Showing 42001 words to 45000 words out of 95238 words
Chapter 15 - BAKON MUNAFIKI!! (BA NA MUTUM DAYA BANE) NA NANA HAFSATU MISS ZOZO.txt
Kai parking lodge din.
Motar Habibi Talba ce agaba sai tashi a baya... Amaal na ganin motar malamin nasu tache,
"Gashinan yazo.. Na je?"
Hindu ta daga Kai ta haska mata harara.. Ta shiga gyara mayafin ta tana mayar dashi gefe..
"Baby H?" Cewar Habib Talba daya fito daga motar yana takowa wajen su. Idanun sa akan Hindu.
"Na'am Habibi..... "
Amaal na ganin sun hadu ta sulalae zata tafi.... Ashe Habib Talba ya hango ta,
"Zo nan..."
Ta waiwayo tana nuna kanta
"Ni?"
"A'ah.... Ni"
Komawa tayi kanta a kasa tace,
"Ina kwana?"
"Lafiya...wait tare na ganku kunsan juna ne?" Ya nuna amaal yana tanbayar Hindu..
"Step sister din sisters dina ce...."
"Omo...." Habib Talba ya fada yana smirking face
Amaal ita ko ajikin ta fatan ta su kyaleta ta tafi .
"Lecture na sai nan da one hour so kafin nan bari muje can mu zauna ko... "
"Sure... Why not?"
"Okay... Yauwa kinga ga motar aboki na can ki bashi key din nan kice ya jirani a office idan nagama zan zo sai mu wuce.."
"Okay tohm." Amaal ta saka hannu ta karbi mukullin.
Kai tsaye ta nufi motar.. Sai kallon motar take kamar akwai ire iren su a agidah. Wata zuciyar ta bata amsa da
"Ai ba dan ku kadai aka kera ba..."
Motar ta nufa ta kwankwasa ..yana danna waya ... Batare daya daga Kai ya dubi me kwankwasawar ba azaton sa habibi abokin sa ne. Ya sauke mudubin kasa,
Ta zura hannu ta mika mukullin cikin zazzakar muryar ta tache,
" Gashi inji Malam Habibi... Zan nuna maka office dinsa wai ka jira shi idan ya gama zai zo ku tafi..",
Cikin daga kai da sauri domin muryar ta na shige da wadda ke sanya shi nutsuwa ya daga kai kenan ya sauke akan kyakkywar fuskar ta.....
_ADVERT๐_
_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_
_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._
_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._
_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_
_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_
_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_
*_MATSO KIJI_*๐๐ผ๐๐ผ๐๐ผ๐๐ผ๐ฅ๐ฅ๐ฅ๐ฅ๐ฅ๐ฅ
*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*
_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR โKASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at๐
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan๐
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan๐
09033181070
VIP๐ฅ๐ฏ
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*๐ฅฐ
Zafafa๐ซถ๐ฅ
[9/9, 12:24 PM] Hafsaat๐: _BAKON MUNAFIKI_
_(BA NA MUTUM DAYA BA NE)_
_NA:_
_NANA HAFSATU_
_PAGE: 28_
_BM vip arewabook: https://arewabooks.com/book?id=64a96774d6e097b6d856cfb9._
___
Kanta a gefe ganin bai karbi mukullin ba wulakanci ne ko bai ji bane ga lokacin lectures dinta na kurewa.. Hakan ya sa ta juyar da kanta tache,
"Ga shi inji Malam Habibi....w...,
Ta nemi labbanta da kasa furta sauran kalmomin da zasu karashe zancen...
Sai kache ba shine ya gama kalleta ba. Yadda ya hade fuskar sa ya fuzge mukullin kamar fadaa ita lamarin nasa ma sai ya fara bata tsoro kuma ganin kamar yaga wata dodo..
Bude murfin motar yayi... Ya koma ya rufe yana wani shan kamshi. Ita dai ganin yayi kamar be santa ba yasa ta juya tayi gaba ..
"Baki iya gaisuwa bane....?"
Ta jiyo muryar sa a bayan ta... Tana cigaba da tafiyar ba tare data jiyo ba tache,
"Ina kwana...?"
"Yana gidan ku ...."
Tabe baki tayi... Dama tasan salon ya gasa mata magana ne.. Har office din ta rakashi tache,
"Gashi...."
