Showing 3001 words to 6000 words out of 82977 words
Chapter 2 - MIJINA SIRRINA COMPLET BOOK BY UMMI AISHA.txt
yaya kabeer ba amma
Koma dai menene sannu ahankali zata tambayi Maman....
*_Ummi Shatu_*๐๐ป
[7/8, 6:42 AM] Humaira Khaleel: ยฎ *HASKE WRITERS ASSO*
*MIJINA SIRRINA...!*๐น
_(Labarin K'auna)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*5*
aishaummi.blogspot.com
~~~Bata kara bi takan maganar ba suka cigaba da hirarsu ita da maman har ta kammala cin abincin da takeyi ta tashi tabar falon ta koma dakinta tana rikeda wayar mama, lafewa tayi akan gadonta suna yin waya da yaya kabeer, sun dauki lokaci mai tsawo kafin suyi sallama nadiya ta tashi ta shiga wanka ta fito ta shirya tasaka uniform din islamiyyarta domin karfe uku suke tafiya su dawo karfe shida na yamma,
Hannen kannenta ta kama suka yiwa mama sallama suka tafi, sai da misalin karfe shida da yan mintuna suka dawo, dawowarsu tayi daidai da zuwan yaya kabeer shi da wani abokinsa,
Nadiya bata bari sunga fuskarta ba tafara gaidasu,
"Baiwar Allah ya kiketa boye kaine kamar marar gaskiya,kodai bakida gaskiya?" Abokin yaya kabeer din yace da ita,
"Kabarta kawai musty domin yar kauye ce" yaya kabeer yafada cikin barkwanci da tsokana, ita dai nadiya shiru tayi musu tana jinsu sai dai ta lura wannan abokin na yaya kabeer wanda aka kira da musty sai faman binta da kallo yake, duk inda ta waiga sai taga yanata kare mata kallo,
Ganin haka yasa ta takura ta shige gida yayinda yaya kabeer ya mara mata baya,
A soron gidan suka tsaya kowannensu fuskarsa dauke da murmushin kauna,
"Yaya kabeer ina ka samo wannan abokin mai shegen kallon tsiya?"
Dariya maganarta ta bashi dan haka ya fara darawa yana kallonta,
"Wai musty? Abokinane unguwarmu daya sannan tare muka yi karatu dashi"
Dan karamin tsaki taja, "Allah na tsani mutum ya tisani agaba yayita kallona"
"To yanzu dai nayi laifi tunda har na kawo wanda yayi miki abinda bakya so, ayi min afuwa..."
Murmushi tayi, "ni ai ba laifi nace maka kayi minba amma dai wannan abokin naka gaskiya ya fiya kallo da yawa"
"To ai nabaki hakuri"
"Nahakura"
"To zan iya tafiya?" Yace da ita cikin tsokana,
"Zaka iya mana yaya kabeer..."
"To fara shiga gida nagani"
Wucewa tayi tana murmushi ta shige cikin gida sannan shima kabeer din ya juya yafita.
Fuskarta dauke da fara'a ta shiga cikin gidan, zaune ta tarar da mama da kannenta tana yimusu shari'a wanda kusan kullum aikin kenan amir da amira kamar zasuga hanjin cikin junansu,
"Ke kuma a ina kika tsaya su Amira suka rigaki shigowa?" Mama ta tambayeta idanuwanta akanta,
"Mama yaya kabeer ne ya tsayar ni wallahi.."
Shiru Maman tayi ta mayar da hankalinta gasu amir taci gaba da yimusu sulhu, yayinda ita kuma nadiya ta ajiye jakar islamiyyarta ta shiga kitchen domin ta jiyo tuwon da mama keyi ya fara kauri alamun ya kama,
Itace ta karasa girkin sannan ta fito daidai lokacin abbansu ya dawo nan kuma dukkaninsu suka dunguma zuwa falonsa kamar yadda suka saba.
