Showing 87001 words to 90000 words out of 95238 words
Chapter 30 - BAKON MUNAFIKI!! (BA NA MUTUM DAYA BANE) NA NANA HAFSATU MISS ZOZO.txt
fa daya fara kokarin suje su kwanta zata fara kuka tana rokon sa ya yi hakuri don tsoro da fargabar daren farkon su ya da'daa mata a zuciya.
Sai dai Al-mustapha ya dan rage zafi da Yan wasu abubuwan na jikinta har ya samu nutsuwa. Gashi yana matukar bata tausayi sam kuma baya mata dole. yadda take so din haka yake biye mata... Ta sake tabbatarwa da lalle yana kaunar ta sosai...
Rannan ya dawo daga office kamar ko da yaushe ta tare shi tayi masa sannu da zuwa ta kawo masa abinci ta tara masa ruwan wanka yayi komai.
Lokacin bacci nayi ya fita kan zai sayo maganin mura dana zazzabi. Bayan ya futa ya dawo kansa na masa ciwo.. Amaal duk ta rude ta rasa inda zata saka kansa. Tanata bashi kulawa harda hawaye.
Ganin hakan yasanya Al-mustapha sake marairaicewa kan magashiyan fa bashi da lafiya sosai a dole, kwanan sa biyu yaki zuwa ko kofar gidah.
"Ina ne kuma yake maka ciwon yanzu?" Ta tambaye shi da damuwa shimfide a fuskar ta..
"Kai na da kafafu na..." Ya sake langabewa..
Amaal duk ta gigice tace,
"Sannu Allah ya baka lafiya mai dorewa ko su Hajiya zaa gayawa ne dan Allah ?"
Ya kamo hannunta da sauri ya dora akan kirjinsa yana runtse idanu yace,
"Zan warware ba sai an kira kowa ba. Idan ma sika zo zasuce depression dina ne meye dalilin daya jawo damuwar... Kingane?"
Amaal ta daga Kai da sauri tana raba idanu... Ashe kenan tashin ciwon nasa lefin ta ne..?
"Sannu.."
"Yauwa..."
"Me kake so yanzu?"
"I want you Maryaam..... Please" Ya fada yana sauke numfashi ...
Shiru tayi.. gabanta ya tsananta bugawa. Ya saka hannun sa akan saitin zuciyar ta yana jin yadda yake bugawa da sauri..
Ya sake kankameta yana shafa kanta,
"Banason shiga damuwar ki ko ya ya ne Maryam.. yadda bugun zuciyar ki ya sauya ya sani shiga cikin wani muwuyacin hali dan Allah kiyi hakuri da kalaman dana fada.. Maryaam ki yafe mun kaunar ki ce sanadi.. Dan Allah kiyi hakuri babbar kyauta da muhimmanci a gareni shine samun ganin kyakykyawar fuskarki. burina shine naga bayyanar fitar murmushi akan kyakykyawar fuskarki. Kuma ace nine sanadin yinsa . Inaso ki fahimci cewa burina a koda yaushe ki kasance cikin farin ciki... Dan Allah ki gaggawar cire damuwar hakan a ran ki... Wasu lokutan in ina tinanin ki Maryaam hatta sunana ban iya tunawa, soboda a sanda nake tunanin ki, babu abunda ke da mahimmaci kuma agareni sai ke... Maryaam bar sa damuwa a ranki... Ba don haka na ke kaunar ki ba ke din nake kauna ba wai kwadayin ki nake ba...Masoyiyata, ina son ki fiye da yadda kike tunani. Ina son kasancewa tare da ke domin kina farantawa zuciyata ko da murmushin ki ne kawai. Kallon ki kadai kan sanya in samu kuzari, duk wata kasala da lalaci in ji ta gushe. Ke ce farin cikina.. Maryaam har yanzu bakya so ko ya ya? Uhm...? Wifey..."
