Showing 3001 words to 6000 words out of 95238 words
Chapter 2 - BAKON MUNAFIKI!! (BA NA MUTUM DAYA BANE) NA NANA HAFSATU MISS ZOZO.txt
BIYAR PAID NOVELS_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
_®️NANA HAFSATU (MSS XOXO)_
__AREWABOOKS:MSSXOXO_
_WATTPAD:MISSXOXO00_
_FREE PAGE: 003_
______________
*Yana* karasa fadar abunda zai fada ya juya don tafiya wajen tukawar ya zauna bayan ya bawa abokin tukinsa hannu sun gaysa.
"Amaal... Amaal.." mahaifiyar ta dake kusa da ita acikin jirgin ta dan tabo ta.
"Na'am! Hayateey... Magana ki ke?" Ta tambayi mahaifiyar tata tana sosa idon ta daya da yatsanta na dama da ke mata kaikayi.
"Gyara kwanciyar taki zaki, kin bata kwanciya kin fara munshari."
"Wai har bacci ya dauke ni Hayateey?"
"Chab! Muna shigowa kina zama ai kika fara baccin."
"Tun safe nake jinsa naki komawa saboda inason sayo rigunan nan."
"Na gaya miki kar ki sake maimaita abunda kikayi yau ko?"
"Eh Hayateey."
"Yauwa banason neman magana. Kiyi kokari idan Allah ya sauke mu lafiya kije ki roki gafarar mahaifin ki."
"Hayateey. Abbiey yasan da zuwana mart din fa."
"Bata lokacin da kikai achan badan Allah ya temaka pilot din bezo da wuri ba ai da tuni munyi missing flight."
Dan rau rau tayi da idanu, Ta kara saukar da kanta kasa. Ahankali tamkar mai rada tace,
"Garin sauri har wani bakin balarabe na zubarwa milkshake a jikin sa."
"To Allah ya kyauta ya tsare gaba."
"Amin."
"Sai ki dinga lura kina tsayar da hankali waje daya idan kina tafiya. Tafiya ba nutsuwa ai dole haka ta dinga faruwa. Kin dai bashi hakuri ko?"
"In shaa Allah! Eh na bashi." Kasan zuciyar ta ta tuno yadda ya chusa mata tissue papers din a bakin ta. Ko sauraron ta bai ba kuma yayi gaba...
"To Allah ya kiyaye gaba."
"Allahumma Aameen."
"Kwanta tunda baccin ki ke ji."
"Tohm Hayateey nagode."
Gyara kwanciyar tata tayi ta dau wani abu dake gefen kujerar ta rufe idanun ta da shi. Hadi da jan wni kawataccen abu kaman asaberi ta rufe windown setin ta. Ba dadewa kuwa bacci yayi awon gaba da ita.
°°°°°°. °°°°°.
Sun dau awoyi a sama kafin Allah cikin ikon sa da buwayar sa ya sanya jirgin su ya sauke a filin jirgi na tashi da ke babban birnin Abuja Nigeria.
Haj. Jameela ta saka hannunta akan Amaal tana dan bubbugun bayan Amal din.
"Tashi mana..."
"Hayateey bacci nake ji sosai"
"Wane bacci bayan mun sauka. Tashi mana."
Ahankaki tashigaa bude manyan idanunan ta sauke akan mahaifiyar ta dake kokarin mayar da takalman ta sau ciki.
"Amaal."
"Nàm Hayateey."
"Tashi muje."
"Tohm..." Ta sake fada tana murza saman idanun ta.
Cikin saka hannu a baki ta bayan ta saki hamma tache,
"Ina dan kunnen hayatey?"
"Wane dan kunne amaal?"
"Gurasa fa?"
Haj jameelah ta mike tsaye tana murmushi.
"Kinsan na dauka idanun ki biyu ashe magagin baccin nan naki ne." Riko ta tayi bayan ta fadi haka. Yayin da amaal din ke ta tangadin bacci.
Futa sukai can haraba. Tuni sun hallata. Abbiey ne kawai baya waien.
Suna tsattsaye wasu a zazzaune .
