Showing 45001 words to 48000 words out of 56438 words

Chapter 16 - Yar Mahaukaciya Part 1 Complete Hausa Novel By Husaini S Abdullah.txt

16 Mar 2026

12

binsu a baya, sai da suka isa ƙofar room aka dakatar dasu aka rufe ƙofar.A Respect ‘yan sanda ne suke tattaunawa da D.P.O, suna rubuta bayanai, suna tambayar masu gadi, kowa yana ba da nasa labari cikin ruɗani.

Numfasawa D.P.O yayi Ya dubi S.P.

“Wannan ba fashi na dare kawai ba,Wannan shiri ne tun da dadewa.”
Abi da tsaiwar sa kenan ya kalleshi cike da tsoro.

“Shiri? Kana nufin akwai wanda ya san Ammar? Ko yake ƙulla masa wani mugu abu Tom wane zaiyi wa ammar haka?”

D.P.O ya ɗan ja numfashi.

“Za mu bincika komai. Daga maganin da ya sha, zuwa mutanen da suka shiga gidan.”
Ummu da ke tsaye gefe guda ta jikinta ya yi sanyi. Ta tuna mafarkin da ta yi a daren jiya. Hawaye suka sake gangaromata

“Ya Allah… ka nuna mana gaskiya, ka tona asirin masu mugunta.”

Dan-danan Labari ya yaɗu asibitin ya fara cika da jama’a. Kamar wutar daji, labarin abin da ya faru da Ammar da Sadiya ya watsu cikin dangi da abokai. Motoci manyan mutane suna jerin gwano ɗaya bayan ɗaya, zuciyoyi cike da fargaba.
Alhaji Ɗan Dubai ne ya shigo har da matar sa fusakar da gaba ɗaya ta gama bayyana tashi hankali yana tsaiwa ya kalli Abi.

“Abi, me ya faru ne, Allah yasa dai Ammar yana raye?” Alhaji Ɗan Dubai ya tambaya cikin rawar murya. Kamar wanda yake jira ya gunza ihu

“No ka kwantar da hankali ka AMMAR insha Allah zai tashi yana raye, kuma Alhamdulillah, amma yana cikin wani hali mai tsanani, Ammar yana bukatar addu'a mu.”

Suna ji haka, matar Alhaji Ahmed Ɗan Dubai ta saki kuka, tare da zauma kan kujerar tana bugun ƙirji.
“Inna lillahi wa inna ilaihi raji‘un! A daren aurensa kuma?wanne wace iri masifa ce Ita ina ita amrya ko tana wanne hali?”

Babu wanda ya kula ta saboda Da ‘yan uwan Ammar su fara zuwa ‘yan uwa na jini da na ne da wanda suke mazauna Kano haka dangi Ummu suma duk sun kewa asibiti,Kowa tambaya yake yi, kowa kuka yake yi, amma babu wanda ke da cikakkiyar amsa. Ummu tana zaune a kujera, hannunta a ɗauke da tasbihi, bakinta na motsi da zikiri, idanuwanta sun kumbura da kuka.
Ba da jimawa ba, daga ɓangaren Sadiya ma labari ya isa gasu Sumayyah da Baba Hauwa haka suka hauwo abin hawa suka zo Asibiti, Lubna da Sumayyah sunyi koka sosai dan sun shiga sunga Sadiya A halin da take cike ciki.

Karshe Nurse hana shiga tayi guri Sadiya.
“Dan Allah kuyi hakuri da fatan za a yi haƙuri, marar lafiyar tana bukatar hutawa.”

Wata daga cikin Innar Sadiya ta yi magana da murya mai cike da zafi, da masifa.

“Wane irin zalunci ne wannan?A dake mu kuma a hanamu kuka wallahi Allah ya tunawa Duk wanda yayiwa Sadiya Asiri?”