Tunda musty abokin kabeer yaga nadiya yaji ta kwanta masa arai domin yarinya ce mai hankali sannan kuma mai nutsuwa gata da kunya da ganin girman nagaba, gani daya da yayi mata yasashi kamuwa da sonta dan haka batare da ya shawarci abokinsa kabeer ba ya samu mahaifinsa yayi masa maganar nadiya domin shi dagaske yake sonta bada wasa ba sannan son aure yake yimata ba na yaudara ba shiyasa ma yake son mahaifinsa yaje ya tambayo masa aurenta,
Aranar da ya sanar da mahaifinsa aranar yaje ya samu baban nadiya daf da lokacin sallar magrib, kasancewar abba mutum ne mai karrama bako sai da ya karrama baban musty sosai ya fito musu da ruwa sukayi salla kamar dama sun san juna sannan baban musty yafadawa abba abinda ke tafe dashi,
Shiru abba yayi kafin ya cewa baban musty zai tambayi nadiyan ko tasan musty din inyaso duk yadda sukayi da ita zai kirashi a waya ya fada masa, anan suka yi exchanging din phone numbers dinsu abba ya shiga gida,
Lokacin da yashiga falonsa nadiyan ya samu ita da mama suna cin tuwo tare, su kuma yaran an zuba musu taliya suna ci,
Sai da abba ya bari sun gama cin abincin sannan yayi gyaran murya yace,
"Nadiya zo nan"
Kusa dashi ta koma ta zauna, "gani abba"
"Bakon da nayi dazu saboda ke yazo.."
Ras,ras gaban nadiya ya fadi saboda bata san abinda tayiba,
"Abba laifi yace nayi masa?"
Murmushi abba yayi,
"Ba laifi kikayi masa ba nadiya, yazo nemawa dansa aurenki ne, sunan yaron wai Mustapha abokin kabeeru ne yayanki"
Ba karamin faduwa gaban nadiya ya sake yiba, nan fuskar musty ta bayyana acikin zuciyarta lokacin da ya kafeta da ido yana yi mata wannan kallon kurullar..
*_Ummi Shatu_*๐๐ป
*MIJINA SIRRINAH...!*๐น
_(Labarin K'auna)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
ยฎ *HASKE WRITERS ASSO.*
*6*
aishaummi.blogspot.com
~~~Shiru nadiya tayi saboda bazata iya fadawa abba cewar yaya kabeer take so ba,
"Nadiya ya naji kinyi shiru ne?"
Muryar abba ta dawo da ita cikin hayyacinta,
"Abba babu komai.."
"To Mustapha dai ya turo mahaifinsa tunda babu wata matsala zan sanar dasu inyaso yafara zuwa har kusamu ku daidaita"
"To abba" ta fada kanta akasa, ita dai mama tana zaune tana jinsu amma har akayi aka gama batace ko uffan ba,
Mikewa nadiya tayi ta fita zuwa dakinta gaba daya tama rasa abinda yake yimata dadi acikin zuciyarta, gashi bata son fadawa yaya kabeer domin gudun sakashi cikin damuwa,please call me ta tura masa nan take ya kirata,
"Yaya kabeer yau ban ganka ba"
"Nidinma yau ban samu ganin fuskar gimbiya nadiya ba amma nasan dalili.."
"Wanne daliline?" Ta tambayeshi cikin dokin jin abinda zai fada,
"Yau naje unguwa ne sai dazunnan nadawo shiyasa ban shigoba, amma gobe sammako zan dako da sassafe inyi karin kumallo da kyakkyawar fuskarki"
Dariya abinda yafada ya bata dan haka tafara dariya,
"Kaji yaya kabeer da abin dariya sai kace wani abinci da zakace zakayi karin kumallo da fuskata"
"Ni ai kinfi abinci, da ace za a ajiye min ke inyita kallonki to da na tabbata bazanji yunwa ba.."
Wata dariyar ta sake yi har tana kokarin fadowa daga kan gadonta,
"Yaya kabeer zaka sa cikina ya fashe dan dariya gashi dama naci tuwo na koshi dayawa.."