Can sai gashi ya taho da wani dattijo zai yi kaman shi. Sai pilot din jirgin da suka hau.
Suka nufi inda suke suka tsaya. Suka gayshe su cikin girmamawa. Ya nuna matan na sa dake wajen su uku"
"Ga Hajiya Hadiza itace first wife dina."
"Da girman kujerar ki, Ina gaisuwa uwar gidah " Cewar abokin amb junaid.
Hajiya hadiza ta sake washare hanci da baki yaudin ya tabo inda yake mata kaikayi. Don haka ta sake baje fatar labbanta tana murmishi sosai
"Shine aminin nawa da nake gaya muku Ina da shi."
"Allah sarki."
"Sunan sa Alhaji Abubakhar mai dingishin kudi... Wannan Kuma ....
Ya juya zai dafo kafadar hisham ashe hisham din yabar wajen yana waya.
Yana dawowar ya gaishe da su yana tsaye waje daya.
"Yauwa ga yaron namu nan sunan sa, Hisham. Pilot ne na jirgin sama, Kuma kwararre ne a fannin..."
Amaal ta jiya don ganin waye pilot? Idanuwan ta suka sauka akan number da ke jikin aljihun gaban rigar sa. Kai dama ta baya ta jikin blazer dinsa.
Dai dai lokacin da shima idanuwan sa suka tasanma ganinta..Tuni kallon na su ya sarqe. Ya narke mata idanuwan sa akanta duk wani motsi da take yana han kan idanuwan sa.
Ya kasa janye idanuwan sa akanta. Ta janye nata da sauri tana kallon gefe.
Shi kuma gogan tamkar ya samu abun kollo. Tun daga kan yan yatsun kafafuwan ta zuwa goshin ta . Kallonta kawai yake
"Kai Hisham"
Shiru Hisham bai amsa ba. Ashe ya lula duniyar kallon amaal
"Wai Hisham ba magana nake maka ba ne?"
Da sauri ya juya ya fuskanci mahaifin nasa yana sosa keya ... Harara Alhaji Abubakhar ya dankara masa ya juya kawai wajen Amb.
"Wallahi da ka dan mun uzuri sai muzo daga baya ."
"Haha ambassador meye haka?"
"Gani nayi muna da yawa"
"Ba wani yawa, Banki kufi haka ba. Har me dakinna na gaya wa tun dazu itama take tanbayata yanzu zasu karaso? Nace zasu zo in shaa Allah "
Hisham ya rufe briefcase din amb junaid . Suka shiga motici suka nufi gidan Alhaji Abubakhar da ke cikin kwaryar Abuja unguwar:
*ASOKORO...*
*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*
_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
[7/20, 2:57 PM] Hafsaat💞: _*BAKON MUNAFIKI!!!*_
_(BA NA MUTUM DAYA BANE)_
_👺🏡👩👩👦👦_
_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
_®️NANA HAFSATU (MSS XOXO)_
__AREWABOOKS:MSSXOXO_
_WATTPAD:MISSXOXO00_
_FREE PAGE: 004_
_ADVERT👇_
_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_
_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._
_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._
_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_
_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_
_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_
____
ASOKORO
Sannu a hankali motocin suka dauke su zuwa hamshakiyar unguwar ta asokoro da ke birnin Abuja. Tsayawa bayyana tsaruwar unguwar da ke lullube da bishiyu ma bata lokaci ne.
Abu daya zuwa biyu zan iya fayyace muku kamar dankareren gidan Alhaji Abubakhar daya sha kudi ya koshi.
Dauke gidan yake da fenti kalar sararin samaniya. Sai shekin kalar toka ne ke walwali ajikin sa. Ga wasu bishiyu da wani jijjigaggen gate.
Motocin su suka kutsa cikin gidan dake dauke da babbar harabar farfajiya da zaa iya faka motoci da yawa.
Sai kukan tsintsaye ne ke tashi daga garden din da ke gefen wata kofa acikin gidan ta baya.
Ma'aikatan gidan suka tashi da sauri don temakawa bakin da suka ga suna ta fitowa daga cikin motocin.
