Showing 48001 words to 51000 words out of 91674 words
Chapter 17 - SALON SO SABON SALO COMPLETE Book by Momyn Fareesa.txt
Allah";yaduba time k'arfe 1:35am"wayoyinsa ya d'auka"kamar ance yaduba troley d'in"yana murmushi yaduba"komai tasaka da zai buk'ata amma banda boxers"murmushi yakamayi yana tunanin noor d'in sa ta cika kunya sosai"ward rope d'in yanufa yad'akko yasaka acikin troley d'in"bayan yarufe yafito, yarufe ko ina yana sakkowa down stairs d'in"noor ce kawai zaune a parlourn"mamy na ciki"kallo d'aya noor ta masa ta d'auke kanta sbd kishi ya motsa"saita dinga tunanin k'ilan acikin jirgin yahad'u da wata"tashi tsaye tayi tak'i yarda su had'a Ido"shi kuwa gaba d'aya yamaida attention nasa akanta"noor menene?bbu komai yaya sadeeq"karka makara kazo kaci abinci saika tafi ko?"ke kinci abincin?"bazan iya ciba bayan kai baka ciba"Allah sarki nooryn yaya sadeeq"to laifin menayi ba'a son kallona?"d'an murmushi yasub'uce mata ta dubesa taga ita yake kallo"bakayin laifi awajena yaya sadeeq"nima haka baby"yafad'a yana matsowa dab da ita suka nufi dining area"agaggauce ta zuba masa abinci a plate "da nufin shi yaci ita zataci nata"abin mamaki sai cewa yayi idan noor bazakici da niba na k'oshi da abincin"batayi mgn ba tasaka spoon tana d'an tsakura tana fatan Allah yasa harsu gama mamy bata fito ba"shine d'azun kika gudu sbd nataso ko?"eh mana nasan ko mugunta zakamun"kamar fa kin sani Allah kuwa"sai Allah yataimakeki kin gudu" yafad'a yana ajiye spoon d'in yamik'e tsaye yagoge bakinsa"my noor muje na yiwa mamy sallama"ah ah zan jiraka a parking lot pls"dato ya amsa yanufi bed room d'in mamy"noor kuwa troley nasa taja ta fita"koda yafito shida mamy da nufin yad'auki troley d'in yaga be gansaba"yana murmushi yace"noor harma ta d'aukar mun kenan?"wai troley d'in?"Eh mamy"tana ina ?"tana bakin get zamuyi sallama ta wuce gida"to shikenan hakan yayi kyau"insha Allah idan angama azumi sai atura anema maka aurenta nagaji da ganin wannan rashin kunyar taka sadeeq"gashi ita noor tanada kunya kai kuma bbu ko?"k'asa yayi da kansa yana murmushi da tunanin noor zata yadda ta soshi har suyi aure ma??Allah yatsare yabada sa'a ka kula da kanka"to shikenan mamy dan Allah ki kulamun da noor"babu damuwa zan kula da ita sadeeq"dg haka yatafi yana d'agawa mamy hannu"noor kuwa na zaune cikin mota har iro yabud'e mata back sit ta shiga"ya amshi troley d'in kayan sadeeq yasaka aboot"tayi shiru tana tunani"ahaka sadeeq yabud'e k'ofar yashigo yana fad'in saifa kayi sauri befi saura 20 minit ba yaragemun"dato iro ya amsa ya shigo"sadeeq yadubi noor yaga tayi shiru"summyn yaya sadeeq shi kad'ai menene kuma?"kanta ak'asa tace"bbu komai fa "ban yardaba saikin fad'amun menene? yafad'a Ahankali cikin taushin murya"cike da yarinta tace"bakai bane zaka manta dani kamar yadda