Showing 18001 words to 21000 words out of 56438 words
Chapter 7 - Yar Mahaukaciya Part 1 Complete Hausa Novel By Husaini S Abdullah.txt
yace uffan har ya samu guri ya zauna da Kallo Baba Zulai ta bishi,kujera yar tsugono ya dasa ya zauna tare da ƙare mata kallo.“Babarmu Wai yanzu matar nan dan ta tsinka mana mutunci shine taje ta kwanta A kango Shikuma shege yaron can Tanimu har da ɗaukar ta ya tafi da ita gidan su dana ce ya kawota sai yace in ya kawota wai me zamu yi mata banda azabtar wa”Sallati tasa da tafa hannu"Shikenan ta daɗa ja mana zagi a kasuwa” ƙwafa ya yi zai yi magana malam ya shigo.
*Lagos*
Bayan ASP Mubarak ya saki Classic Don bai zarce ko ina ba sai Gidan Alhaji Ɗan Dubai tin da Alhaji Ɗan Dubai ya gansa yasan ba lau ba dan yana ta zagi da turanci yana sai an biya shi kuɗi sa da sauri ya tare cikin ladabi iri na riƙaƙu yan Duniya."What happened is Classic?”Sai da ya buga tsaki kafi yace.“ Follow me, my money, the girl ran away from the police.”
Sai da ƙirjin Alhaji Ɗan Dubai ya buga lalashi ya fara yana nuna masa wasu yan mata, fur classic yace bai san wanan ba ƙarshe bindiga ya ciro a ciki Aljihu sa ya fara harbin ƙasa da gudu Alhaji Ɗan Dubai ya shiga wani ɗaki ya ɗauko masa kuɗi sa sai da ya irga yaga ko biyar bai taɓa ba sanan ya fita.asahar ya lailayo ya maka“Wallahi Yariyar nan bata ci banza ba, sai naje gurin Tsoho ubanta an biya ni duk abin da na kashe, ni za'ayiwa bura uba”
*Nasarawa Kano*
Tsakani Hajiya da Ammar juna suka kalla ya ɗauke kai, Hajiya ta fara shafa bayan ta."Sumayyah kuma shine sai kinyi kuka kar ki damu insha Allah Gobe zan sa ya mai dake Ai zaki gane ko?”Kai ta ɗaga mata.sai da Hajiya ta lallashe ta sosai sanan suka fita har Ammar ɗin.
Suna fita ta sauke ajiyar zuciya,“Allah… badan niba, Allah ka bani kwanciyar hankali… ka raba ni da tsoron da ya cinye zuciyata.” hannunta ta sa ta sharce hawayen da suka gangaro mata.Sai da Tayi Addu'a sosai sanan ta kwanta.
Tunda ya koma ɗaki bacci gagarar sa ya yi a fili ya furta"Wai ita me yake damu ta duk da hawalar da tasha buri take ta koma cikin su?” tsaki ya ja ya sake juyawa ya gyara kwanciyar sa.
Tun Asuba Sumayyah ta shirya take juyi ciki ɗaki gajiya tayi ta zauna gefe gado ta sauke Nufashi a fili ta ce."Su fa masu kuɗi basa son tashi da wuri sai aita fama basu tashi ba, yanzu ma inaga tara tayi amma basu tashi daga bacci ba”
Sai tara 'Yar aiki Hajiya ta kira ta, jikin sai rawa yake ta fita parlour ƙasa, Hajiya ce kawai kan Daining tunda ta hango Sumayya fara'ar taƙaru "Sunu da zuwa yar albarka ina fata kin tashi lafiya?”kasa jurewa tayi tana zuwa zata gaida ta ta fashe da kuka, Murmushi Hajiya tayi ta ɗagota ta rungume ta kamar yarinya ƙarama.
