dole,
Shikam murmushi yakeyi ganin ta tashi sai wani cin magani take, idan da sabo yasaba ganin wannan cin maganin nata sai dai kuma shi yadau alwashi bazai taba barinta ba har sai ya mallaketa ya koyar da ita sonshi sannan sai ta kamu da tsananin sonshi fiyeda yanda yake sonta duk da zuciyarshi tana fada masa cewar tana sonshi kawai damuwarta ce ta rinjayi son shiyasa takasa bayyanar mishi,
Yanda take shan tea din kamar magani takesha,
"Baby bazaki ci kwan ba?"
"Zanci.."
"To ci"
Karba tayi tafara gutsira ahankali tana ci har ya isheta,
Mamace ta shigo, ganin amadi baici breakfast dinba yasata fara fadin,
"Yaya kuma zakazo ka zauna baka ci abincin ba, dan Allah rabu da ita kaje kaci abincinka, ita ai ba karamar yarinya bace da sai an lallabata.."
Murmushi yayi saida mama tawuce sannan yayi magana ahankali wanda iya nadiyan ne kadai taji abinda yace,
"Mama bata san ni lallabaki nake yiba fiyeda yadda ake lallaba karamin yaro ko jariri..."
Sake daure fuska tayi ta kawar da kanta, tashi yayi daga kusa da ita yaje ya zauna akujerar dake fuskantarta yafara shan tea din data rage yana cin guntun wainar kwan da ta bari,
Iya Wanda ta rage yaci ya ajiye cup din da filet din nan amira ta shigo tace masa mama tace yaje su gaisa da Abba saboda abban fita zaiyi,
Tashi yayi yabi bayan amira zuwa falon Abba, suna zaune shida mama amadi ya shiga suka gaisa har zai tashi Abba ya dakatar dashi,
"Ahmad dama ina son zanyi magana dakai.."
"To Abba"
"Ahmad kasan da cewar nadiya dai ba budurwa bace dan haka babu bukatar ayi dogon nema akanta saboda yanzu tawuce wannan lokacin, kasancewar ta taba yin aure harda arzikin yara guda biyu sannan dan uwanta ta aura wanda dani da mahaifinsa uwarmu daya ubanmu daya"
"Hakane Abba"
"To idan har dagaske ka shirya auren nadiya ina son ka turo magabatanka duk da cewar ban san yanda kukayi da itaba, amma naji komai awurin mahaifiyarta dan haka yanzu abinda nake so dakai shine ka turo magabatanka, amma kaji ka amince zaka aureta ahaka?"
"Ehh Abba zan aureta ahaka kuma insha Allah magabata na zasuzo, nagode madallah, Allah yakara girma"
"Amin, Allah yasanya albarka acikin neman, zaka iya tafiya"
Tashi amadi yayi yafita zuciyarsa tayi masa wani irin sanyi duk da yasan akwai matsalar da zai fuskanta daga ita yar rigimar tasa amma yasan insha Allah wannan mai saukine domin zai jure komai indai daga gareta ne.
Tana zaune a inda yabarta bata san abinda yake faruwa ba saboda koda wasa bata zaci mama zata kaiwa Abba maganarba, shiga falon amadi yayi ya dan saci kallonta nan yaga ta hade rai kamar zatayi me,
"Baby banfa kawo miki kayan dubiya ba"
"Dama ai ban nemaba"
Murmushi yayi yaje kusa da ita ya sunkuya saitin fuskarta,
"Allah ya huci zuciyarci da wasa nake nakawo miki me zaki sha aciki? Lemo ko ayaba?"
Kawar da kanta tayi tayi banza dashi,
"Baby bazaki amsa minba? To bari naje na shigo miki dasu saboda yanzu zan koma gida akwai abu muhimmi da naci karo dashi da sanyin safiyar nan.."