kayi waccan tafiyar baka nemeni ba"idan zan manta da kaina ayanzun to zan manta dake noor"wancan karen dana tafi shak'uwarmu dake bekai hakaba"kuma banida contact naki"kuma atime d'in murnan tafiyata kikeyi"amma yanzun gashi kuma bakya son na tafi ko? Hakane yaya sadeeq ka kulamun da kanka ka rik'e addininka karka kula wacce baka saniba.... murmushi kawai yakeyi yana kallonta da sauraronta"ya k'ara yadda noorynsa yarinya ce"wai bazata fito kai tsaye tace karya kula mace ba"shine ta fake da nasiha"ganin tayi shiru yace"kamar tayaya zan kula da addinina?"nifa ina nufin kadinga sallah kan time yadda kasaba"to shikenan naji naki nasihar saiki saurari tawa nima"na farko ko chats kikayi da wani namiji jikina zai bani haka"kuma ban amince ki kula wani namiji ba"sbd me yaya sadeeq?"sbd banaso"yafad'a fuska bbu walwala"kanta ak'asa tace"insha Allah zan kiyaye"yauwa kokefa"yafad'a lokacin da iro yayi parking sbd sun iso air port d'in"gaban noor yafad'i dataga har iro yafita dg cikin motar"noor zan tafi befi saura 6 minit afara kiran fasinjaba"yafad'a Ahankali zuciyarsa cike da rauni"Allah yatsare yadawo dakai lafiya yaya sadeeq"Ameen my noor"toki d'ago kanki sai kimun mgn kina kallona ko?"yafad'a yana zaro wayarsa yashiga camera"kinga pics da vedio zan mana sbd idan natunaki saina kallah ko?"yafad'a yana matsowa dab da ita"ta d'ago kanta tana tsuke d'an bakinta ta kallesa"yana murmushi ya d'aukesu.... hannunta guda yakama yasaka cikin nashi"ta d'ago kanta da sauri zatayi mgn saiya d'auka yana dariya"sai kuma yafara musu vedio yana fad'in koki d'ago kona rungumeki....atsorace ta d'ago kanta tana zaro ido"yakama murmushi"ta shagwab'e fuska tana turo baki"sai kuma ta b'oye fuskarta da tafikan hannayenta"sosai yadinga musu vedio suna shirme"kafin yasaka wayar aljihun jeans d'in jikinsa yana fad'in"yanzun iro zai mayar mun dake gida"noor nabaki amanar kanki ko fita zakiyi kisanarmun ta waya kinji?"duk abinda yadace na buk'ata sbd azumi zamuyi mgn ta waya zan turo"d'ago kanta tayi saiga hawaye....yah salam!kar muyi haka dake"bakyaso hankalina yakwanta na sami k'arfin gwiwar yin abinda yakaini?"girgiza kanta tayi"yauwa to kiyi shiru kinji?bana son ganin hawayenki"yafad'a yana k'ok'arin kai hannu zai share mata hawayen"tayi saurin matsawa" yayi murmushi yana fad'in insha Allah akwai time d'in da abinda yafi hakama zan miki batare dakin damuba"yana fad'in haka yafita dg cikin motar"yatsaya bakin k'ofar yana kiran sunanta anutse"ta d'ago kanta suka had'a ido"murmushi yamata"yana kama kunnansa ya wani shagwab'e fuska"noor murmushi yasub'uce mata"dan yadda yayi yabata dariya"yaya sadeeq kaje kaji sai munyi waya"bazakiyi kukan ba?"kanta ta gyad'a masa yad'aga mata hannu yatafi"iro yashigo motar yaja suka wuce gidan innah"zuciyar noor cike da kewar sadeeq.....