"Wai wai, wai, overfeeding kikayi ai? Oya tashi ki fara exercise ina jiyoki daga nan"
Tashi tayi tana dan murmushi,
"Allah yaya KB jina nakeyi nagaji nidai ban son exercise dinnan.."
"To yi tsalle guda goma ina kirga miki, oya fara"
Tsalle tafara tanayi yana kirga mata har sai da tayi guda ishirin sannan ya barta takoma saman gado ta kwanta tana haki,
"Washh, yaya kabeer wlhi kabani wahala da yawa"
"Waye yasa kici abinci yayi miki over?"
"Kaine.."
"A'a ni karki yimin sharri.."
Murmushi tayi kafin tabashi amsa wayar tayi shutdown, komawa tayi ta kwanta tana cikeda farin ciki.
Kamar yadda kabeer yafada kuwa da safe sai gashi yazo lokacin ko school su nadiya basu tafiba, asalima lokacin suke shiryawa, kanta babu ko dan kwali tana cikin kitchen tana cin soyayyen dankalin da mama ke soyawa sai gashi ya shigo, ba karamin mamaki nadiya tayiba domin ta zaci wasa yake yimata da yace zaizo da sassafe ya ganta,
Dan tsananin kunya kasa gaisheshi tayi tana jinshi da mama suna gaisawa daga nan yawuce ciki falon abba,
Bata bari yaji fitarta zuwa makaranta ba ta zare jiki tagudu.
Abangaren Mustapha kuwa ba karamin dadin labarin da mahaifinsa yazo mishi dashi yajiba musamman ma da yaji cewar ba ayiwa nadiya mijiba asalima ko tsayawa da samari bata fara yiba,wanka ya dauka ya shirya ya fito ya nufi gidansu nadiyan,
Tana falon abba tana yiwa su amir homework yaro yayi sallama yace wai nadiya taje inji Mustapha, kamar bazata yi motsiba har saida taji mama tayi magana sannan ta tashi tafita zuciyarta babu dadi,
Tsaye ta sameshi ya saka hannuwanshi acikin aljihu yana yimata murmushi sai dai ita ko kadan bai burgeta ba, sallama tayi masa ya amsa cikeda kulawa nan suka gaisa yafara koro mata jawabi,
"Nadiya wato tun ranar farko dana soma ganinki Allah ya jarrabi zuciyata da sonki da kaunarki saboda yabawa da nayi da hankalinki da nutsuwarki,ina fata zaki bani hadin kai har nakai ga cimma burina da muradina na mallakarki..."
Saida taji yayi shiru sannan tayi magana,
"Yaya Mustapha nagode da soyayyar ka agareni,hakika duk Wanda yace yana sonka to ya gama yimaka komai kuma bakada kamarshi,to amma nikuma inada wanda nakeso"
Cikeda mamaki ya kalleta saboda shidai mahaifinsa yace mahaifinta ya sanar dashi babu wanda yake zuwa wurinta,
"Kina da wanda kikeso? Waye?"
"Yaya kabeer ne abokinka"
Jin abinda tace yasashi yin shiru nawasu yan lokuta kafin daga bisani ya kalleta,
"Shikenan nadiya nagode da kika fada min gaskiya baki rufeni ba, kuma nayi farin ciki da jin cewa kabeer ne wanda kike so domin mutumne shi mai kyakkyawan hali da dabi'a mai kyau, Allah ya tabbatar da alkhairi"
Sallama yayi mata ya tafi nan itama ta juya ta shiga cikin gida tana dauke da farin cikin cewar tagama da babin Mustapha..