Nan dinma shirun tayi dan haka yafita yaje wurin motarsa ya bude yafara fito da siyayyar da ya iyo mata, kayan marmari babu abinda babu, lemon kwali da na gwangwani da malt, ga madara, da kanshi ya shigar da kayan cikin gidan nan amira ta tayashi kasancewar amir baya nan yatafi sumaila hutu gidan umman sumaila,
Atare mama da Abba suka fito,lekawa falon Abba yayi yai mata sannu nan ta gaisheshi ya fita yatafi wurin aiki bayan yayiwa amadi godiyar wahalar da ya iyo ta siyayya,
"Baby bari naje nakoma sai munyi waya ko? Allah yabaki lafiya kinji"
"Amin" tafada fuskarta aturbune, duk sai amira dake tsaye taji babu dadi saboda ita bataga laifin amadi ba,saurayi mai class irinshi kyakkyawa mai ilmi komai nashi na classic guys amma sai faman wahalar dashi nadiya take,
"To baby bye"
Fita yayi yana yiwa amira sallama, "amira sai anjima Allah yakara sauki"
"Amin yaya Ahmad Allah ya kiyaye hanya angode madalla"
Kallon nadiya Amira tayi, "Anty nadiya gaskiya wallahi abinda kike yiwa yaya Ahmad yayi yawa, kiri kiri fa kike nuna bakya sonsa gashi yayita yimiki magana amma kiyi banza dashi sai kin gadama zaki amsa masa..."
"Ke ina wasa dake? Ni sa'arki ce? Karki yimin rashin kunya wallahi yanzun nan jikinki zai gaya miki.."
"Idan kuwa kika kuskura kika dakar min'ya nima sai na yimiki dan banzan duka" mama tafada bayan ta shigo cikin Falon saboda taji duk abubuwan da suka fada,
Fada mama taci gaba dayi,
"Haba abubuwan naki sun wuce hankali, narasa wanne irin kafiya da shegen taurin kai Allah yabaki, yarinya sai kace mutanen farko ataurin kai, shi wannan yaron meye nashi aciki da zaki rinka wulakantashi, sai kace shine yaje yace kabeer din ya sakeki? Akanki aka fara rabuwar aure da zakibi ki tsangwami yaro kamar shine yayi miki silar mutuwar auren, to bari kiji abinda amira tafada miki gaskiya tafada sannan wallahi mutukar baki so mai sonki ba to kuwa zakiso makiyinki, haba kaji min yarinya mai masifar taurin kai kamar baki san kaddara ba?"
Hawayene sharrrr suka fara bin kumatun nadiya ita bacin ranta wato harsu mama summa manta da bakar azabar da tasha da damuwar da ta tsinci kanta ashekarun baya ata sanadiyyar da namiji, har ciwon hawan jini sai da yakamata da tazo da karar kwana ma tana iya mutuwa amma shine yanzu tun ba aje ko inaba har sun manta suna ganin laifinta saboda kawai wannan yar karamar yaudarar da amadi ya shiryo mata,
"Yanzu mama laifina kuka gani kenan? Kun manta halin da nashiga abaya, kun manta damuwar da yaya kabeer ya jefani?"
"To ai nadiya mutane basu taru sun zama dayaba, kowa da halinsa, kimanta da kabeer ki fuskanci Ahmad mai sonki nagaskiya.."
"Wallahi nidai mama bana sonshi, ni bana sonshi, bana sonshi, haka yaya kabeer ma sai da nace bana sonshi amma aka matsanta min har sai da na aureshi daga karshe yayi min butulci,ni bazan yi aure yanzu ba.."
Tafada cikin kuka tareda kifa kanta ahannun kujera tana kuka....
*_Ummi Shatu_*👌🏻
[19/08, 7:22 p.m.] Ummy Aysha: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
_(Labarin k'auna)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_
_Page 47-49 nayi shine domin jin dadinku Aunty's din anty amadi, ANTY MAIJIDDA, ANTY BARAKA, ANTY SIS & MOMCYN ANAS.._
*47*
aishaummi.blogspot.com
*T*sayawa kawai mama tayi tana kallonta amma acan k'asan zuciyarta tausayinta take ji saboda tasan tsoron sake shiga irin halin data shiga abaya take yi sai dai amma kuma tunda ta samu mai sonta da gaskiya ai bazasu zuba mata ido har ya sub'uce mata ba,
Juyawa mama tayi ta fita bata sake magana ba tabar nadiya tanata faman shasshekar kuka, Amira ce taje kusa da ita ta zauna tafara bata baki,
"Anty nadiya dan Allah kiyi shiru, Allah ya baki hakuri amma wallahi yaya Ahmad yana sonki ni tausayinshi ma nake ji saboda gaba d'aya bashida buri sai na kyautata miki, baya son b'acin ranki nasan ma wallahi ko auren ma kukayi sai yanda kikayi dashi tunda yana son farin cikinki.."
