Showing 15001 words to 18000 words out of 114314 words
Chapter 6 - HAJAR Book Complete document by Feenerh_feeche .txt
da take shanya kayan da ta gama wankewa tayi wuf ta shiga ɗaki, jikinta ne ya bata cewa ya sayyadi Nura ne yau yazo wajen Baba daman ya gaya mata zaizo, Baba ya ɗauki kofin ruwa ya sha sannan ya rufe ragowar abincin ya miƙe ya saka takalmi yayi soro, yana zuwa ya tarar da wasu mutane su uku, biyu zasu kai sa'anninsa ɗayan kuma matashi ne, matashin ne ya russuna yace "Baba barka da fitowa", Baba ya kallesa ya amsa, shi dai bai shaida su ba, Baba ya miƙa musu hannu su kay musabaha, ɗaya daga cikin manyan yace "daman munzo da wata magana ne", Baba yace "toh" ya koma cikin gida ya amso tabarma a wajen Umma, tinda Maama taga ya fita soro da tabarma taji hankalinta bai kwanta ba, ta kalli Maimuna da take zaune akan dokin ƙofa tana shan rake ita da Nabila tace "Maimuna leƙo mana su waye suka zo wajen Babanku", Maimuna ta ɗauki rakenta ta ɓalla sai kace sabuwar kamu ta wuce ƙofar soro ta laɓe, leƙawa ta farayi ta hango su a zazzaune, da sauri ta dawo da kanta tace "ya sayyadi Nura" sai kuma ta kasa kunne, kaf abinda suka zanta karaf a kunnuwanta tana naɗa, taɓe baki tayi ta dawo cikin gida tana zabga tsaki, Maama ta dakata da sharar da take tace "su waye??", Maimuna ta zauna dokin ƙofa ta ɓalli rage tace "wai neman izini suka zo yi a wajen Baba na neman waccan shegiyar", Maama ta saki tsintsiyar hannunta tace "neman izini kamar ya??", Maimuna ta hura buɗaɗɗen hancinta tace "ni dai a yadda na fahimta sunzo nemawa ɗansu auren shegiya ne", Maama ta zaro ido tace "aure??", Nabila ta zubar da tuƙar raken bakinta tace "Hajarar??", Maimuna ta kallesu duka tace "meye naga kun wani firgita ne??, bafa wani mai arziƙin ne yake nemanta ba, Nabila kin tuna ya sayyadi Nura??", Nabila tace "kwarai ma kuwa", Maimuna tace "toh shine fa yazo tare da iyayensa", Nabila ta daka wata shewa tace "waii tsiya ta ɗakko tsiya, da wannan ruɓaɓɓen shagon nasa zai riƙeta", Maama tace "kun sansa ne??", Nabila tace "farin sani ma kuwa, ya sayyadin islamiyyar mu da muka dena zuwa ne, wllh bashi da komai, matsolo ne ainun", Maama ta gasa mata harara tace "dalla gafara can, da bashi da komai ɗin ke kin taɓa kawo kamarsa ne eyee ko wanda bai kaishi matsolontaka ba?, wllh kun bani kunya duk irin samarin da kuka tara babu wanda ya taɓa zuwa gidan nan da maganar arziƙi, kuna zaune sai kace tsumammun kayan wanki waccan shegiyar zata cigaba", Maimuna tace "chaɓ, ina wani cigaba wajen Nura, wllh ci baya daii", Maama tace "ja can amma dai ta fi ku ko??", Maimuna tace "wllh bata fini ba nida nake da Alhaj, kuma yace aurena zaiyi, lokacin zuwa wajen Baba ne kawai bai samu ba". Baba ne ya dawo ciki ya naɗo tabarma a hannunsa, kan dardumarsa ya koma ya zauna ya kirawo Umma, Umma ta fito ta tsugunna tace "mal gani". Baba ya wassafa mata kaf abinda ya faru ya ƙarƙare da cewa "da har kuɗin aure suka ce zasu bayar na dakatar dasu sbd inaso na binciki yaron kuma a tabbatar da yarinya itama tana so", Umma tace "to mal Allah ya tabbatar da alkhairy". Maama da tayi karaf da kunnenta ta rangaɗa wata shegiyar guɗa ta cigaba da shararta.