“Allah ya mayar miki da farin cikin da aka kwace miki. Banso ki zama raguwa kizama mace me juriya da jajurcewa!,” Hajiya ta furta cikin tausayi, tana shafa bayanta.ajiyar zuciya kawai Sumayya take saukewa. cikin sigar lalashi ta ce.“Allah ya ba ki kwanciyar hankali fiye da wanda kika taba samu Abaya ina fata daga yau baƙin ciki ki ya ƙare, Zan cigaba da Addu'a Yariyata Sumayyah, farin cikin na har abada ya luluɓe wanan zinariyar zuciyar.”
Ammar da ya fito yanzu ciki Shadda sa bazum blue block ta masa kyau kamar sabo ago yana tsaye a bakin ƙofa, yana binsu da kallo baisan me yasa ba, yake jin ƙaunar Yariyar duk lokaci da yaga Hajiyar sa tana janta ajiki.basu yi tunani ya zo ba.
Idonsa ya sauka a kan Sumayyah, yadda take jijjiga kai da yadda take tsanan ta kukan ta, da hannunta da ke rike da Hajiya kamar bata so ta sake ta yaji ɓaci ran yanayin da hmya fara haduwa da ita.kasa shiga yayi ya kasa komawa.Zuciyarsa tashiga bugawa da sauri.“Wannan yarinyar… me suka mata haka?”Ya fada a ransa cikin zafin rai.“Me ya sa duniya tayi mata tsauri har haka? Kuma me yasa tun ranar farko da na ganta zuciyata ke jin kamar ina da hakkin kare ta?”
lumshe idon sa ya yi dan danan wani irin ɓacin rai mai zafi ya taso masa.ya furzar da iska mai zafi, ƙoƙarin juyawa yake Hajiya ta kira shi.
“Ammar.” tsayawa ya yi cak.
“kazo ka rareshe ta zan haura sama kayi break fast din da ita kafi na fito”Kai ya daga a hankali, don shi in akwai abin da yake masa wuya bai wuce yawan magana ba.kujerar daining yaja wace take kallo tata ya zauna shuru ne ya ratsa su, na wasu daƙiƙu gani ba zata yi magana ba ya fara juya Spoon aciki Chips wanda yake haɗe da soyayaye waina kwai, ya na kallo ta.“Kina kuka Saboda kin fiso ki koma inda za'a maida ki baiwa ko?”
Jajaye ido ta ta ɗago."A'a saboda Inna tane kawai ina tsoro abin da zai sameta”
Shiru ne ya sake ratsa tsakani su sanan ya dago kamar me ciwo hamgum.
“Ki sani daga yanzu zan tsare ki. Zan kare ki. Kuma babu wanda zai kara cutar da ke.”Ya faɗa yana kallo fuskar ta.Goge guntu hawaye fusakar ta tayi."Nagode Amma Ina so na koma Bunkure Inna ta tana can tana..…”tsawa ya daka Mata ido sa dan-danan ya yi ja jikin sa har rawa yake gani ta fashe da kuka yasa shi ɗaukar gogar ruwa mai sanyi yasha,yana ajiyewa ya tashi ya matsa kusa da ita, ba tare da ya taba ta ba.“Ki daina tsoro.ki sani zan maida ki gida yau shikenan tunda bakya son zama damu”
Shuru tayi ba tare da tace komi ba har ya gama ci ya goge baki sa da tissues ya miƙe “kije ki shirya zan fito da mota”Har sai da hakonta suka fito saboda murna, kallo ya bita dashi har ta haura sama shikuma ya fita.
Bayan kamar 20 mintes Hajiya ta fito sai da ta fara shiga Bedroom ɗim da Sumayyah take ta kira ta sanan suka sauka ƙasa suna zuwa Ammar ya shigo yana duba agogo wayar sa ya kalli Hajiya.