"Zo nan...."Ya kira ta ganin ta juya zata tafi,
"Dan Allah... Zan makara a lectures ne " ta fada tanata rau rau d idanu muryar ta a sanyaye a kuma shagwabe kasancewar haka take magana amman wani sai ya dauka yanga ce...
Ya samu kansa da son sake jin muryar tata... Yana wani muzurai yache,
"Wato kula maza kike ma ko?"
"What?"
"Oh yes.... Da kawar ki Habibi yake magana right?"
Takaicin tambayoyin sa tamkar ta daka tsalle ta sharara masa mari. Kasancewar shi din dogo ne sosai ya fita tsawo. Duk kuwa da ita dinma doguwa ce... amman ya kere ta a tsawp
"Tambayar ki nake.... Ko anan ma rashin kunyar zaki mun ne?"
"Kayi hakuri... Ni ba rashin kunya nake maka na... Sauri nake zan shiga lectures dan Allah..."
Har ya zura mukulli zai bude kofar office din sai kuma ya fasa... Yana takawa wajenta tana ja baya... Har ta kai karshen bango. Gabanta na tsananta bugawa tamkar zai fado. Gashi tayi masa kyau tamkar ya rungumeta da halal dinsa ce...
Ya saka hannu daya ya tokare ta.... Ta juyar da fuskar ta gefe... Kamshin turaren jikin sa na Tom-Ford ya gauraye ta baki daya..
Kasa kasa yace,
"Baki bani amsar tanbaya ta ba.... Kula maza kike ko?"
"Dan Allah ka k.....
Bata karasa ba wayar ta tafara ringing. Tayi haka zata dauka yayi sauri ya wafce ya matsa gefe ta bi shi tana rokan sa,
"Dan Allah ka bani wayata..."
"Yaya Hisham..... Waye Yaya Hisham? Kaf zuriyar Ardo kandemi bamu da Hisham... Ohh daya daga cikin samarin ki ne ko?"
"Yaya Hisham dan.... Dan aminin abbiey ne, Dan Allah kayi hakuri kaban wayata."
"Ai dole ki so na naki wayar ki saboda samarin ki kala kala.... Waya sani ma ko habibin ma saurayin ki ne"
"Ni malami na ne... Sannan ba wata kawata da ke kula shi. Wadda kake zaton ko kawata ce suke tare ba kowa bace fache Yaya Hindu.."
"Hindu?"
"Dan Allah kaban wayata..."
"Je ki lectures din ki dawo..."
"Dan Allah kayi hakuri ina amfani da ita a lectures wajen browsing. Dan Allah kaban wayata"
"So kike kawai na baki kiyi waya da beloved dinki Haysam"
"Hisham.."
"Oh harda gyarawa? wato na furta sunan saurayin ki ba dai dai ba ko?"
Langabar da kai tayi... Kanta a kasa tace,
"Ka bani wayata... Please"
"Magana zaki gaya mun?"
"Ni ban isa ba"
"Gashi nan karan kada miya dan abokin bappah ma kina ce masa yaya.ban cancanci ki kirani da yayan ba sai wani ka ban waya ta.... Ko dan kinga kin fara girma? Kina shiga cikin yammata? Ko kin dauka nima Ina cikin admirers dinki kamar Aayan?"
"Kayi hakuri...." Ta shiga bashi hakuri don dik bata ga abunda yayi zafi dazai dinga ga samata maganganu ba..
"Yauwa karki dauka nima ko irin Aayan ne me rawar jiki akan ki... Ko a kafa aka dauran ke sai na kunche..You're not my type, not even close. ...... "
Kasa cewa komai tayi... Tsananin kiyayyar da yake mata yayi yawa.
"Yauwa gwara ki sani don renin na ki yayi yawa... Ko mata sun kare ni Al-mustapha ba zan taba iya soyayya da ke ba.... Baki da abunda nake so a mache ke baki ma cika macen ba. Yanzu kike tasowa. Kina Wani ji da kan ki...
Bai karasa ba still kiran Hisham ya sake shigowa.. cike da takaici ya cilla mata wayar ta dauka da sauri zata tafi ya daka mata tsawa,
"Ke..."
Tsayawa tayi. Amman zucjyar ta sai ta kasa hakuri. Hawayen data ke makalewa na cin nutincin daya ke ta mata ne suka fara zuba a kyakkywar fuskar ta.
