Showing 15001 words to 18000 words out of 56438 words
Chapter 6 - Yar Mahaukaciya Part 1 Complete Hausa Novel By Husaini S Abdullah.txt
har ya manne da jiki ya bushe jiki sa na rawa yana anbato Sunan Allah ya ƙarasa inda take sai da ya gurfana agabta kafi ya fara yaya fa mata ruwan ikin wata iri tsawa kamar mace zaki ta kurma wani Uban ihu btare da buge-buge tana surutai”Idona kar ka zo zai cire min ido wayo ido na ya faɗo ƙasa.”Kasa daurewa Tanimu ya yi fusgo ta tare da rungume ya fashe da kuka, sai A lokacin Inna ta saki ajiyar zuciya tare da yin shuru a kan ƙirji Tanimu tana maida ajiyar zuciya sai da ya yi kuka sosai sanan ya rabata a ƙirjin sa cikin wata iri murya yace.“Baba zaki je gidan mu.?”Kai ta girgiza masa da ido ɗaya take kallo sa dan yada ido ya kunbura sosai ko ɗaga shi baza ta iya ba. Ruwa ya miƙa mata ta amsa, ko ƙarar haɗiyar ruwa baka ji hakan ta shanye ta yar da ledar sanan ta kalle shi.
"Zaka kaini guri Sumayyah, tana kuka na goyata zaka kaini nono zata sha.”Ido ya rintse wasu hawaye masu zafin suka gangaro masa,"Zan kaiki yashi muje zaki ci tuwo?”Baki ta washe ƙoranta,wanda suka jima da dafewa da dauɗa."Zanci zaka saimi 'Yar tsala akwai daɗi.”Kai ya ɗaga mata mikewa tayi da Sauri tana sosa kanta.shi ya fara fita ita kuma tabi bayansa tana tafe tana waige dan Garbu Gizo yake mata har suka isa gida. Suna Zuwa Inna zuwaira ta tare ta takawo hannun zata taɓa ta da Sauri ta janye.
"Kar ki taɓa ni zan gayawa Sumayyah”Shuru tayi ta kalli Tanimu Yanzu abin na farko ka yi mata dabara mu gasa mata iri ya buɗe sai muga yadda yayi sai kaje guri Ade likita ka sanar da ita ko akwai magani da zata bata saboda kumburin ido.”Kai ya daga cikin Sarewa dan shirya farga yake ido ya buɗe tun da yaga idon yake fargaba.
Da wayo da dara aka gasa mata ido sai da suka yi anfani da Dangwali yaɓa(Vasili) sanan ido ya buɗe wata ƙara Tanimu yasa tare da yin baya numfashi sa na ɗaukewa, Jikin Inna zuwaira na rawa tace.“Tanumi lafiya me ka gani a cikin ido kake ƙwallah ihu haka?”Kuka ya fashe dashi, da Sauri Inna zuwaira ta karaso.
"Inaalillahi wa Inna ilahi rajuun!”Sai da ta maimaita sau Uku kafi ta sana ido ta ya fara fitar da hawaye, ciki kuka Inna zuwaira tace.
"amma ko waye ya yi wa wanna baiwar Allah haka Yaci Amma kuma Allah bazai taɓa bari sa yaji dadi ba Ya umurce ina ganin Baiwar Allah nan bala'in ta sake gani ba domin kwayar ido tashe kuma...”Cikin kuma Tanimu ya dakatar da Inna sa."Insha Allah ina zata sake gani Zata warke zata sake gani da ido ta bani da tabbaci Allah yana gani kuma zai yi iko sa akanta.”Jiki Asanyaye tace."Allah yas.”
Duk yadda suka so ta yarda suyi mata wanka Inna kitayi hakan yasa suka barta dole taci tuwo sosai dan sai da taci kwasa uku. A guri ta kwanta ta kama bacci.Sai da tayi bacci Tanimu ya kallo Inna sa jiki babu Kwari.
“Inna bara naje Guri Ade nayi mata bayani ko akwai wani taimako da zata biya mana.”Addu'a ta masa da fatan nasara sanan ya fita.
YUSUF
Tunda Tanimu ya tafi da Inna Yusuf ya gani murmushi mugunta ya yi ya koma dandali ya ci gaba da sanfgar gaban sa.tare da ƙiyasta Shari kala-kala acikin ransa.
Lokaci da Tanimu ya isa kamis ɗin Ade lita ya samu mutane biyu dole yabi layi bayan sun fita ya faɗa mata komi saidai baice mata Matar Malam Sule Gidaɗo bace.A iya ɗan karatu da tayi yasa ta dube shin tace.