Sauran dangi suka amsa da Amee.
A gefe guda,manyan mutane ɓangare Ammar sun taru kusa da ICU. Wasu na addu’a, wasu na kuka, wasu kuma zuciyarsu ta cika da fushi. Wani ƙani Ummu mai Suna Masuwar yace.

“Wallahi duk wanda ya aikata wannan, aiki sai ya fuskanci fushin Allah!”
Abi ya ɗaga hannu ya ce.
“Ku kwantar da hankalinku. Wannan ba lokaci ba ne na hayaniya, lokaci ne na addu’a. Da Addu'a Allah ya tona musu Asiri ko suwaye”Da Ameen suka Ammsa, sanan kowa ya koma ga Ubangijinsa.

Alhaji Ɗan Dubai kam duk wanan haukar da yake bai kula da Sumayyah ba a tunani sa Sumayyah ce kwance buri sa Ya mutu shikenan buri sa ya gama cika ko yaji ta farfaɗo yaje ya faɗa mata shine sikar shigar ta wanan hali sanan ya karasa kashe ta...
[2/5, 11:40 AM] OUMMU MUWADDAH: *📚🌸YAR MAHAUKACIYYA📚🌸*



Mallaki:
Husaina S Abdullah
(Oummu Muwaddah)
📚©2025 -- Duk haƙin mallaka na musamman ga marubiciya.


____________free book _page-28


*Kauye Gidaɗo*

Baba Hauwa ce da Lubna suka shirya don zuwa Asibitin Kofar ɗaki Su Sumayyah ta tsaya ta kira ta."Sumayyah ko zaki? ki fito muje kiga hali da take ciki?”kai ta ɗaga.

"Eh Baba zani bara na wanke kafa ta sai mutafi ”

Tom tace ta fita, Sumayyah tabi bayan ta wanke jikin ta tayi sanan ta saura kaya awaje ta samesu Sunjima sanan suka samu abu hawa.

Malam ne da Baba Zulai sai Doctor suke gudu zuwa room ɗin da sadiya take kwance kuka Baba Zulai take tana kwaɗa ihu suna zuwa kofar aka dakatar dasu Doctor yashiga gudanar da aiki sa. Sai da ya shafe 1 hours ya fito yana yakice gumu Malam ya kira lokacin ya yi dai-dai da Fitowar Abi daga room din da Ammar yake tare suka shiga Officer din Doctor sai da yayi rubuce-rubuce sanan ya dago ya kalle su.

“Da Farko ina me baku haƙuri domin yariyar nan ta gamu da Gang rape (ma'a fyaɗe na kungiya , ma'ana mazaje fiye da ɗaya sun haɗu sun tilasta wa mace yi abu ba tare da yardarta ba.)
Wanda ya haifar mata STIs ma'ana matsalar ƙwaƙwalwa,da yawan tsoro da firgici,”

Doctor na tsaigata zance sa Malam ya kurma ihu.

" Inaalillahi wa Inna ilahi rajuun Shikenan Sadiya yanzu duk buri ki bazai cika ba Wallahi da zanga wanan mutane da Kashe su shine mafita agare Ni tsinanu na Ala....

"Assalamu alaikum Abi wai Wanan mutum shi kaɗai aka ilata yake tamana surutu baya gani Ammar ko tashi yar yar Gwal ce da duk zai shi...

"Dan Allah Alhaji Ahmed kayi shiri tariyar Abin a tausaya mata ne dama Haka Allah ya ƙaddara akanta wanan abu zai faru bakan marainiyar Allah wace Mahaifiyar ta Ta jingina da ita Sai gashi Sadiya ya Allah kabawa Sadiya Lafiya ka dub iri zalunci da akayi wa barwar ka Ka tona Asiri wanda suka aikata mata wanan mumunan aiki”

Ras gaban Alhaji Ɗan Dubai ya buga Muryar sa na rawa ya fara tambayar Abi.