Amaal na fitowa daga mota ta sauke nannauyar ajiyar zuciya. Sakamakon gajiya dake dawainiya da ita ga wani bacci dankararre dake kokarin rufe mata idanu.
Dakyar ta iya jan kafafun ta tabi bayan ayarin na su da suka shiga cikin gidan bakunan su dauke da sallama.
Alhaji Abubakhar ne agaba sai Hisham dake biye masa abaya. Sai tawagar su amaal dake bayan su.
Daga sama ta sakko. Kana kallon ta sau daya kasan matar gidan ce. Duba da tsananin kama da suke yi da Hisham din. Sai dai Hisham din ya debo tsawon mahaifin na sa Alhaji Abubakhar. Amma komai na mahaifiyar sa ya dauka harta murmushin da take yi.
Sanye take cikin wadatacciyar doguwar riga ta atamfa. Samfarjn style din T-bubu. Ta yane kanta da babban mayafi.
"Bismillan ku lale marhaba... Ku zazzauna dan Allah..Hisham basu nan su zauna mana ka koma can."
Amsawa suka shiga yi baki dayan su . Nan suka sake sabuwar gaisuwa daya bayan daya bayan sun zazzauna akan kujerun parlorn. Dake parlorn babban ne dake shake da setin kujeru uku kowanne kuma Turkish Royal. Da suka tsaru karshen haduwa.
Tashi tayi ta nufi wata kofa wadda itace zata sadaaka da kitchen. Tana kiran,
"Hadiza kuzo ke da su Laure."
"Toh Hajiya."
Cikin mintuna kalilan sai ga maaikatan sun fara ajiye tirarrukan abinci da abin sha.
"Ga bandaku na uku anan akwai biyu a sama. Ga wajen sallah can da hijabai."
Suka shiga yi mata godiya. Amb junaid na daga zaune bayan ya sha ruwan robar da ke hannun sa ya ajiye yace,
"Sannu da kokari... Mun tashe ku a tsaye. Allah ya saka da alkhairi."
"Bakomai...Mune da godiya. Allah yabar zumunci."
"Allahumma Aaameen." Yan parlorn baki daya suka hada baki wajen amsa ta
Mai gidan ta. Alhaji Abubakhar ya ce da ita,
"Yau buri na ya cika, babban bakon mu da nake burin kasancewar ziyarar sa agidah na yazo . Takanas da kansa da iyalan sa. Gaskia nayi matukar farin ciki. Shine Ambassador Junaid da nake gaya miki yana Madina shi da iyalan sa baki daya... Tun lokacin da aka bashi mukamin har ya zuwa ajiyewar aikin sa bayan shekaru hudu ne yanzu nake ji ko yallabai?"
"Eh shekaru hudu ne ranka ya dade" Amb. Junajd ya amsa shi.
"To kiga fa.... Sai yanzu Allah yayi ya waiwayo gidah Baki daya da iyalan sa. Bai fara sauka a koina ba sai gidah nan ya amshi tarin gayyatar da nake ta masa. Ina rokon ya zoyarci gidan ya zama bako na."
Amb junaid yayi murmushi kawai yana girgiza kai,
"Baka da dama ranka ya dade"
"Allah yallabai dagaske na ke. Ai kowa ya sani. Naciri babbar tuta. Har garin nukaa zani takanas nayiwa Hajiya godiya."
"Saboda transit din da mukayi anan?"
Suka tafa suna kyalkyalewa da dariya. Ragowar yan parlorn na tayasu. Idan ka cire Amaal da Hisham a gefe da ke wa juna kallon kasan idanu...
"Toh Allah yasa dai su iya cin cimar tamu ta nan ko daddyn Hisham?"
"Chi kai... Ai bamu baro gidah ba. Dukkanin abincin da ake ci a Nigeria munaci acan. " Cewar Hajiya hadiza tana karkada kafa daya kan daya.
Haka dai suna yar hirarrakun su jefi jefi, Suka kammala cin abinci tas. Don wanu abun ma ko tabashi basuyi ba. Dubada girke girken da akayi musu suna da yawa . Don haka sai sadaukar da wasu akayi ga mabukata awaje.