“Gaskia Tanimu ba zan yake maka hukunci ba saboda ba nan bangare na karanta ba Salima Ni bangare Haihuwa karantar yanzu abu masu sauki san baka magani sabar da kunburi dana zazzaɓi ta fara anfani dashi kafi muga yadda halin zaiyi.”Godiya ya mata akayi lifai kudi magani 2k da haka ya koma gida.
Washegari dai da suka kai ruwa rana tasha magani sanan ya nuna fushi Da ta yarda aka mata Inna Zuwaiara tayi mata wanka a cikin kayan ta ta bata wasu marasa nauyi riga da zani tasa. Tayi kyautar a guri bacci ya sake ɗauke ta ɗan Zazzaɓi ne sosai ajikin.
*** *LAGOS* ***
Tun da ya fita har Sallah magariba Ammar bai dawo Hospital ba Hakan kuma yasa taji babu daɗi cikin ranta tace."Sumayyah ki lalaɓa shi ya kaiki kano ko yaƙi maida ki sai ki hudu saidai kin fita daga Wanan baƙi gari da yadawo dake.wawa sawa har guri goma babu Ammar babu shi ƙarshe kwanciyya tayi da haka bacci ya ɗauke.
Washegari da wari wata Nurses ta shigo da wata sabuwar abaya Black ce mai adon Pink colour,Da kallon Summayyah bita, Zuwa tayi ta dafata."Yayanki yace ki shirya Yanzu zai zo zaku tafi Kano.”Da sauri ta dira ta faɗa Bratheroom bata jima ba ta shirya tayi kyau kamar, kyawunta ya fito tamkar yariya yar shekara Ashirin da Biyar ido ta tamkar an zana mata kwali duk yadda ta wuƙilta su sai sun ɗau hankali mai kallo su,bata juma da fitowa ba Ammar ya shigo fusakar sa babu yabo babu falasa.sai da ta ɗan rusuna"Ina kwana?”"Kina lafiya?”Da haka bai sake kallo taba ya ya nufi Hanyar fita da Sauri tace.“Kayana fa a ina an zuba su?”Bai kalle taba sai agogo Diamond ɗin da ya kalle.“Ki jefar dasu bamu buƙata ki gito ina mota.”Zata sake magana ya fice, kayan tabi da kallon,sanan ta juya tafita, ko a mota agaba ta ya zauna ta zauna abaya drive ya kasi zuwa Airport. Tsoro tashi hankali babu iri wanda bata shiga taruɗe sosai da taji wai ita zata hau jirgi har ya fara taka ƙafar bene Summayyah na tsaye juyowa yayi cike da mamaki yana kallo ta gani bazata ta bashi ammsa ba yasahi boɗe baki ɗakar."Jirgin ba mota bace da zai tsaya jiran ki.”Madadi ta bashi amsa sai ta fashe da kuka abin kona masa rai yayi ya dawo azafafe ya damƙi hannu ta ido sa har ya canja kallah.
“baki gaji da gari bane kike kuka ko so kike na maida ki inda na ɗauko ki?”kai ta fara girgiza masa muryat me cike da shagaɓa da yarinta ta buɗe."Ina ji tsorodan Allah me zai hana mu tafi a Kafa inaga zaifi.”Dariya da take da mugu tsada wace ko iyaye sa sukan sha wahala kafi suga yayi ta, Saboda yawan surutu da da dariyar sa baza ka taɓa gane damuwar sa ko farin cikin ba. Dariyar ya fara mata ita kanta kallo sa take gashi yana mata guzo sai ya yi mata kalla da yan ciki finafinai India iri masu Bala'in kyaunan tawani fanni kuma kana ganisa Kasan Balarabe ne, sai kuma ya fara bata tsoro ita sai yanzu ta fahimci fari sa ba iri namu bane yasha banban ga manyan ido wanda in ya tsare ka dasu dai ka kasa kama kwanta iya kasubar da kaɗai zata tabbatar maka da zaki ne a tsaye zaki da ya amsa sunan, tariga ta gama dulmiya da kallo sa taga ya juya izuwa mara fara'a yace.
“Tom ke jiki ki gwada tafiya ƙasa sai mu haɗi a can”Gani da gaske shigewa zai ya barta yasa ta cire talman ƙafar ta ta kwasa aguje har taje inda yake tsaye rigar jikinsa ta kama gam kamar me shiri buga yaƙi da kuraye haka ta rintse ido suka shuga ciki ba ita ta sake shiba sai da yace."Ki cikani kar ki yagamin riga.”A hankula ta fara buɗe ido har ta sake akan zaratan mazaje Manyan ido sa sun juma a haka ƙarshe Ammar ya sake bashi tare da hura isa.babu juma aka kawo musu Kayan ciye-ciye.