"Hajiya zan kaita Daddy yana hanya nasan har na dawo bai iso ba”Kai Hajiya ta jinjina Hawaye ya cika ido ta,kwana biyu da tayi da Sumayya tashiga ranta sosai. Rungume ta tayi
"Allah ya kare ki ya duba rayiwar ki, Zanzo na duba ki kafi azumi sanan Zaki zomi da Sallah kinji 'yata?”
Kai ta ɗaga tana hawaye“Eh Hajiya zanzo Nagode Allah ya dubaki yadda kika kula dani”Babar Ket ta miƙa mata."Ammar zai baki kuɗi ɗinki kisa wasu,Wasu kuma ki bari sai Sallah”Har ƙasa ta zube ta sake mata godiya sanan suk fita Ya zauna A drive seat ita kuma for seat, tun da suka tafi, ya saka waƙar India mai sa tausayi kamar yaresa na gado haka yake bi waƙar cikin Sallo, satar kallo sa kawai take shikam idon sa yana kan hanya yana bin wakar yana jin daɗi yanayi hanyar ƙauye Saboda yanaso rayuwar ƙauye. Sai da suka yi nisa Sosai ya kalle ta."Ke Kar fa ki saida nifa.”
Jiki ta ne ya hau rawa tana rantsuwa"Wallahi Ya Ammar bazan sai da kaiba Ni ban san ma yadda ake sata ba, nan ne hanyar garimu ko...ko wan can Zaka tambaya mun kusa shiga Gari giɗado”
Burki ya taka yana kallo yadda duk ta ruɗe dariya ya fara mata, sai kuma tayi shuru,suman tsaye tayi bata taɓa gani wanda dariya take ma kyauba iri Ammar shi komi yayi kyau yake masa, maganar sa taji.
"Ki rage tsoro ko Kya samu sallama aciki ranki ”shuru tayi ya sake kunna motar...
****
Malam na shogowa ya bisu da kallo, wuyansa da kwato carbi mai dubu.gyran murya ya yi.“Tom lafiya aka tsaya cirko-cirko kuna kafe ni da kallo.?”Ajiyar Zuciya Baba Zulai ta sauke.
"Malam inafa Lafiya ace Matar nan shikenan kullum ta riƙa ja mana zagi da sunan Mahaukaciya ce ita gaskiya ya kamata ka ɗauki mata ki...”Duk abin da ya faru ƙarya da gaskiya sai da ta haɗa, Nan kuwa ya hau kamar fulawa da aka zan baɗa Mata yis. Cikin fushi ya kalli Yusuf.
"Kai Yusuf duk yadda za'ayi kaje ka dawo da ita ayau ba sai gobe...
Sallamar Alhaji Ɗan Dubai ce ta hana kowa motsi Yusuf ya miƙe yana rawa."Yau kace akwai cin uwar sabada agidan nan tab Malam Mutumin kane yazo wata ƙila wasu kuɗi yazo ƙarawa.”
Tafiya Malma ya yi da sauri har Malin-malin ɗinsa tana niyar kada shi.Baba Hauwa tace.“A'a Malam yi a hankali”
Yana fita ya iske Alhaji Ɗan Dubai a tsaye cikin nan nasa agaba, kansa sai tsatsafar gumi yake na azaɓa,yana niyar Zubewa Alhaji Ɗan Dubai ya shaƙi kwalar Malam Sule Gidaɗo.
"kar ka tsunguna min Tsoho Alla kwankwan nunafiki dama gadar zare ka shirya min na gama baka kuɗi shine kuka sa Police sukaje suka karɓa maka yar ka tom Wallahi baku isaba yadda kake ganina tsohon ɗan tasha ne goge ɗan bariki, Bani da dama guri neman na Abinci”Ba Malam ba hata Yusuf da Khalid sai da tsoro ya shigesu lallai yau su haɗu da ƙwallo dan Iska, yadda yake ruwan Ashar tsaf zai danfara malam A ƙasa.