★Nurain zaune a farar kujera a compound ɗin gidansu Ruqayyah yana jiran fitowarta, wayarsa yake latsawa a hankali, saida ya jingine 20mins amma bata fito ba abinda bai taɓa faruwa ba, dialing numbernta yayi, tana yin picking speaking keenly tace "ina zuwa dearest" ta katse kiran, after like 5mins ta fito sanye da hijab da riga da skirt na atamfa, taja kujera ta zauna tana facing ɗinsa tace "sorry na saka jira", wayarsa ya kashe ya saka a pocket yace "na ɗauka ma kwalliya aka tsaya tsara min", murmushin gefen baki tayi tace "ka jira lokaci, kwalliya har saika gaji da ita", ya ringa kallonta sai kuma yace "ehen ina jinki you said you want to talk to me", wasa ta farayi da fingers ɗinta tace "kana ji dearest", yace "all ears", ta sunkuyar da kanta tace "ina so a ɗaga lokacin bikin mu"............✍️
💛 HAJAR 💛
by Feenerh_feeche
{10...}
With a weird facial expression Nurain ya kalli Ruqayyah, kallonta ya ringa yi ya kasa cewa komai, shirun da taji yayi ne yasa ta ɗago kanta sukay ido huɗu, tayi sauri ta sunkuyar da kanta tace "ina maka magana fa", keenly yace "naji ai, why Ruqayyah?, mesa kike so a ɗaga lokaci?", without looking at him tace "sai naga kamar za a matse maka hidima, dearest banaso ka matsawa kanka akan aurenmu, kabi komai a hankali, a maida lokacin nan da 10months kaga zaka fi balancing..", ido ya zaro yace "10 what?, Ruqayyah are you kidding me?", tace "no dearest i am not kidding", ajiyar zuciya ya sauke yace "look Ruqayyah ba dai damuwanki karna takura kaina ba, babe just relax Insha Allah komai zaizo cikin sauƙi, karki wani damu i planned for it", ajiyar zuciya ta sauke tace "alright", yace "good, yanzu wane shirye-shirye kika fara?", tace "ni ban fara shirin komai ba amma yanzu zan fara", yace "ohk, all the expenses on me", tace "Ohk". da haka kuma suka koma firarsu ta masoya mai daɗi. A kwana a tashi, bikin Nurain da Ruqayyah yau saura 3weeks cif kuma a yau ne aka shirya kai lefe, Anty Zulaiha da Sakeena step sis din Nurain da suke same father da Anty Mardiyya ƙanwar Abba sune jigajigai sai sauran ƴan uwa su biyar aka kai lefe. gaskiya an zuba bajinta, both sides sunyi ƙoƙari sosai, ammafa Ruqayyah ta samu lefe na gani na faɗa ba ƙarya. Nurain yana zaune a kan kujerar balconyn ɗakinsa dake up stairs yana jiran yaga motocin da aka tafi kai lefe dasu sun fara dawowa, ai kam yana ganin dawowar tasu ya sakko down stairs ya fita balcony, Anty Zulaiha da sauran suka wuce cikin gida, Nurain ya amshi baby boy ɗin hannun Sakeena yace "yawwa ƴar uwata fatan dai basu ƙara mana lokaci ba?", Sakeena ta kallesa up and down tace "Nurain ni ka raina kenan ko?, nice baka jin kunya ba?, mesa baka tambayi anty Mardiyya ko Zuhaiha ba saini karkatacciya bishiyarka mai daɗin hawa ko?", yace "ohh wllh kin fiya son girma", handbag ɗinta ta ɗauka ta rufe motar tayi gaba tace "zaka ga son girma alhaji". yana kallonta ta shiga ciki ya shafa kansa shima ya shiga. A palour ya tarar dasu sun baje haja suna mayar da yadda akai, Mami ma na tare dasu suna wassafa mata yadda akai, Noor ta zazzaro ido tana dashare tooth a cikinsu, Allah kaɗai yasan yadda ta tamawa bikin nan, Nurain ya zaga ta bayan kujerar da Sakeena take ya ɗora mata Ayman a laps, ta juya ta kallesa tace "Au bazaka riƙemin shi ba, yanzu daga hidimarka na dawo kuma nagaji", yace "zan je Hospital ne akwai wani urgent patient da zan duba ne", tace "in this Noon?", yace "yeah, naso ma na makara fa na tsaya naga dawowarku ne", tace "Ohk saika dawo saika mayar dani gida banzo da Mota ba", yace "Ohk".