Sai da akyi sanarwa sanan Jirginsu ya tashi daga Lagos zuwa Kano. Hasken rana ya ratsa ta ta ciki gilashin jirgii kallo ƙasa ta fara tana jin sabuwar rayuwa a gareta.
A gefe ta kuma Ammar ne yake duba wayar hannuesa,sai dai zuciyarsa da ido ta ya rasa me a ciki su da suke hanna shi ƙare mata kallo, wata zuciyar tace "Kasani ko idanuwata suna tattare da wani Sirrin da suka fi naka”A fili yace "Ni..!No Bazai iyuyu ba.”Da kallo Sumayya ta bushi bata da iko tambya. Shima A hankali ya juyo ya kalle ta, sai ta ɗauke kai tana murmushi tana ji ƙirjinta na wata iri bugawa.Tunda kan yadda take wasa da yatsu hannu ta zuwa rigar da ta rufe mata ilahirin jikinta tabi da kallon ya sauke ajiyar zuciya Aciki tanshi yace.
“Wannan yarinyar ba kamar kowace ba ce. Ƙaddara ce ta haɗa mu, Allah ya bani iko nikaya guri iyaye ta lafiya ba tare da cutarwa ko zanba ba.”
Karfe uku da rabi na rana jirgin su Ammar ya sauka a Filin jirgin Mallam Aminu Kano.Lokaci da sanyi iska ya sauya iska tana kaɗawa a hankali. Sumayyah ce ta fara fitowa cikin nutsuwa, sanye da doguwar riga ta abaya mai launin baƙa kanta lullube da scarf mai laushi wanda Ammar ya siya mata a Lagos.
Tun daga nesa, Hajiya Maryam ta fito daga mota tana murmushi. Fuskarta cike da annuri da natsuwar mace mai hankali da kima fara ce sai dai farinta iri na fulani ne baka na Ammar ba. Ammar ne ya ƙarasa inda take ya rungume ta cikin girmamawa."Nayi kewar Hajiyata da Daɗan Girkinta mai sani nutsuwa.”
Sumar kansata sosa ciki farin ciki “Nima haka Ammar ɗin Hajiyar ka tafika shiga damuwa da rashi shi na Sa'o'i.”
Juyawa ya yi ya kalli Summayyah wace take jira ace At ta gudu"Hajiya ga wacce nake gaya miki,tana buƙatar hutu da kulawa nan Hajiya ta ba da ganan ba.”
Yalwata far'ara ta tayi ta kalli Sumayyah cike da tausayi da fahimta tamkar ta juma da sani ta.“Assalamu alaikum, ‘yata ƙaraso kiji Dumin Mahifiyarki Karki biyew Ammaru.”
kasa ƙarasawa Sumayyah tayi sai durƙusawa da tayi cikin ladabi, ta amsa.
“Wa alaikumus salam Ina Wuni da fatan mun same ki lafiya?.”Hannu ta ta kama ta haɗa ta da jikin ta"Tashi dan Allah” gefe Fuskat Summary ta shafa.“Ki kwantar da hankalinki, kin samu gida. Ki ɗauke ni kamar uwarki, ba buƙatar jin tsoro ko kunya nice mahaifiyar Ammar ki sa Aranki kuma Mamanki ce” hawaye suka ciko idon Sumayyah, ta kasa magana, sai dai ta girgiza kai tana share hawayenta. Ammar ya juyo ya yi murmushi ciki ransa ya ji daɗin yadda Hajiya ta karɓe ta da buɗaɗɗiyar zuciya.“Hajiya Itafa kuka nayiwa yariyar nan wahala dam kin daina Wahalar da kanku ki Kani gida na kagu naci Girgiki nan naki mai sani ba manta da kowa da komi.”bata biyewa Ammar ba sai da ta samu Sumayyah tayi shu sanan suka shiga mota Ammar ne agaba kusa da drive Hajiya Da Sumayya kuma a back seat.
Suna is gidan Sumayyah ta fara bin gidan da kallo,gida ne mai tsari da kwalliya irin ta Larabawa lambuna har ukune kowane cike yake da Bauchi kayan ciye-ciye iri na kasashe waje,da furanni masu kamshi kala-kala ruwa na gudana daga bututun fountain a tsakiyar su.