"Dan Allah kayi hakuri .... Yaya Al-mustapha!! Zan shiga lectures." Tana karasa fada tayi gaba sam taki waiwayowa tana ji yana sake daka mata tsawa tayi banza da shi...
Yaci mata mutinci akan lefin data basan na meye ba... Ya tozarta ta akan hukuncin da shi kadai yasan kan sa.. Ya gasa mata maganganu akan fadan daya kirkire shi haka kawai ba tare dama sanjya ba...
Haka ta karasa Ardo kandemi auditorium (one thousand sitters) inda zasuyi lectures. tana tafe tana tsiyayyayar da ruwan hawaye...
Agaban auditorium din taci karo da kawayenta su biyu a tsaye da sauran yan ajin... Suna ganin ta suka tako wajen ta
"Ke meye haka....kukan me kike?" Hafsat kawarta ta tanbaye ta
"Ai shine... Babes meya faru? Ko menstrual cramps kike?" Cewar Zaarah dayar kawar ta su..
Bata amsa su ba ta dubi sauran mutanen wajen tace,
"Ya haka? Ina lectures din?"
"Ke mike jira dama... Wai baze samu zuwa ba ya bada handout aje ayi karatu zeyi open test next class din sa...."
"Alhamdulillah....." Ta sauke katuwar zuciya tana goge hawayen
"Wait..... Gurlll. Karki cemun akan lectures kike kuka?"
"Hakane ma.... Zaarah kin gano ta."
Murmushi tayi jin abunda suka fada. Maganar da Al-mustapha ya gaggaasa mata suka sake zuwa mata kai... Ta girgiza musu kai kawai tache,
"Ko daya....thou rasa lectures dinma ya dameni. Na dauka an shiga..."
"Zo nan ki wassafa mana labari... " Suka ja hannun ta suka koma wajen wasu kujeru suka zauna,
"Meya faru....?"
"Plss babes"
"Kun cika damuwa wallahi.... Allah ba komai.. Ba wani abu"
"To fada mana koma menene dai..."
"Ni da ...."
"Yaya Hisham...?"
"Bassam?"
Dariya sika bata yadda suka fara fado sunaye... Ta girgiza kai kawai.
"To waye please?"
"Ni da Yaya na ne...."
"Mts... Shine kika kuka? Ai dama wasu yayyun maza haka suke sai a slow.."
"Chill babes.... Komai mai wucewa ne... Bare fadan yan uwa baya karewa idan ba aure kayi ka bar musu gidan ba."
Dariya tayi kawai tana kada musu kai alamun tohmmm...
"Muje gashassh suya muci abinci kafin next lecture din ko?" Cewar Zaarah kawar su.
"Yauwa daman Ina craving tsiren kodar nan.." Hafsat ta fada tana rataya jakarta
Amaal ta mike tsaye suka nufi gashash suya and cafe dake cikin jami'ar ta su..
__
__
Tana tafiya ya saka hannun sa ya naushi bango cike da jin haushi kansa da kansa...
Ya akai wadannan maganganun sika fita daga bakin sa? Babu dadi abunda ya mata gaskia..
Gashi ba zai iya bin ta yaba ta hakuri ba... Ya nufi inda yaga tayi ta bache masa da gani da alama da sauri tabar wajen..
Jikin sa a sanyaye ya saka mukulli ya bude ofishin ya shiga.. Mema kwan ya zauna sai ya nemi bango ya jingina da shi ya daga kansa yana tunanin bakaken maganganun daya gasa mata...
Abunda zuciyar sa take son fada daban .... Wanda bakinsa da labban sa suka furta daban..
Ya saka hannu ya dafe kansa yana jujjuya shi...
"Goddamn it!!!..... Kayi shirme Al-mustapha... Kayi shirme"
Knocking office din akayi sai kuma ya turo kofar ya shiga.. bakin sa dauke da sallama...
"Ahh... Guy kana Ina ne?" Ya shiga dube dube..
Ya juya zai rufe kofar ya lura da Al-mustapha ya rakube a bangon bayan kofar kansa a sama ya lula duniyar tunani....
"Maza... Meye haka?" Ya tambaye shi yana girgiza kafadar sa..
Sai a sannan Al-mustapha ya dawo daga duniyar tunanin daya tafi...