D'agowa nadiya tayi fuskarta shabe shabe da hawaye,
"Haba Amira ai bai kamata yanzu ace dole sai nayi aureba tunda nayi auren nan naji abinda ke cikinsa, yanzu dan Allah ko a mafarki kin tab'a zaton cewar yaya kabeer zaiyi min haka? To shi da yake dan uwanama jinina ga abinda yayi min inaga wanda yake bare banida hadin komai dashi? Yaya kabeer fa jiya yazo gidan nan yace min wai dole sai nabashi yaranshi har da su zancen zai kaink kotu akai.."
Baki bude dan tsananin mamaki Amira ta kalleta, "yaya kabeer din? Dan rashin mutunci ko dan me? Mutumin da bai sake bi takan yaranba amma shike ikirarin abashi su?"
"Wallahi Amira dagaske nake ba karya ba, tsabar bacin ranshine da fargaba ya haifar min da rashin lafiyar da nake ciki yanzu"
"Allah ya rufa asiri amma ai babu alkalin da zai bashi su fadeel yanzu.."
Mama dake waje tana jin duk abinda suke fada amma batace komai ba sai dai ta cika da mamakin kokari irin na kabeer.
Lokacin da Amadi ya koma gida yayi niyyar sanar da hajiya maganar aurenshi da nadiya amma sai yaji ta tareshi da maganar cewar gobe yayyunshi zasu zo saboda dama sukan ware lokaci na musamman suzo gidan gaba dayansu su dan tattauna su sada zumunci bayan kamar sati biyu sai kowa yakoma inda ya fito jin haka yasashi yin shiru har sai yan uwan nashi sunzo sannan zaiyi maganar,kiran nadiya kuwa tunda ya dawo yake kiranta duk da idan ta dauka bata yimasa magana da yawa daga uhm sai um um amma hakan bai hanashi sake kiranta yaji jikinta ba, kowacce rana yana yi mata waya sau 8 koma fiyeda haka.
Washe gari tunda safe baki suka fara sauka, anty dija itace tafara zuwa itada yaranta guda uku biyu maza mansur da muhsin sai mace guda daya Amal, hajiya rasa inda zata saka jikokinta tayi dan murna, dakin amadi sukaje suka tasheshi daga baccin da yake ta hanyar yin tsalle akansa dole babu shiri ya tashi, zuwan anty Dija da kamar minti 20 Anty siyama tazo domin ita agari take tana zuwa yaya yaseen na zuwa shima amma shi baizo da matarshi da yaranshi ba shi kadai yazo nan gidan ya gauraye da hirarsu da shewarsu yaran anty Dija da anty siyama kuwa sai wasansu suke suna tsalle ajikin amadi,
Girke girke kala kala hajiya tasa aka shirya musu amma kuma duk da murnar ganinsu bai sa ta manta da shalelenta amadi ba domin komai tace autanta komai autanta.
Sai bayan sallar azahar sannan anty hamida tazo wacce ita amadi ke bi nan gida yasake hargitsewa da murna, cikeda murnar ganin juna suka shiga gaggaisawa kafin su hau table domin diban garar da hajiya tasa aka shirya musu, kowa acikinsu tsokanar amadi yake yi sai kace wani kakansu daga kowa ya debo tsokanarsa sai yace autan hajiya ko anty amadi kaza,
Har dare suna tare afalon hajiya suna shan hirar yaushe gamo sai misalin karfe 11 sannan suka fara kokarin neman makwanci,
"Anty amadi adakinka fa zamu kwana yau sai dai ka dawo falo kan doguwar kujera.." Anty Dija ta fada tana rikeda amal akan kafadarta,
"A'a babu mai kawo min auta falo yana dakinsa kuje ku k'ak'aba adakina kuda 'yayanku" hajiya ta fada,
"To hajiya" anty Dija ta amsa mata tawuce dakinta, dakinshi shima amadi yawuce yaje yayi shirin bacci yana son ya kira nadiya yana tsoron ko tayi bacci kar ya tasheta daga karshe dai yayi hakuri ya kyaleta bai kirata ba.
Kamar koda yaushe yanda suka saba suna tattauna abubuwan da suka shafesu akowanne zama yauma sunyi irin wannan tattaunarwa saida amadi yaji kowa ya gama fadin abinda yake son fada sannan yace yanada magana,
"To autan hajiya muna jinka meya faru?" Yaseen yace dashi,
"Yaya dama wata yarinyace nake so kuma iyayenta sunce naturo magabata na.."