Fashewa tayi da kuka sosai ta kankame shi tamau.... Baki daya ita kanta haushin kanta take data kasa bayyana masa yadda take jin sa a ranta. Tana kaunar sa daidai misali ita din wacece da har zata hanashi abunda yake dole akanta? Kullum har sai ya rike ta amince dashi tukunna? Bai taba mata dole ba. Bai taba tauye mata hakki ba' Bai taba hantarar ta ba. Bai taba ko da bata ransa akan lefin tane. Adadin soyayyar sa yake bayyana mata zalla kullu yaumin..
"Here and now, let love express on my behalf what I feel for you. I love you more than love itself can offer. There are many ways to be happy in this life, but all I really need is you.. Maryaam kuka? Lle bakya so na dan Allah Maryaam ki bari na sallame ki kamar yadda kike muradi banason tauye miki hakki maryaam s...
Bai karasa ba ta kamo bakinsa ta sanya cikin nata. Sunbatar sa take cikeda nuna masa irin kaunar da ita din take masa ... Hawaye nabin kuncinan dukkanin su.. Ta janyo hijabin ta tazare gaba daya ta jefar da shi... Al-mustapha zai yi magana ta hana shi ta hanyar saka masa dan yatsanta tace,
"Kaine mafi tsuma zuciya da nishad'i mafi 'karfin kore damuwar zuciyata basu kasance a tare da ni ba sai bayan da na had'u da kai. Kai ne ka zamo tauraron da hasken sa yayi sanadiyar raba zuciyata da ba'kin duhun da ta dad'e a ciki. Had'uwa da kai ya kawo canji mai yawa a cikin rayuwata. .Tunda nake a rayuwa ta, ban taba zaton zan shiga irin farin cikin da nake ciki yanzu ba. Soboda kai, na daina shiga damuwa, Har ila yau ina kara godewa ubagiji da ya hadani da miji wanda na dade ina mafarkin samu. Na dade ina rokar ubangiji da ya nuna mun irin wannan rana da zan sami miji wanda zai soni irin soyayyar da bazai iya misaltuwa ba kuma nasamu...When I look into your eyes, I can see a reflection of the two of us and the life I hope we’ll share. I know you’re the only one I want to share the rest of my life with... Ina kaunar ka irin kaunar da baki yayi kadan wajen furtawa. Ina kaunar ka irin kaunar da alkalami yayi kadan wajen rubutawa.. Ina kaunar ka irin kaunar da zuciya keyiwa rai.. rai keyiwa gangar jiki. Ina kaunar ka sosai Al-mustapha na...."
Gaba daya ya gigice zaiyi magana tayi saurin sake hade bakunan su waje daya... Ta kashe side lamp ta zare kayan jikin ta ta jefar. Ta fara zare nasa, Al-mustapha kamar almara yace,
"Maryaamu..."
"Sssshh I have the right"
Ya taya ta ta cire nasa kayan ... Taja musu bargo ta rufe su suka bude sabon shafin soyayya. Ranar dai Al-mustapha ya tabbatar maryamun sa dagaske tana kaunar sa. Domin ta nuna masa zallar kauna daren ranar.. ya samu gamsuwa fiye da yadda yake tunani. Sai shi mata albarka ya dinga yi. Domin daren ranar sun gurji soyayya tsmkar cin Kwan makauniya. Lamarin sai fatan Allah ya basu zaman lafiya da kaunar juna da yalwar arziki.
::::::
Ko da safe ma hakan ce ta kasance. Al-mustapha mamaki ya cinye shi gaba daya. Domin yadda maryaam ta saki jikin ta da ranta tamkar ba ita ba. Ya sharara son ransa..
Tare sukai aikin gidan gaba daya suka gyara ko'ina gwanin ban sha'awa tamkar da can din masoya ne.
Tanada lectures din rana... Direbobi kuma kowanne an aike shi. Gashi yanada meeting na gaggawa a lokacin. Sai Hamid ne ya temaka ya kaita makarantar har bakin department dinsu......