Duk layi da motar Ammar ta gilma sai Yara sun bita suna “laaaa ga balaraɓe tare da 'Yar Mahaukaciya kamar bai san da zaman yaran ba haka yake tunƙi cikin nutsuwa.
Tunda suka tinkari ƙofar gidan su gaban ta ya fara faɗuwa.
" Inaalillahi wa'inaalaihi rajun, Wa nake gani kamar Alhaji Ɗan Dubai.”Ta faɗa tana me sake kallo Ƙofar gidan nasu da mutane suka fara taruwa, Gani shine yasa ta sauri riƙe hannu Ammar.
"Shine wallahi..!Kar muje shine Wallahi..! shine nasan zuwa ya yi ya maida ni dan Allah mu koma kar ka kaini gurinsu nasan Babana basu ni zaiyi kuma ga Yaya Yusuf aguri.”
Kuka take kamar zuciyar ta zata fito, Ammar kam kamar be san akan mai take magana ba ya cigaba da tuƙi sa cikin kwanciyar hankali har suka ƙarasa inda Su Baba Malma suke......
Shering and like
[11/17/2025, 1:01 PM] OUMMU MUWADDAH: https://whatsapp.com/channel/0029Vb1QRwY5vKACPNI7B73a
*📚🌸YAR MAHAUKACIYYA📚🌸*
Mallaki:
Husaina S Abdullah
(Oummu Muwaddah)
📚©2025 -- Duk haƙin mallaka na musamman ga marubiciya.
____________free book _page-10
Cikin fidda rai ta cire hannu ta daga jiki hannu sa ba tare da ya kalle taba yace.“Wan can ne Mahaifi naki?”Kai ta ɗaga masa hawaye masu zafi suka gangaro mata "Amma Kace zaka kula dani kuma Hajiya ta ce Amana ce ni A hannun ka.me yasa zaka mai dani in da na baro?”
Sai da ya buɗe murfi motar sanan yace"fita muje”Jiki babu ƙwari ta beɗe 'Yan matan ko nace ƙwailaye kwaye su Sadiya ne ɗaya daga ciki ta waiga karaf ido ta ya kai kan Sumayya, Rashida da take gefe Lubna ta kwaɗa shewa.“La Shikenan ma Baban su Sadiya ga 'Yar mahaukaciyar nan ta dawo sai ya tafi da ita can su ƙarata”
Ido Malam da yayo waje ya fara kar-katar da kai yana kallo In da aka ce Sumayya na guri da sauri Alhaji Ɗan Dubai ya saki Malam Sule Gidaɗo ya tako inda Sumayya take tsaye jikin sa na kyarma.Hannu Yasa zai riƙe ta Muryar Ammar ta karaɗe guri.
“Kar kayi kuskure ɗora hannu ka a kanta,Otherwise, you will regret it in a way you have never experienced in your life.” DA fari ya ɗauka Wanine daga ciki Yaran Malam,Ciki matsanan cin ɓacin rai ya waigo."Ko Ubanka Malam gashi Bai isa...ya..”
Kasa ƙarasa zagi da ya ɗako yayi saboda wanda ya gani agaban sa.Ɗan A tajiri mai kuɗi nan wanda Duniya take Alfahari dashi (Ammar Sheikh Kareem Al-Labban)Mashahurin attajiri.An san sa a ko’ina saboda yalwar arziki da sirrin
kasuwanci.yana tsaye kamar bashi ba,ya harɗe hannu sa, murya na rawa ya fara magana ciki ƙinƙina.
"Ammar ɗana kaine anan?Me ya kawo ka wanan kauye maye Alaƙa ka da wanan mutanan??”
Ɗaure fusak yayi kamar bai taɓa dariya ba“Ni zan tambaye ka me ya haɗa ka da ƙanwata ka sani ko scend ɗaya ka sake tamakar ka sallami kanka daga guri aiki ne bana ji akawai wanda zai mai daka matsayi da kake kai.”