Shiru dukkaninsu suka yi babu wanda yayi magana shi kuwa yaseen zubawa amadi ido yayi kawai yana kallonsa,
"Kai anty amadi me yakaika nemo aure tun yanzu?" Anty Dija ta fada tana mamakinsa,
"Anty wacce nake so Nagani shiyasa.."
"Ai ko zakayi aure sai kabari ka cika 30 years tukunna ko" anty hamida ta fada,
"Nifa badake nake ba" yace da hamida saboda ita yake bi sakonshi ce,
"Kar dai kayi min rashin kunya" tafada tana harararshi,
"Waima duk ba wannan ba kai yanzu ko ance za ayi maka aure sai ka yarda? Iya masters fa gareka kadai, sannan baka da gida bakayi gida ba, baka jima da fara aiki ba, haba anty amadi kadai sauya shawara" anty siyama ta fada,
"Anty nidai ko banida gida zanyi aure yanzu"
"Baza kayiba, babu wanda zaiyi maka aure yanzu, ka bude kunnenka dakyau ma kaji karatu zaka koma nanda next month dan haka karka sake yimin maganar aure yanzu.." Yaseen yace dashi cikin fada, jin babu wanda ya goya masa baya yasa idanuwanshi kadawa suka yi jajur zuciyarshi ta soma radadi...
_*Ummi Shatu*_👌🏻
[19/08, 7:22 p.m.] Ummy Aysha: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
_(Labarin k'auna)_
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
® *HASKE WRITERS ASSO.* _Home of expert & perfect writers_
*48*
aishaummi.blogspot.com
*Z*uciyarshi na wani irin rad'ad'i ya dubi yayan nashi idanuwanshi jajur,
"Yaya to idan banyi aure yanzu ba sai yaushe zanyi?"
"Sai lokacin da ka girma ka isa aure, kai bama tun dadewa nayi maka gargadin kula yan mata ba? Wato sai da ka kula su ko har wata tayi nasarar janye hankalinka, to bari kaji in fada maka wani abu kai da yin aure sai nan da 5 ko 6 years amma banda yanzu"
"Yaya ni wallahi bazan iya kara ko nanda shekara daya batare da nayi aure ba"
Jin abinda yace yasasu dukkaninsu kallonsa cike da mamaki,
"Kai yanzu har ka isa aure? Lallai amma wallahi kayi kankanta da yin aure yanzu.." Anty hamida ta fada tana jijjiga kai,
"Idan nayi kankanta da aure amma ai banyi kankanta da yin iskanci ba..."
Wata tsawa yaseen ya daka masa, "wallahi karka kuskura, idan har ka kuskura kayi abinda bakinka yake fada wallahi sai na raunata ka sai nayi maka illa, harmu zaka duba kace ka isa yin iskanci? To bismillah ga wurin nan kaje kayi, tunda abin naka ma hakane to wallahi kasar zaka bari karatu zaka koma.."
"Yaya ni bance zan zama dan iska ba amma maganin hakan kawai ayi min auren nan kuma ko karatun zan koma to afara yimin aure tukunna"
"Idan bakinka yasake ambaton kalmar nan sai na fasa maka baki, wai yaron nan yaushe ka zama haka ohhhh lallai kam kaje jami'a kaga yan mata dole kazo gaban idona kana fada min haka amma to kasani bamu shirya yi maka aure yanzu ba karka ji da wai" yaseen yafada cikin fad'a,
Tashi amadi yayi ya wuce dakinsa idonshi yana kokarin kawo kwalla,
Ita dai hajiya tunda aka fara maganar batace ko k'ala ba saboda yaseen shine babba kuma yanzu shine kamar uba ga amadi shiyasa bazata goyi bayan amadin ba gudun kar wata matsala kuma ta kunno kai amma ita tana jin zata goya masa baya tunda auren yake so gashi da bakinsa yana cewa idan ba ayi masa ba zai zama dan iska,
Tunda Amadi yabar wurin su anty Dija suke tattauna maganar da yayansu yaseen amma ita anty hameeda ta dan sauko tana ganin gara ayi masa auren tunda ya nuna yana so sai dai yaseen ya kafe kai da fata yace ko zai yi masa aure sai ya shekara 35.
Tunda amadi ya shiga daki ya zauna yake kuka rabon da yayi kuka har ya manta domin tun rasuwar mahaifinsu amma yau akan nadiya ya zauna yana kuka, har hajiya ta shigo kukan yake