_ADVERT👇_
_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_
_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._
_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._
_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_
_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_
_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_
*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*
_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
_*BAKON MUNAFIKI!!!*_
_(BA NA MUTUM DAYA BANE)_
_👺🏡👩👩👦👦_
_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
_®️NANA HAFSATU (MSS XOXO)_
_AREWABOOKS:MSSXOXO_
_WATTPAD:MISSXOXO00_
_PG:50.. (FINALE/KARSHE)_
_________
***Har bakin department dinsu Hamid ya kai hancin motar sa ya sauke Amaal.
"Nagode sosai Yaya Hamid... "
"Allah ya bada sa'ar karatu kanwata. "
"Aameen Yaya... Sai na dawo"
"Toh sai kin dawo"
Fita tayi daga cikin motar bayan ta gyara zaman laffayar dake naade a ajikin tah.
Ta shige cikin department din nasu tana daga masa hannu yana daga mata.. Bai bar wajen ba sai da ya tabbatar ta shige ciki, sannan ya juya kan motar ya koma kan titin da zai sadakaa da wajen makarantar...
Dai dai wani garden bayan ka wuce department din su Amaal ya hango bayan wani namiji da wata mace. Namijin yana daaga wa macen hannu cike da faada yadda yake nuni da ita zaka san masifa yake yi sai watsa hannu baya yake yi..
Rage gudun yayi ya shiga tafiya a hankali da motar yana muskutawa gaba sosai... Kamar Hindu? tabbas ita din ce dai da wannan malamin na su Amaal don ya zo shi daurin auren ma.
Kafin Hamid ya karasa dai dai saitin su Habibi Talba yabar wajen bayan ya sake gaggaasawa hindun bakaken maganganu.
Ta tsugunna ta kife kanta da cinya tana kuka sosai harda shessheka.. Hamid ya samu zuciyar sa da karaaya don baki daya baya son sauraron kukan mace. Bayason yaga mace na zubar da hawaye musanman akan 'da namiji...
Ya fita daga cikin motar sa ya nufi inda Hindun ke tsugunne tana kuka..
"Hindu...." Ya samu kansa da kiran sunan ta karo na farkon a rayuwar sa. Domin basu taba magana ba.
Da sauri ta daaga kai... Duk azaton ta ko Habibi ne ya dawo ya bata hakuri. Kallon su ya sarke dana juna... Ta samu kanta da kasa dauke idanun ta daga kansa... Sanye yake cikin kananun kaya ya dora blazer akai. Ba karamin kyau yayi ba.. ita kuma tana cikin doguwar riga ta atamfa ta yafa dan karamun mayafi
Handkerchief ya zaro daga gaban rigar sa, ya saka yatsu biyu saitin fuskar ta ya murza su suka bada sauti ganin tayi kamar mutum mutumi,
"Snap outta it.... Ungo rike ki goge hawayen ki kinji...?"
Tabi hannun nasa da hankicin da kallo...
"Malam Ina ruwan ka da ni?"
"Wooo. I mean no harm Hindu... Daga temako? Haka kike dama?"
"Ni banason munafurci saura kaje ka gayawa su Abbiey kace ka ganni a haka.. Daman kun saba ai halin gado kuka dakko. Yi sauri kafi ruwa gudu kaje ka fada... Mtssss! Aikin kawai"
Hamid yayi murmushi yana girgiza kai yace,
"Na gano ma ba lefin gayen daya barki bane kece me lefi"
"Dalla Malam ware ka bani waje.. Ina ruwan ka? Kawai saboda shisshigi . Wait biyo ni kayi kenan tun daga gidah dama dan ka dau rahoto ka kai musu?"
Hamid ya sake yin dariya har yana rike cikin sa, Hadi da saka dayan hannun sa ya dafe bishiya.
Hindu ta kalle shi ta dalla masa harara tana yamutsa fuska ta cigaba da cewa,
"Naci dubu sai ceto. Kurwata kur wallahi nan gani nan bari... Wanda yayi gaba yayi gaba na baya sai labari. Shi zakaran da Allah ya nufa da chara ko ana muzu ana shaho sai yayi s....