Zubewa Alhaji Ɗan Dubai yayi gwiwa har ƙasa.“Ɗana Ammar ka teamka,kamin rai wallahi Alhaji shine gatana Aiki nan shine gatana ba..wai...
"Shut up your mouth here. Kasan da haka kake aikata haramci kana safara yara ƙanana kai Guba ne a cikin al'uma, karka kuma min magana in kuwa ka sake kasani Wallahi..! wallahi..!! Wallahi..!!! Ka kori kanka”
Da haka Ammar bai sake cewa komi ba sai motar sa da ya nuna masa.Takalman sa Alhaji Ɗan Dubai ya kwasa a hannu ya shige mota tare da bari layi da Gudu. Sai A lokaci Yusuf ya saɗaɗa kusa da Malam tare da yi masa magana cikin raɗa.
"Malam yariyar nan fa ta sake zuwa da Alkairi kasan wanan yaro waye kuwa?”Kai Malam ya girgiza yana kafe Ammar da kallon kamar wanda zai gudu ya barsa.
"Malam Maifinsa hata ƙasashe waje so suke su kulla kasunci dashi Ai nasan kana ji Sheikh Kareem Al-Labbani
Mashahurin attajiri nan a rediyo ko?”Malam ya daga kai jiki sa yana rawa kamar mazari Yusuf ya sake cewa.
"Tom wanan yaro da kake gani zubi Larabawa ɗansa ne wasu na cewa shi kaɗaine ɗansa aduniya wasu kuma sunce yana da ƙanwa”
Tun kan Yusuf ya rufe baki Malm ya zube a gaban Ammar."Sannu da zuwa! Yanzu kake tafe? Ke Sumayya dan Ubanki tarbiyar da na baƙi kenan kina gani ɓaƙo ki barshi a waje?”Tunda Malam ya fara Zuba, Ammar yake binsa da ƙallo yaga Son Abin duniya a ido Malam yaga tsantsagaro son kai a tatare dashi.
Sumayya ce ta ƙaraso inda Baba ya zube kamar kayan wanki ido nan yaci uban farin kwali kamar tsoho kwarto."Yace ka shiga.”
Kamar bazai magana ba, bayan wasu mintes ya dubeta“Ina Innar taki take?”yana faɗa ya sake tsuke baki sa gulma Jama'a suka fara.
"Kai kunji 'Yar mahaukaciyya ta yowa Balarabe asiri ya biyo ta har Ƙauye Giɗaɗo yana neman Mahaukaciyar Uwar ta”Duk iri surutu da suke yana jinsu amma bai ce musu uffan ba.Malam naji haka ya miƙe “tashi muje ciki dama tun yau kwana biyu muke nema ta Wallahi ko sama ko ƙasa Mun rasa ta, ai kasan Mahaukata da Ɗan banzan yawo tom ai kan nasu ne ba ɗaya ba duk nisan guri haukarsu gaya mus.....
Bai kai ƙarshe ba Sumayyah ta tafi luuuuuu zata faɗi sumamiya.
***
Kwanan Inna biyu a gidan su Tanimu ta samu kulawa Sosai kuma ido ta ya warke babu kumburin sai dai bata gani da ido ɗaya dan ƙwayar ido ta fashe, Abinka da cutar mara Lafiya hakan bai wani ɗaga mata hankali ba Inna Zuwaiara ce ta fita gidan Baban ɗanta Babandi Sai Tanimu kawai ta bari a gidan. Surutu kawai Inna take wanda baka gane mai take nufi shikuma yana duba takardu makarantar sa sai dai ƙirjin sa yana yawan bugawa ya rasa dalili haka.