In bada ban tasan Ammar bai taba cutar da ita ba da cewa zatayi sai da ita yazo yi ran Iya fallo in zaka iya cewa Allah ya gama salamar ka anan gidan duniya maganar Hajiya ce ta dawo da ita daga duniyar tunani da ta lula,"Sumayya kije ga daki can na biyun da yake samma Nana ne ɗakin ki koyi wanka zan Sa Hameda mai aiki ta kawo miki kayan da zaki sauya, sannan ki fito mu ci abinci.”
Godiya tayi sanan ta shiga ɗakin cikin mamaki.take bin ɗaki da kallo kaya na more rayiwa babu abin da babu manyan turaruka masu ƙamshi ga makeke Mirror da zaka iy gani kanka tundaga ƙafar ka har izuwa kanka, bed din tabi da kallo balcket gado green ne sai fulawoyin da akayi ado da su white haka ma labule launin su ɗaya da zani gado, da ƙamar window ce daga sama da ke fitar da iska mai sanyi.tsaya wa tayi a tsakiyar ɗakin tana kallon komai kamar mai mafarki.
A hankali hawaye ya sulalo mata.
“Ya Allah… har yau ina raye. Ina gidan da ba a mafarki ba, dama ace Inga inna ta cikin gidan nan dama ace zata zo muji daɗi nan ko da Na wuni ɗaya.”ta zauna a gefen gado, ta rufe fuska da tafin hannu tana kuka cikin ɗaciki zuciya”Fa tunani halin da innar ta take ci.
Bayan tayi duk abin da Mahafiyar Ammar ta umarce ta, ta fito da doguwar riga ta Abaya dan babu kayan gargajiya kamar nata a gidan tunda ba wasu yara ne dasu ba, tun da ta hango ta baki hajiya yaƙi rufu wana ji wani farin ciki in taga Sumayyah tanaji wata ƙauna ta musamman a tare da ita.
Kallo ɗaya Ammar ya mata ya ɗauke kai suka zauna a dining. Hajiya Maryam tana kallonta tana nutsuwa da tausayi yarinyar. A hankali tace.
"Ammar baka faɗa min sunan kanwar taka ba” sai da yayi miƙa kamar wanda ya gaji kafi ce."Gajiya ki tambaye ta zata gaya miki”Tasan Zai riƙa,mai da kallo ta tayi kan Sumayyah
“ 'Yata, mene sunanki?”saibda ta saci kallo Ammar taga loma kawai yake zuvawa kamar bai san da zaman taba sanan tace.“Sumayyah Yar mah.....” kallon. Da Ammar ya tsare ta dashi ne yasa haɗi ragowa abinci ba bi shiri, Murmurshi Hajiya tayi.
“Da kyau. Sunan ki sunane na masu albarka. Kin san ma’ana sunan?”Ta girgiza kai tayi tana wasa da da COKALI hannu “Ma'nar Sumayyah, shine mace wacce take da tsarkin zuciya.”Idonta ne ya sake cikowa da hawaye taa ce.“Da gaske Hajiya? to Allah ya sa nima na cancanci hakan.”
Ammar da yake ke gefe yana goge bakin sa da Tissues, bai ce komai ba sai dai zuciyarsa ta cika da tausayin ta bai san lokacin da ya fara ba kuma yanji zai iya temaka mata koda kuwa hakan zai zama yankewa nashi farin ciki.
Kwana biyu da zuwan Sumayyah ta fara sabawa da gidan. Hajiya ta fara koya mata yadda ake kula da furanni,da yadda ake yin girke-girke na Lebanon da Hausa, tana koya mata karatu da adu’o’in safe da yamma.
Ranar Asabar suna zaune a lambu, rana na. taho faɗuwa. Iskar yamma tana kaɗawa, furanni suna motsawa. Ammar ya fito daga Part ɗinsa da ke gidan, yana sanye da Three quarter wando na jeans sai t-shirt copy colour ta kama ƙirji sa ta fitar da ainihi surar sa, ƙamshi yake yana taku cikii izza hannunsa ɗauke da fulas.
Idon sane yakai kan Sumayyah tsaiwa ya yi yana kallon yadda take bawa furanni ruwa, tana murmushi cikin natsuwa.daga gani yanayi ta na Farin ciki da haka.Hajiya ta lura da yadda yake kallonta, sai tayi gyran murya tayi murmushi cikin hikima.
“Ammar…” ta kira shi cikin natsuwa, juyowa yi“Na’am Hajiya?”