*waiwaye*
tun bayan tafiyar noor islamiya"Abba dahiru yazo da mashin ya d'auki umma" acewar zasuje gidan wani abokinsa"tun suna tafiya bata tambayarsa sun iso harta fara tambayarsa"saidai yace" an kusa zuwa"sunyi tafiyar kusan awa guda"suka iso bakin k'ofar wani gida me get fari"yayi horn aka bud'e masa get"mariya nata kalle kalle dan ita ko za'a kasheta batasan anguwar dasuka zoba"bayan sun shiga cikin gidan yakafe mashin d'in yana danna waya yayi wata hanya mariya ta bishi"acikin wani parlour na alfarma sukayi sallama"maza biyu da wata mace na zaune kan kujera"haka nan mariya keta jin fad'uwar gaba"tunda ta shigo mazan ke binta da wani irin mayen kallo har suka zauna ta gaishesu da musu yamai jiki?"suka amsa"macen ta zuba mata ruwa a cup ta mik'a mata"Abba dahiru dai na zaune gefenta"bayan ta amsa tasha"tafara jin jiri da bacci bacci"atake ta sulale kan kujera tana jin dariyar Abba dahiru da fad'in gata nan ku biyani kud'ina"dg haka bata koma sanin Inda kanta yakeba.... Abba naganin haka yakama dariyar mugunta yana fad'in wlh zaku huta sosai ajikinta"kamar yadda kace Alh kuyi mata alluran b'atar da hankali"ku barta anan har abada nidai na siyar muku"Alh yadubesa yace"gobe kadawo idan munji yaya take saimu biyaka"sbd gsky inaga nizan barta ina nemanta kawai banda Alh idris"Abba yamik'e tsaye yace"to ad'an bani wani abu saina tafi nasan mi zance idan naje gida ta yadda za'a manta da ita"dubu goma suka bashi yatashi yayi tafiyarsa gab da magrib....mariya kuwa sai wajen isha'i ta farka tana furta *innalillahi wa inna ilaihir raju'un! la'ilaha illah antassubuha naka inni kuntu minal zakimun* tafad'a tana bud'e idonta ta ganta cikin duhu"da alama a wani bed room take"saidai tana ganin haske kad'an kad'an dake cikin parlour ta window"gabanta nata fad'uwa sbd ranta yabata siyar da ita Abba yazo yayi"tashi tayi ta ganta ko hijab bbu ajikinta"sai dan kwali kawai"da sauri ta nufi wajen k'ofar ta bud'e"bbu kowa a parlourn sai wannan macen ta d'azun"ta dubi mariya da sauri tana fad'in kin tashi?"banza ta mata ta nufi k'ofa"matar ta bita zata rik'eta"aikuwa dayake k'arfafface ta masgeta ta fice aguje dg parlourn" cikin sa'a ta sami bakin get bbu kowa, ta bud'e ta fito tana hamdala"ashe matar tasanarwa sauran mutanan dake gidan"aikuwa aka biyo mariya"tana gudu tana waiwaye taga sun biyota"cikin rashin sa'a ta nufi bakin titi"wata mota ta kawo ta tureta! tayi sama ta dawo k'asa kanta yafashe ta baje wajen.....hakan yafaru kan idon wad'anda suka biyota"hakan yasa suka juya kawai"sbd sun tabbatar koda bata mutuba zata sami wata matsala"arikice saurayin daya kad'eta yafito dg cikin motar ya d'auketa yayi asibiti da ita......
Abba dahiru kuwa washe gari yadawo"suka bashi 200k batare da sun sanar masa wani abu yafaruba"
mariya kuwa kwananta 3 a asibiti ana bincikarta da bata taimakon gaggawa"kafin dg bisani aka gano tayi lusing memory nata"sbd kanta yabugu sosai"saidai likita yasanarwa Aliyu (wanda ya tsintseta) insha Allah nan gaba kad'an zata iya warkewa ko kuma idan taga idon data sani....kusan satinta 2 a asibiti Aliyu da mahaifiyarsa hjy kulu da Abban sa Alh ibrahim suna bata kulawa"dg k'arshe ta koma gidan Alh ibrahim da zama"masu aiki na bata kulawa"acewar Alh ibrahim idan ta k'ara warkewa za'a cigita danginta ta hanyar nuna pic nata agidan tv da jaridu k'ilan agano danginta.....