★Alhmdll acikin wannan taƙin result ɗin Hajar na NECO ya fito kuma taci sosai, Nura ne ya amshi takardun ya shiga fafutukar nema mata school of Nursing tinda shine burinta a karatu, Soyayya tsaftatacciyar mara algus Hajar da Nura suka yiwa junansu, a yanzu kam sun buɗe sabon shafi a soyayyarsu tinda sun samu lasisi mai kyau, Hajar na zaune a tsakar gida akan kujera tana buga game a sabuwar wayarta Android da Nura ya kawo mata shekaran jiya, Umma ta leƙo daga ɗaki tayi kiranta, tarar da ita tayi tana ƙoƙarin zura hijab tace "yanzu zaki tafi?", Umma tace "shirya mu tafi", Hajar tace "tom, amma Sabra fa idan ta dawo daga islamiyya", Umma tace "da wuri zamu dawo ai, wllh banyi niyyar zuwa dake ba amma ina tsoro na barki ke kaɗai a gidan nan ga Sa'adatu ma naga tazo", Hajar tace "Umma nifa na dena shiga sabgarsu, na miki alƙawari fa kuma Baba ma nayi masa", Umma tace "A'a shirya dai mu tafi, haƙurinki siƙewa yake". Hajar ta canza kayan jikinta na tsakar gida zuwa wata riga da skirt na atamfa Maroon da zanen manyan flowers pink wacca ta fito da hasken fatarta, mayafi mai ɗan girma pink ta yafa, Umma ta kalleta tace "sai kace zaki gidan biki, asibiti fa zamu", Hajar tace "Umma bafa kwalliya nayi ba, kaya kawai na canza, dan kuma zani asibiti sai nayi shiga hajaran majaran", Umma ta sake kallonta taga dai eh yanayin jikinta ne mai amsa. Hajar ta saka wayarta a handbag ɗin Umma ta ɗauki padlock a kan window, Huzaifa ne ya shigo wanda yazo hutun session daga FUD, cike da ladabi ya gaishe da Umma, Hajar tana gama rufe ɗaki da padlock ta gyara mayafinta ta gaishesa, Hajar da Umma suka wuce, Maama ta yaye labulen ɗakinta tace "uwarka ce ita kake gaisheta?, nace Uwarka ce iyee?, wllh kai da Nasiru da badan a gida na haifeku ba da na rantse na kuma rantsewa canje akaimin a asibiti", ya girgiza kai ya shiga ɗakinsu. Hajar da Umma suna isa Hospital suka bi dogon corridorn da zai kaisu ward A, Umma ta murɗa ƙofa ta shiga da sallama, masu jinyar patient dinda take gadon farko suka amsa mata, tayi musu ya me jiki kana ta fara duba gadon mara lafiyar da suka zo dubawa, Hajar da take biye da ita ta hango Anty Jamila daga can gefen gadon ƙarshe na ward din, Hajar tace "umma ga su can", bayan sun gaisa ne suka duba Wasila wacca take matsayin cousin ɗinsu Umma, Hajar dai gefe ta koma suka jone da Hafsa, Umma ta kalli Anty Jamila tace "waye a wajenta", Anty Jamila tace "Amina ce, tin ɗazu take sintiri zuwa wajen Nurse ɗinda tace ta ringa bibiyarta sbd likitan da zai dubata tin safe ake jiransa baizo ba", Umma ta kalli Wasila da take jin jiki tace "yanzu tin safe likitan baizo ba, wannan wane irin rashin tausayi ne, kai Allah ya gyara mana ƙasar mu", Anty Jamila tace "Ameen", Nurse Jidda ce ta shigo ta duba Wasila tace "ya ƙirjin har yanzu yana miki zafin?", Wasila ta jinjina kai alamar eh, Nurse Jidda tace "Sorry, insha Allah yanzu doctorn da zai dubaki zaizo" ta fita daga ward din, Hafsa ta kalli Hajar tace "wllh Nurse ɗin nan tanada kirki, a yadda Nurses suke zabga rashin mutunci ga patient ita dai banga tayi haka ba", Hajar tace "naji Anty ɗazu tana cewa wai likita baizo ya dubata tin safe ake jiransa?", Hafsa tace "eh muma wajen 1hour kenan da zuwan mu ana jiransa", Hajar ta taɓe baki tace "uhmm