Hamid ya sake fashewa da draiya. Ya tsugunna a saitin da take yana dubanta sosai yace,
"Akan me zan ke bibiyar ki Hindu...? Ina tunanin wannan shine karo na farko a rayuwata da magana ta fatar baki ta taba hadamu.... Amaal na kawo tanada lectures, An rasa direbobi kowanne yanada aiki... Menene hujjar biyo ki fisabilillahi kema inde ba zuciya da kika biyewa ba, Mai sake sake akan wani dalili gotai gotai da ni zan dinga bibiyar ki, Meye hadani da ke Hindu? Kamar wanda suka saba da har haka zata shiga tsakanin su?look! Abu na biyu wucewa nazo yi zan koma gidah sa sauketa da nayi kenan na taho kan titin nan na hangi bayan mace da namiji kamar suna fada dubada yadda ta baya naga yana watsa hannu yana nuni da yatsa... Macece tanada rauni kuma zubar da mutunci ne ace mace budurwa baliga suna sa'insa da namiji a bainar jama'a akan titi...."
"Toh Ina ruwan ka? Ba sai ka wuce ka tafi ba? Da kai akeyi? Wannan ai shisshigi ne da kankanba... Sai kayi wucewar ka kama hanyar ka na meye zaka tsaya har ka tako kafafu kazo saboda tsabar gulma....?"
Hamid ya sauke katuwar ajiyar zuciya ya sake gyara tsgunnen da yayi yace da ita,
"Koma meye hada ku kiyi hakuri... A matsayin ki na mace be dace kizo nan ki tsugunna kina zubar da hawaye akan wani da namiji ba, Shawarar da zan baki a matsayina na namiji shine ki dena zubar da hawayen ki akan namiji. Duk namijin dayaga kin damu dashi fiye da yadda ya damu dake Allah wulakanci zaki ta gani kala kala...."
"Toh Ina ruwan ka?"
"Shawara ta rage ga mai shiga rijiya hindatullah... Na bar ki lafiya"
"Dan shisshigi kawai"
"Allah ya baki hakuri... Kiyi hakuri ki yafemun shisshigi na ne yaja mun kam.. Amma fa ni haka nake bana gani nayi shiru"
Mtscew... Hindu taja tsaki tana tabe baki.. Hamid ya mike daga gurfanen da yayi ya nufi motar ya shiga ya tafi. Hindu tabi bayan motar da kallo tana hararar ta, Tamkar itace ta mata lefin...
"Dan Allah ki fita daga rayuwata wai ana dole ne? Wallahi bana son ki, Ba zan taba son ki ba. Karki kara kuskura ki zo waje na kina mace sam baki da class ba kida kamun Kai. Ki sani ke din bakya cikin jerin irin matan da ni Habibi Talba nake so... Wallahi da nayi soyayya dake ko auren ki gwara na mutu ba aure akai na kinji Allah ... Kuma wannan rana ta zama itace ta karshe da zaki sake zuwa ki neme ni Allah idan kika sake ko kika kirani a waya sai na zo wajen mahaifan ki na gaya musu su ja miki kunne ki fita a harkata.. Dumbass " ta shiga tunano kalaman da Habibi Talba ya gaya mata tana runtse idanu hawaye masu dumi suka shiga zuba daga idanun nata.
Jikinta duk ya mutu... Ji take inama a dauki ranta ta mutu kawai a lokacin saboda tsananin duniyar data mata zafi shikenan itada Habibi Talba ba haske ? Ba zatayi soyayya dashi ba kenan har ta kai ga sunyi aure?
"Wayyo Allah na" ta fada tana hawaye sosai..
Kiran direba ne ya shigo wayar ta ta dauka ya sheda mata da yana bakin department yana jiran ta...