"Alhaji..wai... Wai..me naji kana faɗa ne kana nufi dama Ammar ba Sumayyah ya aura ba wata ce daban?”

Kai ya jinjina.

"Tabbas Ammar ba ita ya aura a lokacin da Kuma je Ɗaura aure........Ni kuma na gargaɗi kowa kan kada a sanar da kowa barshi a haka”

" Inaalillahi wa Inna ilahi rajuun hassbinallahu wani'imar³”

Sai da ya mai-maita sau uku sanan ya fita yana yarkata gumi yana zuwa respect suka hadu da Sumayyah da Baba Hauwa da Lubna da suke neman ida ɗaki Sadiya yake sai ga Gaban Alhaji Ɗan Dubai ya sake bugu gani Tabbas ba Sumayyah bace saboda kaɗuwa da tashi hankali baisan Lokaci da suka bar guri ba fita ya yi ya fara kiran number Dama duka uku ya ɗauka.

"Hallo....!hello..!! Dama ban taba sani kai mahaukaci kauye bane sai yau da kasan ba yariyar bace shine baka sanar dani Dama Wallahi ka guji haɗuwa ta dakai Sai na kashe ka sai ɗai-ɗaita rayiwar duk wani dangika tsinanene ɗan Haram”

Dariya Dama ya bushe da ita.

“Hhhh karya kake Ɗan Dubai na daka na ba da ruwa uban waye yasan yariyar in ba kaiba.”

"Dakata ƙarami ɗan iska duk abinda kaci nawa dai-dai da nera ɗaya ka dawo da abu na Nabaka nan da awa 2”

Dariya Dama ya sake bushewa ya yi, cikin kaukausar furci ya ce.

“Ahamed wallahi yadda aka n manaci ya mutum baya dawowa Tom naci kuɗi nan kasani duk yadda kakai da tauri rai guri kazo kuma duk wani shiri da zaka yi na riga ka yi shashashan banza da yofi”

"Haka kace Dama zan nuna ma Ni kwallo shege ne zan nuna maka na fika zafi kai kasani Ni rayiwar Lagos nayi kai ka faɗan ina kaje abariki.”

“Matseeeeee Shasha tsohon banza”

Yana faɗi haka Dama ya katse wayar. Kafa yayi yana juwa suka yi ido huɗu da Abi rassss kirji sa ya buga kame-kame zai fara Abi ya dakatar dashi da zaiwa.

"Alhaji Ahmed ko kaga Fu'at jiki Ammar ne ya motsa wai karkarwa yake zasu shiga dashi ICU Shine na fito ne mansa.”

Idanuwan sa ya Lumshe tare da saki wata ajiyar zuciya.ya saki murmushi godiya da Allah.

"A'A Alhaji ai tun da mukazo ban sake gani sa Amma Alhaji har yazu ina jinjina lamari nan yanzu Ammar ya auri wata ba Sumayyah ace nakasa samu labari.

Batare Da Abi ya tanka masa ba ya koma cikin hospital yabar sa yana bige-bige waya.

Bayan Sun Sumayyah sun fita daga gida babu jumawa Ɗaki Innar Sumayyah da ya tsage ya fara buɗewa,babu kowa a gidan sai Inna ciki hukunci Ubangiji gaban dagi ya shafece ya zube, ba tare da ya danne kowa ba ihu Inna take na kiran sunan sumayya da haka moƙota suka riƙa shigowa dan temaka mata wasu matasa ne guda biyu suka fitar da Inna gidin maina tare shifiɗa mata buhu ta zauna. Khalil ne ya shigo Baba Hauwa ya kira ya sanar da ita abin da ke faru Umarni ta bashi yakai Inna ɗaki ta, sanan su kwashe buliluka su kaisu gefe guda da haka suka yi sallama bata sanar da Sumayyah gudu karta ɗaga hankali ta.