Bayan nan bandakin suka shisshhga suka yi tsarki. Masuyin sallah suka yiyyi. Mazan suka fita sukayi jam'i awaje. Kafin daga baya suka dawo ciki aka cigaba da hira.
"Ni fa nayi mamakin girman Hisham."cewar amb junaid.
Hisham dake gefe ya saka hannun sa a bayan kansa ya shafo keyar sa yana kakaro murmushi..
"Allah Alhaji? Dan dai ka dade baka ganshi bane. Gashi nan ya zama cikakken pilot."
"Kwarai kuwa tunda shine ya dakko mu ai daga can zuwa nan.. Don badan Allah ya temaka ma yayi dan tsaiko ba ai da tuni jirgi ya daga yabar mu. Amaal ta tafi siyan abu a shago lokacin ya kure."
"Ai gwara ku tsautsayi ne. Shi fa saboda tsabar wauta jakar wayoyin sa data kayan sa ya manta a shagon wani baban abokin aikin sa balarabe. Wai wani abu ya zube a rigar tasa yaje ya canza waye waye duk shirme dai. Nace wannan ai wauta ce. Sai ache saboda jirgin mu ne."
Hisham ya tsrae Amaal da idanu. Kallon su ya sarke tayi saurin janye nata. Shi kuma yaki dauke nasa sai ma sake kafeta da yayi da idanun har ta kasa nutsuwa sosai tanata mutsul mutsul awajen zaman ta.
"Menene hakane Amaal?" Cewar Hajiya J. mahaifiyar ta.
"Bakomai Hayateey zama na na gyara." Tana daga idanun ta suka hada kallo yayi mata murmushi. Domin sarai ya jiyo abunda ta fada da ma tanbayar da mahaifiyar tata ta mata.
"To ai tsautsayi ne wannan yana iya jawa kan kowa. Banga lefin sa ba ga mai lefi, wannan yarinyar fa ita da gangan fa tana sani tatafi siyayyar shago itama. "
Alhaji Abubakhar yayi murmushi jin abunda amb junaid ya fada. Ya dan juya ya kalli amaal din,
"Itama yar wajen ka ce?
"Ta karshe ce ma..."
"Auta ce kenan?"
Amb. Junaid ya daga masa kafin yace,
"Eh auta ce..... Sunan Hajiya taci ai."
"Haba?"
"Allah kuwa."
"Ma shaa ALLAHU mai babban suna... Uwata ta kai na. Me ake kiran ki da shi?"
Cikin sanyayyar muryar ta mai sanyin da dadi ga duk wanda ya saurara. Ahankali a kuma nutse cike da tarbiya ga biyayya ga wanda kanta a kasa tace,
"Maryam... Amma Amaal ake kira na da shi ...."
*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*
_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
[7/20, 9:32 PM] Hafsaat💞: _*BAKON MUNAFIKI!!!*_
_(BA NA MUTUM DAYA BANE)_
_👺🏡👩👩👦👦_
_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
_®️NANA HAFSATU (MSS XOXO)_
__AREWABOOKS:MSSXOXO_
_WATTPAD:MISSXOXO00_
_005_
_SHAFIN KARSHE NA KYAUTA/LAST FREE PAGE_
__
°°°Hisham ya daga kai da sauri ya kalleta, Itama wannan karon shi din take kalla. Ba wanda ya janye idanun sa. Mamaki take ashe ba balarabe bane. Yayin da shi dinma hakan take a tasa zuciyar. Yana mamakin dama ba balarabiya bace?
"Gata nan kaman Hisham itama ita kadai ce awajen mahaifiyar ta."
"Allah sarki .. Allah ya raya mana su baki daya ya musu albarka."
"Allahumma Aameen." Cewar amb. Junajd ya sake muskutawa ya gyara zaman sa. Kafin ya cigaba da cewa,
"Ga Hadiza fa ... Ko ka sheda ta?"
"Kwarai kuwa nasan hadiza ba kanwar su labbo ba?"
"Tabbas itace.... Lalle baka da mantuwa, To ga yaranta nan Abubakhar daya ci sunan marigayi yaya?"