Afusace Alh labaran yashigo....✍️
wannan book d'in nakudine idan kina buk'atar siya serious normal grp 300
Vip grp 1000
via 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
Ki turo shaidar biyanki ta what's app number d'ina 08100084251
Idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitarmun Allah ya isa ban yafe miki bayafe miki ba........ Afusace Alh labaran yashigo cikin parlourn gidansa yana huci"hjy jamilah ta dubesa tana fad'in lafiya dai Alh?"kaida baka gajiya da saurin fushi"tsaki yaja yana fad'in kamar ni wannan d'an iskan yaron zai hana shiga gidan su"wane yaro kenan?"sadeeq mana"nazo zan shiga masu gadi suka hanani da fad'in shine yace"kar akoma barina nashiga"tab'e baki hjy jamilah tayi sbd tasan Abba son mamy yakeyi"tana yatsina fuska tace"zance kaje yi kenan ko?"bansaniba ina ruwanki?"tab'e baki tayi tana fad'in kaji dashi wlh"sadeeq dai yanuna bayayi dakai da zahida" to akan me bazaku barsaba?"ni banga abin tada jijiyar wuya ba"tunda ya hana abarka ka shiga gidansu ai shikenan"har abada dai kana nan amatsayin uba awajensa"in ma da niyar tozarci yamaka haka dan kansa"zahida kuma tunda tazo rannan tana kuka yamareta sbd wata yarinya nace ta fidda shi aranta"sbd dama can Inda taji maganata data barsa "koda shine autan maza tunda yanuna baya sonta"amma sbd kaida ita kuna kwad'ayin abun hannunsa"yasaka kuka k'i yin zuciya kuka nace....kinga Jamila kimun shiru da wani zancen banza naki ko ranki yab'aci wlh"babu shegen daya isa yatozartani nida y'ata na barshi"dama ke ciwon zahida kika sani ko darajarta?"wlh muddin ina numfashi dg shi har Aminar sai sun san ba'a shiga huruminah afita lafiya......subahanallahi ! haba Alh be kamata kana irin wannan furucin ba....doguwar tsuka yaja yabar parlourn kamar zai tashi sama yana baza malum malum "hjy jamilah ta tab'e baki tana fad'in ina jiye maka ma nauyin dukiyar maraya dakaci abaya sbd sai Allah ya tambayeka....
Afannin hamisu kuwa yau kwanan sa 8 kenan agidan yari"yasha wahala sosai da k'yar adaren yau yayi nassarar gudowa dg gidan jarin"wajen k'arfe 12:30am yadiro ta katangar gidansu"atsorace su inna saratu da Abba suka tashi "aikuwa suka ganshi"yayi bak'i k'irin yanata d'oyi"hamisu kaine ka gudu?"cewar Abba"Eh mana Abba"nagaji da zaman wahala da takura"hakane gsky tsakaninmu da noor saidai muce Allah ya isa wlh"cewar inna saratu"hamisu yace"tana ina y'ar iskar?"yo tana gidan innah mana tunda acan takoma"rannan naje bata nan tana wajen aiki"inna tayita mun fad'a nadaiyi shiru"cewar Abba"hamisu yashak'i iska yafesar yana fad'in wlh saina d'auki fansar abinda tamun"yo ai fad'i b'arnar baki in gaya maka"in tana tak'ama wannan d'an gayun ya tsaya mata to gib'i zaka yiwa rayuwarta ta hakane shima zai gujeta yatsaneta"sbd nasan dai sonta yakeyi"cewar Abba"hamisu yamik'e tsaye yana fad'in adaren gobe zanje har gidan innar na keta mutuncin y'ar iska"hakan shine hukuncin daya dace da ita"cewar inna saratu"Abba yayi shiru yana tunani"hamisu yace"zanyi wanka da asuba tayi nabar gidan nan karma azo nemana dg police station"kuma agobe zan gudu nabar garin nan bayan nacika k'udurina akan noor"koda anzo nemana bbu wanda zai ganni"eh haka yaka mata kayi" cewar Abba"hamisu yaja ruwa yashiga bayi"bayan yafito ya kwanta"ana fara sallar asuba yafice dg gidan yanufi dandalinsu na y'an iska y'an shaye shaye.....