Tare da maƙota aka rika fitar da kasar da har suka kwashe tass shawar suka yanke su haƙa fandisho kafi Malam ya dawo zaiji daɗi haka. Haka kuwa sunayi dan danan da Almajiran Malam suka fara haka ana ciki haƙan Ililu Almajiri Malma ya haƙo wata leda mai rubutu har da turare a ciki babu wanda ya sanarwa ya zare ya zura cikin aljihu sa ya fita, a babban zo zaure ya tsaya ya fito da takar dar takarda ce ta farraƙu mai dauke da sunan Ammar da Sumayyah salati yake yana jingina rashi imani na Babba Zulai sai gashi Allah ya sakawa Sumayyah abin da suka aikata ya koma kansu.

Gabaɗa yan gidan Malam ne a zaune a respect kowa zance zuci yake wani na Aiyana alkairi wasu akasin haka Nurses ce ta shigo.

“Ina 'yan uwan Sadiya zaku iya shiga ta farfaɗo , Amma dan Allah banda yawan surutu.”

Hamdallah sukayi suka tafi jiki babu ƙwari, tun da suka shiga Sadiya take zubar da hawaye, Malam da Baba Zulai ne jiki gado suna aiki yi mata saunu, ciki harɗewa murya ta fara kiran sunan Sumayya.

"Sumayyah zonan.. Zonan dan Allah?”Jiki babu gwari Sumayyah ta ƙara sa baki gado hannu ta miƙa mata.

“Sadiya Yajiki naki Allah ya baki lafiya Insha Allah zaki warke ki koma gidan ki ciki Aminci”

Katse ta tayi da cewa.

“Sumayya ba wanan nake bukata ba yafiyar ki nake nema da ta mahaifiyar ku na sani mun cutar daku ko iya hakin ku bazai bari na rayu ciki salama”

Kuka Sumayyah ta fara.

"A'a Sadiya ni bantaba ruƙe ki araina ba Wallahi na yafe miki har abada Allah ya baki lafiya kijin”

Goge hawaye ta tayi tace.

"Dan Allah in na mutum ki auri Ammar dama miji kine ba nawa ba,muka shiga muka fita Ni da Batun sai da muka raba gashi na aure shirye sai dai haka bai zame min alkairi ba”

Da gudu Sumayyah ta fita tana kuka kallo ta Ya maida kan Baba Zulai.

"Babarmu dan Allah ki tuba ki koma ga Allah wallahi wanan ishara ce Allah ya nuna mana tun anan duniya mun azabat da Innar Sumayyah da Sumayyah mun hana tayi rayiwar jin dadi yau gashi muda muke gani mun samu duniyar bata da Ana fani a dare Aurena agaban miji da na aura maza bakwai sunyi min faɗe sun yiwa zuciya ta baban ila wanda mune mukajawa kanku zunibi da muka aikata ne yake biyar mu, kisani ki da zan rayu sau dari zan mutum sauri saboda mijin da na aura zai riƙa kallo na da wanan abi duk da nasan bama rayuwa zan yiba.

Kuka Babba Zulai take tana kifta mata ido, Murmushi takaici Sadiya tayi.

“Babanmu kaine kashi bayan duk wani abu da muke aikatawa kaine ka daure mana gidan muci zarafi baiwar Allah nan tun da na taso ban taba gani kayi wa Inna kallo mace ba baka taɓa yiwa Sumayyah kallo 'yar da ka haifa ta a ciki kaba, kaine silar ciwo Inna, kaine ka wargaza gidan ka da kanka Shim wai wane iri uba muke dashi da yake ƙirƙiran malami kaci Ammar mahaifi Inna tabba Allah bazai barkuba.”

Tana faɗi haka ta fara firgita tana fisge-fishe da haka doctor ya kora su waje.