"Ka dawo?"
"Inata sallama ma na dauka baka man wallahi... Da niyar zan rufe kofar kuma sai na gano ka.. meya ke faruwa ne? "
"Bakomai... Kai na ne yake ciwo amma ya dena..."
Ya samu waje ya zauna... Shima Habibi ya zauna akan kujerar dake fuskantar wadda Al-mustapha yake akai...
"Ya kan yanzu?"
"Ya dena..."
"Yauwa ma shaa Allah... Kaga yarinyar data rakoka office dinnan?"
Al-mustapha ya muskuta ya gyara zaman sa yana kallon habubi Talba sosai,
"Yeah...what about her? Menene please.. eh?"
"Omo... chill! Kaga yadda ka gigice kuwa ..."
"Aboki na get to the point please.."
"Well.... Ni fa nayi mata... I want to wife her... Long story short ba wani kwana kwana maza so na ke na auri yarinyar nan ..."
Wayar sa dake hannun sa ce ta subuce ta fadi a kasa jin abunda Habibi Talba ke fada..
Habibi Talba da sauri ya dakko wayar yana kallon screen dinta,
"Kaci screen wallahi ta fashe... Meye haka?"
Al-mustapha ya karbi wayar ya jefata a aljihu yana duban Habibi Talba
"Kace me?"
"Malam wayar ka taci screen"
"Ba damuwa ai.... Amaal... Kasan Maryam Amaal ne?"
"Sunanta kenan?"
Wani dogon tsaki Al-mustapha yaja ya dankara masa lafiyayyar harara yace,
"Kaketa wannan dogon turancin da ko saninta bakai ba? That aside naga budurwar kache tazo kuna zance amma bata gaban ka kana planning auren wadda baka ma san sunan ta ba... Banza mahaukaci. Ka cika yaudara wallahi ", Ya karasa fada yana mai jan dogon tsaki..
"Look.... Naji kache sunan ta Maryam Amaal... A'ina ka santa?"
"Kai a'ina ka santa?"
"Student dina ce mana..."
"Ni kuma cousin dina ce... First cousin ma kuwa"
"Shikenan... Yaya Al-mustapha... In-law... Dan Allah kabani ita"
Al-mustapha ya daga kai ya sake hararar sa yana girgiza kai,
"Kacika kule kulen yammata"
"Wai waccen yarinyar nacacciya datayita kirana har yau na amince muka hadu? Maza wallahi bata gabana.. tun a Instagram take bibiyata kasan tsawon shekarun da take nace mun kuwa? Bamu taba haduwa ba sai yau shima gajiya nayi da nacaccen nacinta tacika stalking yau dai na ce sai dai tazo my hadu ni bazan samu zuwa ba.. tana ta roko na shine fa tazo..."
Al-mustapha ya taba baki yana yamutsa fuska,
"Ka yarda dani mana... Yauwa sannan tare suke ma da ita Maryam Amaal din"
"Kawarta ce ko?"
"No... Not really... Baby H din tace amaal kanwar kannenta ne da suke uba daya...yadda na lura kaman amaal din agidan su baby H din take a zaune ko? I dunno dai...cuz inata tanbayarta akan Amaal din taki bani amsa kaman basa good terms haka.. kasan mata one can't tell... "
Al-mustapha yayi shiru yana jujjuya sunan wai baby H...
"Wai Hindu?"
"Exactly... Amma dai da baby H na santa"
"Okay...."
"Kasanta?"
"Well... Yar uwata ce dai itama... Amma ba kaman yadda muke da amaal ba... Duka dai agidah daya ake under same roof.. Amma dai ita Hindu din itace ke agidan su Amaal din"
"Woah.... Amma ita meyasa take haka?
"Bangame take ba? Me kake nufi.. oho dai matsalar ku ce kai da ita... "
"Ni fa kade na hadani da ita wallahi bana son ta."
"Amma kai banza ne wallahi . Baka santafa kache.. akan wane dalilin tataso tazo har wajen ka?"