*_Ummi Shatu_*๐๐ป
[7/13, 6:59 AM] Ummi A'isha๐๐ป: *MIJINA SIRRINA..!*๐น
_(Labarin k'auna)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
ยฎ *HASKE WRITERS ASSO.*
*7*
aishaummi.blogspot.com
~~~Hankali kwance nadiya ta koma gida taci gaba da gudanar da harkokinta, soyayyarsu itada yaya kabeer kuwa kullum sake yin gaba take tana kara kulluwa, koda yaushe suna makale awaya suna hira, sannan kusan koda wanne lokaci yana gidan mutukar nadiyan tana nan.
Tunda nadiya ta sanarwa da mustapha cewar tanada wanda take so yaji hankalinsa ya dan tashi amma idan yatuno da cewar kabeer ne wanda take so din sai yaji ranshi ya danyi fari saboda yasan kabeer zai riketa riko na gaskiya wannan dalilin ne ma yasashi sanarwa da mahaifinsa yanda suka yi da ita, shima mahaifin nasa baiyi k'asa a gwiwa ba ya kira abban nadiya ya fada masa abinda yafaru gudun kar aga musty din yadaina zuwa bayan kuma manya sun shiga, shiru abban nadiya yayi saboda shidai a iya saninshi nadiya bata da wani saurayi amma tunda yaji haka to ya zama dole ya tuntubeta da zarar ya koma gida.
Kamar yadda al'adar gidan take yauma zaune suke dukkaninsu a falon abba suna kallon tashar mbc drama, rage karar volume din tv din Abba yayi yace,
"Yawwa nadiya kafin na manta zo ina son magana dake.."
Kusa da mama ta dan matsa tana kallon abba,
"Nadiya yaron nan mustapha da yazo wurinki yace kince masa kinada wanda kikeso hakane..?"
Kai ta dagawa abba, "hakane Abba"
"To waye?" Abba yasake tambayarta, kamar bazata yi magana ba dan kunya ta daure tace,
"Abba yaya kabeer ne"
Shiru abban ya danyi fuskarsa dauke da murmushi,
"To kira min kabeer din, dama yau ai naga baizo gidanba"
Tashi tayi ta fita tana cikeda murna, wayar mama ta dauka ta kirashi,
"Yan mata.."
"Yaya kabeer albishirinka?"
"Goro" yafada yana murmushi,
"To kazo abba yana kiranka"
"To ai baki fada min albishir din da kika yimin ba"
"Idan kazo zakaji"
"To gani nan zuwa"
Katse wayar tayi ta koma falon abba tana jin kamar ta daka tsalle dan tsananin murna,
Tana shiga falon abba ta dan saci kallon mama nan taga fuskar Maman babu walwala sosai amma dai batayi magana ba,
Nan kuma taji ranta ya dan sosu saboda tasan bacin ran mama yanada alaka da maganarsu itada kabeer tunda tun jimawa Maman ke yimata gargadin cewar karta bari soyayya ta shiga tsakaninta da kabeer,
Tana ta tunanin abinda zaije yazo aranta taji sallamar yaya kabeer nan tayi hanzarin jan hijabinta ta rufe fuskarta saboda kunya sai dai amma tun kafin ya karaso kamshin turarensa ya rigashi karasowa,
Cikin nutsuwa yayi sallama ya shiga bayan abba ya amsa masa, nan kuma su amir sukayi kansa suka cuccukumeshi domin yasaba basu sweet duk lokacin da yazo,
Yau dinma saida yabisu ya basu daya bayan daya sannan suka kyaleshi ya nemi wuri ya zauna, cikeda girmamawa ya gaisheda abba da mama,
"Kabeeru dalilin da yasa kaji nace kazo shine nadiya ce tazo min da wani zance cewar kai da ita kuna son junanku hakane?"