Bayan sati ɗaya Allahmmdullilah jiki Ammar kullu kara samu sauƙi yake dan Har likita aka kira daga waje har ya fara sarrafa jikin sa kuma yana iya furta ɗai-ɗai, Doctor ya kira Ummu da Fabi da Fu'at da zai riƙa kula dashi gida zaune suke suna jiran cewar likita. Bayan sun gaisa ya fara gargaɗi da cewa.

"Da fargo sai mugodewa Allah subhanahu wata'ala domin Ammar ya auna arziki ba karami ba sai dai ina gargaɗi ku, ba kowane abinci zaku riƙa bashi ba sai wanda muka umarce ku dashi. Kamar.Shayi mara kauri,Pap/custard, sai shinkafa mai laushi hankali turawa, kayan lambu, ku guji mai maiyawa aciki, da Yaji, abinci mai nauyi har sai mu sake dubawa”


Godiya suka yiwa doctor sanan ya dauko wata farar takarda zan rubta wanan magunguna sai a karni a pamis zaki riƙa bashi Vitamins (B-complex)saboda taimako jijoyoyi, da kuma kariya daga ciwo hanta da koda.zamu haɗa ku da kwarare likita wanda zai riƙa masa gwaji (monitoring& tests) da Blood test, Urine test,ECG, CT-EEG, wanda bama fata , insha Allah nan da Wani lokaci indai abin dokar likita after 1 month ma zai dawo dai-dai.”

Hannu Abi ya bashi sanan ya nufasa yace.

"Doctor ita fa yariyar naji kace ta haɗu da tsoron da firgici kuma har yanzu banji kuna faɗi mataki da Za'a ɗauka na gargawa ba....
[2/5, 1:09 PM] OUMMU MUWADDAH: *📚🌸YAR MAHAUKACIYYA📚🌸*



Mallaki:
Husaina S Abdullah
(Oummu Muwaddah)
📚©2025 -- Duk haƙin mallaka na musamman ga marubiciya.


____________free book _page-29

Maganar ta domi Allah sai mun haɗa da rokon Allah cutar wace an riga an zutar da ita ba'yi reping ɗinta dan ta rayuwa ba ayin ne dan ta rasa rayuwar ta gaba ɗaya sai dai muna baki ƙokarin mu insha Allah zata warware baki ɗaya”

Tashi sukayi jiki babu kwari, sai da suka shiga ɗaki Sadiya suka mata yaji sanan suka miƙe kamar daga Sama suka ji maganar Sadiya.

"Maman Ammar...!!”Da Sauri Ummu ta dawo dan gaba ɗaya tausayi Sadiya take gani take kamar Aure Ammar ne ya ja mata.zama yayi ta kama hannu sadiya.

"Ɗiya ta Sadiya me ya faru kina son wani abune?”

Shirin hawaye da ya gangaro mata ta sa gefe hannu ta ta goge.

“bana son komi sai neman gafara Ammar na mucutar da shi mun rabashi da wace yake so yake kauna mun rabashi da farin cikin dan Allah ko bana raye ina neman Alfarma ki roƙamin gafara guri sa,.”da sauri Ummu ta rungume ta wasu hawaye masu zafi ta goge ta sau saita murya.

“kar ki damu insha Allah zaki tashi ki koma ɗaki ki, kuma ki Sani tun kafin zuwan mu Duniya Allah ya riga ya rubuta al'amari sa wanda babu wanda ya isa ya goge kisani da ke Da Ammar da Sumayyah wanan zane ƙaddara kune dole kuma sai ya faru, babu wanda ya isa ya goge ki ne mi. Gafara guri Allah maji roƙo bayi sa insah Allah zai yafe miki, Allah yayafe mana baki ɗaya”

Kai ta jijina Ummu ta miƙe ta dubi Baba Zulai.

"Yanzu Fu'at zai kawo muku abinci Zuwa Yamma dan dawo”

Godiya tayi da Sa albaka sanan Ummu tabi Abi mota wance Har da AMMAR aciki.