"Daya daga cikin abunda yasa bana son ta kenan ma... Batada kamun Kai... Kicewa saurayi ko'ina yake zaki zo ki same shi bakya jin fargaba? Na biyu kizo da wata iriyar shiga dake nuna tsiraicin ki awaje? Na uku tasaka wani seductive turare saura kadan nayi aika aika Allah yatemaka wallahi korarta fa nayi... Could you imagine.... Tana saka hannu tana wani tattaba ni... Tana macen? Ina martaba da kimar ta suke? Wai ahaka kake tunanin zan zabeta komai awaje ga Amaal dake killace jikinta da komai nata yarinya me nutsuwa da hankali? Kai nifa nayi mata wallahi.... Ka gayawa su Bappah zan aiko manya gaskia... Aurenta kawai nakeson yi ba sai an dau wani lokaci ba..
Al-mustapha ya mike bayan ya girgiza masa kai kawai,
"Meye haka muna magana?"
"Office zan tafi mana..."
"Magana mike fa akan Amaal kanwar ka . Da nake so da aure"
"An bada ita tuntuni...."
"Bangane ba...?"
"Ina nufin an bawa wani auren ta tun tuni..." Yana karasa bashi amsa yayi gaba abinsa
Habibi Talba yabi bayan sa yanata kiran sunan sa..
"Aboki na sai mun sake magana... " Al-mustapha ya fada yana mai bashi hannu sukayi musabaha
Wani malami da zai zarta su a shekaru yazo wucewa suka tsaya suna gaysawa...habjbi talba ya nuna Al-mustapha yana cewa da dayan malamin,
"Shine amini na da nake gaya maka fa... Architect Al-mustapha jalaludden........
...
_ADVERT๐_
_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_
_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._
_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._
_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_
_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_
_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_
*_MATSO KIJI_*๐๐ผ๐๐ผ๐๐ผ๐๐ผ๐ฅ๐ฅ๐ฅ๐ฅ๐ฅ๐ฅ
*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*
_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR โKASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at๐
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan๐
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan๐
09033181070
VIP๐ฅ๐ฏ
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*๐ฅฐ
Zafafa๐ซถ๐ฅ
[9/10, 10:09 PM] Hafsaat๐: _BAKON MUNAFIKI_
_(BA NA MUTUM DAYA BA NE)_
_NA:_
_NANA HAFSATU_
_PAGE: 29_
_BM vip arewabook: https://arewabooks.com/book?id=64a96774d6e097b6d856cfb9._
---
Habibi Talba ya saka hannu ya dafa kafadar malamin ya cigaba da cewa,
"Al-mustapha wannan shine architect kuma Dr, Aliyu da nake gaya maka guru ne a faculty din nan... Shine overall best kaman kai.."
Al-mustapha yayi murmushi... Shima Dr. Aliyu murmushin yayi... Suka hada hannu suka sake gaisawa,
"To Dr.. Aliyu da Habibu sai na sake zagayowa in shaa Allah.."
"Zakaci uban ka idan ka sake cemun Habibu na gaya maka sunana Habibi banason wulakanci.. alright sai nazo sake ganin sabon office in shaa Allah..Allah yasa an bude a sa'a Allah kuma ya sanya alkhairi."
"Allahumma Aaameen.."
"Toh Arc.. Al-mustapha sai anjima.." Dr Aliyu yayi masa sallama.. ya bawa habibi Talba hannu suka sake gaysawa ya shige ciki...
Shi kuma Al-mustapha ya shiga cikin mota ya zauna zai bar wajen .. Habibi Talba ya sake zura kansa ta glass.. ya saka hannu ya tokare da hannuwan sa duka biyu,
"Meye ne?" Al-mustapha ya tambaye shi cike da kosawa,
"In-law please .."
"In-law din uban ka?"
"Aboki na please hear me out... Allah ba da wasa nake ba inason Maryam Amaal kaga yadda malamai ke admiring nata kuwa? Kasan beauty with brains ce wallahi.. komai ta hada .. "
"Okay bama kai kadai bane kenan kuna da yawa?"
"Kwarai haramun ne?"
"Amma anyi mutanen banza masu son daliban su"
"Lefi ne?"
"Dalla matsar da hannuwan ka zan tafi ni."
"To wai kai ba abun farin ciki bane ace kanason kanwar ka?"
"Matsa na wuce Malam..."
Habibi Talba ya bude baki can ya saka hannun sa ya rufe baki yana nuna Al-mustapha da yatsa..
"Menene?" Al-mustapha ya tambaye shi yana tada motar da key..
"Ko son ta kake ne?