Kafi Baba malam ya taɓa ta tuni Ammar ya ɗauke ta, ya kalli Malam."Ka nuna min ɗaki Mahaifiyar ta zan kaita can”
Dukan uku-uku ƙurji Malam ya shiga yi dan zai iya rantse wa da Allah tun da Sumayya tasa ƙafa ta fice babu wanda ya ƙara tura kansa ciki. Jikinsa na ɓari suka kutsa ciki gidan,Baba Hauwa ce ke wanki jikin tulu ruwa gani mutun ya shigo Salam daga kasan maƙoshi yasa ta miƙewa tare da dafe ƙirji.
"Wa'innahu Sulaimanu Wa'innahu..
"Ke sakarai Shasahar mutun ne Ba Aljani ba, kina nufi Akwai wani sheɗani da zai iya tun karan Gidan Malma Sule batare da Ayar Allah ta kona shiba, Tom wanan da kike gani babban mutum ne,baƙo Sumayyah ne.”Malam ya faɗa tare da nunawa Ammar ɗaki,tsaki ta doka musu.
"Matsee Yaya Zulai kizo kiga wani Iko Allah 'Yar Mahaukaciya ta jawo mai jan kunuwa”Da gudu Baba Zulai ta fito zani a hannu. Lokaci da ta fito Ammar ya juya musu baya ya shigar da Sumayya cikin ɗaƙi.Kasa jurewa tayi tabi bayan sa daga Window ta tsaya tana leƙa su.
Ammar yana zuwa ya shinfiɗar da ita kan ya galgalaliyar tabarma ido sa har ya canja launi ya ɗago ya kalli Yusuf"Inaso Mahaifiyar ta ta dawo kafi ta farfaɗo ko nawa ne zan baka, Abani ruwa”
Da gudu Yusuf ya fita har yana Turai Baba Zulai. Saboda tsabar kiɗima zaici kuɗi.tunda ya fita yake falfala gudu bashi ya tsaya ba sai atsakar gidan Su Tanimu yana zuwa ya fara kurma wa Inna kira.Inna da take gefe a zaune, ta miƙe ta koma bayan Tanimu tana kuka."A'a baza niba zai zaneni baza niba”
Ran Tanimu ne ya ɓaci“Kar ki damu babu Uban da ya isa ya fitar dake daga gidan nan.”Yana fadi haka ya kama hannu ta suka fita taskar gida. Yusuf yana tsaye ya zuba uban doro.yana Gani Inna ya tafi,Hannunta ya kama"Zo mutafi gida Ga shegiyar yar kican mai jaye jaye maza ta....
Jin hanunta ko motsawa baiba yasa shi waiga wa Tanimu ya gani ya ruƙe mata hannu."Babu inda zata duk lokaci da tatashi gani ta tazo ta ganta anan gidan Amma baza ta sake shiga wacan baƙi gidan naku ba marasa mutunci azzalumai.....
Mari Yusuf ya dauke tanimu dashi, ciki zafi nama Tanimu ya rama ko kawa ce ta kaure musu ciki Jim zafi Yusuf ya fara ihu.
"Wayo jama kuzo ku taimaka min Tanimu zaiwa matar babana faɗe,babu mutane a gari ne dan Allah ku fito kar ku bari yaci mutunci aure”
Ta ko ina mutane suka riƙa shigowa Abinka da kar-kara har da masu Sandina kamar 'yan farauta, batare da bincike ba suka rufe Tanimu da duka har suka far fasa masa jiki.
Inna Zuwaiara da ta tunkari gidan taji hayani ta kaure yasa ta faɗa da gudu, Fuskar Tanimu ta gani duk an bubuge ta har da jini sallati tasa ta tura kai cikim mutane tare da bawa ɗanta kariya, cikin hikima da dabara tayi musu bayanin, zagi Yusuf suka fara gani reshe yana neman juyewa da mujiya yasa shi Sulalewa ya gudu.
Lokacin da Ta koma Sumayyah ta farfaɗo kalo kalo Suka fara da Ammar da Yusuf Malam ya gane tambayar Yusuf yake so yi amma girman kai tsiya ya hana shi magana cewar Malam.
"Kai