Sunkuyar da kai kabeer yayi cikeda kunya yace "hakane abba"
Dan fara'a abba ya fadada cikeda jin dadi yace,
"To kabeeru babu shakka naji dadin wannan labari domin hakan zai kara dankon zumunci da aminci a tsakaninmu domin nadiya yar uwarkace, sannan ni mahaifinka ne ako ina zan iya tsayawa in nema maka aure bare agidana,dan haka ni a matsayina na mahaifin nadiya nabaka ita a matsayin matar aure ko bana raye ban yadda nadiya ta auri kowanne namiji ba face kai har sai dai idan kaine ka sauya akalarka, dan haka abinda nake so dakai shine da zarar ka koma gida ka sanarda yaya cewa ga abinda mukayi dakai saboda sonake yi nadiya na gama makaranta ayi bikinku da ita batare da andauki dogon lokaci ba"
Ai kabeer najin abinda Abba yace yaji kamar an yimishi bushara da gidan aljanna, nan wani dadi ya rufeshi zuciyarsa ta samu wata nutsuwa mai kayatarwa tuni yafara yiwa abba godiya,
"Abba nagode madalla, Allah yasaka da alkhairi, Allah yabar zumunci abba.."
"Babu komai kabeer ai duk abinda nayi maka kaina nayiwa domin kai d'anane halak malak"
Saida kabeer ya sake jaddada wata godiyar sannan ya tashi ya fita, cikeda jin kunya nadiya tabi bayanshi, tana zuwa tsakar gida kuwa ta iskeshi lafe ajikin bango dama ita yake jira ya harde hannuwansa ajikin kirjinshi,
Kallonshi tayi yasha gaye cikin wata rantsattsiyar purple colour din shadda galila wacce tasha dinkin buba dan haka ba karamin kyau yayiba,
"Yanzu kaji albishir din da nayi maka dazu?" Tafada cikeda murmushin kunya,
"Naji wannan dalilinne ma yasani shirya baki tukwici, rufe idonki"
Rufe idonta tayi tana murmushi, "yaya kabeer Allah dai yasa nima chocolate din zaka bani irin wacce kabawa su amir..."
Bata iya karasawa ba saboda jin lebenshi akan nata, take jikinta yafara rawa tayi gaggawar bude idonta, nan ta juya zata gudu yayi saurin rikota,
"Ai abba yace yabani ke ko baya raye nine mijinki, tsananin farin cikine yasa kikaga nayi miki haka so karki fassara ni da wata manufa, ko ba komai dai kin san ni yayanki ne dan haka bazan taba cutar dakeba"
Har lokacin bata iya yin magana ba saboda tsantsar kunyar da ya haddasa mata,
"Yaya kabeer nidai.."
Hannunta ya rike ya matsa kusa da ita tareda leka fuskarta wadda ta kawar gefe guda,
"Kedai me?"
"Nidai kasani jin kunya"
Murmushi yayi ya mike tsaye yana kallonta zuciyarsa cikeda farin ciki...
*_Ummi Shatu_*๐๐ป
[7/13, 6:59 AM] Ummi A'isha๐๐ป: ยฎ _HASKE WRITERS ASSO._
*MIJINA SIRRINA...!*๐น
_(Labarin k'auna)_
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*8*
aishaummi.blogspot.com
~~~ "Wai kina nufin haka zamuje gidan kina yimin wannan kunyar?"
Murmushi ta danyi "wai yaya kabeer ni duk ba wannan ba yaushe zaka zo muyi hira irin wacce muka dade ba muyiba?"
Daga kai yayi yana kallon sararin samaniya alamun tunani fuskarsa kuma kunshe da murmushi,
"Uhmmm, ina jin zanzo a weekend saboda ranar ne banida aiki da yawa sannan kema kina gida.."
"To Allah ya kaimu, yanzu dai bari nakoma ciki saboda kai naga kana cikin farin ciki.."
Dakatar da ita yayi ya hanata tafiya,
"Ina kuma zakije bayan akwai labarai da yawa da nake burin ji daga gareki"
"Labari kuma yaya kabeer? A wannan daren?"