******************
Tunda sadeeq yatafi Abuja bashida wani aiki daya wuce tunanin noor da kuma kiranta ta waya kuma suyi chats"kwanansa 3 aka fara azumi"wanda tun daren daza'a fara azumi ya aiko da abinci da abinda zasu buk'ata da kayan tea mota guda akai gidan inna"sannan gidan su jummai ma yabada ankai"noor kuma 100k yaturo mata wai su dingayin cefane"sannan yasanar mata bayan sallah insha Allah zasu bar wannan gidan su koma wani" wanda har kusan fad'a sukayi datace bata amsar kud'in d'awainiyarsa tayi yawa agaresu"dan ita kanta innah dai ta fahimci sadeeq da noor son juna sukeyi"kuma kayan daya kawo tace"sunyi yawa bazama atab'asu sbd sunada kayan abinci"jummai kuwa takira noor tasanar mata ankawo musu kayan azumi" ta musu godiya awajen sadeeq"wanda hakan ba k'aramin dad'i yayiwa noor ba"tunda yatafi kullum agidan mamy take zuwa"acanma take shan ruwa kwana 2 da fara azumi"wanda yayi daidai da gobe sadeeq zai dawo dg Abuja"fad'in murnar da noor ke ciki dashi kansa sadeeq d'in bata bakine"komai yagani acan na y'an gayu wayayyu saiya siyawa noor"troley guda babba yashak'e mata da kayan sallarta kala 7 masu kyau da tsada"ga hand bags da shoes"sai veils da jewelries"da kayan shafa"itama mamy troley nata daban yake"gaba d'aya jinsa yakeyi kamar yabud'e ido yagansa a bauchi"be yarda yana son noor ba saida yayi kwana 5 baya tare da ita"gashi yanzun sai tayita jin nauyinsa bata sakewa dashi"shi kansa tunda akafara azumi idan yakirata da asuba sai kuma da dare suke waya shikenan"sbd da rana be samun time d'in kiranta.
Adaren yau wanda yayi biyu ga watan azumi"da misalin k'arfe 1:11 am hamisu yadiro agidan inna"gaba d'aya duk bacci sukeyi ansha ruwa an kwanta ahuta"kamar da wasa noor dake kwance kan babban gadon innah taji ana shafa jikinta"atsorace ta farka tana sakin ihu.....wanda yasaka innah da zainab farkawa"da jafar dake soro"hamisu ya d'auke noor da gigitaccen mari yana haska fuskarsa da flash light d'in wayarsa dantaga ko waye "ta koma sakin k'ara tana turashi"inna da jafar dayayo d'akin suka saki salati"noor na ihu tana fad'in wlh innah hamisu ne..... k'ara d'auketa da mari yayi ta saki kuka mecin rai tana k'ok'arin guduwa yarik'eta yana fad'in ayau zan shayar dake bak'in ciki da b'acin rai ta hanyar keta mutuncinki.... innalillahi wa inna ilaihir raju'un! Cewar inna akid'ime tana lalubar gabanta sbd bata gani da dare"jafar kuwa kan gadon yanufa yana insha Allah bazaka sami nassara ba"koka barta kona tara maka mutane wlh"kai k'aramin alhaki jeka dg waje ko kuwa na maka dukan daka kwanta jinya wlh"ko kuwa kasan meta mun ne?to fansa nazo na d'auka itama taji zafi da k'unci aranta"kamar yadda nima naji" yafad'a yana k'ok'arin hayewa saman noor"tayi saurin janyewa tana dukansa da pillow tana tuna sadeeq nata"wlh koka fita ka bani waje kona tsinewa mahaifinka"kaji d'an iskan yaro la'ananne"kazo nan kace zaka mana d'ibar albarka"idan kacika tantiri kazo da rana mana"wato shi dahirun ne yaturoka kayi haka kome?? cewar inna tana fashewa da wani irin kuka....yayinda hamisu beji be gani sunata artabu da noor tak'i yarda ko jikinta yatab'a"dg k'arshe tayi nassarar sakkowa dg samqn bed d'in"hakan yayi daidai da shigowar jafar wanda yafita dg cikin d'akin"yana rik'e da tab'arya"hamisu bema lura da shiba yana k'ok'arin fisgo noor aikuwa yaji abu kamar saukar guduma asaman kansa"yasaki