Sai data sake bude sabon wani shafin kukan tayi mai isar ta, kafin ta katse hawayen ta ta nufi motar ta shiga yaja su suka koma gidah
Hamid yana tafiya a mota yana dariya. Shi gaba daya ma Hindun dariya take ba shi. Gefe daya Kuma maduakakin tausayin ta ne ya kama shi... Tabbas Habibi Talba bai kamata ya dinga wulakanta ta ba tunda tana kaunar sa... Akace ka so me son ka.. sannu a hankali sai ya bita da sigar lallashi ya rabu da ita cikin ruwan sanyi...Amma hayaniya da hargagiya sam babu dadi... Ita kuma yakamata ace ta san itadin macece akwai limit dinta. Babu namijin dake son mace marar kamun kai da bibiyar diddigi.. Son ma so wani sam bashi da dadi. Ka so a so ka shine magana.... Na turawa sukance one sided love/ unrequited love....
_______
*MARYAAM-AMAAL*
Central mosque suka je suka yi sallah, Sannan suka koma theatre don halartar dayar lectures din data rage musu..
Lectures din was boring... Gaba daya ba dadi. Wasu daga cikin daliban hira kawai suke, Wasu na ciye ciye, wasun su kuma mafi yawa bacci suke yi... Yayin da wasu ke ta latse latsen wayar su. Amaal na daga zaune tana jujjuya wayar hannun ta. kawayen ta kuma sun kifa kan su akan benci suna bacci...
Tunanin ta ya lula duniyar Al-mustapha... Idanuwan ta Al-mustapha kawai suke so su gani, Kunnuwanta daddaad'ar maganar sa kawai suke so su ji, Gangar jikin ta na son kasancewa da shi... Zuciyar ta na bugun rashin sa akusa da ita... Ran ta na kewar sa..
Message ta shiga ta rubuta masa sako da,
"Habiby...♥️Fatan kana lafiya? Ka ci abinci kuwa? Ina class lectures din very boring...Ina son ka. Ka kula min da kanka. kasantuwar mu a raye cikin ruhi guda d’aya ya sanya zuciyoyin mu bugawa cikin lokuta makamanta juna.. Honey bunny na♥️ Ina nan zaune cikin class amma zuciya ta tana tare da kai. Kai ne kawai nake gani na ji sanyi a cikinta. Ina nan ina jiran dawowar ka nayi kewar ka sosai..."
Tana gama tura masa ta shiga gallery. Hotunan su kawai ta shiga kalla tana zooming fuskar Al-mustapha... Murmushin fuskar ta sai fadaaada yake yi.
"Banza uwar son miji...." Cewar Zaarah kawarta da ta tashi daga kwanciyar da take ta leka tana kallon Amaal na zooming fuskar Al-mustapha.
Amaal tayi dariya kasa kasa kar malamin su ya jiyo su tace,
"Ai ba haram bane... Halaliyata nake kallo.. Nayi missing dinsa ne ba zaki gane ba"
"Kwata kwata fa 2 to 4... 4 to 6 ne damu amma wannan awoyin kadan har kinyi missing dinsa? Sannu Juliet matar Romeo"
"Ke... Ba zaki gane ba ne... Amma duk second daya sai na tuno Habibi na... Ina kaunar sa fiye da yadda kalamai da baki zasu bayyana miki..."
"Matsalar ku ce"
"Ahhh! No vex mana.. Zaki shiga daga ciki keda Uthman zaki bamu labarin zallar kauna"
Zaarah ta tabe baki tana yamutsa fuska... Suka fashe da dariya baki daya..
Al-mustapha na zaune a ofishin sa yana danna na'urar me kwakwalwa ta computer da ke gaban sa. Karar shigowar sako ya shigo wayar sa.. Janyo ta yayi ganin Amaal ce wadda ta turo hakan yasa shi yin murmushi tun kafin ma ya karanta.. Ya kwantar da kansa ajikin kujerar ya bude sakon yana karantawa yana lumshe idanu hadi da sakin tattausan murmushi, Yaja kasan leben sa yana hango hotan fuskar ta a zuciyar sa...
Sai da ya maimaita sakon data turo sau shida, yana yi yana komawa farko yana tisawa kamar wata hadda... Tukun sannan ya mayar mata da reply,
"Habibty.... My whole world ♥️♥️ Alhamdulillah, Na ci baby na, wani snacks