'kwarai Yaya. Allah ya gafarta masa."
"Amin Amin, Muna ce da shi sadeeq, Daga shi sai mai bjye masa wancen safwan, Sai Na'eelah da najwa ga sunan a jere."
"Sai kuma Hindu da baka fada ba. Saboda ita agola ce? Wallahi Alhaji ka sauya halin ka. A wajen bare ma sai an raba hali. Hindu dai ko ban aure ka ba ai idan da kara kai ma yar kace. Tunda ni da kai a duk tsatso daya muka fito. Wannan 'ya tace itama Hindu amman ba shine uban ta ba kamar yadda bai lissafo da ita ba. Mahaifin ta dan uwa ne agare mu ni da shi. Mahaifin ta shine babban cousin a family din kandemi" Cewar hadiza matar sa ta fari.
Tamkar kasa ta tsage ya fada haka yake ji... Kunya duk ta dabaibaye shi. Gashi ita datai maganar ko a jikin ta tacigaba da danna wayar hannun ta.
Parlorn yayi tsit kamar ruwa ya cinye su. Chan dai Alhaji Abubakhar yayi breaking silence din yace,
"Su kuma wadannan yan biyun fa ga sunan kamar su daya baa gane su.?"
Amb junaid ya juya ya jalle su yana murmushi. Kafin ya saka yatsa yayi nuni da haj jameelah yace,
"Ga kuma jameela. Itace mai daki na ta biyu bayan hadiza. Kamar yadda na gaya maka dazu. Amaal ce kawai Allah ya albarkance ta da ita... Itama sai bayan shekaru.."
"Haka... Allah ya raya su duka Amin."
"Amin amin... Sai mai dakina ta karshe... Ruwaida.. Gata nan. Itace mahaifiyar yan biyun da kake magana yanzu. Su kadai ne yaranta."
"Ma shaa ALLAHU... Allah yayi musu albarka ya raya su duka Amin.."
"Allahumma Ameen."
Ya sake daga robar ruwa ya kafa a baki ya sha bayan ya sauke dankarereriyar ajiyar zuciya yace,
"Hadiza, Jamila, Ruwaida...." Ya kira sunayen matan nasa daya bayan daya..
Dukkanin sh suka juya suna kallon sa. Suka kuma kasa kunne don jin abunda zai ce,
Ya saka yatsa yayi nuni da Alhaji Abubakhar yace,
"Wannan shine babban aboki na da nake gaya muku. Kai ya wuce aboki ma ya zama amini. Ya kere wasu da suke ganin su yan uwan na ne na jini. Ya mun abunda a duniya bazan taba mantawa da da tarin allhairinnsa agare ni ba."
"Kabar maganar nan Junaid... Haba mana kamar wasu yara sakarkaru."
"Kyale ni sai na fada... Amini na ne... Alhaji Abubakhar mai murmushin kudi'. Ko a wani hali kuka tsinci kanku a duniya da rai na ko bayan rai na, Ku kuma godewa Allah daya azurta ku da shi. Ku kira shi a ko'ina ne zai zo yayi bakin kokarin sa. Mutumi ne da yake adali, Mai dattako, cikar kamala, alheri, Mutunci, gaskiya, Amana da rikon ta, tausayi, kawaici, kauda kai, hakuri, da Imani ga biyayya, ga ladabi ga kamewa, ga temako... Alhaji Abubakhar mutumi ne da baya gajiyawa wanda yasan halacci ba kuma ya mantawa da alkhairi komai tarin sharrin da ka bishi da shi, Yayi da jikin sa yayi da aljihun sa ...zuwan mu zuwa Nigeria ko ince dawowar mu da dik wani zuwa hutu da duk wata tafiya Dr abubakhr ya dauke mun ita ni da iyali na da ahali na gaba daya free of charge muke shiga kasashe...Allah ya saka masa da alkhairi ya biya masa dukkanin wasu bukatn sa Amin... Ga matar sa nan kuna gani sunan ta Aisha.. Ga kuma dan su da Allah ya azurta su da shi Hisham shine matukin jirgin daya kawo mu man... Bugu da kari ma jirgin mahaifin sa ne