k'ara yana dafe kansa"atake goshinsa yafashe yana jini"wlh koka fitar mana dg gida kona Ida fashe maka kai"cewar jafar"yayinda noor keta kuka tana tuna kalaman sadeeq na cewa" hankalinsa be kwan taba da zamanta dg ita sai su innah agidan"ashe da gaskiyarsa ga abinda yazo yafaru"hamisu kuwa yana layi da ganin jiri yafito dg cikin d'akin inna yanufi soro yazare sakatar yafita"jafar yarufe gidan jikinsa asanyaye yana tsananin tausayin noor.....gaba d'aya duka gidan sunyi jigum jigum kowa jikinsa asanyaye yake"noor tasha kuka inna na bata hak'uri da nuna mata ta godewa Allah da komai yazo da sauk'i"burun hamisu bai cika ba"itadai tayi shiru tanata jan ajiyar zuciya"idan ta tuna gobe sadeeq zai dawo sai taji sanyi aranta"wayarta ta d'auka ta kashe sbd tasan daya kira da asuba yaji muryarta haka zaya damu" yayita tambayar menene ke damunta?"sai bayan tayi sahur da sallar asuba ta samu ta koma bacci"sai wajen 9:am ta farka"sosai takejinta cikin farin ciki sbd tasan zuwa 4 pm sadeeq ya iso gida tunda anan zaisha ruwa"wanka tayi ta shirya cikin abaya black colour"ta yane kanta da mayafin"ko powder bata shafa ba"ta sanarwa inna zataje gidansu jummai acan ma zata sha ruwa"inna ta dubeta tana fad'in kiyi hak'uri ki cire damuwa aranki"ni kaina Inda inada wanda zai kaiki wajen ummanki dana saka an kaiki ko hankalinki zai kwanta"ga zainab nan tana shiri zataje ta kiramun saude"zamuyi mgn da ita zai gane kuransa shi dahirun"babu komai dan Allah inna ki barsu in sha Allah ta shima zamuyi dg gidan nan bayan sallah idan yaya sadeeq yadawo"hmm! takwara kenan?"niba k'aramar yarinya bace" bar ganin banyi bokoko ba sarai nasan soyayya kukeyi ke dashi kina b'oyewa ne"fatana shine dan Allah yake sonki"sbd yasan dai ke marainiya ce kuma talaka"in har da gske yakeyi yayi mgn bawai yayita kashe mana kud'i ba"b'ata fuska noor tayi batace komaiba tafice dg d'akin"koda ta fito bakin titi nafef ta tsayar"kai tsaye anguwar ankil aka sauketa"bayan ta sallami me nafef d'in ta shige gidan su jummai"jummai ce kawai tsakar gidan tana wanke wanken azumi"umma na d'aki tana bacci"ah ah k'awata b'atan kai kikayi kome?"d'an murmushi noor tayi ta shigo ta zauna suka gaisa tana hawaye ta sanarwa jummai komai"salati kawai da sallallami jummai keyi had'e da mamakin tsagerancin hamisu"wayyo Allah k'awata"ki barsu da Allah" nasan sadeeq naki zaiyi maganinsa"bazan ma sanar masa bama jummai"meyasa noor?"sbd nasan mummunan mataki zai d'auka"nasan halin yaya sadeed da zafin zuciya"shi kuma hamisu dama fansa yazo yad'auka sbd nayi sanadiyar zamansa kurku"dama yaya sadeeq d'in baya gari yau zai dawo"wai har yanzun be fad'a miki yana sonki ba?"murmushi noor tayi ta sanar mata warning d'in daya mata da zai tafi Abuja"hahahahaha k'awata kenan! wlh sonki yakeyi"kuma dole ya ajiye wani abu aransa yafurta"karki sake ki nuna masa kin gane yana sonki wlh"ki barsa ya furta da bakinsa"noor na murmushi tace"to shikenan k'awata"bara na tafi sbd inaso na shirya masa abin bud'a baki"ki gaishe da umma"dg haka sukayi sallama noor ta fito dg gidan"zata hau adaidaita taga halima zata wuce"ido suka had'a bbu wanda yayiwa d'an uwansa mgn"noor ta d'auke kanta ta shiga cikin nafef d'in"ta zaro wayarta dake kashe tana tunanin k'ilan yaya sadeeq nacan yadamu da wayar a kashe"da wannan tunanin suka iso gidan mamy"abakin get noor ta had'u da iro driver"