“Inaji Ajiki na Sumayyah.Allah ya kawo ta gare mu da hikima. Ka kula da ita, saboda wata rana, zaka gane dalilin hakan.Ina roƙan ka dan Allah karka bari tayi kuka”
Ya ɗan yi shiru, yana tunani.“In Sha Allah Hajiya zan ƙoƙarin haka,”ya masa cikim ladabi guri ya nema ya zauna suka shiga wata hirar.
Da dadare, Sumayyah tana kwance tana kallon POP.tayi nisa cikin tunaninta kan abin da ya faru,a gidan Alhaji Ɗan Dubai, safarar mata, da yadda Ammar ya cece ta.numfashi ta sauke
“Ya Allah, idan wannan sabon farkon rayuwata ne, ka bani ƙarfin juriya, ka saka da alheri ga wanda ya ceci ni. Kasa na koma guri Inna ta cikin Amince kabawa inna ta kariyya”
A gefe guda, Ammar ne, a zaune bisa makeken gado da sanyi A.c dana fanka yana ratsa kwanyar sa,yana duba wasu takardu,duk da ainki da ya sha masa kai zuciyarsa bata daina tunanin Sumayyah ba. Maganar sa lokaci da ya ceceta ta dawo masa cikin kunuwana sa.“Na gode, ka ceci rayuwata.”
takardun ya rufe, ya lumshe ido, yana murmushi a hankali.
“Sumayyah…” ya faɗa a hankali...
Bacci ne ya fara daukar ta Cikin bacci tayi mafarki inna ta ciki wani iri hali mai ban tsoro tana ta kuka gashi kamar wawake take bata tagi abinda ke gabanta. Wani iri ihu ta kurma hakan yasa Ammar jin igiyar saboda dare ya fara yi. Bare ma uguwa iri tasu babu hayaniya bare kaka sa ji wani sauti ciki han zari ya miƙe.
“Sumayyah..!me yake faruwa da ita....”Wani ihu nata ya sake ji ko takalman bai nemaba ya fita da gudu kafin ya karasa Hajiya taje.
Lokaci da ya shiga Bedroom ɗin Hajiya tana zaune ta sata ajiki ta tana tofa mata Ayatulkursiyyu dasu li'ilafi Jamal yasa ta samu ƙaramar nusuwa maganar Ammar ce tasa ta waigawa.
“Hajiya Me ya faru da ita?”cikim ruɗewa Hajiya tace."Wallahi nima Ammar ban sani ba Na fara bacci naji kukan ta yanzu nake son naji me yake faruwa ko wani abu ya tsorata tata.”
Hannu sa ya harɗe kan ƙirjin sa ya kalle ta da kyau har yanzu kuka take."Sumayyah Me kika gani ya tsorata ki da bazaki iya Salati ba sai ihu?”tsare ta ya yi da ido tana ɗagowa sai ta sake fashewa da kuka.
“Dan Allah ku mai dani guri Inna ta bata da Kowa saini ina tsoro ta batta wallahi ta shiga wani hali bazan yafewa kaina ba dan Allah Hajiya kisa ya maidani Giɗaɗo ko dan Inna ta”Tana faɗi haka ta sake fashewa da sabo kuka wanda ya ɗagawa Hajiya hankali...
*Amin Afuwa dama na faɗa muku Update ba Kullum ba*
*Albisiri kuma masu jira Agama littafin ITACE KADDARA TA tom kuzo ku mallaki naku daka kuɗi ƙalilan babu tsada ku karanta Complete ɗinsa ₦ ɗari uku tabiya buƙata kar ki bari Labari Sultana da Sultan Hajiya ya wuce ki, ko hawan jini gare ki Tom ga magani sa nan Ki nemi Littafin itace Kaddara ta ki kore damuwa da takaici Duniya.Ga account number da number da zaki tura shedar biya domi ki mallaki naki*
*Account number 0341904756. USAINA SALISU GT Bank: SHEDAR biya 08168621656*
[11/16/2025, 4:04 PM] OUMMU MUWADDAH: https://whatsapp.com/channel/0029Vb1QRwY5vKACPNI7B73a
*📚🌸YAR MAHAUKACIYYA📚🌸*
Mallaki:
Husaina S Abdullah
(Oummu Muwaddah)
📚©2025 -- Duk haƙin mallaka na musamman ga marubiciya.
____________free book _page-9
*Gidan Malam Gidaɗo*
Yusuf ne ya shigo ko Sallam babu tsaki ya ke tare da ball da kwanika Babu wanda