Tunda da suka shiga mota abubuwa suke dawo masa sabani Hoton Sumayyah yake dawo masa gaban sa na tsanan ta faɗuwa sai dai ya kasa manya lokaci da yake cewa Sadiya yake so ba Sumayyah ba wani waye ne ya zubo masa wanda Fu'at ne ya lura da hakan ƙasa yayi da Muryar yace.

“yaya dai ko jikin ne?”

Kauda kasa gefe yayi dan baya bumatar jin komo daga baki kowa buri sa suje gida. Su Abi na fita Sumayyah da Lubna suka shigo cikin Asibiti lokaci da suke shiga ɗaki da Sadiya take Lokacin Babba Zulai ta fara rafka Sallati.

“ Inaalillahi wa Inna ilahi rajuun hassbinallahu wani'imar wakil ƙaluu Inaalillahi wa Inna ilahi rajuun me zan gano Sadiya..! Sadiya dan Allah ki tashi kar ki mutu mi barni wallahi duk Ni najawo don Abun duniya na da gani cewa Sumayyah naza ta hutaba gashi na kashe 'yata da kaina”

Da gudu Sumayyah da Lubna suka ƙarasa cikin ɗaki gani Sadiya a sankame ido ta akafe tana kalli saman ɗaki zaka san tafiya tayi nisa Lubna na ɗora hannu aka zata kallah ihu doctor da Nurses guda biyu ruka shigo kora su sukayi waje suka hau gwaje-gwaje babu bata suka tabbatar da rai yayi halinsa.

(Allah sarki Sadiya ashe cuta bata tashi ba Allah ubanji ya yafe miki Allah yasa mutuwa tazama hutu agre ki dama musulmi baki ɗaya. Shi yasa akullum ake so ka riƙa aikata alkairi baka san Sa'id da zata zoba ko kana tafe ka da ciwo ko babu)

Bayan sun gama tabbatar wa Doctor ya fito da gudu Baba Zulai ta tare shi.

"Ta mutu ko Likita Ni dama nasan tun da tayi Salati Nasan ta mutum?”

"Dan Allah Hajiya kiyi mata Addu'a duk wani musulmi in ya rigamu gidan gaskiyar addu'a yafi bukata ba koke ko....

Kafi doctor ya kai ƙarshe Baba Zulai ta sulale ƙasa asume Lubna kuwa tana guza ihu ta hau aljanu Sumayyah kuwa hawaye take da furta sunaye Allah. Sai da suka juma ahaka Yusufa ya shigo ciki kaɗuwa da tashi hankali tunda yaji abin da ya faru ya fara kiraye kiraye waya Fu'at ma da shigowar sa kenan Abi ya sanarwa da rasuwa tuni suka ɗungumo zuwa asibitin.

Cikin ƙanƙane lokaci asibiti ya cika koke-koke da Aljanu babu kalar wanda dangi Baba Zulai da masoyan ta basu baya kwanar Baba Zulai Ramatu ce ta guza ihu ta taho da gudu ta shaƙi wuyan Sumayyah. Tana Magana iri ta masu iskokai.

"Sai kinci Ubanki kece kika tira mutane su illata Sadiya da mijinta saboda kina baƙi ciki bai aure ki wallahi sai kin faɗi gaskiya ko mucilla ki uwa duniya, Yiiiiii Ayyyyyyy baizai yuyu ba”

Da sauri Baba Hauwa ta je inda Ramatu ta shaƙe wuyan sumayya.

“Haba Ramatu ya kike magana kamar ƙugurmar Jahila”

"Ki daina kiran goɗiyar mu wanna Ba Ramatu bace Sarki fatake ne aguri nan”

Ummu da shigowar kenan ta daure fusakar ta ko tsoro Babu ta tsaya gaban Ramatu.

"Malama cikata in ba haka ba Wallahi sojajin da suke baki geta su fitar mana dake banda shirka da so sai Kum bata gawar mamaciya so kuke sai kun sake

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login