wannan rashin sanin darajar ɗan Adam ne...", wani ƙamshi wanda ba baƙonta bane ta shaƙa wanda ya katse sauran maganar bakinta daga fita, Nurse Jidda na leading dinsa har ya iso gaban gadon ya kalli Wasila with care, few minutes ya gama aikinsa, Hajar da ta gama fahimta shine likitan da ake jira tin safe ta juya idanunta akansa tana so ta tuno inda tasan wannan fuskar, coily hair dinsa da kuma ƙamshin da ta fuskanci nasa ne yasa kwanyarta ta amsa, a take ta ganesa a zuciyarta tace (no wonder, wllh an cuci doctors), kasa ɗauke idonta tayi daga kansa tana yamutsa fuska, Dr Uthman ya kalli Nurse Jidda yayi alama da hannu, tace "yess doctor". ya juya zai bar wajen sai kuma ya juyo ya kalli wajen da tin shigowarsa yaji kamar an zuba masa arwa, a take idanunsu suka sarƙe, ya ƙanƙance nasa, yayi wani slight smirk ya juya da tafiyarsa, Hajar taji cewa itama yanzu ne ya kamata ta rama abinda yace mata rannan, da sauri ta miƙe ta wurgawa Hafsa wayarta a cinya ta zura takalmi, Umma tace "ina zaki?", tana tafiya tace "yanzu zan dawo" ta fita daga ward din da sauri sbd karya ɓace mata, long corridorn ta tsaya tana kallo, ta kalli hagu taga bata hangosa ba, tana kallon right taga har ya kusan fita daga block din, ta daka tsaki tace "sauri sai kace lantarki" ta bisa da sauri-sauri gudu-gudu, ai kam har ya fita daga block ta cimmasa, railern stairs ta riƙe tace "ɗan dakata Doctor", the voice sound familiar and the name inkiyarsa ce a hospital, these two reason make him to turn around, kallon 1sec yayi mata ya zuba hannayensa a pocket ya juya zai cigaba da tafiyarsa tace "Fake doctor, i think the name fit you, wanda baisan darajan ɗan Adam ba bazai zama real doctor ba saidai Fake", tinda yake bai taɓa encounter da trouble maker irin wannan little girl din ba, kuma ko kaɗan baiji zafin maganar da ta gaya masa ba saima ya tsinci kansa da yin murmushin gefen baki sai kuma ya juya da nufin kallonta, amma tini har tayi nisa da barin wajen tana tafiyarta cikin nutsuwa.
★Biki bidiri bireɗeɗe, saura 1week cif aka fara gudanar da shagali, Ruqayyah dai ba tay wani event ba duk tace bata buƙata, Nurain kam ya sakar mata bakin aljihu duk abinda ta tambayesa sai yace gashi indai money ne, ranar juma'a ne ɗaurin aure, ranar Alhamis aka daki mother's Eve tare da kamun amarya, Ruqayyah ta fito daga toilet bayan tayi wanka ta wanke nude make-up din da aka mata ta mother's Eve, friends ɗinta su huɗu ne a ɗakin, Meema ce ta miƙo mata wayarta tace "it has been ringing for a while", Ruqayyah ta goge hannunta da yaji jan ƙunshi a jikin farin towel ɗin data ɗaura sannan ta karɓi wayar, wani kiran ne ya sake shigowa da ringing tone ɗinda tayi setting musamman sbd Nurain, murmushi tayi ta kara wayar a kunne, ajiyar zuciya taji ya sauke kana yace "ina kika shiga ne?", tayi wasa da kwayar idonta tace "ina kam zan shiga", yace "Ohk, sleep tight for today, tomorrow in my arms", ƙit ta kashe wayar ta harareta, ta dannata a silent sbd tasan definitely sai ya sake kira, kolacca mai sanyi ƙamshi ta ɗakko ta murza a jikinta sannan ta ɗela gado ta rufa da duvet, wayarta ta danna taga message from dearest, da sauri ta mayar masa da reply, few minutes saiga wani saƙon nan ya sake shigowa, ta mayar da reply, a haka dai sukay