"To da sai awanne daren?" Ya tambayeta yana murmushi,
"A'a yaya kabeer karfa ka sauya min maganata zuwa wata daban"
Murmushinsa ne yasake karuwa, "kaji min yarinya da wayo, wai ke waye ya koya miki wayone? Ni ban taba ganin first born mai wayo irin nakiba"
Dariya tayi ta rufe fuskarta, "har nakaika wayo? Kaima fa first born dinne amma kafini wayo ma"
"A'a ban fiki wayoba zadai muzo daya, musamman ma tunda zuciyoyinmu sun kasance guda daya, sannan nan bada dadewa ba zamu zama abu daya..."
Dariyace ta kwace mata nan tayi baya da sauri tana dariya,
"Nidai yaya kabeer natafi da wannan sai anjima.."
Shima dariyar yayi ya daga hannu alamun bye bye yana cewa,
"Ok bye yanmatan yaya kabeer"
Har taje daf da dakin mama dariyar take, a kofar daki taga mama tsaye fuskarta babu walwala sannan da alama ita take jira,
"Mama..."
"Zo nadiya" Maman ta fada idonta har ya danyi ja saboda bacin rai, jiki asanyaye nadiya tabi bayanta zuwa cikin bedroom dinta domin basu tsaya a falo ba,
Zama mama tayi agefen gado itama nadiyan ta zauna,
Kamo hannuwan nadiya mama tayi tana kallonta,
"Nadiya nasan ke yarinyace karama wacce bata gama sanin rayuwa ba, wadda hankali bai gama ratsata ba, wacce bata san rayuwar aure ba, wacce bata san irin gwagwarmayar da kowacce mace keyi agidan aurenta ba, bawai ina son rabaki da kabeer bane nadiya a'a sai dai ina son kisani shi auren zumunci yafi komai gyara zumunci idan har yayi dadi amma yafi komai b'ata zumunci mutukar baiyi dadiba shiyasa zakiga tun farko ban so soyayyarku da kabeer ba saboda kabeer dan dakinane akwai zumunci mai karfi tsakanina dashi haka iyayensa, bana son azo ayi abu ba aji dadinsa ba zumunci ya baci.."
Gaba daya jikin nadiya yagama yin sanyi saboda jin abubuwan da mama ta fada dan haka take taji jikinta ya fara yar rawa,
"Mama kiyi mana addu'a kawai akan Allah yasanya albarka acikin al'amarin amma ni sam bazan iya rabuwa da ya kabeer ba saboda nafara sonsa tun ban san wacece niba.."
Shiru mama tayi tana kallonta batare da tace komaiba, ita akwai abinda ta dade tana hangowa wanda ita nadiya ko kadan bazata iya hangoshi ba domin akwai kuruciya atattare da ita sosai saboda gaba daya yanzu bazata wuce shekaru 15 ba aduniya dan haka yanzune tafara saninma menene rayuwar,
"Shikenan nadiya tunda kin kasa fahimtata shikenan bazan hanaki abinda kikeso ba Allah ya sanya alkhairi da albarka acikin tarayyarki da kabeer"
Idanuwan nadiyane suka ciko da kwalla nan tayi saurin tashi ta fita saboda sai take jin kamar yanzu ne zata tafi tabar mamanta da yan uwanta,
Duk da cewar mama sunyi haka da nadiya bata iya hakura ba tashi tayi taje ta iske abba a falonsa yana zaune shida su amir da waleeda nan ta tashesu tace sutafi dakinsu suje su kwanta,bayan fitarsu ta samu wuri ta zauna kusa da abba,
"Abban nadiya wata magana nake son muyi dakai amma ta fahimta, dafarko ina son ka fahimceni ka gane cewar ni bawai bana son kabeer ne ko kuma yana da wani mummunan tabo awurina ba, kawai nidai bana son maganar aurensa da nadiya ne saboda auren zuminci bashida alfanu mutukar ba ayi daceba amma idan har aka dace yayi dadi to zumunci yana sake kulluwa,
Ban so lokaci daya farat daya ka amince ka bawa kabeer nadiya ba saboda gaskiya nidai auren zumunci baya daya daga cikin abinda nake son yiwa 'yayana.."
Abba bai