ta tura text message har basu san dare yayi sosai ba, text ɗinda ya shigo na ƙarshe hopping daga Nurain yake sai taga akasin haka. minti goma ta ɗauka tana karanta message din, a hankali ta tashi zaune ta kalli agogon wayarta, 3:00am passed, Meema da sauran friend ɗinta duk sun sheme. a hankali ta sakko daga kan gadon ta kunna fitilar wayarta sbd idan ta kunna ta ɗakin haske zai iya farkar da wani wanda a halin yanzu bata son kowa yasan abinda take shirin aikatawa sai zuwa gobe da safe tinda dole a sani. press din kayanta ta buɗe, gaba ɗaya kayanta masu kyau an riga an shirya mata su a box, waɗanda suka rage duk wanda bata buƙata ne na bayarwa, gashi box ɗin tana ɗakin Momy. sleeping gown din jikinta ta cire ta saka wata Abaya wacca ta Meema ce, cikin sanɗa ta fita a ɗakin ta wuce na Momy, a hankali ta murɗa handle ta shiga cikin sanɗa, ta haska fitilar wayarta ta buɗe box ɗin da kayanta suke, 5sets ta ɗiba ta zazzage jakar kayan Kulsum elder sister ɗinta ta zuba a ciki, ta ɗauki jakar ta fita, A palour ta ajiye jakar a kan kujera sai kuma ta juyo ta koma ɗakin Momy, bedside ta janyo a hankali ta ɗakko Jotter da biro tayi rubutu, ta yage papern ta soketa ajikin lamp sannan ta mayar da Jottern, Momy ta motsa tace "waye a nan?", Ruqayyah tayi tsam sai kuma tace "Momy nice, nazo neman paracetamol ne zan sha kaina ne yake ciwo", Momy ta fara ƙoƙarin miƙewa daman bata daɗe da kwanciya ba kuma tin shigowar Ruqayyah ta farko taji ɓuruntu, Ruqayyah tace "Momy ki koma ki kwanta na samu a jakar Kulsum" ta miƙe ta fita a ɗakin jikinta na rawa. ajiyar zuciya ta sauke ta ɗauki jakarta ta fita compound, iyakarta kenan domin daga nan bazata iya yin gaba ba sbd gate a garƙame yake, can bayan wani ƙaton drum da ake tara shara ta koma ta raɓe, she spent almost 2 and half hours there kafin abinda tayi fako ya wanzu, a kan idonta Daddy ya buɗe gate ya fita Masallaci Sallahr asuba, and she used that as an opportunity to fulfilled her mission...........✍️
💛 HAJAR 💛
by Feenerh_feeche
{11...}
★Da misalin ƙarfe bakwai da arba'in na safe, Hajar ce zaune a gaban rariya tana rege waken kulele, a hankali take humming song tana aikinta, Naseer ne ya shigo hannunsa riƙe da damin doyar da ya siyo a Zaria, Hajar ta amsa sallamarsa tace "yaya sunnu da dawowa ya hanya?", yace "lafiya hajara" ya ƙarasa ciki, damin doyar ya ajiye a ƙofar ɗakin Baba kana ya shiga ciki, Naseer ya kalli Baba ganin yadda ya rame sosai, ya samu waje ya zauna suka gaisa, Baba yace "har kun juyo?", Naseer yace "Eh, sai gobe Insha Allah zanyi lodin Lagos", Baba yace "to Allah ya taimaka", Naseer yace "ga doya nan na shigo da ita", Baba ya saka masa albarka tare da addu'ar Allah ya ruɓanya masa, Naseer yace "Ameen, bari na shiga na gaida Maama" ya miƙe ya fita daga ɗakin, a ƙofar ɗakin Maama ya tsaya yayi sallama, shiru yaji ba a amsa ba ya sake yin wata sallamar nanma dai shiru, ya ɗan yaye labule ya leƙa, Maama tana zaune ta miƙe ƙafa tana karkaɗata, Nabilah tana kwance a kan gado tana bacci kamar mushe don ko sallar asuba ba tay ba, Maimuna kuma tana shafa man bleeching a fuska ta dauɗe kunnuwanta da earpiece, ido huɗu Naseer sukay da Maama wacca take kallon ƙofar kuma tana jinsa tayi burus, takalminsa ya cire ya shigo ya samu waje